POPULARITY
Kungiyar masu hankoron kare shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ta koka kan yadda gwamnatinsa ta gaza wajen samar da tsaro da kuma walwala ga talakawan kasar. Shugaban kungiyar Mustafa Salisu Musa Fanandas ya ce, abubuwan da ke faruwa a Najeriya sun sha bam-bam da abin da shugaba Buhari ya shaida musu kafin hawansa kan karagar mulki. Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsa da Abdurrahman Gambo Ahmad.
A Juma'ar da ta gabata ne shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya aike da wata tawaga mai karfi da ta kunshi shugaban hukumar tsaro ta DSS da babban sufeto janar na ‘yan sandan kasar zuwa jihohin Sokoto da Katsina sakamakon tsanantar hare-haren ‘yan bindiga wadanda a cikin makon da ya gabata suka kone fasinjoji sama da 30 wadanda ke kan hanyar balaguro a motar safa. Dangane da wannan Michael Kuduson ya tattauna da Aminu Bala Sokoto, masanin tsaro a Najeriya ga kuma zantawarsu.
Shirin 'Kasuwa akai miki Dole' na wannan makon tare da Ibrahim Malam Goje ya duba sabon kudin yanar gizo na eNaira da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya kaddamar, domin dacewa da zamani wajen farfado da tattalin arziki Najeriya da kuma saukaka hada-hadar kudade a yanar gizo.
Yau Litinin shugaban Najeriya Muhammadu Buhari zai kaddamar da Nairar da za a rika hada hadar-ta, ta intanet wato eNaira, a fadarsa dake birnin Abuja, kuma eNairar za ta fara aiki ne daga lokacin da aka kaddamar da ita. Matakin na zuwa ne bayan da aka jinkirta kaddamar da Nairar a farkon wannan wata na Oktoba. Dangane da wannan batu Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dr Kasim Kurfi, masanin tattalin arzikin a Najeriyar, ga kuma yadda zantawarsu ta kaya.
Shirin kasuwa a kai miki dole na wannan mako tare da Ahmed Abba ya yi nazari kan sabuwar dokar man fetur da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sanyawa hannu. Za ku iya latsa alamar sauti don sauraron shirin.
A cikin shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan makon , Bashir Ibrahim Idris ya mayar da hankali ne a kan dakatar da harkokin kamfanin sadarwa na Twitter da gwamnatin Najeriya ta yi biyo bayan goge wani sako da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya wallafa. Masana harkar sadarwa sun tofa albarkacin bakinsu.
Shugaban Kasar Chadi Idris Deby ya bayyana cewar rashin kai hare-hare da rundunar sojin hadin kai ta kasashen Najeriya da Nijar da Kamaru da kuma Chadi ke yi na daga cikin matsalolin da suka hana samun nasarar yakin. Bayan ganawa da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, Deby ya bukaci sake fasalin yakin da kuma kaddamar da Karin hare-hare. Dangane da wannan batu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Sarkin Gwandu na 19, Manjo Mustapha Haruna Jokolo mai ritaya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da yayi amfani da tattaunawa da kuma tafarkin siyasa wajen shawo kan matsalolin tsaro da suka addabi kasar. Babban Jakadan Majalisar dake Najeriya Edward Kallon ya bayyana haka lokacin da ya jagoranci wata tawaga zuwa fadar shugaban, inda yake cewa matsalolin tsaron da suka addabi kasar dake da sassa daban daban na da wahalar magance su. Dangane da wannan shawara Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ambasada Ibrahim Kazaure, tsohon ministan ayyuka na musamman a Najeriya, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
Matsalolin rashin tsaro a yankunan jihohin arewa maso yammacin Najeriya na cigaba da ciwa ‘yan asalin yankin tuwo a kwarya, kasancewar a duk rana sai kara samun munanan hare-hare ake daga ‘yan bindiga duk da matakan tsaron da ake dauka. Kan sha’anin tsaron ne Garba Aliyu Zaria ya tattauna da mai martaba Sarkin Gwandu na 19, kuma tsohon mai tsaron lafiyar shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a zamanin mulkin soja, Alhaji Mustapha Haruna Jokolo, wanda yayi tsokaci kan halin da ake ciki da kuma mafita daga matsalar tsaron.
Kungiyar agajin kasar Faransa ta Action Against Hunger ta sanar da kashe jami’an ta guda 4 da kungiyar Boko Haram tayi garkuwa da su tun a watan Yuli. Kisan ya gamu da suka daga Majalisar Dinkin Duniya da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da kuma kungiyar agajin dake taimakawa mutane 300,000 da rikicin Boko Haram ya tagayyara. Kan wannan batu muka baku damar tattaunawa a wannan litinin.
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ne game da nasarar da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya samu ta sake lashe kujerar shugabancin kasar wa'adi na biyu bayan doke babban abokin hamayyarsa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar. Tuni Jam'iyyar PDP ta bayyana sakamakon zaben a matsayin mara inganci tana mai zargin tafka magudi a zaben,yayinda ta ce, za ta shigar da kara a kotu.