Podcasts about bashir ibrahim idris

  • 7PODCASTS
  • 623EPISODES
  • 5mAVG DURATION
  • 5WEEKLY NEW EPISODES
  • Aug 14, 2026LATEST

POPULARITY

20192020202120222023202420252026


Best podcasts about bashir ibrahim idris

Latest podcast episodes about bashir ibrahim idris

Bakonmu a Yau
Muna iyaka ƙoƙarinmu wajen ganin an yi zaɓen Osun ba tare da matsala ba - INEC

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Aug 14, 2026 3:38


A ranar Asabar 15 ga watan Agustan 2026 ake sa ran gudanar da zaɓen gwamnan jihar Osun, wanda tuni ya yi sanadin halaka mutane sama da 30 a lokacin yaƙin neman zaɓe. Rundunar 'Yansanda dai ta tura muƙaddashin Sifeto Janar Isyaku Muhammmad da Kwamishinoni 30 da kuma wasu ƙarin jami'ai dubu 15,000, domin tabbatar da tsaron masu kaɗa ƙuri'u da jami'an zaɓen. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hajiya Zainab Aminu Abubakar, mai magana da yawun hukumar zaɓen ta Najeriya.

muna tare osun najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Farfesa Muhammad Dukku kan gazawar jihohi wajen karɓar tallafin inganta Makarantu

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Aug 13, 2026 3:37


Hukumar kula da ilimin Firamare a Najeriya ta roƙi gwamnonin ƙasar da su yiwa Alla su je su karɓi naira biliyan 332 waɗanda yanzu haka ke ajje a Banki, domin inganta ilimi a jihohinsu. Shugabar hukumar Aisha Garba ta ce baya ga naira biliyan 65 da aka ware domin kai ɗaukin gaggawa, akwai kuma naira biliyan 267 da ke ajje domin amfanin jihohin. Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Muhammad Dukku, tsohon shugaban hukumar kula da ilimin Firamare a jihar Gombe ga kuma tattaunawarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....... 

ku ban ki gombe najeriya hukumar bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Ƴunkuri na hadin kai na ƴan adawa domin fidda dan takara guda a Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Aug 12, 2026 3:34


Yan adawar Najeriya sun fara wani sabon yunkuri na hadin kai a tsakanin su domin fidda dan takara guda da zai fafata da shugaban kasa Bola Tinubu a zaben shekara mai zuwa. Wata kungiyar dake kiran kan ta G100 ke jagorancin wannan sabon yunkuri, yayin da ta sanar da taron da za ta yi a makon gobe. Dr Ibrahim Modibbo na daya daga cikin shugabannin ta, kuma ya yi wa Bashir Ibrahim Idris a tattaunawar da suka yi kan lamarin

yan domin wata takara bola tinubu g100 najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Koma bayan da ƙungiyoyin kwallon ƙafar Najeriya ke fuskanta a harakar wasanni

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Aug 11, 2026 3:44


Ga alama ƴan Najeriya da dama sun fusata da yadda ƙungiyoyin kwallon ƙafa na ƙasa ke cigaba da samun nasara a wasannin da suke a nahiyar Afirka. Bayana gazawar da ƙungiyar Super Eagles ta yi na kasa zuwa gasar cin kofin duniya da aka kammala a Amurka da Canada da kuma Mexico, yanzu kuma Super Falcons ta mata ta gaza samun nasara a gasar WAFCON Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar da Bashir Ibrahim Idris ya yi da Alhaji Yusuf Musa Sakatare a ma'aikatar wasanni ta jihar Nasarawa.....

canada mexico ga afar koma bayan super eagles nasarawa najeriya afirka amurka bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Dalilan da suka sa ƙasashe ke rububin ƙulla alaƙa da Ɗangote

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Aug 7, 2026 3:38


Fitaccen attajirin Najeriya Aliko Ɗangote yau ya zama fuskar Afrika a harkokin kasuwanci, da zuba hannayen jari, inda shugabannin ƙasashen Duniya ke nemansa ruwa a jallo domin zuba jari a ƙasashensu ta hanyar samar da masana'antu. Bayan samar da gagarumar matatar man fetur a Najeriya, a kan dala biliyan 20, wadda a yau kimarta ya zarce Dala biliyan 40, yanzu haka ya fara aikin faɗaɗa ta domin zama mafi girma a Duniya, baya ga shirinsa na gina wata sabuwar matatar man a Gabashin Afrika. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziƙi, Hon Sama'ila Muhammad, a kan wannan shahara ta Ɗangote. Sai a latsa alamar sauti da ke sama domin sauraron wannan tattaunawa.

afrika sai suka dala bayan duniya najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Umar Kwairanga kan yadda kasuwar hannayen jarin Najeriya ta yi zarra a duniya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Aug 6, 2026 3:39


Masu ruwa da tsaƙi a harkokin tattalin arziki sun yabawa Najeriya dangane da ci gaba da kasuwar hannayen jarin ƙasar da ta zama ta farko a duniya, wajen zarce ta Seoul da London da kuma New York, sakamakon wasu sauye sauye da aka aiwatar. Domin sanin irin matakan da suka samar da wannan ci gaba, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr. Umar Kwairanga shugaban majalisar gudanarwar hukumar kula da hada-hadar hannayen jarin Najeriya, lokacin wata ziyara da ya kawo ofishin RFI Hausa a Lagos.

Bakonmu a Yau
Dr.Dauda Muhammad Kontogora kan ficewar Guinea daga tsarin kuɗaɗen bai ɗaya na Afrika

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Aug 5, 2026 3:26


Shirin samar da kuɗin bai ɗaya na ƙasashen ECOWAS ya sake samun koma baya saboda sanarwar da ƙasar Guinea ta bayar da ficewa da shirin. Domin sanin tasirin matakin da kuma abinda ke iya haifarwa , Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr. Dauda Muhammad Kontogora, masanin tattalin arziki a Najeriya, ku danna alamun saurare domin jin yadda zantawar tasu ta kasance.

afrika guinea domin shirin ecowas daga dauda najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Dr Dauda Kontagora kan koma baya a shirin samar da kuɗin ECO

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Aug 5, 2026 3:26


Shirin samar da kudin bai ɗaya na ƙasashen ECOWAS ya sake samun koma baya saboda sanarwar ƙasar Guinea na ficewa. Domin sanin tasirin matakin da kuma abinda ke iya haifarwa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Dauda Muhammad Kontagora, masanin tattalin arziki a Najeriya, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar.

ku guinea koma domin shirin samar baya ecowas dauda najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Barrister El-Zubair Abubakar kan jerin ƴan ta;ara a Najeriya da INEC ta fitar

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Aug 4, 2026 3:30


Hukumar zaɓen Najeriya ta gabatar da jerin sunayen ƴan takarar zaɓen shekara mai zuwa da takardun shaidar ilimin da suka mallaka. Bisa doka ana buƙatar duk mai sha'awar tsayawa takara ya gabatar da shaidar kammala karatun firamare kafin ya shiga a dama da shi, daga muƙamin Kansila zuwa shugaban ƙasa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Barrister El-Zubair Abubakar, ga kuma yadda tattaunawar su ta kasance.

bisa barrister zubair abubakar jerin najeriya hukumar bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Sani Ahmed Toro kan taƙaddamar sayar da hannayen jarin FIFA

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jul 31, 2026 3:29


Daukacin kasashe 55 dake cikin hukumar kwallon kafar Turai sun kaɗa kuri'ar kin amincewa da shirin sayar da hannayen jarin FIFA, tare da barazanar kauracewa wasannin cin kofin duniyar da za'a gudanar nan gaba. Kasashen sun yi fatali da shirin shugaban FIFA Gianni Infantino na sayar da kashi 20 na hannun jarin kamfanin. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Tsohon Sakatare Janar na hukumar kwallon kafar Najeriya, Hon Sani Ahmed Toro. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

fifa toro sani jarin turai najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Aliyu Dawobe kan sabbin alƙaluman ICRC game da mutanen da suka ɓace a Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jul 30, 2026 3:25


Kungiyar agaji ta ICRC ta rage alkaluman mutanen da ƴan uwan su ke nema a yamkin arewa maso gabashin Najeriya, sakamakon tashin hankalin boko haram, daga dubu 24,000 zuwa dubu 17,000. Kungiyar ta bayyana haka ne a wata sanarwar da ta rabawa manema labarai. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Daraktan hulda da manema labarai na kungiyar, Aliyu Dawobe wanda ya bayyana mana dalilan rage alƙaluman. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

game suka icrc najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Ɗalillan da suka sa tsaro ke ƙara tabarbarewa a Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jul 28, 2026 3:34


Yan bindiga a Najeriya sun sace wani babban mai shari'a a jihar Kebbi, kwanaa guda bayan kama shugaban karamar hukuma a jihar Zamfara. Wannan mataki na zuwa ne a daidai lokacin da suke cigaba da sace mutane a yankin ba tare da kakautabawa ba. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hira da Bashir Ibrahim Idris ya yi da Farfesa Bello Bada......

yan suka shiga zamfara kebbi wannan najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Yadda ƙasashen duniya ke takaita amfani da shafukan sada zumunta ga yara

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jul 22, 2026 3:35


kYanzu haka akalla ƙasashe duniya 20 suka bayyana dokar haramtawa yaran da ba su kai shekaru 16 amfani da kafofon sada zumunta ba, saboda illar da hakan ke haifar. Cikin wadannan kasashen akwai Birtaniya da Faransa da China da Brazil da Indonesia sai kuma Malaysia. Shiga alamar sauti don sauraron karin bayani a hirar da Bashir Ibrahim Idris ya yi da Umar Saleh Gwani masanin sadarwa...

china brazil indonesia malaysia duniya yadda shiga cikin faransa birtaniya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Kabir Baba kan buƙatar dakatar da gina matatar man Dangote a Kenya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jul 17, 2026 3:34


Ƙungiyar Greenpeace dake kare muhalli a duniya ta buƙaci dakatar da shirin gina sabuwar matatar man Dangote da za ta laƙume Dala biliyan 17 a ƙasar Kenya, saboda yadda aikin zai yiwa muhalli da sauran hallitun ruwa illa. uni wannan kira ya haifar da mahawara, la'akari da yadda sabuwar matatar za ta taimakawa al'ummar Gabashin Afirka baki ɗaya. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Kabir Muhammad Baba, masanin tattalin arziki. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

Bakonmu a Yau
Najeriya na neman goyon bayan China wajen yaƙi da ta'addaci - Bello Dambazau

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jul 9, 2026 3:38


Najeriya na tattaunawa da China wajen ganin ta samu goyon bayan da ya dace a fasahar zamani da kuma makamai domin shawo kan matsalolin tsaro da suka addibi ƙasar. Sabon jakadan Najeriya a ƙasar China Janar Abdurrahman Bello Dambazau mai ritaya ya bayyana haka a tattaunawar da suka kayi da Bashir Ibrahim Idris. Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirar.

china ku bello bayan najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Dakta Isa Abdullahi akan soke lasisin wasu ƙananan bankuna da aka yi a Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jul 2, 2026 3:34


Babban Bankin Najeriya na CBN ya sanar da soke lasisin wasu ƙananan bankuna 46 saboda saɓawa ƙa'idar aiki. Waɗannan bankuna sun haɗa da guda 12 a Kano da wasu takwas a Lagos, baya ga wasu ɗaiɗaikun jihohi. Domin sanin tasirin wannan mataki, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Isa Abdullahi, masanin tattalin arziki, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai. 

wa lagos akan cbn kano domin abdullahi wasu najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Baba Usman Ngelzerma,kan tsangwamar da Fulani ke fuskanta a kudancin Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 24, 2026 3:26


Fulani makiyaya a Najeriya sun koka dangane da irin tsangwama da kuma barazanar da suke fuskanta a kudancin ƙasar, sakamakon matsalar tsaro da kuma garkuwa da mutane da ake fama da shi. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da shugaban ƙungiyar Miyetti Allah, Baba Usman Ngelzerma. Ku danna alamar sauraro domin jin cikakkiyar tattaunawar.

baba ku usman fulani najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Dakta Abdulhakeem Garba kan cikar Birtaniya shekaru 10 da ficewa daga EU

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 23, 2026 3:29


Yau ake cika shekaru 10 da ficewar Birtaniya daga cikin kungiyar ƙasashen Turai domin cin gashin kan ta wajen gudanar da harkokin mulki da kuma kasuwancin ta ba tare da sanya hannun ƙungiyar EU ba. Bayan share shekaru ana tattaunawa, Birtaniya ta fita a hukumance a ranar 31 ga Janairun 2020. Wannan mataki na Birtaniya ya canza taswirar siyasa, tattalin arziki, da dangantakar kasuwanci ta duniya baki ɗaya Domin duba tasirin wannan mataki da kuma nasarar da za'a ce ƙasar ta samu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Abdulhakeem Garba Funtua, mai sharhi kan harkokin siyasar duniya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

european union domin bayan daga garba shiga yau turai wannan birtaniya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Gobe za a gudanar da zaɓen gwamna a jihar Ekiti ta kudancin Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 19, 2026 3:33


Gobe ne hukumar zaɓe a Najeriya ke gudanar da zaɓen gwamnan Ekiti da ke yankin kudanci, inda ƴan takara 13 za su fafata. Ana kallon wannan zaɓen a matsayin zakaran gwajin dafi ga sabon shugaban hukumar zaɓen Farfesa Joash Amiputan. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai magana da yawun hukumar Hajiya Zainab Abubakar. Latsa alamar sauti don sauraren yadda zantawarsu ta gudana...

gobe najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Amnesty ta ci gaba da matsa wa gwamnatin Najeriya lamba kan ceto ɗalibai

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 18, 2026 3:37


Ƙungiyar Kare Hakkin Bil'adama ta Amnesty International ta bukaci gwamnatin Najeriya da ta dauki matakai na gaggawa don kare dalibai da kuma ceto wadanda har yanzu suke hannun masu garkuwa da mutane. Ƙungiyar ta jaddada cewa gazawar hukumomi wajen kawo ƙarshen hare-hare da sace-sacen dalibai na nuna cewa rayuwar yara na cikin matsananciyar barazana. Ƙungiyar ta bukaci Shugaba Tinubu da ya dauki matakin gaggawa na kawo karshen satar yara da kai hari makarantu, tana mai cewa iyaye sun gaji da romon bakar da ake musu. Amnesty ta zargi gwamnatin da kasa kare kananan hukumomi, musamman a jihar Zamfara da sauran yankunan Arewa daga hare-haren yan bindiga. Kungiyar ta nuna damuwa kan yadda tsadar rayuwa da matsalar tsaro ke raba iyalai da muhallansu, lamarin da ke jefa yara da dama cikin yunwa da rashin ilimi. Kan wannan ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Daraktan Ƙungiyar a Najeriya Isah Sunusi. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Bakonmu a Yau
Akwai takaici yadda wasu ke son haddasa gaba tsakanin ƙabilu a Plateau-Joyce Ramnap

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 17, 2026 3:38


Gwamnatin Jihar Filato da ke Najeriya ta bayyana matuƙar damuwar ta dangane da yadda ta ce wasu na amfani da hukuncin wata kotu dangane da baiwa wasu Hausawa takardar zama ƴan ƙasa domin haifar da tashin hankali a tsakanin al'ummar da suka kwashe shekaru da dama su na zaman lafiya da juna. Gwamnatin ta ja kunnen al'umma inda ta ce waɗanda ba su gamsu da hukuncin ba na da hurumin ɗaukaka ƙara kamar yadda dokokin ƙasa da suka tanada. Bashir Ibrahim Idris ya tuntuɓi kwamishiniyar yaɗa labaran jihar da ta gabatar da sanawar, Joyce Ramnap kuma ga yadda zantawarsu ta gudanar a kai.

jos plateau gaba yadda wasu najeriya akwai hausawa bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Dakta Abubakar Sadiq kan matakin rushe wasu jam'iyyu siyasa a Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 16, 2026 3:34


Wata babbar kotu a Najeriya, ta bai wa hukumar zaɓe ta INEC umarnin soke wasu jam'iyyun adawa har guda biyar, saboda saɓawa dokokin zaɓen shekarar 2023 na ƙasa samun kashi 25 na ƙuri'un da aka kaɗa. Jam'iyyun sun haɗa da ADC da AA da APP da ZLP da Acoord Party. Tuni wannan hukunci ya haifar da mahawara da kuma zargin yunƙrin haa 'yan adawa shiga zaɓe mai zuwa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Abubakar Sadiq Gombe, shugaban Jam'iyyar adawa ta SDP. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

app jam aa adc sadiq sdp wata abubakar shiga tuni wasu najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Abubuwan da ya kamata ku sani a gameda gasar cin kofin duniya ta 2026

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 11, 2026 3:34


Yau ake fara gasar cin kofin duniya ta bana, inda ƙasashe 48 za su fafata domin samun zakarar bana. A karon farko ƙasashe uku ne ke daukar nauyin gasar, wato Amurka da Cnada da kuma Mexico kuma kalla yan wasa 1,248 da alkalan wasa 52 za su jagoranci wasanni 104 da za'a kwashe kwanaki 39 ana yi. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar da Bashir Ibrahim Idris ya yi da tsohon Sakataren hukumar kwallon kafar Najeriya Hon Sani Ahmed Toro.....

mexico sani duniya shiga yau amurka bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Samaila Abdullahi Muhammad kan rahoton IMF game da ƙaruwar talauci a Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 10, 2026 3:33


Asusun bada lamuni na duniya IMF ya ce sauye-sauyen da gwamnatin Najeriya ke yi na ƙarfafa tattalin arzikin ƙasar, sai dai kuma sun haifar da ƙarin ƴan Najeriya sama da miliyan 60 da suka faɗa cikin talauci. Ku danna alamar saurare domin jin tattaunawar Bashir Ibrahim Idris, da masanin tattalin arziki a Najeriya Samaila Abdullahi Muhammad kan wannan batu.

game imf ku abdullahi najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Farfesa Bello Bada game da ta'azzarar matsalar tsaro a yankin Arewacin Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 9, 2026 3:27


Yankin arewacin Najeriya na ci gaba da ɗanɗana kuɗar sa a hannun ƴan bindiga, waɗanda ke kai hari suna sace mutane da kuma hallaka su ba tare da ƙauƙautawa ba. ko a jiya sai da ƴan bindigar suka yi garkuwa da wata tawagar masu neman sulhu da su a jihar Zamfara, baya ga wasu ɗaruruwa da ke hannun su a jihohi da dama, a daidai lokacin da gwamnoni da ƴan majalisun yankin suka mayar da hankali a kan siyasa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Bello Bada na Jami'ar Usman Dan Fodio da ke Sokoto. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana...........

game ku bello bada sokoto zamfara najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Tattaunawa kan ci gaba da shari'ar neman hana Jonathan tsayawa takara a Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later May 8, 2026 3:30


Kotu a Najeriya yau ta ci gaba da sauraron shari'ar neman hana tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan tsayawa takarar zabe mai zuwa, kwana guda bayan wasu tarin magoya bayan sa sun bukaci ya shiga zaben mai zuwa. Dangane da matsayin dokar zabe a kan takarar ta Jonathan masanin shari'a, Farfesa Shehu Abdullahi Zuru na Jami'ar Baze dake Abuja, ya mana tsokaci a kai yayin zantawarsa da Bashir Ibrahim Idris. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

gaba abuja baze takara goodluck jonathan kotu najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Ambasada Kazaure kan kiran wasu ƴanmajalisar Najeriya na kwace lasisin MTN da DSTV

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later May 7, 2026 3:37


Wasu daga cikin Ƴan Majalisun Dattawan Najeriya sun buƙaci ɗaukar matakai maus tsauri a kan Afirka ta Kudu, ciki harda kwace lasisin kamfanonin su na MTN da DSTV saboda yadda ake kai wa ƴan ƙasar hari ake kuma kashe su. Majalisar ta yanke hukuncin tura tawaga Afirka ta Kudu domin tattaunawa da hukumomin ƙasar, yayin da shi ma bangaren gwamnati ya tura ministan harkokin waje. Ambasada Ibrahim Kazaure, tsohon Jakadan Najeriya a Saudi Arabia ya yi tsokaci a kai, a tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris.

saudi arabia kiran mtn dstv kudu wasu najeriya afirka majalisar bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Tinubu ya ce babu gudu ba ja da baya kan samar da ƴan sandan jihohi

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later May 1, 2026 3:35


Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake jaddada aniyar sa ta samar da Yan Sandan jihohi domin samar da tsaro. Tinubu ya bayyana haka ne yayin ganawa da masu ruwa da tsaki na jihar Filato mai fama da tashin hankalin. Alhaji Isa Tafida Mafindi, wanda ya wallafa littafi a kan samar da Yan Sandan jihohi ya mana tsokaci a kai, yayin tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

babu samar baya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Fargaba ta mamaye zukatan ƴan Najeriya dangane da makomar adawa a ƙasar

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Apr 30, 2026 3:34


Yan Najeriya na cigaba da bayyana fargaba dangane da makomar ƴan adawar ƙasar dangane da zabe mai zuwa , la'akari da cewar akasarin jami'iyyun adawar na fama da rikice-rikicen da ka iya hana su takara. Akan wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Alhaji Kabir Muhammad Baba, ɗan siyasa a jihar Bauchi. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar......

akan asar shiga bauchi najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Farfesa Abdulƙadir Suleiman akan cika shekaru 3 da yaƙin Sudan

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Apr 16, 2026 3:24


Yayin da aka cika shekaru uku da fara yaƙin basasar ƙasar Sudan, Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla mutane miliyan 14 suka bar muhallansu, baya ga daruruwan da suka rasa rayukan su. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Abdulkadir Suleiman Muhammed na Jami'ar Abuja, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.

sudan abdul akan abuja suleiman adir yayin majalisar dinkin duniya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Abdulaziz Abdulaziz game da ziyarar Tinubu a Birtaniya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 18, 2026 3:36


Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya fara ziyarar aiki a Birtaniya inda ya samu kyakkyawar tarba daga hukumomin ƙasar. Wannan ziyara na zuwa ne a dai dai lokacin da Najeriyar ke fuskantar matsalolin tsaro iri-iri. Dangane da ziyarar ta Tinubu da kuma alfanunta ga ƙasar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai taimakawa shugaban kan harkokin tsaro Malam Abdulaziz Abdulaziz kuma ga yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

game ku abdul aziz bola ahmed tinubu wannan najeriya birtaniya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Dakta Yahuza Getso kan dawowar hare-haren Boko Haram a jihar borno

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 17, 2026 3:32


A baya-bayan nan ƙungiyar ta'addanci ta Boko Haram ta tsananta kai hare-hare jihar Borno da maƙwabtanta wanda ya sabbaba asarar ɗimbin rayuka kama daga na jami'an tsaro da kuma fararen hula. Kafin yanzu anga lafawar hare-haren ƙungiyar, sai dai a baya-bayan nan ta dawo da hare-hare ba ƙaƙƙautawa inda ko a tsakanin ranakun Lahadi zuwa yau Talata ta kashe mutane da dama a jihar ta Borno wadda ta shafe shekaru aƙalla 17 tana fama da matsalolin tsaro. Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tsaro Dakta Yahuza Ahmed Getso. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.

ku boko haram haren borno talata najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Dr Kasim Garba Kurfi kan makomar tattalin arzikin Najeriya a yaƙin Gabas ta Tsakiya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 12, 2026 3:31


Ana saran Najeriya ta shiga cikin jerin ƙasashen da za su amfana da yaƙin Iran wajen samun maƙudan kuɗaɗe ta hanyar cinikin man fetur da ake nema ruwa a jallo. Sai dai masana na bayyana cewar wasu matsalolin cikin gida na iya rage tasirin samun kuɗaɗen da ake hasashe.   Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Bashir Ibrahim Idris da DR. Kasim Garba Kurfi, masanin tattalin.......

iran ku sai kasim garba najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Yara sama da miliyan 6 ne ke fama da tamowa a Arewacin Najeriya - ICRC

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 11, 2026 3:38


Ƙungiyar agaji ta ICRC ta ce aƙalla yara ƙanana da ke ƙasa da shekaru 5 miliyan 6 da dubu 400 ke fama da tamowa a yankunan arewa maso gabashin Najeriya da ya kwashe shekaru 15 ya na fama da rikice rikicen Boko Haram da arewa maso yamma da ke fama da rikicin ƴan bindiga, sai kuma arewa ta tsakiya da ke fama da rikicin manoma da makiyaya. Mai magana da yawun ƙungiyar Usman Kundili Bukar ya bayyana haka a tattaunarsa da Bashir Ibrahim Idris. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu.......

sama ku fama boko haram icrc najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Dr Isa Abdullahi illar yaƙin Amurka a Iran ga tattalin arziƙin duniya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 10, 2026 3:13


Ƙasashen duniya sun fara jin raɗaɗin yaƙin Iran sakamakon tashin farashin man fetur a kasuwannin duniya, wanda ya shafi harkokin yau da kullum. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Isa Abdullahi, masanin tattalin arziki a kan lamarin, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

iran ku duniya abdullahi amurka bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Ibrahim Garba Wala kan sabon shugaban NMDPRA da Tinubu zai naɗa

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 18, 2025 3:38


Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya maye gurbin Engr Faruk Ahmed da Aliko Dangote ya zarga da hana ruwa gudu wajen harkokin kula da kasuwancin mai da kuma bada lasisi ta NMDPRA, tare da shugaban hukumar NUPRC. Fadar shugaban Najeriya ta ce jami'an biyu sun sauka daga mukaman su ne bisa dalilai na ƙashin kan su. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ibrahim Garba Wala kan lamarin. Ku latsa alamar sauti don jin yadda tattaunawarsu ta gudana...

ku wala garba najeriya shugaban bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Amb Abubakar Cika kan zargin Najeriya da AES ke yi na keta haddin samaniyarsu

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 10, 2025 3:36


Ƙasashen AES da suka hada da Mali da Nijar da kuma Burkina Faso, sun ƙalubalanci Najeriya sakamakon saukar gaggawar da jirgin sojin ta da ya yi a Burkina. Waɗannan ƙasashe na zargin Najeriya da keta haddin sararin samaniyar yankin su. Domin tattauna wannan batu da kuma yunkurin juyin mulkin da ya gudana a Benin, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Amb Abubakar Cika, tsohon Jakadan Najeriya a Iran. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana...........

Bakonmu a Yau
Air Commodore Baba Gamawa mai ritaya kan juyin mulkin da bayyi nasara ba a Benin

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 9, 2025 3:07


Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya jinjinawa sojojin ƙasar saboda rawar da suka taka wajen murkushe yunkurin juyin mulkin da aka samu a Jamhuriyar Benin. Tinubu ya ce hare haren sojin sama da kuma tura sojojin ƙasa cikin ƙasar, sun bada gagarumar gudumawa wajen kawar da sojojin da suka sanar da kwace ikon. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Air Commodore Tijjani Baba Gamawa mai ritaya. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu................

baba ku commodore benin nasara bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Dakta Isa Abdullahi kan matakin CBN game da cire kudi a bankuna

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 4, 2025 3:27


Babban Bankin Najeriya ya sanar da cire shingen kuɗaɗen da jama'a ke ajiyewa a bankuna da kuma ƙara yawan kuɗin da ake ɗauka a bankin. Bankin ya ce daga yanzu an ƙara yawan kuɗin da mutum ka iya cirewa daga naira 100,000 zuwa naira 500,000, yayin da bankin ya ci gaba da riƙe naira N100,000 a matsayin kuɗin da mutum guda ka iya cirewa a ATM a rana guda. Domin duba tasirin wannan mataki, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki Dakta Isa Abdullahi, na Jami'ar Kashere, da ke jihar Gombe a Najeriya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

game atm domin cire gombe abdullahi shiga kudi n100 najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Yadda aka tarawa Najeriya dala miliyan 30 domin samar da tsaro a makarantu

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 3, 2025 3:37


Ƴan Najeriya na ci gaba da neman bayani a kan yadda wasu kuɗaɗen da aka tara, da yawan su ya kai dala miliyan 30 domin samar da tsaro a makarantu suka shiga, sakamakon sake dawowar satar ɗalibai a yankin arewacin ƙasar. A ƙarƙashin wannan shirin da ya fara a shekarar 2014, kasashe da dama suka tallafawa Najeriya, cikin su har da ƙasar Norway da ta bada dala miliyan guda, da wata dala miliyan guda daga Bankin Raya ƙasashen Afirka na AfDB, sai kuma Fam miliyan guda daga gwamnatin Birtaniya. Gwamnatin Switzerland ta bada taimakon dala miliyan takwas, yayin da Amurka ta bada dala miliyan biyu, sai kuma Qatar da ta bada dala miliyan biyu, yayin da ƴan kasuwan Najeriya su kuma suka bada taimakon dala miliyan 10. Ganin yadda aka kasa samar da tsaron a makarantu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Abubakar sadiq Umar Gombe.  Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

norway qatar fam domin dala samar yadda tarawa shiga najeriya afirka amurka birtaniya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Janar Sani Kukasheka kan kalubalen tsaron da ke gaban Christopher Musa

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 3, 2025 3:35


Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatar da sunan Janar Christopher Musa mai ritaya ga majalisar Dattawa domin amincewar ta ya zama ministan tsaro. Christopher Musa ya yi aiki a matsayin babban hafsan tsaron Najeriya daga ranar 23 ga watan Yunin 2023 zuwa 30 ga watan Octoban 2025, lokacin da shugaban ƙasar Bola Ahmad Tinubu ya yi masa ritaya. Idan majalisa ta amince, Janar Musa zai maye gurbin Badaru Abubakar da ya yi murabus a ranar Litinin. Bayanai sun nuna cewa fannonin da Musa ya fi ƙwarewa a kai shine fatattarkar ƴan ta'adda, da dubarun yaƙi, kasancewar ya yi aiki a matsayin jagoran rundunar sojojin Najeriya da ke kula da tsaron iyakokin Najeriya ta arewa maso gabashi da kuma yankin tafkin Chadi, haka nan ya kuma yi aiki a matsayin guda daga cikin dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya a Sierra Leone, da kuma wasu ayyukan a Amurka da Majalisar Ɗinkin Duniya.. Domin sanin tasirin wannan nadin da kuma kalubalen dake gaban Janar Musa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon kakakin rundunar sojin kasa ta Najeria, Janar Sani Usman Kukasheka mai ritaya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

sierra leone domin sani idan duniya shiga chadi najeriya amurka majalisar bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Farfesa Tukur Abdulƙadir akan juyin mulkin Guinea Bissau

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 27, 2025 3:34


 A jiya ne sojoji suka hambarar da gwamnatin shugaba Umaro Sissiko Embalo, sakamakon rikicin zaɓen shugaban ƙasar da aka yi a ƙarshen mako, a daidai lokacin da ake shirin gabatar da sakamako yau Alhamis. Shugaban da madugun yan adawa duk sun yi iƙrarin nasara, a kasar da ta yi ƙaurin suna wajen juyin mulki. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Tukur Abdulkadir dangane da juyin mulkin, wanda shi ne na biyar a kasashen Afirka ta Yamma, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai. 

abdul akan guinea bissau adir yamma afirka alhamis shugaban bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Farfesa Bello Bada kan matakan rufe makarantu saboda dalilan tsaro a Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 26, 2025 3:40


Gwamnatocin wasu jihohin dake arewacin Najeriya sun sanar da matakan rufe makarantun firamare da sakandare, wasu ma harda jami'oi, domin kaucewa matsalar garkuwa da daliban da ake samu, wanda ya kara ta'azzara a kasar. Domin duba tasirin matakin da kuma halin da yankin ya samu kan sa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Bello Bada na Jami'ar Usman Dan Fodio dake Sokoto. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

bello bada domin rufe shiga sokoto najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Malam Ahmad Abdurrahaman kan ɗaukar sabbin ƴansanda dubu 30 a Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 25, 2025 3:35


Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bada umarnin ɗaukar sabbin ƴansanda dubu 30 da kuma janye masu gadin manyan mutane ba bisa ƙa'ida ba. Domin sanin tasirin wannan mataki da kuma yadda zai taimaka wajen inganta tsaro a ƙasar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon mataimakin Sifeto Janar na Ƴansandan Najeriya Malam Ahmad Abdurrahaman.  Ku latsa alamar sauti donjin yadda zantawarsu ta gudana.............

ku malam domin dubu najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Amnesty ta zargi Chadi da gazawa wajen ɗaukar matakan kare mutanen da ake cin zarafin su

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 21, 2025 3:33


Ƙungiyar Amnesty International ta zargi hukumomin ƙasar Chadi da gazawa wajen ɗaukar matakan kare mutanen da ake cin zarafin su, sakamakon rikici tsakanin manoma da makiyaya a ƙasar, yayin da ta ce  tsakanin shekarar 2022 zuwa 2024, an kashe mutane 98, baya ga jikkata sama da 100 da kuma tilastawa ɗaruruwan iyalai barin muhallin su. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Isa Sanusi Daraktan kungiyar a Najeriya, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.

amnesty international amnesty chadi najeriya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Hon Sani Ahmad Toro kan yadda Najeriya ta gaza samun tikitin World Cup

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 18, 2025 3:37


Fatan Najeriya na samun gurbi a gasar cin kofin duniyar da za'a yi a shekara mai zuwa ya gushe, sakamakon rashin nasarar da ƙungiyar Super Eagles ta yi a hannun ƙasar Congo. Wannan shi ne karo na biyu a jere da Najeriya ba zata je gasar ta dunitya ba, bayan gaza zuwa Qatar shekaru 4 da suka gabata, kafin wannan karo. Bashir Ibrahim Idris, ya tattauna da tsohon sakatare janar na Hukumar Kwallon Kafa Najeriya, Hon Sani Ahmad Toro game da wannan koma baya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana a kai.

Bakonmu a Yau
Hon Hamisu Mu'azu Shira kan dambarwar da ke tattare da babban taron jam'iyyar PDP

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 14, 2025 3:47


Shugaban kwamitin shirya babban taron Jam'iyyar PDP na ƙasa a birnin Ibadan dake Najeriya, Umar Fintiri, wanda shi ne Gwamnan Adamawa, ya ce babu abinda zai hana su gudanar da taron da suka shirya gobe asabar. Fintiri ya bayyana haka ne bayan wani gagarumin taron da masu ruwa da tsaki na jam'iyyar da suka gudanar yau a birnin Abuja. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hon Hamisu Mu'azu Shira, ɗaya daga cikin jiga jigan jam'iyyar, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana a kai.

jam shira abuja pdp ibadan taron najeriya shugaban bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Abubakar Ibrahim kan taron sauyin yanayi na COP30 da ke gudana a Brazil

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 11, 2025 3:37


An bude traon Majalisar Dinkin Duniya a kan sauyin yanayi da ake kira COP 30 a Brazil inda masana muhalli da sauyin yanayi daga kasashen duniya da kuma kungiyoyin kare muhallin ke halarta a kasar Brazil. Za'a kwashe makwanni biyu ana gudanar da wannan taro wanda zai mayar da hankali a kan ci gaba ko akasin haka da aka samu a kan wannan matsala. Dakta Abubakar Ibrahim, Malami kuma mai bincike a Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria ya yi tsokaci a kan matsalar musamman ganin irin illar da take yi a yankin arewacin Najeriya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawarsa da Bashir Ibrahim Idris.

brazil cops za taron abubakar shiga najeriya malami majalisar dinkin duniya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Barr Abdullahi Jalo kan ƙoƙarin warware barazanar Trump na kai hari Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 6, 2025 3:37


Yayin da ake ci gaba da lalubo hanyar warware matsalar barazanar Donald Trump na kai hari Najeriya, wasu masana na bayyana cewar ta hanyar diflomasiya kawai za a iya warware wannan dambarwa. Barr Abdullahi Ibrahim Jalo na ɗaya daga cikin su. Ku latsa alamar sauti don sauraron yadda tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris ta gudana..............

Bakonmu a Yau
Ambasada Abubakar Cika kan barazanar kai wa Najeriya hari da Amurka ta yi

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 4, 2025 3:37


Yayin da hukumomin Najeriya suka yi watsi da barazanar shugaban Amurka na kai wa ƙasar hari saboda zargin kashe Kiristoci, ƴan kasar da dama na ci gaba da bayyana ra'ayi a kan matsayin na shugaba Donald Trump. Daga cikin waɗanda suka bayyana ra'ayin su a kan wannan barazana har da tsohon Jakadan Najeriya a ƙasar Iran, Ambasada Abubakar Cika, kamar yadda za ku ji a tattaunawarsu da Bashir Ibrahim Idris.  

donald trump iran hari daga abubakar yayin najeriya amurka bashir ibrahim idris