POPULARITY
Taron Jam'iyyar PDP a ƙarshen makon da ya gabata, ya amince da bai wa yankin kudancin ƙasar damar gabatar da ɗan takarar zaɓen shugaban ƙaasr da za ayi a shekarar 2027, ya yin da ya haramtawa waɗanda suka fito daga arewacin ƙasar tsayawa takara. Tuni aka bayyana cewar wasu kusoshin jam'iyyar na zawarcin tsohon shugaban ƙasar Goodluck Jonathan da Peter Obi domin tsaya musu takara. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon Sakataren jam'iyyar, Sanata Umar Ibrahim Tsauri game da lamarin. Ku latsa alamar sauti don sauraron yadda zantawarsu ta gudana.................
Manyan hafsoshin tsaron ƙasashen Afrika sun bayyana aniyar aiki tare a tsakaninsu domin tunƙarar matsalolin tsaron da suka addabi nahiyar, musamman ayyukan ta'addanci. Wannan ya biyo bayan taron da suka halarta a Najeriya. Dangane da wannan, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Janar Idris Bello Danbazau mai ritaya dangane don jin alfanun wannan sabin yunƙuri , ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana akai. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....
Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah wadai da kisan ƙarin ƴan jaridu 5 da Isra'ila ta yi a asibitin Khan Younes. Daraktan ƙungiyar a Najeriya, Malam Isa Sanusi ya buƙaci ƙasashen duniya da su tilastawa Isra'ila mutunta dokokin duniya wajen kare ƴan jaridun da ke gudanar da aikin su a ƙasar. Ku latsa alamar sauti don jin yadda tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris ta gudana............
Ƙungiyar Fulani ta Miyetti Allah a Najeriya, ta nesanta kan ta daga goyan bayan ayyukan ta'addancin da wasu ɗai-ɗaikun ƴaƴanta keyi, tare da bayyana cewar ita ta fi jin raɗaɗin matsalar. Shugaban ƙungiyar Baba Usman Ngelzerma ya ce aƙalla Fulani 20,000 aka kashe, yayin da suka yi asarar shanu sama da miliyan 4 ga ayyukan ta'addancin a shekaru 5 da suka gabata. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Bashir Ibrahim Idris.............
Majalisar Dattawan Najeriya ta bayyana cewar ya zama dole ta yi dokokin da za su takaita yadda kafofin sada zumunta ke neman haifar da tashin hankali a cikin kasar. Shugaban masu rinjaye a Majalisar Bamidele Opeyemi ya bayyana haka, sakamakon zargin neman jefa kasar cikin tashin hankalin da matasa ke yi ta wadannan kafofi. Dangane da wannan yunkuri, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin harkar sadarwa,Malam Umar Saleh Gwani. Latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana...
Gwamnan Jihar Kaduna da ke Arewacin Najeriya, Uba Sani ya ce matakin soji kawai ba zai iya magance ayyukan ta'addancin da ake fuskanta a ƙasar ba. Gwamnan ya ce ya zama wajibi a magance matsalolin da ke haifar da matsalar baki ɗaya da suka haɗa da talauci da nuna banbanci da rashin shugabanci na gari da kuma bai wa matasa dama. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abubakar Sadiq Muhammad, tsohon malami a jami'ar Ahmadu Bello akan matsalar ta tsaro a ƙasar. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu...................
Gwamnatin Najeriya ta bayyana shirin amfani da malaman addini wajen wayar da kan jama'a wajen rungumar amfani da abincin da aka sauyawa kwayar halitta da ake kira GMO. Shugaban hukumar kula da irin wadannan abinci Farfesa AbdullahI Mustapha ya bayyana haka a tattaunawarsa da RFI Hausa. Ganin yadda jama'a ke dari darin amfani da irin wannan abinci, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin kula da harkar lafiya, Farfesa Yusuf Abdu Misau, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Gwamnatin Najeriya ta bayyana nasarar kama shugabannin ƙungiyar ƴan ta'adda da ake kira Ansaru mai alaƙa da Al'Qaeda, wadda tayi ƙaurin suna wajen kai munanan hare hare a jihohin Neja da kwara. Mai baiwa shugaban ƙasar Najeriya a kan harakokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu ya bada wannan sanarwar. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Tsofan kakakin runduna sojin Najeriya Janar Sani Usman Kukasheka ga kuma yadda zantawarsu ta gudana. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hira......
Rahotanni daga sassan Najeriya na bayyana faɗuwar farashin kayan abinci, abinda zai taimakawa talakawa wajen samun sauki. Sai dai manoman ƙasar na ƙorafi a kan asarar da suka ce sun tafka. Domin tabbatar da samun saukin farashin, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da shugaban ƴan kasuwar hatsi ta duniya da ke Dawanau a jihar Kano, Alhaji Mustapha Yusuf Mai Kalwa. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattawaunawar tasu.............
A ranar Jumma'a ake saran shugaban Amurka Donald Trump zai yi wata ganawa da takwaransa na Rasha Vladimir Putin dangane da yadda za'a kawo ƙarshen yaƙin da ake gwabzawa a Ukraine. Sai dai wasu da bayyana damuwa kan yadda shugabannin suka manta da batun tsagaita wuta a yaƙin Gaza, ganin yadda ake ci gaba da asarar rayukan ɗimɓin rayuka. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr. Abdulhakeem Garba Funtuwa dangane da yunkurin ƙasashe duniyar na samaun tsagaita wuta da kuma watsi da halin da ake ciki a Gaza.
Bankin Duniya ya ce ya amince da buƙatar bai wa Najeriya dala miliyan 300, domin amfani da shi wajen inganta rayuwar mutanen da rikici ya raba da muhallansu a yankin arewacin ƙasar. Sanarwar Bankin ta ce za ayi amfani da kuɗaɗen ne wajen tallafawa irin waɗannan mutane da waɗanda suka basu matsuguni domin ganin sun koma masu dogaro da kan su, maimakon dogara da kayan agaji. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ibrahim Garba Wala, ɗaya daga cikin masu fafutukar kare hakkokin jama'a a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana................
Sojojin Najeriya sun yi nasarar hallaka ƴanbindiga sama da 100 a ƙaramar hukumar Bukkuyum dake jihar Zamfara, sakamakon wasu hare haren sama da suka kaddamar a kan su. Rahotanni sun ce sojojin sun yi amfani da bayanan asiri ne wajen kai harin kan ƴanta'addan waɗanda aka ce yawansu ya kai 400 a dajin a Makakkari. Wannan na daga cikin nasarorin da sojojin Najeriya suka samu a ƴan kwanakin nan. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ad Farfesa Bello Bada na Jami'ar Usman Danfodio dake Sokoto, wanda ya ce wannan shi ne labarin da ƴan Najeriya ke farin cikin ji. Ga yadda tatatunawar su ta gudana a kai.
A Najeriya, ga dukkan alamu an samu rarrabuwar kawuna tsakanin dillalan man fetur, sakamakon shirin Aliko Dangote na jigilar man daga matatarsa da ke Lagos zuwa gidajen mai a sassan ƙasar. Yayin da shugabannin dillalan ke adawa da shirin Dangoten, kananan dillalan sun bayyana gamsuwar su da shirin, kamar yadda za kuji a tattaunawar Bashir Ibrahim Idris da Alhaji Ladan Abdullahi Garkuwa.
Matsalolin tattalin arziki a Najeriya ya taimaka wajen watsi da matsayin matsakaitan mutane da ke tsakanin al'umma, inda yanzu ake da attajirai ko matalauta kawai. Masanan na gabatar da dalilai daban daban da suka yi sanadiyar samun wannan matsala, wadda ta haifar da wagegen gibi a tsakanin al'umma. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Bashir Ibrahim Idris da Dr Abbati Bako.......
'Yan asalin jihar Zamfara da ke Najeriya, na ci gaba da bayyana matuƙar damuwarsu dangane da ƙaruwar hare-hare da kisan jama'a da 'yan bindiga ke yi. Mazauna wannan jiha da ke Arewa maso Yammacin ƙasar, sun buƙaci haɗin kai tsakanin gwamnatin jihar da ta Tarayya da zumar samar musu mafita ta dindindin. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Sulaiman Shu'aibu Shinkafi daga jihar. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Sama da shekaru biyu bayan ɓarkewar yakin basasar ƙasar Sudan, kasashen duniya sun kau da kan su, yayin da ake ci gaba da hallaka fararen hula. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abdulkadir Suleiman Muhammad, a kan dalilin da ya haifar da yaƙin da kuma yadda ƙasashen duniya suka juyawa ƙasar baya. Latsa alamar sauti domin sauraren hirar...
Ƙungiyar agaji ta ICRC ta bayyana cewar akwai yiwuwar fuskantar matsalar yunwa a arewa maso gabashin Najeriya sakamakon tashin hankalin da ya tilastawa manoma ƙauracewa gonakin su. Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawar Bashir Ibrahim Idris da Farfesa Abba Gambo...
A ranar Litinin ne tsofaffin 'Yan Sandan Najeriya da suka yi ritaya suka gudanar da zanga-zanga a biranen ƙasar da kuma Abuja, saboda gabatar da ƙorafi akan yadda ake biyan su fansho da kuma neman fitar da su daga tsarin da ake amfani da shi yanzu haka. Bayan kammala zanga zangar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da CSP Abubakar Abdullahi dashe mai ritaya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana a kai. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Shugaba Paul Biya na Kamaru mai shekaru 92 ya bayyana aniyar sake tsayawa takara don neman wa'adi na 8 na mulkin ƙasar da nufin ci gaba da yiwa ƙasar hidima. Shugaba Biya ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta. Sai dai ko yaya jama'ar Kamaru ke kallon wannan mataki, dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Isma'ila Muhammed ɗan siyasa a ƙasar ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar..
A jiya Lahadi, 13 ga watan Yulin nan ne Allah ya yi wa tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari rasuwa yana da shekaru 82 a duniya. Bayan kasancewa shugaban gwamnatin sojin Najeriya daga shekarar 1983 zuwa da 1985, ya sake dawowa a matsayin farar hula, inda ya mulki ƙasar daga shekarar 2015 zuwa 2023. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Faruk Adamu Aliyu, ɗaya daga cikin makusantan Buhari akan wannan rasuwa da irin rayuwar da yayi. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....
Rahotanni daga Najeriya sun ce mutane da dama ne suka rasa rayukansu sakamakon haɗurran motoci da aka samu a ƙarshen mako cikin jihohin Kano da Jigawa da Bauchi da Lagos da kuma jihar Oyo baya ga Lagos da kuma jihar Kogi. Wannan na zuwa ne a dai dai lokacin hanyoyin motoci ke ci gaba da taɓarɓarewa, yayinda wasu direbobin ke tuƙi cikin yanayi na maye ko kuma saɓawa dokokin tuƙi. Dangane da wannan matsala da ke kaiwa ga asarar ɗimbin rayuka, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Adamu Idris Abdullahi Sakataren ƙungiyar direbobin sufuri ta NURTW da ke Abuja ga kuma yadda tattaunawarsu ta kasance. Sai ku latsa alamar sauti don saurare.
A ƙarshen makon da ya gabata aka samu ambaliyar ruwan sama a sassan birnin Kano, a dai dai lokacin da damina ta fara kankama a jihar. Wannan matsalar ta haifar da matsaloli ga mazauna da kuma baƙin da ke zuwa birnin. Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da shugaban ƙaramar hukumar Dala, Hon Siraj Ibrahim Imam, Kuma ga yadda zantawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti son sauraron cikakkiyar Hirar.
Wasu daga cikin jiga-jigan ƴan adawar Najeriya sun haɗa kansu wajen komawa jam'iyyar ADC domin shirin tunkarar gwamnatin APC mai mulki da suke zargi da rashin iya mulki, Yayin gabatar da sabbin shugabannin, ƴan adawar sun sha alwashin ceto talakan Najeriya daga halin ƙuncin da ya samu kansa. Sai dai wasu na cewa neman mulki ne kawai suke yi amma ba don talakan Najeriya ba. Bashir Ibrahim Idris ya tattauwa da shugaban cibiyar horar da ƴan Jaridu ta IIJ da ke Abuja, Dr Emman Shehu, kuma ga yadda zatawarsu ta gudanar.
A Najeriya mayaƙan sa kai a jihar Zamfara sun yi nasarar hallaka wasu daga cikin manyan kwamandojin ƴan bindigar da suka hana zaman lafiya a jihar, cikinsu har da Kachalla Ɗanbokolo da wasu tarin magoya bayansu. Domin sanin tasirin wannan nasara ga jama'ar yankin, Bashir Ibrahim Idris ya tattauba da masanin harkar tsrao, Dr Yahuza Getso. Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar
Gwamnatin Najeriya ta sha alwashin dasa itatuwa biliyan 20, a kokarin da take yi na magance gurgusowar hamada da tsananin zafi , har ma da sauyin yanayi. Mataimakin shugaban kasar Kashin Shetimma ne ya bayyana hakan, yayin da yake jawabi a wajen wani taroa kasar Habasha. Game da tasirin wannan, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Muhammad Adamu Dansitta. Dannan alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar.
Yau ake cika shekaru 80 da rattaɓa hannu kan yarjejeniyar da ta samar da Majalisar Ɗinkin Duniya da aka gudanar a Birnin San Francisco da ke Amurka, a ranar 26 ga watan Yunin shekarar 1945. Bikin cika shekaru 80 din na zuwa ne a daidai lokacin da Majalisar mai wakilai 193 ke fuskantar kalubale da dama, waɗanda suka hada da makomar ta ko kuma ci gaban tasirinta baki ɗaya. Kan wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ambasada Abubakar Chika, tsohon jakadan Najeriya a Iran. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana..........
Ƙungiyar agaji ta ICRC wadda ke aiki a yankin arewa maso gabashin Najeriya, ta bayyana damuwa da janyewar wasu ƙungiyoyin agaji da ke bai wa ƴan gudun hijira tallafi a yankin. Babban jami'in yada labaran ƙungiyar a Najeriya, Aliyu Dawobe da ke ziyarar aiki a Lagos, ya mana ƙarin bayani dangane da halin da suke ciki. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Bashir Ibrahim Idris...........
Shugabannin ƙsashen Yammacin Afrika da ke ƙarƙarshin ƙungiyar ECOWAS sun sake bayyana damuwarsu dangane da ƙruwar matsalar tsaro a yankin. Yayin taron da suka gudanar a ƙarshen mako, shugaban ƙungiyar mai barin gado kuma shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake gabatar da buƙatarsa ta tabbatar da rundunar tsaro ta haɗin gwiwar da zata tinkari wannan matsalar. Bashir Ibrahim Idris ya tattaunawa da Janar Sani Usman Kukasheka mai ritaya,tsohon kakakin rundunar sojin Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu..........
Yayin ake ci gaba da bikin cika shekaru 50 da kafa Ƙungiyar Haɓaka Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika ECOWAS/CEDEAO, a wannan karo za mu yi dubi a game da wasu daga cikin muhimman ayyukan da ƙungiyar ta yi a fagen yaƙi da rashawa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna Dr Abdullahi Shehu, tsohon jakadan Najeriya a Rasha, kuma wanda ya jagora hukumar ta GIABA tsawon shekaru 8. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tasu...........
Ranar 28 ga watan Mayu, wato gobe Laraba kenan, Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afrika ECOWAS, ke cika shekaru 50 da kafuwa.An dai samar da ƙungiyar ne cikin watan Mayun shekarar 1975 a birnin Legas, inda a wacccan lokacin ta ƙunshi ƙasashe 15. A tsawon lokacin da ta shafe bayan kafuwarta, ECOWAS ta taka rawa muhimmiyar rawa ta fuskar tsaro, ciki kuwa har da kawo ƙarshen yaƙe-yaƙen da suka nemi wargaza ƙasashen Saliyo da Liberia. Kan haka ne kuma Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da, Air Comodore Tijjani Baba Gamawa ɗaya daga cikin sojojin da suka bayar da gudunmawa a waccan lokaci.
Kungiyar kasashen Afirka ta Yamma ta ECOWAS ta bayyana shirin kafa sabuwar rundunar hadin kai wadda za ta dinga yaki da yan ta'addan da suka addabi yankin. Wannan na da cikin shirin shugabannin yankin na dakile ayyukan ta'addanci, da suka ƙi ci suka ƙi cinyewa.Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Janar Kape Alwali Kazir mai ritaya a dangane da wannan shiri.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
A yau 21 ga watan Mayun 2025, shekaru 18 kenan da Radio France International ya fara yaɗa shirye-shiryensa a cikin harshen Hausa, wanda kuma shi ne harshen na farko daga Afirka da RFI ta fara yaɗa shirye-shiryenta da shi. Malam Bashir Ibrahim Idris, shi ne Babban Editan RFI Hausa, ya yi muna ƙarin bayani a game da yadda rediyon ya fara da kuma irin ci gaba da ya samu a waɗannan shekaru. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawar da Ƙaribullah Abdulmajid Namadobi ya yi da shi...........
Da aalam dai har yanzu da sauran rina a kaba ga hukkumar JAMB, mai shirya jarabawar shiga manyan makarantu a Najeriya a game da matsalar da aka samu a lokacin jarabawar wannan shekarar sakamakon ƙorafin da wasu jihohin arewacin ƙasar ke yi akan ware wasu jihohi huɗu na kudu da hukumar ta yi don sake zana jarawabar. Tuni dai wasu suka yi barazanar zuwa kotu tare da kira ga gwamnati da ta saka baki a lamarin. Kan haka ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Barrister Abdullahi Jalo, masanin doka.
Babban Hafsan tsaron Najeriya, Laftanar Janar Christopher Musa ya ce baya ga amfani da makamai wajen tinkarar mayakan Boko Haram, farfado da Tafkin Chadi zai taimaka wajen samarwa jama'ar yankin sana'oi. Wannan ya biyo bayan ziyarar aikin da ya kai Maiduguri bayan kazaman hare haren da boko haram ta kai cibiyoyin soji.Dangane da wannan bukatar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da wani mutumin yankin, Farfesa Sheriff Muhammad Almuhajir.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Hukumar kula da jarabawar shiga manyan makarantu a Najeriya ta JAMB ta nemi gafarar jama'ar kasar saboda matsalolin da aka samu wajen jarabaswar bana, wadda ta kai ga dalibai sama da miliyan guda da rabi suka kasa samun makin da ake bukata. Shugaban hukumar Farfesa Ishaq Oloyede cikin hawaye ya nemi gafarar jama'a da kuma daukar alhakin lamarin.Dangane da wannan matsala, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Umar Saleh Gwani masanin harkar sadarwa.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Wasu rahotanni a Najeriya na bayani akan karuwar samun mutanen dake fama da rashin lafiyar dake da nasaba da kwakwalwa, sakamakon yanayin rayuwar yau da kullum. Domin sanin tasirin matsalar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Balarabe Sani Garko na Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Gwamnonin Arewacin Najeriya tare da Sarakunan yankin sun gudanar da wani taro na musamman domin sake duba matsalolin tsaron da suka addabi yankin, a dai-dai lokacin da mayaƙan Boko Haram da ƴanbindiga ke ci gaba da hallaka jama'a ba tare da ƙaƙƙautawa ba. Bayan kammala taron, Bashir Ibrahim Idris ya tintibi Farfesa Bello Bada na Jami'ar Usman Dan Fodio da ke Sokoto. Kula latsa alamar sauti don sauraron yadda zantawarsu ta gudana akai...........
Dalilan da suka sanya 'yan Najeriya ke ƙara faɗawa cikin mawuyacin hali sanadiyyar talaucin da ya yi musu katutu. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziƙi a Najeriya Dr Kassim Garba Kurfi.Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawar...
Majalisar dokokin ƙungiyar ƙasashen ECOWAS ta gudanar da taron ta a Lome da ke ƙasar Togo, wanda ya mayar da hankali kan tsadar sufurin jiragen sama a yankin. Bayan taron, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Sanata Ali Muhammed Ndume, daya daga cikin shugabannin taron. Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar tattaunawar tasu.............
Yau manyan limaman dariƙar Katolika na duniya sama da 130 ke fara gudanar da zaɓen Fafaroma domin maye gurbin Francis da ya rasu a makon jiya.Domin sanin yadda ake gudanar da zaɓen, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Archpishop Ignatius Kaigama, daya daga cikin manyan limaman Katolika a Najeriya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana akai. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.....
Gwamnatin sojin Jamhuriyar Nijar ta bai wa hafsan sojojin ƙasar umarnin cewar babu wanda zai tafi ritaya a cikin wannan shekarar, sakamakon wasu matsalolin tsaron da kasar ke fuskanta. Dangane da wannan umarni, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Sani Yahya Janjuna, mai sharhi akan lamuran yau da kullum, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana akai.
Katafaren kamfanin sadarwar Meta da ya mallaki Facebook da WhatsApp ya yi barazamar ficewa daga Najeriya, saboda cin tararsa da hukumomin ƙasar suka yi na Dala miliyan 290, sakamako karya ƙa'idodin aikinsa. Najeriya ta samu kamfanin ne da laifin talla ba bisa ƙa'ida ba, da kuma rashin alkince bayanan asiri na jama'ar dake hulɗa da shi.Dangane da wannan dambarwa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hon Samaila Muhammed, masanin tallalin arziki da kuma sadarwa, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana akai.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar
Yau shugaban Amurka Donald Trump le cika kwanaki 100 a karagar mulkin ƙasar, tun bayan rantsar da shi a ranar 20 ga watan Janairun shekarar nan. A tsawon wannan lokaci, shugaban na Amurka ya ɗauki mabanbantan matakai da suak girgiza sassan duniya.Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Tukur Abdulkadir na Jami'ar Kaduna, don jin yadda masana ke kallon salon kamun ludayin Donald Trump ga kuma tattaunawarsu.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar..
Kungiyar Amnesty International ta tabbatar da mutuwar mutane 26 sakamakon harin ƴan bindiga a wurin hakar zinaren da ke jihar Zamfara. Daraktan ƙungiyar a Najeriya, Malam Isa Sanusi ne ya tabbatar da haka a tatatunawar da suka yi da Bashir Ibrahim Idris. Ku latsa alamar sautin don sauraron cikakkiyar tattaunawar tasu...........
Yayin da ƙungiyar ECOWAS ke cika shekaru 50 a wannan mako, mun shirya muku rahotanni da hirarraki daban-daban dangane da gudunmawar da ƙungiyar ta bayar a cikin waɗannan shekaru. Daga cikin su akwai rawar da dakarun ECOMOG suka taka wajen magance rikice-rikice da aka samu a ƙasashen Liberia da Saliyo.Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Air Commodore Tijjani Baba Gamawa mai ritaya, ɗaya daga cikin sojojin da suka yi aikin samar da zaman lafiyar. ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
Ƙungiyar Lauyoyin Najeriya ta bayyana rashin amincewar ta da matakin da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya ɗauka, na dakatar da gwamnan Jihar Rivers Siminalayi Fubara da majalisar dokokin jihar, tare da naɗa kantoman soji. Kungiyar tare da jam'iyyun adawa da kuma wasu masu sharhi na cewa matakin ya saba dokar ƙasa. Dangane da wannan matsayi, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin shari'a Barr Solomon Dalung. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu..........
Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar sun ce an fara samun saukin karancin man fetur da aka fuskanta a kwanakin da suka gabata, abinda ya jefa jama'a da dama cikin halin kunchi. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Muhammadu Gamatche, shugaban gamayyar kungiyoyin masu motocin sufuri ta kasa a Nijar, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana
Hukumar EFCC dake yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya ta sanar da kwato kuɗaɗen da suka kai naira Triliyan guda a shekarar da ta gabata, abinda ke nuna irin nasarar da ta samu, baya ga samun nasara a kotu a shari'o'in da suka kai sama da 4,000.Dangane da wannan nasarar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Isa Sanusi, Daraktan Ƙungiyar Amnesty a Najeriya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiya hirar...........
Shugaban Ƙasar Ghana John Dramani Mahama ya ƙaddamar da wani shirin diflomasiya domin shawo kan ƙasashen Nijar da Mali da Burkina Faso, wadanda suka fice daga cikin ƙungiyar ECOWAS.A ƙarshen makon da ya gabata, shugaban ya ziyarci waɗannan ƙasashe guda uku, inda ya gaba da shugabannin su.Dangane da tasirin wannan ziyarar, Bashir Ibrahim Idris ya tatauna da Dr Elharun Muhammad na Cibiyar kula da manufofin ci gaban ƙasashe dake Kaduna, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Ƙungiyoyin mata daban daban na ci gaba da gudanar da zanga zanga dangane da zargin cin zarafin da Sanata Natasha Uduaghan ke yi kan shugaban Majalisar dattijan ƙasar Godwill Akpabio na neman yin lalata da ita, wanda ya sanya matan miƙa buƙatar murabus ɗinsa, kodayake jami'an tsaro sun yi amfani da hayaƙi mai sanya ƙwalla wajen tarwatsa dandazonsu. Dangane da yadda tarin mata ke fuskantar cin zarafi walau a wuraren ayyuka koma a tsakar gari, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hajiya Khadija Suleiman Saulawa wata mai rajin kare haƙƙoƙin mata a Najeriya ga kuma yadda zantawarsu ta gudana.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.