POPULARITY
Gobe ne hukumar zaɓe a Najeriya ke gudanar da zaɓen gwamnan Ekiti da ke yankin kudanci, inda ƴan takara 13 za su fafata. Ana kallon wannan zaɓen a matsayin zakaran gwajin dafi ga sabon shugaban hukumar zaɓen Farfesa Joash Amiputan. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai magana da yawun hukumar Hajiya Zainab Abubakar. Latsa alamar sauti don sauraren yadda zantawarsu ta gudana...
Ƙungiyar Kare Hakkin Bil'adama ta Amnesty International ta bukaci gwamnatin Najeriya da ta dauki matakai na gaggawa don kare dalibai da kuma ceto wadanda har yanzu suke hannun masu garkuwa da mutane. Ƙungiyar ta jaddada cewa gazawar hukumomi wajen kawo ƙarshen hare-hare da sace-sacen dalibai na nuna cewa rayuwar yara na cikin matsananciyar barazana. Ƙungiyar ta bukaci Shugaba Tinubu da ya dauki matakin gaggawa na kawo karshen satar yara da kai hari makarantu, tana mai cewa iyaye sun gaji da romon bakar da ake musu. Amnesty ta zargi gwamnatin da kasa kare kananan hukumomi, musamman a jihar Zamfara da sauran yankunan Arewa daga hare-haren yan bindiga. Kungiyar ta nuna damuwa kan yadda tsadar rayuwa da matsalar tsaro ke raba iyalai da muhallansu, lamarin da ke jefa yara da dama cikin yunwa da rashin ilimi. Kan wannan ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Daraktan Ƙungiyar a Najeriya Isah Sunusi. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Gwamnatin Jihar Filato da ke Najeriya ta bayyana matuƙar damuwar ta dangane da yadda ta ce wasu na amfani da hukuncin wata kotu dangane da baiwa wasu Hausawa takardar zama ƴan ƙasa domin haifar da tashin hankali a tsakanin al'ummar da suka kwashe shekaru da dama su na zaman lafiya da juna. Gwamnatin ta ja kunnen al'umma inda ta ce waɗanda ba su gamsu da hukuncin ba na da hurumin ɗaukaka ƙara kamar yadda dokokin ƙasa da suka tanada. Bashir Ibrahim Idris ya tuntuɓi kwamishiniyar yaɗa labaran jihar da ta gabatar da sanawar, Joyce Ramnap kuma ga yadda zantawarsu ta gudanar a kai.
Wata babbar kotu a Najeriya, ta bai wa hukumar zaɓe ta INEC umarnin soke wasu jam'iyyun adawa har guda biyar, saboda saɓawa dokokin zaɓen shekarar 2023 na ƙasa samun kashi 25 na ƙuri'un da aka kaɗa. Jam'iyyun sun haɗa da ADC da AA da APP da ZLP da Acoord Party. Tuni wannan hukunci ya haifar da mahawara da kuma zargin yunƙrin haa 'yan adawa shiga zaɓe mai zuwa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Abubakar Sadiq Gombe, shugaban Jam'iyyar adawa ta SDP. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Yau ake fara gasar cin kofin duniya ta bana, inda ƙasashe 48 za su fafata domin samun zakarar bana. A karon farko ƙasashe uku ne ke daukar nauyin gasar, wato Amurka da Cnada da kuma Mexico kuma kalla yan wasa 1,248 da alkalan wasa 52 za su jagoranci wasanni 104 da za'a kwashe kwanaki 39 ana yi. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar da Bashir Ibrahim Idris ya yi da tsohon Sakataren hukumar kwallon kafar Najeriya Hon Sani Ahmed Toro.....
Asusun bada lamuni na duniya IMF ya ce sauye-sauyen da gwamnatin Najeriya ke yi na ƙarfafa tattalin arzikin ƙasar, sai dai kuma sun haifar da ƙarin ƴan Najeriya sama da miliyan 60 da suka faɗa cikin talauci. Ku danna alamar saurare domin jin tattaunawar Bashir Ibrahim Idris, da masanin tattalin arziki a Najeriya Samaila Abdullahi Muhammad kan wannan batu.
Yankin arewacin Najeriya na ci gaba da ɗanɗana kuɗar sa a hannun ƴan bindiga, waɗanda ke kai hari suna sace mutane da kuma hallaka su ba tare da ƙauƙautawa ba. ko a jiya sai da ƴan bindigar suka yi garkuwa da wata tawagar masu neman sulhu da su a jihar Zamfara, baya ga wasu ɗaruruwa da ke hannun su a jihohi da dama, a daidai lokacin da gwamnoni da ƴan majalisun yankin suka mayar da hankali a kan siyasa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Bello Bada na Jami'ar Usman Dan Fodio da ke Sokoto. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana...........
Kotu a Najeriya yau ta ci gaba da sauraron shari'ar neman hana tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan tsayawa takarar zabe mai zuwa, kwana guda bayan wasu tarin magoya bayan sa sun bukaci ya shiga zaben mai zuwa. Dangane da matsayin dokar zabe a kan takarar ta Jonathan masanin shari'a, Farfesa Shehu Abdullahi Zuru na Jami'ar Baze dake Abuja, ya mana tsokaci a kai yayin zantawarsa da Bashir Ibrahim Idris. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...
Wasu daga cikin Ƴan Majalisun Dattawan Najeriya sun buƙaci ɗaukar matakai maus tsauri a kan Afirka ta Kudu, ciki harda kwace lasisin kamfanonin su na MTN da DSTV saboda yadda ake kai wa ƴan ƙasar hari ake kuma kashe su. Majalisar ta yanke hukuncin tura tawaga Afirka ta Kudu domin tattaunawa da hukumomin ƙasar, yayin da shi ma bangaren gwamnati ya tura ministan harkokin waje. Ambasada Ibrahim Kazaure, tsohon Jakadan Najeriya a Saudi Arabia ya yi tsokaci a kai, a tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris.
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake jaddada aniyar sa ta samar da Yan Sandan jihohi domin samar da tsaro. Tinubu ya bayyana haka ne yayin ganawa da masu ruwa da tsaki na jihar Filato mai fama da tashin hankalin. Alhaji Isa Tafida Mafindi, wanda ya wallafa littafi a kan samar da Yan Sandan jihohi ya mana tsokaci a kai, yayin tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...
Yan Najeriya na cigaba da bayyana fargaba dangane da makomar ƴan adawar ƙasar dangane da zabe mai zuwa , la'akari da cewar akasarin jami'iyyun adawar na fama da rikice-rikicen da ka iya hana su takara. Akan wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Alhaji Kabir Muhammad Baba, ɗan siyasa a jihar Bauchi. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar......
Yayin da aka cika shekaru uku da fara yaƙin basasar ƙasar Sudan, Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla mutane miliyan 14 suka bar muhallansu, baya ga daruruwan da suka rasa rayukan su. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Abdulkadir Suleiman Muhammed na Jami'ar Abuja, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya fara ziyarar aiki a Birtaniya inda ya samu kyakkyawar tarba daga hukumomin ƙasar. Wannan ziyara na zuwa ne a dai dai lokacin da Najeriyar ke fuskantar matsalolin tsaro iri-iri. Dangane da ziyarar ta Tinubu da kuma alfanunta ga ƙasar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai taimakawa shugaban kan harkokin tsaro Malam Abdulaziz Abdulaziz kuma ga yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
A baya-bayan nan ƙungiyar ta'addanci ta Boko Haram ta tsananta kai hare-hare jihar Borno da maƙwabtanta wanda ya sabbaba asarar ɗimbin rayuka kama daga na jami'an tsaro da kuma fararen hula. Kafin yanzu anga lafawar hare-haren ƙungiyar, sai dai a baya-bayan nan ta dawo da hare-hare ba ƙaƙƙautawa inda ko a tsakanin ranakun Lahadi zuwa yau Talata ta kashe mutane da dama a jihar ta Borno wadda ta shafe shekaru aƙalla 17 tana fama da matsalolin tsaro. Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tsaro Dakta Yahuza Ahmed Getso. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Ana saran Najeriya ta shiga cikin jerin ƙasashen da za su amfana da yaƙin Iran wajen samun maƙudan kuɗaɗe ta hanyar cinikin man fetur da ake nema ruwa a jallo. Sai dai masana na bayyana cewar wasu matsalolin cikin gida na iya rage tasirin samun kuɗaɗen da ake hasashe. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Bashir Ibrahim Idris da DR. Kasim Garba Kurfi, masanin tattalin.......
Ƙungiyar agaji ta ICRC ta ce aƙalla yara ƙanana da ke ƙasa da shekaru 5 miliyan 6 da dubu 400 ke fama da tamowa a yankunan arewa maso gabashin Najeriya da ya kwashe shekaru 15 ya na fama da rikice rikicen Boko Haram da arewa maso yamma da ke fama da rikicin ƴan bindiga, sai kuma arewa ta tsakiya da ke fama da rikicin manoma da makiyaya. Mai magana da yawun ƙungiyar Usman Kundili Bukar ya bayyana haka a tattaunarsa da Bashir Ibrahim Idris. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu.......
Ƙasashen duniya sun fara jin raɗaɗin yaƙin Iran sakamakon tashin farashin man fetur a kasuwannin duniya, wanda ya shafi harkokin yau da kullum. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Isa Abdullahi, masanin tattalin arziki a kan lamarin, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya maye gurbin Engr Faruk Ahmed da Aliko Dangote ya zarga da hana ruwa gudu wajen harkokin kula da kasuwancin mai da kuma bada lasisi ta NMDPRA, tare da shugaban hukumar NUPRC. Fadar shugaban Najeriya ta ce jami'an biyu sun sauka daga mukaman su ne bisa dalilai na ƙashin kan su. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ibrahim Garba Wala kan lamarin. Ku latsa alamar sauti don jin yadda tattaunawarsu ta gudana...
Ƙasashen AES da suka hada da Mali da Nijar da kuma Burkina Faso, sun ƙalubalanci Najeriya sakamakon saukar gaggawar da jirgin sojin ta da ya yi a Burkina. Waɗannan ƙasashe na zargin Najeriya da keta haddin sararin samaniyar yankin su. Domin tattauna wannan batu da kuma yunkurin juyin mulkin da ya gudana a Benin, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Amb Abubakar Cika, tsohon Jakadan Najeriya a Iran. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana...........
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya jinjinawa sojojin ƙasar saboda rawar da suka taka wajen murkushe yunkurin juyin mulkin da aka samu a Jamhuriyar Benin. Tinubu ya ce hare haren sojin sama da kuma tura sojojin ƙasa cikin ƙasar, sun bada gagarumar gudumawa wajen kawar da sojojin da suka sanar da kwace ikon. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Air Commodore Tijjani Baba Gamawa mai ritaya. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu................
Babban Bankin Najeriya ya sanar da cire shingen kuɗaɗen da jama'a ke ajiyewa a bankuna da kuma ƙara yawan kuɗin da ake ɗauka a bankin. Bankin ya ce daga yanzu an ƙara yawan kuɗin da mutum ka iya cirewa daga naira 100,000 zuwa naira 500,000, yayin da bankin ya ci gaba da riƙe naira N100,000 a matsayin kuɗin da mutum guda ka iya cirewa a ATM a rana guda. Domin duba tasirin wannan mataki, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki Dakta Isa Abdullahi, na Jami'ar Kashere, da ke jihar Gombe a Najeriya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Ƴan Najeriya na ci gaba da neman bayani a kan yadda wasu kuɗaɗen da aka tara, da yawan su ya kai dala miliyan 30 domin samar da tsaro a makarantu suka shiga, sakamakon sake dawowar satar ɗalibai a yankin arewacin ƙasar. A ƙarƙashin wannan shirin da ya fara a shekarar 2014, kasashe da dama suka tallafawa Najeriya, cikin su har da ƙasar Norway da ta bada dala miliyan guda, da wata dala miliyan guda daga Bankin Raya ƙasashen Afirka na AfDB, sai kuma Fam miliyan guda daga gwamnatin Birtaniya. Gwamnatin Switzerland ta bada taimakon dala miliyan takwas, yayin da Amurka ta bada dala miliyan biyu, sai kuma Qatar da ta bada dala miliyan biyu, yayin da ƴan kasuwan Najeriya su kuma suka bada taimakon dala miliyan 10. Ganin yadda aka kasa samar da tsaron a makarantu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Abubakar sadiq Umar Gombe. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatar da sunan Janar Christopher Musa mai ritaya ga majalisar Dattawa domin amincewar ta ya zama ministan tsaro. Christopher Musa ya yi aiki a matsayin babban hafsan tsaron Najeriya daga ranar 23 ga watan Yunin 2023 zuwa 30 ga watan Octoban 2025, lokacin da shugaban ƙasar Bola Ahmad Tinubu ya yi masa ritaya. Idan majalisa ta amince, Janar Musa zai maye gurbin Badaru Abubakar da ya yi murabus a ranar Litinin. Bayanai sun nuna cewa fannonin da Musa ya fi ƙwarewa a kai shine fatattarkar ƴan ta'adda, da dubarun yaƙi, kasancewar ya yi aiki a matsayin jagoran rundunar sojojin Najeriya da ke kula da tsaron iyakokin Najeriya ta arewa maso gabashi da kuma yankin tafkin Chadi, haka nan ya kuma yi aiki a matsayin guda daga cikin dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya a Sierra Leone, da kuma wasu ayyukan a Amurka da Majalisar Ɗinkin Duniya.. Domin sanin tasirin wannan nadin da kuma kalubalen dake gaban Janar Musa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon kakakin rundunar sojin kasa ta Najeria, Janar Sani Usman Kukasheka mai ritaya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
A jiya ne sojoji suka hambarar da gwamnatin shugaba Umaro Sissiko Embalo, sakamakon rikicin zaɓen shugaban ƙasar da aka yi a ƙarshen mako, a daidai lokacin da ake shirin gabatar da sakamako yau Alhamis. Shugaban da madugun yan adawa duk sun yi iƙrarin nasara, a kasar da ta yi ƙaurin suna wajen juyin mulki. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Tukur Abdulkadir dangane da juyin mulkin, wanda shi ne na biyar a kasashen Afirka ta Yamma, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.
Gwamnatocin wasu jihohin dake arewacin Najeriya sun sanar da matakan rufe makarantun firamare da sakandare, wasu ma harda jami'oi, domin kaucewa matsalar garkuwa da daliban da ake samu, wanda ya kara ta'azzara a kasar. Domin duba tasirin matakin da kuma halin da yankin ya samu kan sa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Bello Bada na Jami'ar Usman Dan Fodio dake Sokoto. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bada umarnin ɗaukar sabbin ƴansanda dubu 30 da kuma janye masu gadin manyan mutane ba bisa ƙa'ida ba. Domin sanin tasirin wannan mataki da kuma yadda zai taimaka wajen inganta tsaro a ƙasar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon mataimakin Sifeto Janar na Ƴansandan Najeriya Malam Ahmad Abdurrahaman. Ku latsa alamar sauti donjin yadda zantawarsu ta gudana.............
Ƙungiyar Amnesty International ta zargi hukumomin ƙasar Chadi da gazawa wajen ɗaukar matakan kare mutanen da ake cin zarafin su, sakamakon rikici tsakanin manoma da makiyaya a ƙasar, yayin da ta ce tsakanin shekarar 2022 zuwa 2024, an kashe mutane 98, baya ga jikkata sama da 100 da kuma tilastawa ɗaruruwan iyalai barin muhallin su. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Isa Sanusi Daraktan kungiyar a Najeriya, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.
Fatan Najeriya na samun gurbi a gasar cin kofin duniyar da za'a yi a shekara mai zuwa ya gushe, sakamakon rashin nasarar da ƙungiyar Super Eagles ta yi a hannun ƙasar Congo. Wannan shi ne karo na biyu a jere da Najeriya ba zata je gasar ta dunitya ba, bayan gaza zuwa Qatar shekaru 4 da suka gabata, kafin wannan karo. Bashir Ibrahim Idris, ya tattauna da tsohon sakatare janar na Hukumar Kwallon Kafa Najeriya, Hon Sani Ahmad Toro game da wannan koma baya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana a kai.
Shugaban kwamitin shirya babban taron Jam'iyyar PDP na ƙasa a birnin Ibadan dake Najeriya, Umar Fintiri, wanda shi ne Gwamnan Adamawa, ya ce babu abinda zai hana su gudanar da taron da suka shirya gobe asabar. Fintiri ya bayyana haka ne bayan wani gagarumin taron da masu ruwa da tsaki na jam'iyyar da suka gudanar yau a birnin Abuja. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hon Hamisu Mu'azu Shira, ɗaya daga cikin jiga jigan jam'iyyar, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana a kai.
An bude traon Majalisar Dinkin Duniya a kan sauyin yanayi da ake kira COP 30 a Brazil inda masana muhalli da sauyin yanayi daga kasashen duniya da kuma kungiyoyin kare muhallin ke halarta a kasar Brazil. Za'a kwashe makwanni biyu ana gudanar da wannan taro wanda zai mayar da hankali a kan ci gaba ko akasin haka da aka samu a kan wannan matsala. Dakta Abubakar Ibrahim, Malami kuma mai bincike a Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria ya yi tsokaci a kan matsalar musamman ganin irin illar da take yi a yankin arewacin Najeriya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawarsa da Bashir Ibrahim Idris.
Yayin da ake ci gaba da lalubo hanyar warware matsalar barazanar Donald Trump na kai hari Najeriya, wasu masana na bayyana cewar ta hanyar diflomasiya kawai za a iya warware wannan dambarwa. Barr Abdullahi Ibrahim Jalo na ɗaya daga cikin su. Ku latsa alamar sauti don sauraron yadda tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris ta gudana..............
Yayin da hukumomin Najeriya suka yi watsi da barazanar shugaban Amurka na kai wa ƙasar hari saboda zargin kashe Kiristoci, ƴan kasar da dama na ci gaba da bayyana ra'ayi a kan matsayin na shugaba Donald Trump. Daga cikin waɗanda suka bayyana ra'ayin su a kan wannan barazana har da tsohon Jakadan Najeriya a ƙasar Iran, Ambasada Abubakar Cika, kamar yadda za ku ji a tattaunawarsu da Bashir Ibrahim Idris.
A Najeriya, babban abin da ya fi ci wa al'ummar yankin Arewacin ƙasar tuwo a ƙwarya ita ce matsalar rashin tsaro, inda hare-haren ƴanbindiga ke ci gaba da haddasa asarar rayukan jama'a, da gurgunta harkar noma da kuma kasuwanci a yankin baki-ɗayansa. Dangane da haka ne Bashir Ibrahim Idris ya zanta da ɗaya daga cikin dattawan yankin Alhaji Shehu Ashaka, ga kuma yadda zantawarsu ta kasance. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
Har yanzu ana ci gaba da zaman ɗar-ɗar a ƙasar Kamaru sakamakon tashin hankalin da ya biyo bayan zaɓen shugaban ƙasar da aka bayyana shugaba Paul Biya a matsayin wanda ya samu nasara. Shugaban 'yan adawa Issa Tchiroma Bakary da ya zo na biyu ya ƙi amincewa da sakamakon, inda ya buƙaci jama'a da su sake fitowa zanga zanga a ranakun litinin da Talata da kuma Laraba na makon gobe, yayin da a ɓangare ɗaya gwamnati ke barazanar ladabtar da duk wanda ya saɓa dokokin ƙasar, ciki harda shi Isa Tchiroma. Domin tattauna halin da ake ciki a ƙasar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon Jakadan Kamaru a Faransa, Ambasada Muhammadu Sani. Ku alatsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...
Yayin da ake shirin fara taron sauyin yanayi na duniya da ake kira COP30 a Brazil, a ranar 10 ga watan gobe, ƙungiyar OXFAM ta fitar da sanarwa inda take sake bayyana damuwa a kan rashin ɗaukar kwararan matakai wajen aiwatar da yarjejeniyar da aka ƙulla shekaru 10 da suka gabata a birnin Paris. Game da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da darakatar ƙungiyar ta OXFAM a Nahiyar Afrika Malama Fatima Nzi Hassan. Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar.
Ga alama yajejeniyar tsagaita wutar da Isra'ila ta ƙulla tsakaninta da Hamas, wadda Amurka ta tsara ta kama hanyar rugujewa, sakamakon umarnin da Firaminista Benjamin netanyahu ya bayar na ƙaddamar da sabbin hare-hare a Gaza. Wannan ya biyo bayan abinda ya kira ƙin bada gawarwakin sauran Yahudawan da Hamas ta yi garkuwa da su. Domin tattauna wannan dambarwa, Bashir Ibrahim Idris, ya tuntuɓi Dakta Abdulhakin Garba Funtua, mai sharhi a kan harkokin Gabas ta Tsakiya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.........................
Katafaren kamfanin Dangote, ya sanar da shirin faɗaɗa matatar sa mai samar da tacaccen gangar mai 650,000 zuwa miliyan guda da 400,000 a kowacce rana. Shugaban rukunin kamfanin Dangote Alhaji Aliko Dangote ya ce za'a kwashe shekaru uku ana aikin faɗaɗa matatar wadda ya ce za ta zama mafi girma a duniya. Dangane da wannan ci gaba ne kuma Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da babbar manajar rukunonin kamfanin, Fatima Aliko Dangote. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.....
Sannu a hankali ƙananan bankuna na bada gagarumar gudumawa wajen ci gaban tattalin arzikin Najeriya, la'akari da yadda jama'a ke komawa hada hada da su maimakon manyan bankunan da aka sani a baya. Ko a jiya Moniepoint ya sanar da samun jarin Dala miliyan 200 domin inganta harkokin sa. Domin sanin tasirin wadannan ƙananan bankunan, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki, Dr Isa Abdullahi na Jami'ar Kashere. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana..................
Babbar Cibiyar rundinonin sojin Najeriya ta yi watsi da rahotannin dake cewa an yi yunkurin juyin mulkin a kasar, abinda ya kai ga kama wasu hafsoshi guda 16. Daraktan yada labaran Cibiyar janar Tukur Gusau ya shaidawa Bashir Ibrahim Idris a zantawarsu cewar, sojojin da aka kama ana tuhumar su ne da laifin saba dokoki na soji amma ba juyin mulki ba. Ga yadda zantawarsu ta gudana.
Ƙungiyar Amnesty International a Najeriya ta shirya wani taro a Lagos domin horar da matasa a kan yadda za su kare haƙƙoƙin jama'a a yankunan da suka fito.Taron wanda zai gudana a shiyoyin Najeriya guda 6 ya ƙunshi matasa daga shiyar kudu maso yammacin kasar. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Daraktan ƙungiyar a Najeriya, Malam Isa Sanusi. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.............
Jiga-jigan Jam'iyyun adawa a Najeriya da suka haɗa da gwamnoni da ƴan majalisun tarayya da na jihohi na rige-rigen komawa jam'iyya mai mulki ta APC. Na baya-bayan nan da ya koma jam'iyyar ta APC shi ne gwamnan jihar Bayelsa yayinda na Taraba ke kan hanya, kan hakan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar PDP na ƙasa Ambasada Ibrahim Kazaure akan wannan lamari ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.......
Kwamitin Majalisun Najeriya da ke yiwa kundin tsarin mulki gyaran fuska ya bada shawarar sake dokar zaɓe ta yadda za a dinga gudanar da zaɓuɓɓuka a watan Nuwamba domin bada damar kammala shari'u kafin lokacin rantsar da waɗanda suka samu nasara. Domin sanin tasirin wannan shiri, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abbati Baƙo mai sharhin kan harkokin siyasa ga kuma yadda tattaunawarsu ta kasance. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar....
Malaman Jami'o'in Najeriya sun kare matakin ƙungiyarsu na tsunduma yajin aikin gargaɗi na makwanni 2, inda suka zargi gwamnati da yaradara. Wannan kuwa na zuwa ne duk da gargaɗin da gwamnatin ƙasar ta yi na amfani da dokar nan ta babu aiki babu biya duk malamin da ya shiga yajin aiki na ASUU. Shugaban ƙungiyar Malaman reshen Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria, Farfesa Haruna Jibril ya yiwa Bashir Ibrahim Idris ƙarin bayani a tattaunawar da suka yi kamar haka... Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....
Ƴan Najeriya na ci gaba da bayyana ra'ayoyi dangane da wasu daga cikin mutanen da shugaban ƙasar Bola Tinubu ya yiwa afuwa a makon jiya, inda suke bayyana rashin dacewar afuwar da akan wasu waɗanda suka aikata manya laifuka. Daga cikin waɗanda ake muhawara a kan su akwai masu kisan kai da masu safarar ƙwayoyi da kuma masu safarar makamai. Domin tattauna wannan batu Bashir Ibrahim Idris, ya zanta da Ibrahim Garba Wala, guda cikin masu fafutukar kare haƙƙin Bil'Adama a Najeriya.......... Latsa alamar sauti domin sauraron zantawarsu................
A ƙarshen wannan mako ne jama'ar ƙasar Kamaru za su kaɗa kuri'a a zaɓen shugaban ƙasa, inda ƴan takara 10 ke neman shugabanci, cikin su harda shugaba Paul Biya dake neman wa'adi na 8. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon Jakadan Kamaru a Faransa, Ambasada Muhammad Sani game da zaɓen. Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawarsu...
Rundunar Ƴansandan Najeriya ta sanar da karɓar umarnin kotu na dakatar da kama motocin dake ɗauke da bakin gilashi, inda ta umarci jami'an ta da su dakatar da kamen har zuwa lokacin da za'a kammala shari'ar. Wannan ya biyo bayan rugawa kotu da wasu lauyoyi suka yi domin hana aiwatar da dokar da suka ce za ta take haƙƙin Bil Adama. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Barr Suleiman Muhammed, lauya mai zaman kansa. Ku latsa alamar sauti domin jin tattaunawarsu...
Shugaban Hukumar zaɓen Najeriya Farfesa Mahmood Yakubu ya kawo ƙarshen aikin sa a INEC, inda ya miƙa ragamar tafiyar da hukumar ga May Agbamuche.Yayin miƙa ragamar aikin, Yakubu ya roƙi kwamishinonin hukumar da su bai wa Agbamuche haɗin kai wajen gudanar da ayyukan ta na riƙo zuwa lokacin da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai naɗa wanda zai maye gurbinsa.Tuni dai tambayoyi suka yawaita game da wanda zai maye gurbin Yabubu a matsayin shugaban hukumar ta INEC, dangane da wannan batu Bashir Ibrahim Idris ya tattaunawa da Malam Ibrahim Garba Wala. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar..........
Yau ake cika shekaru biyu cif da ƙazamin harin da Mayaƙan Hamas suka kai Isra'ila wanya ya hallaka Yahudawa fiye da dubu guda sanadiyyarsa ne kuma aka faro wannan yaƙi na Gaza da ya kashe Falasɗinawa fiye da dubu 60. Wannan yaƙi shi ne mafi muni da duniya ta gani a wannan ƙarnin wanda ya rushe fiye da kashi 90 na gine-ginen yankin. Dangane da wannan ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin siyasar ƙasashe don jin tasirin wannan yaƙi ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar...
Yayin da ake ci gaba da tsokaci a kan matsalolin da suka shafi matatar Dangote da ƙungiyar PENGASSAN, wani hamshaƙin Dan kasuwa, Alhaji Abdulsalam Abdulkarim Zaura, ya buƙaci gwamnatin Najeriya da ta shiga lamarin domin kawo ƙarshensa. Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawarsa da Bashir Ibrahim Idris....
Matsalar cin hanci da rashawa na ci gaba da yiwa Najeriya illa a ɓangarori daban-daban, lamarin da ke haifar da tarnaki wajen ci gaban ƙasar. A yayinda manazarta ke ci gaba da sharhi kan ci gaban da wannan ƙasa ta yammacin Afrika ta samu cikin shekaru 65 da samun ƴancin kai daga Ingila da kuma irin matsalolin da suka dabaibaye wannan ƙasa. Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon shugaban hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC a ƙasar Abdurrashid Bawa. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawarsu.