Bakonmu a Yau

Follow Bakonmu a Yau
Share on
Copy link to clipboard

A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban…

Rfi - Azima Bashir Aminu


    • Nov 17, 2025 LATEST EPISODE
    • weekdays NEW EPISODES
    • 3m AVG DURATION
    • 1,028 EPISODES


    Search for episodes from Bakonmu a Yau with a specific topic:

    Latest episodes from Bakonmu a Yau

    Sanata Bala Mohammad kan zaɓen sabbin shugabannin jam'iyar PDP a matakin ƙasa

    Play Episode Listen Later Nov 17, 2025 3:44


    Babbar jam'iyyar adawa a Najeriya, PDP ta gudanar da babban taronta na ƙasa a birnin Ibadan na jihar Oyo da ke yankin Kudu maso yammacin ƙasar, inda ta zaɓi sabbin shugabanninta a matakin ƙasa. Jam'iyyar ta ɗauki tsauraran matakai yayin taron mai cike da cece-kuce, ciki harda korar wasu manyan jiga-jiganta da suka haɗa da ministan Abuja Nyesom Wike da wasu ƙarin mutum 10. A tataunawarsa da Ahmad Abba, gwamnan jihar Bauchi kuma shugaban gwamnonin PDP, Sanata Abdulkadir Bala Mohammad, ya ce umurnin kotu suka bi wajen gudanar da wannan taro kuma sun samu nasara. Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawar tasu............

    Hon Hamisu Mu'azu Shira kan dambarwar da ke tattare da babban taron jam'iyyar PDP

    Play Episode Listen Later Nov 14, 2025 3:47


    Shugaban kwamitin shirya babban taron Jam'iyyar PDP na ƙasa a birnin Ibadan dake Najeriya, Umar Fintiri, wanda shi ne Gwamnan Adamawa, ya ce babu abinda zai hana su gudanar da taron da suka shirya gobe asabar. Fintiri ya bayyana haka ne bayan wani gagarumin taron da masu ruwa da tsaki na jam'iyyar da suka gudanar yau a birnin Abuja. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hon Hamisu Mu'azu Shira, ɗaya daga cikin jiga jigan jam'iyyar, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana a kai.

    jam shira abuja pdp ibadan taron najeriya shugaban bashir ibrahim idris
    Dr Harbau kan asarar kasuwar hannayen jarin Najeriya mafi muni a shekaru 10

    Play Episode Listen Later Nov 13, 2025 3:32


    Kasuwar hada-hadar hannayen jari ta Najeriya ta tafka hasarar Naira Tiriliyan 4 da Biliyan 600 a ranar Talata, sakamakon matakin da masu linƙaya cikin kasuwar suka ɗauka na sayar da hannayen jarinsu cikin gaggawa saboda dalilai da dama ciki har da tsoron faɗuwa. Hasarar ta fiye da Naira Tiriliyan 4, ita ce mafi muni da kasuwar hannayen jarin Najeriyar ta fuskanta cikin shekaru 10. Domin jin dalilan da suka janyo aukuwar hakan da sauran lamura masu alaƙa, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Aminu Idris Harbau masanin tattalin arziƙi a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar...

    Ba mu taɓa bai wa wani ɗan ta'adda ko anini ba – Malam Uba Sani

    Play Episode Listen Later Nov 12, 2025 3:54


    Dai dai lokacin da wasu jita-jita ke nuna cewa mahukuntan Najeriya kan biya kuɗaɗen fansa ga ƴan bindiga gabanin kuɓutar da ɗimbin mutanen da suke garkuwa dasu, ko kuma ga waɗanda suka aje makamansu a jihohin arewa maso yammacin ƙasar, Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi iƙirarin cewa bai taɓa biyan ko sisin kwabo ga ƴan bindiga ba. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Gwamna Uba Sani da Khamis Saleh................

    Abubakar Ibrahim kan taron sauyin yanayi na COP30 da ke gudana a Brazil

    Play Episode Listen Later Nov 11, 2025 3:37


    An bude traon Majalisar Dinkin Duniya a kan sauyin yanayi da ake kira COP 30 a Brazil inda masana muhalli da sauyin yanayi daga kasashen duniya da kuma kungiyoyin kare muhallin ke halarta a kasar Brazil. Za'a kwashe makwanni biyu ana gudanar da wannan taro wanda zai mayar da hankali a kan ci gaba ko akasin haka da aka samu a kan wannan matsala. Dakta Abubakar Ibrahim, Malami kuma mai bincike a Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria ya yi tsokaci a kan matsalar musamman ganin irin illar da take yi a yankin arewacin Najeriya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawarsa da Bashir Ibrahim Idris.

    brazil cops za taron abubakar shiga najeriya malami majalisar dinkin duniya bashir ibrahim idris
    Gwamnatin Yobe za ta gina sabon asibitin ƙoda a Gashua inda cutar tafi ƙamari

    Play Episode Listen Later Nov 10, 2025 3:21


    Gwamnatin Jihar Yobe dake Najeriya tace za ta ƙara gina manya asibitoci a kananan Hukumomi 3 wadda suka hada da Gashua, Potiskum da kuma Nguru, baya ga gina wani wannan sabon asibitin kula da masu fama da cutar ƙoda a Garin Gashua inda cutar tafi ƙamari a jihar. Haka kuma gwamnatin ta ce zata gina wasu makarantu na musamman a kowacce mazaɓa 178 da ake da su a jihar domin ƙara inganta karatun tun daga tushe. Gwamna Jihar, Mai Mala Buni ne ya bayyana haka a tattaunawarsa da wakilinmu  Bilyaminu Yusuf. Latsa alamar sauti don jin tattaunawarsu....

    Barr Abdullahi Jalo kan ƙoƙarin warware barazanar Trump na kai hari Najeriya

    Play Episode Listen Later Nov 6, 2025 3:37


    Yayin da ake ci gaba da lalubo hanyar warware matsalar barazanar Donald Trump na kai hari Najeriya, wasu masana na bayyana cewar ta hanyar diflomasiya kawai za a iya warware wannan dambarwa. Barr Abdullahi Ibrahim Jalo na ɗaya daga cikin su. Ku latsa alamar sauti don sauraron yadda tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris ta gudana..............

    Shu'aibu Mikati akan tasirin barazanar Trump ga tattali arzikin Najeriya

    Play Episode Listen Later Nov 5, 2025 3:29


    Barazanar Shugaban Amurka Donald Trump kan Najeriya na ci gaba da janyo cecekuce a ƙasar da kuma ƙetare, kuma tuni wannan batu ya fara tasiri a musamman kan tattalin arzikin ƙasar. Faduwar hannayen jarin Najeriya da aka gani a wannan mako, ta janyo hankalin mutane yayin da ake ganin kai tsaye yana da alaƙa da barzanar ta Trump. Rukayya Abba Kabara ta tattauna da kwararre kan harkokin tattalin arziki a Najeriya, Alhaji Shu'aibu Mikati kan wannan batu, ga kuma yadda tattaunawar tasu ta kasance.

    Ambasada Abubakar Cika kan barazanar kai wa Najeriya hari da Amurka ta yi

    Play Episode Listen Later Nov 4, 2025 3:37


    Yayin da hukumomin Najeriya suka yi watsi da barazanar shugaban Amurka na kai wa ƙasar hari saboda zargin kashe Kiristoci, ƴan kasar da dama na ci gaba da bayyana ra'ayi a kan matsayin na shugaba Donald Trump. Daga cikin waɗanda suka bayyana ra'ayin su a kan wannan barazana har da tsohon Jakadan Najeriya a ƙasar Iran, Ambasada Abubakar Cika, kamar yadda za ku ji a tattaunawarsu da Bashir Ibrahim Idris.  

    donald trump iran hari daga abubakar yayin najeriya amurka bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da Alhaji Shehu Ashaka kan matsalolin tsaro a arewacin Najeriya

    Play Episode Listen Later Nov 3, 2025 3:25


    A Najeriya, babban abin da ya fi ci wa al'ummar yankin Arewacin ƙasar tuwo a ƙwarya ita ce matsalar rashin tsaro, inda hare-haren ƴanbindiga ke ci gaba da haddasa asarar rayukan jama'a, da gurgunta harkar noma da kuma kasuwanci a yankin baki-ɗayansa. Dangane da haka ne Bashir Ibrahim Idris ya zanta da ɗaya daga cikin dattawan yankin Alhaji Shehu Ashaka, ga kuma yadda zantawarsu ta kasance. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

    ku najeriya bashir ibrahim idris
    Ambasada Muhammad Sani kan rikicin zaɓen Kamaru

    Play Episode Listen Later Oct 31, 2025 3:39


    Har yanzu ana ci gaba da zaman ɗar-ɗar a ƙasar Kamaru sakamakon tashin hankalin da ya biyo bayan zaɓen shugaban ƙasar da aka bayyana shugaba Paul Biya a matsayin wanda ya samu nasara. Shugaban 'yan adawa Issa Tchiroma Bakary da ya zo na biyu ya ƙi amincewa da sakamakon, inda ya buƙaci jama'a da su sake fitowa zanga zanga a ranakun litinin da Talata da kuma Laraba na makon gobe, yayin da a ɓangare ɗaya gwamnati ke barazanar ladabtar da duk wanda ya saɓa dokokin ƙasar, ciki harda shi Isa Tchiroma. Domin tattauna halin da ake ciki a ƙasar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon Jakadan Kamaru a Faransa, Ambasada Muhammadu Sani. Ku alatsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

    ku domin sani paul biya kamaru talata faransa shugaban bashir ibrahim idris
    Fatima Nzi Hassan kan ta'azzarar sauyin yanayi, yayin da ake gab da fara taron COP30

    Play Episode Listen Later Oct 30, 2025 3:34


    Yayin da ake shirin fara taron sauyin yanayi na duniya da ake kira COP30 a Brazil, a ranar 10 ga watan gobe, ƙungiyar OXFAM ta fitar da sanarwa inda take sake bayyana damuwa a kan rashin ɗaukar kwararan matakai wajen aiwatar da yarjejeniyar da aka ƙulla shekaru 10 da suka gabata a birnin Paris. Game da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da darakatar ƙungiyar ta OXFAM a Nahiyar Afrika Malama Fatima Nzi Hassan. Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar.

    game brazil oxfam taron yayin bashir ibrahim idris
    Dr. Abdulhakim Garba Funtuwa kan dambarwar yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

    Play Episode Listen Later Oct 29, 2025 3:37


    Ga alama yajejeniyar tsagaita wutar da Isra'ila ta ƙulla tsakaninta da Hamas, wadda Amurka ta tsara ta kama hanyar rugujewa, sakamakon umarnin da Firaminista Benjamin netanyahu ya bayar na ƙaddamar da sabbin hare-hare a Gaza. Wannan ya biyo bayan abinda ya kira ƙin bada gawarwakin sauran Yahudawan da Hamas ta yi garkuwa da su. Domin tattauna wannan dambarwa, Bashir Ibrahim Idris, ya tuntuɓi Dakta Abdulhakin Garba Funtua, mai sharhi a kan harkokin Gabas ta Tsakiya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.........................

    ga gaza hamas isra domin garba wannan amurka bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da Muhammad Sani Makigal kan garambawul ɗin Tinubu a ɓangaren tsaro

    Play Episode Listen Later Oct 28, 2025 3:30


    A baya-bayan nan ne, gwamnatin Najeriya ta gudanar wani garambawul ga sha'anin tsaron ƙasar, ciki kuwa har da matakin da shugaba Bola Tinubu ya yi na sauya kusan ilahirin manyan hafsoshin tsaron ƙasar, lamarin da ya janyo cece-kuce. Ra'ayoyi sun mabanbanta game da wannan mataki na garambawul ga ɓangaren na tsaro a Najeriya, inda wasu ke ganin batu ne da ya dace lura da yadda matsalolin tsaro ke ci gaba da ta'azzara, yayinda wasu ke alaƙanta batun da siyasa. A gefe guda, Najeriyar ta gamu da jita-jitar yunƙurin juyin mulki, wanda kuma kwanaki bayan tsanantar jita-jitar shugaban ya gudanar da wannan garambawul, Dangane da hakan ne kuma Michael Kuduson ya tattaunawa da masanin tsaro a ƙasar Muhammad Sani Makigal. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....

    Tattaunawa da Fatima Dangote kan shirin faɗaɗa aikin matatar Ɗangote

    Play Episode Listen Later Oct 27, 2025 3:38


    Katafaren kamfanin Dangote, ya sanar da shirin faɗaɗa matatar sa mai samar da tacaccen gangar mai 650,000 zuwa miliyan guda da 400,000 a kowacce rana.  Shugaban rukunin kamfanin Dangote Alhaji Aliko Dangote ya ce za'a kwashe shekaru uku ana aikin faɗaɗa matatar wadda ya ce za ta zama mafi girma a duniya.  Dangane da wannan ci gaba ne kuma Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da babbar manajar rukunonin kamfanin, Fatima Aliko Dangote. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.....

    ku shirin dangote najeriya shugaban bashir ibrahim idris
    Usman Ture kan zaɓen shugaban ƙasar Cote d'Ivoire na gobe Asabar

    Play Episode Listen Later Oct 24, 2025 3:04


    A Cote d'Ivoire, a jajiberin zaɓen shugaban ƙasar, hukumomi sun ɗauki matakan da suka dace na ganin an gudanar da zaɓen ba tare da an fuskanci wata matsala ba. To domin jin ko a ina aka kwana ,Abdoulaye Issa ya tattauna da Usman Ture,wani ɗan ƙasar ta Cote d'ivoire da ya karɓi katinsa na zaɓe. Latsa alamar sauti domin jin yadda tattaunawarsu ta gudana...

    cote usman ture asar gobe shugaban abdoulaye issa
    Dr Isa Abdullahi kan tasirin ƙananan bankunan a Najeriya

    Play Episode Listen Later Oct 23, 2025 3:32


    Sannu a hankali ƙananan bankuna na bada gagarumar gudumawa wajen ci gaban tattalin arzikin Najeriya, la'akari da yadda jama'a ke komawa hada hada da su maimakon manyan bankunan da aka sani a baya. Ko a jiya Moniepoint ya sanar da samun jarin Dala miliyan 200 domin inganta harkokin sa. Domin sanin tasirin wadannan ƙananan bankunan, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki, Dr Isa Abdullahi na Jami'ar Kashere. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana..................

    ko ku domin dala abdullahi najeriya bashir ibrahim idris
    Sunusi Bature game da taron baje-kolin kafafen yaɗa labarai na-afrika karo na 14

    Play Episode Listen Later Oct 22, 2025 2:43


    An buɗe taron baje kolin kafafen yaɗa labarai na Afrika da ake kira AFRICAST karo 14 a birnin Lagos da ke Najeriya, inda masu ruwa da tsaki a harkar yaɗa labarai daga nahiyar da kuma sassan duniya ke halarta.Domin ƙara inganta ayyukan yaɗa labarai, wasu daga cikin mahalarta wannan taro na ganin cewa ya zama wajibi a samar da dokokin da za su sa-ido kan ayyukan kafafen sada zumunta da kuma sauran hanyoyin yaɗa labarai ta yanar gizo. Sanusi Bature Dawakin Tofa, shi ne mai magana da yawun gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Yusuf, kuma wanda ya wakilce shi a taron, a zantawarsa da Abdoulkarim Ibrahim Shikal, ya ce lalle akwai buƙatar samar da gyara a wannan fanni. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar...................

    game afrika lagos karo domin taron baje kolin najeriya abdoulkarim ibrahim shikal
    Gwamna Dikko Raɗɗa kan shirin bunƙasa lantarki a jihohin Kano da Jigawa da Katsina

    Play Episode Listen Later Oct 21, 2025 3:21


    Gwamnatocin jihohin Katsina da Kano da kuma Jigawa da ke arewa maso yammacin Najeriya sun kulla haɗakar inganta wutar lantarkin ga jihohin uku. Gwamnonin Kano, Jiagwa da Katsina sun shiga yarjejeniyar haɗin gwiwa kan bunƙasa wutar lantarki a jihohin uku da ke arawacin Najeriya, tare da zuba hannun jari a kamfanonin Future Energies Africa (FEA) da na rarraba wutar lantarki a jihohin uku wato KEDCO. Hakan ya fito fili ne bayan wani taro da gwamnonin jihohin uku da suka hada da Malam Umar Dikko Radda da Abba Kabir Yusuf da kuma Umar Namadi suka gudanar a ƙasar Morocco inda suka tattauna da kamfanin Future Energies Africa da Kedco da sauran masu ruwa da tsaki a harkar makamashi. A zantawarsa da RFI Hausa, Gwamnan jihar Katsina Malama Dikko Rada ya ce suna son fito da haryar yin haɗaka a fannin wutar lantarki tsakanin jihohin makwabtan juna ta hanyar zuba jari naira biliyan 50 domin samar da wutar da yankin ke bukata. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar................

    Birgediya Tukur Gusau akan jita-jitar yunƙurin juyin mulki a Najeriya

    Play Episode Listen Later Oct 20, 2025 3:08


    Babbar Cibiyar rundinonin sojin Najeriya ta yi watsi da rahotannin dake cewa an yi yunkurin juyin mulkin a kasar, abinda ya kai ga kama wasu hafsoshi guda 16. Daraktan yada labaran Cibiyar janar Tukur Gusau ya shaidawa Bashir Ibrahim Idris a zantawarsu cewar, sojojin da aka kama ana tuhumar su ne da laifin saba dokoki na soji amma ba juyin mulki ba. Ga yadda zantawarsu ta gudana. 

    ga akan urin najeriya jita bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da Isah Sunusi kan horon da Amnesty ta baiwa matasa a Najeriya

    Play Episode Listen Later Oct 17, 2025 3:39


    Ƙungiyar Amnesty International a Najeriya ta shirya wani taro a Lagos domin horar da matasa a kan yadda za su kare haƙƙoƙin jama'a a yankunan da suka fito.Taron wanda zai gudana a shiyoyin Najeriya guda 6 ya ƙunshi matasa daga shiyar kudu maso yammacin kasar. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Daraktan ƙungiyar a Najeriya, Malam Isa Sanusi. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.............

    lagos amnesty international amnesty taron isah najeriya matasa bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da Ambasada Ibrahim Kazaure kan zauya sheƙar wasu ƴan siyasa zuwa APC

    Play Episode Listen Later Oct 16, 2025 3:25


    Jiga-jigan Jam'iyyun adawa a Najeriya da suka haɗa da gwamnoni da ƴan majalisun tarayya da na jihohi na rige-rigen komawa jam'iyya mai mulki ta APC. Na baya-bayan nan da ya koma jam'iyyar ta APC shi ne gwamnan jihar Bayelsa yayinda na Taraba ke kan hanya, kan hakan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar PDP na ƙasa Ambasada Ibrahim Kazaure akan wannan lamari ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.......

    jam ku apc pdp taraba wasu bayelsa najeriya bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da Dr Abbati Bako game da buƙatar sauya lokacin zaɓe a Najeriya

    Play Episode Listen Later Oct 15, 2025 3:25


    Kwamitin Majalisun Najeriya da ke yiwa kundin tsarin mulki gyaran fuska ya bada shawarar sake dokar zaɓe ta yadda za a dinga gudanar da zaɓuɓɓuka a watan Nuwamba domin bada damar kammala shari'u kafin lokacin rantsar da waɗanda suka samu nasara. Domin sanin tasirin wannan shiri, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abbati Baƙo mai sharhin kan harkokin siyasa ga kuma yadda tattaunawarsu ta kasance. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar....

    game ku domin atar bako najeriya nuwamba bashir ibrahim idris
    Farfesa Haruna Jibril kan dalilan da suka tilasta ASUU tsunduma yajin aiki

    Play Episode Listen Later Oct 14, 2025 3:39


    Malaman Jami'o'in Najeriya sun kare matakin ƙungiyarsu na tsunduma yajin aikin gargaɗi na makwanni 2, inda suka zargi gwamnati da yaradara. Wannan kuwa na zuwa ne duk da gargaɗin da gwamnatin ƙasar ta yi na amfani da dokar nan ta babu aiki babu biya duk malamin da ya shiga yajin aiki na ASUU. Shugaban ƙungiyar Malaman reshen Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria, Farfesa Haruna Jibril ya yiwa Bashir Ibrahim Idris ƙarin bayani a tattaunawar da suka yi kamar haka... Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....

    ku suka jibril haruna asuu aiki wannan najeriya shugaban bashir ibrahim idris
    Malam Ibrahim Garba Wala game da afuwar Tunubu ga wasu Fursunoni

    Play Episode Listen Later Oct 13, 2025 3:29


    Ƴan Najeriya na ci gaba da bayyana ra'ayoyi dangane da wasu daga cikin mutanen da shugaban ƙasar Bola Tinubu ya yiwa afuwa a makon jiya, inda suke bayyana rashin dacewar afuwar da akan wasu waɗanda suka aikata manya laifuka. Daga cikin waɗanda ake muhawara a kan su akwai masu kisan kai da masu safarar ƙwayoyi da kuma masu safarar makamai. Domin tattauna wannan batu Bashir Ibrahim Idris, ya zanta da Ibrahim Garba Wala, guda cikin masu fafutukar kare haƙƙin Bil'Adama a Najeriya.......... Latsa alamar sauti domin sauraron zantawarsu................

    Tsohon Jakadan Kamaru a Faransa Ambasada Muhd kan zaɓen ƙasar ta Afrika

    Play Episode Listen Later Oct 10, 2025 3:32


    A ƙarshen wannan mako ne jama'ar ƙasar Kamaru za su kaɗa kuri'a a zaɓen shugaban ƙasa, inda ƴan takara 10 ke neman shugabanci, cikin su harda shugaba Paul Biya dake neman wa'adi na 8. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon Jakadan Kamaru a Faransa, Ambasada Muhammad Sani game da zaɓen. Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawarsu...

    afrika asar paul biya kamaru faransa bashir ibrahim idris
    Najeriya: 'Yansanda sun karɓi umarnin kotu na dena kama masu baƙi gilashin mota

    Play Episode Listen Later Oct 9, 2025 3:29


    Rundunar Ƴansandan Najeriya ta sanar da karɓar umarnin kotu na dakatar da kama motocin dake ɗauke da bakin gilashi, inda ta umarci jami'an ta da su dakatar da kamen har zuwa lokacin da za'a kammala shari'ar. Wannan ya biyo bayan rugawa kotu da wasu lauyoyi suka yi domin hana aiwatar da dokar da suka ce za ta take haƙƙin Bil Adama. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Barr Suleiman Muhammed, lauya mai zaman kansa. Ku latsa alamar sauti domin jin tattaunawarsu...

    ku mota kama masu kotu wannan najeriya bashir ibrahim idris
    Malam Ibrahim Garba Wala game da wanda ya dace ya maye gurbin Yakubu a INEC

    Play Episode Listen Later Oct 8, 2025 3:36


    Shugaban Hukumar zaɓen Najeriya Farfesa Mahmood Yakubu ya kawo ƙarshen aikin sa a INEC, inda ya miƙa ragamar tafiyar da hukumar ga May Agbamuche.Yayin miƙa ragamar aikin, Yakubu ya roƙi kwamishinonin hukumar da su bai wa Agbamuche haɗin kai wajen gudanar da ayyukan ta na riƙo zuwa lokacin da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai naɗa wanda zai maye gurbinsa.Tuni dai tambayoyi suka yawaita game da wanda zai maye gurbin Yabubu a matsayin shugaban hukumar ta INEC, dangane da wannan batu Bashir Ibrahim Idris ya tattaunawa da Malam Ibrahim Garba Wala. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar..........

    Tattaunawa da Abdulhakeem Garba Funtua kan cika shekaru 2 da yaƙin Gaza

    Play Episode Listen Later Oct 7, 2025 3:31


    Yau ake cika shekaru biyu cif da ƙazamin harin da Mayaƙan Hamas suka kai Isra'ila wanya ya hallaka Yahudawa fiye da dubu guda sanadiyyarsa ne kuma aka faro wannan yaƙi na Gaza da ya kashe Falasɗinawa fiye da dubu 60. Wannan yaƙi shi ne mafi muni da duniya ta gani a wannan ƙarnin wanda ya rushe fiye da kashi 90 na gine-ginen yankin. Dangane da wannan ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin siyasar ƙasashe don jin tasirin wannan yaƙi ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar...

    Tattaunawa da Alhaji Ouba Danlami game da babban zaɓen Kamaru

    Play Episode Listen Later Oct 6, 2025 3:38


    A Kamaru ana ci gaba da yaƙin neman zaɓen shugabancin ƙasar wanda za a gudanar ranar lahadi mai zuwa 12 ga wannan wata na Oktoba, inda ƴantakara 10 ke shirin fafatawa ciki har da shugaba mai-ci Paul Biya. Akwai dai waɗanda suka janye daga zaɓen don mara wa wasu ƴantakarar duk da cewa an tantance su, yayin da wasu suka yanke shawarar mara wa wasu ƴantakarar haka kawai saboda wasu dalilai. Alhaji Ouba Danlami, ya sha tsayawa takarar shugabancin  ƙasar a zaɓukan da suka gabata, to amma ban da wannan karo, ko saboda? Ga ƙarin bayanin da ya yi wa Ahmed Abba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar..

    Tattaunawa da AA Zaura kan rikicin matatar Dangote da PENGASSAN

    Play Episode Listen Later Oct 4, 2025 3:21


    Yayin da ake ci gaba da tsokaci a kan matsalolin da suka shafi matatar Dangote da ƙungiyar PENGASSAN, wani hamshaƙin Dan kasuwa, Alhaji Abdulsalam Abdulkarim Zaura, ya buƙaci gwamnatin Najeriya da ta shiga lamarin domin kawo ƙarshensa. Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawarsa da Bashir Ibrahim Idris....

    dangote yayin najeriya bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da tsohon shugaban EFCC Abdurrashid Bawa kan rashawa a Najeriya

    Play Episode Listen Later Oct 2, 2025 3:33


    Matsalar cin hanci da rashawa na ci gaba da yiwa Najeriya illa a ɓangarori daban-daban, lamarin da ke haifar da tarnaki wajen ci gaban ƙasar. A yayinda manazarta ke ci gaba da sharhi kan ci gaban da wannan ƙasa ta yammacin Afrika ta samu cikin shekaru 65 da samun ƴancin kai daga Ingila da kuma irin matsalolin da suka dabaibaye wannan ƙasa. Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon shugaban hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC a ƙasar Abdurrashid Bawa. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawarsu.

    afrika ku bawa efcc najeriya shugaban bashir ibrahim idris ingila
    Atiku Abubakar akan cikar Najeriya shekaru 65 da samun 'yancin kai

    Play Episode Listen Later Oct 1, 2025 3:49


    Yau Najeriya ke bikin cika shekaru 65 da samun yancin kai daga Turawan mulkin mallaka na Birtaniya. A irin wannan lokaci akan yi tilawa da kuma nazari dangane da ci gaban da kasar ta samu da kuma kalubalen dake gaban ta. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar dangane da halin da kasar ke ciki, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.

    akan atiku abubakar najeriya birtaniya bashir ibrahim idris
    Dalilan rikici tsakanin Ɗangote da masu ruwa da tsaki a harkar man Najeriya

    Play Episode Listen Later Sep 30, 2025 3:31


    A Najeriya, wani abu da ke neman ɗaure wa jama'a kai shi ne yadda ƙasa da shekara ɗaya da ƙddamar da ayyukanta, matatar mai ta Ɗangote ke fuskantar rigingimu daban daban, da suka haɗa da tsakaninta da dillalan mai masu zaman kansu, da ma'aikatan dakon mai wato NUPENG sai kuma wannan karo da PENGASSAN wato ƙungiyar manyan ma'aikatan mai da iskar gaz na ƙasar. A game da waɗannan rigingimu ne Abdoulkarim Ibrahim Ibrahim Shikal ya zanta da masani harkar mai a ƙasar wato Alhaji Ɗayyabu Yusuf Garga, domin sanin wasu daga cikin dalilan faruwar hakan. Ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

    Tattaunawa da Farfesa Ouba Ali Mahamman masanin siyasa game da zaɓen Kamaru

    Play Episode Listen Later Sep 29, 2025 3:34


    A ƙarshen makon da ya gabata aka fara yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a Kamaru, inda mutane 12 ciki har da shugaba mai-ci Paul Biya za su kara da juna a ranar 12 ga watan gobe na Oktoba idan Allah ya kai mu. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Farfesa Ouba Ali Mahamman, masani siyasar Kamaru da ke zaune a birnin Yaounde, wanda da farko ya bayyana bambancin da ke akwai tsakanin wannan zaɓe da kuma waɗanda aka saba yi shekarun baya a ƙasar. Ga dai abin da yake cewa. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

    Tattaunawa da Dakta Bolori akan rage kudin ruwa da babban bankin Najeriya ya yi

    Play Episode Listen Later Sep 26, 2025 3:33


    Babban bankin Najeriya CBN ya sanar da rage kuɗin ruwan da ake sanyawa masu karɓar bashi daga kaso 27.50 zuwa kaso 27 karon farko cikin shekaru huɗu. Wannan ci gaba na zuwa ne a dai-dai lokacin da hukumar tattara haraji ta Najeriya ke cewa ta sami ƙarin kuɗaɗen shiga da kaso 411%, amma hakan ba zai hana ci gaba da ciyo bashi da Najeriya ke yi ba.   A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara, Dr Ahmad Bolori masanin tattalin arziki a Najeriya ce, ragin kwabo 50 kachal yayi matuƙar kaɗan duk da cewa babu wani abu da talaka zai mora a wannan ci gaba. Ga dai yadda tattaunawar tasu ta kasance.

    Emmanuel Macron kan amincewa da ƙasar Falasɗinu da kuma yakin Ukraine da Rasha

    Play Episode Listen Later Sep 25, 2025 3:13


    Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce ƙasar Rasha ta yi rauni sosai a yaƙin da take gwabzawa da Ukraine. Macron ya bayyana haka ne a zantawa ta musamman da ya yi tashar talabijin ta France24 da Kuma RFI a gefen Babban Taron Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya a birnin New York, inda ya taɓo batutuwa da dama ciki har da amincewa da Palesdinu a matsayin ƙasa da daidai sauransu. Da farko dai Emmanuel Macron ya jinjina wa shugaba Amurka Donald Trump ne a game da ƙoƙarinsa don kawo ƙarshen rikicin Ukraine. Ku latsa alamar sauti don sauraron fassarar kalamansa...............

    Maitre Lirwanou Abdourahman kan ficewar Nijar Mali da Burkina Faso daga ICC

    Play Episode Listen Later Sep 24, 2025 3:32


    Burkina Faso, Mali da kuma Nijar sun sanar da janyewar ƙasashensu daga Kotun Hukunta Laifufuka ta Duniya da ke birnin Hague. A sanarwar haɗin-gwiwa da suka fitar cikin daren litinin da ta gabata, ƙasashen uku sun ce sun ɗauki matakin saboda sun lura cewa kotun ta rikiɗe domin zama ƴar amashin ƴan mulkin mallaka. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani dokokin ƙasa da ƙasa Maitre Lirwanou Abdourahman, domin jin ko wataƙila ya yarda da dalilan da wadannan ƙasashe suka gabatar. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

    mali ku burkina faso hague maitre daga duniya nijar najeriya amurka abdoulkarim ibrahim shikal
    Maitre Lirwanou Abdourahman kan janyewar ƙasashen AES daga kotun ICC

    Play Episode Listen Later Sep 24, 2025 3:32


    Burkina Faso da Mali da kuma Nijar sun sanar da janyewar ƙasashensu daga Kotun Hukunta Laifufuka ta Duniya da ke birnin Hague. A sanarwar haɗin-gwiwa da suka fitar cikin daren Litinin da ta gabata, ƙasashen uku sun ce sun ɗauki matakin ne saboda sun lura cewa kotun ta rikiɗe domin zama ƴar amashin ƴan mulkin mallaka. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani dokokin ƙasa da ƙasa Maitre Lirwanou Abdourahman, domin jin ko wataƙila ya yarda da dalilan da wadannan ƙasashe suka gabatar. Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawarsu.................

    Farfesa Tukur Abdulƙadir kan ƙarin ƙasashen da ke amincewa da Falasɗinu

    Play Episode Listen Later Sep 23, 2025 3:45


    Ƙasashen duniya na ci gaba da nuna amincewarsu da samar da ƴantacciyar ƙasar Falasɗinu, a wata guguwa wadda ba'a taɓa ganin irinta ba. Ƙasashen turai da ake ganin suna da ƙyakyawar alaƙa da Amurka irinsu su Burtaniya, Canada da kuma Australia a wannan Karo sun sanar da amincewar su da baiwa Falasɗinu damar zama ƙasa mai cin gashin kanta amma bisa wasu shariɗoɗi. A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara Farfesa Tukur Abdulƙadir ya ce har yanzu da sauran rina a kaba don kuwa amincewar waɗannan ƙasashe ƙadai a fatar baki bata wadatar ba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

    Tattaunawa da tsohon Jakadan Kamaru Ambasada Malam Mohamed Sani kan zaɓen ƙasar

    Play Episode Listen Later Sep 22, 2025 3:38


    A ƙarshen wannan mako ne za a ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a Kamaru, zaɓen da zai gudana a ranar 12 ga watan gobe na Oktoba. To sai dai yayin da jam'iyyar RDPC mai mulki ta bayyana Paul Biya a matsayin wanda zai tsaya mata takara, a nasu ɓangare kuwa, yanzu haka ƴan adawa, na ci gaba da tattaunawa don fitar da mutum ɗaya da zai tsaya zaɓen amadadinsu. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Ambasada Malam Mohamed Sani, tsohon jakada a lokacin mulkin Ahmadou Ahidjo, amma a yanzu yake zaune a ƙetare, inda ya bayyana yadda suke kallon wannan zaɓe.

    malam sani asar paul biya kamaru oktoba abdoulkarim ibrahim shikal
    Ambasada Mohamed Sani kan zaɓen shugaban ƙasa da za a yi a Kamaru

    Play Episode Listen Later Sep 22, 2025 3:38


    A ƙarshen wannan mako ne za a ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa da za a gudanar 12 ga watan gobe na Oktoba idan Allah ya kai mu a Kamaru. To sai dai yayin da jam'iyyar RDPC mai mulki ta bayyana Paul Biya a matsayin wanda zai tsaya mata takara, a nasu ɓangare kuwa, yanzu haka ƴan adawa, na ci gaba da tattaunawa don fitar da mutum ɗaya da zai tsaya musu takara a zaɓen. Kan haka Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Ambasada Malam Mohamed Sani, tsohon jakada a lokacin mulkin Ahmadou Ahidjo, amma a yanzu yake zaune a ƙetare, inda ya bayyana yadda suke kallon wannan zaɓe. Ƙu latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu............

    allah sani paul biya kamaru oktoba shugaban abdoulkarim ibrahim shikal
    Shugabannin ƙananan hukumomin Kwara sun sanar da rufe kasuwannin sayar da shanu

    Play Episode Listen Later Sep 19, 2025 3:06


    Shugabannin ƙananan hukumomi a yankin Kudancin jihar Kwara ta Najeriya sun sanar da rufe dukkannin kasuwannin sayar da shanu da aka fi sani da {Kara}. Mahukuntan sun ce sun ɗauki wannan mataki ne sakamakon tashin matsalolin tsaro da ake samu a kasuwannin. A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara shugaban ƙungiyar Miyetti Allah reshen jihar ta kwara, kuma guda daga cikin jagororin ƙungiyar kasuwannin kara na jihar Alhaji Shehu Garba ya ce sam basu yarda da wannan mataki ba. Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawar tasu....

    sanar rufe najeriya
    Hira da Issa Tchiroma Bakary game da zaɓen Kamaru da ƙoƙarin kawar da Paul Biya

    Play Episode Listen Later Sep 18, 2025 3:18


    Issa Tchiroma Bakary, wanda ya share tsohon shekaru 16 yana riƙe da muƙamin minista ƙarƙashin gwamnatin Paul Biya na Kamaru, a yanzu ya koma ɓangaren adawa inda yake ci gaba da jawarcin sauran ƴan siyasa na ƙasar. Tuni dai wani ƙawance da ya ƙunshi jam'iyyin adawa 11 ya bayyana goyon baya ga takararsa a zaɓen shugabancin ƙasar da za a yi ranar 12 ga watan gobe idan Allah ya kai mu. Radio France Internationale ya zanta da tsohon minista Issa Tchiroma, wanda da farko ya bayyana matsayinsa dangane da wannan goyon baya da ya samu, inda ya ci gaba da cewa.

    Dr. Musa Adamu game da yadda rashawa ke ci gaba da haɓaka a Najeriya

    Play Episode Listen Later Sep 17, 2025 3:03


    Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Nigeria wato ICPC, ta bayyana damuwa kan yadda matsalar rashawa ke ci gaba da haɓaka, duk kuwa da matakan da ta ke ɗauka. A cewar Shugaban hukumar ta ICPC, Dr Musa Adamu Aliyu, a yanzu sun karkata akalarsu ne zuwa ga ƙananan hukumomi, don daƙile matsalar cin hanci da ta yi katutu... Latsa alamar sauti don sauraron ƙarin bayanin da Dr Musa Adamu, ya yi wa wakilinmu Ibrahim Malam Goje........

    Isa Tafida Mafindi-Kan yadda talakawa zasu mori raba fetur da Ɗangote ya fara da motocinsa

    Play Episode Listen Later Sep 16, 2025 3:33


    Kamfanin Dangote ya fara aikin rarraba man fetur daga matatarsa zuwa sassan Najeriya domin saukakawa jama'a, a dai-dai lokacin da manyan dilallan man fetur ke adawa da matakin. Dashi Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki, Alahji Isa Tafida Mafindi a kan yadda talakawa zasu ci gajiyar wannan shirin. Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar.

    Uzairu Abdullahi kan buƙatun likitocin Najeriya masu neman ƙwarewa ga gwamnati

    Play Episode Listen Later Sep 15, 2025 3:29


    A makon da ya gabata ne likitoci da ke neman ƙawarewa a Najeriya suka gudanar da yajin aiki, domin nuna rashin amincewa dangane da yadda gwamnati ke jan ƙafa wajen ƙin biyansu haƙƙoƙinsu.To sai dai bayan da aka fara biyansu wasu daga cikin haƙƙoƙin, sun dakatar da yajin aikin tare da bai wa gwamnati ƙarin makonni biyu domin shafe musu hawayensu. Dr Uzairu Abdullahi, shi ne Editan Mujallar wallafa labarai ta ƙungiyar ya yi ƙarin bayani..... Latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawar da Abdoulkarim Ibrahim Shikal........

    abdullahi masu atun najeriya abdoulkarim ibrahim shikal
    Dr Mubarak Muhammad kan naɗin sabon firaministan Faransa Lecornu

    Play Episode Listen Later Sep 11, 2025 3:32


    Sabon firaministan Faransa Sebastien Lecornu ya karɓi ragamar tafiyar da mulkin daga hannun Francois Bayrou, wanda ƴan Majalisar dokokin ƙasar suka tsige a ranar Litinin ta gabata.Wannan dai shi ne Firaminista na 5 bayan da Emmanuel Macron ya karɓi ragamar mulki domin yin wa'adi na biyu, lamarin da ke nuni da cewa ƙasar na fama da rikici a fagen siyasa. Dr Mubarak Muhammad, mazauni Faransa kuma masani a game da salon siyasar ƙasar, ya bayyana wa Nura Ado Sulaiman mahangarsa a game da wannan batu. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tasu..................

    Mammane Wada kan yadda jamhuriyar Nijar ke ci gaba da shaƙe wuyan masu chachakarta

    Play Episode Listen Later Sep 10, 2025 3:33


    Gwamnatin mulkin sojin  Jamhuriyyar Nijar na ci gaba da kamen waɗanda ke sukar lamirinta da suka hadar da ƴan jarida da masu fafutuka har ma da ƴan siyasa. A wani rahoto da ta fitar a baya bayan nan kungiyar kare hakkin bil Adam Human Right Watch ta soki yadda sojojin da suka kwace muki a ƙasar ke tsare jama'a babu gaira babu dalili. Akan wanan abokin aiki Oumarou Sani ya tattaunawa da Mamane Wada shugaban kungiyar yaki da cin hanci da rashawa ga kuma yadda zantawarsu ta gudana.

    Mamane Wada akan yadda Gwamnatin sojin Nijar ke kama waɗanda ke sukar lamirinta

    Play Episode Listen Later Sep 10, 2025 3:33


    Gwamnatin mulkin sojin  Jamhuriyyar Nijar na ci gaba da kamen waɗanda ke sukar lamirinta da suka haɗar da ƴan jarida da masu fafutuka har ma da ƴan siyasa. A wani rahoto da ta fitar a baya bayan nan kungiyar kare haƙƙin bil Adam Human Right Watch ta soki yadda sojojin da suka ƙwace muki a ƙasar ke tsare jama'a babu gaira babu dalili. Akan wanan abokin aiki Oumarou Sani ya tattaunawa da Mamane Wada shugaban ƙungiyar yaƙi da cin hanci da rashawa ga kuma yadda zantawarsu ta gudana. Latsa alaamar sauti don sauraron yadda tattaunawar ta su ta gudana...........

    Nasiru Garba Ɗantiye kan ƙorafin shugaban majalisar wakilan Najeriya game da yawan ciwo bashi

    Play Episode Listen Later Sep 9, 2025 3:29


    Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya, Abbas Tajudeen, ya koka akan yadda bashi ya ke cigaba da yi wa ƙasar katutu, lamarin da ya ce yana barazana ga bunƙasar tattalin arziƙinta. Tajuddeen, wanda ya bayyana haka jiya Litinin a Abuja, ya ce bashin da ke kan Najeriya a yanzu ya kai wani matsayi mai ban tsoro, inda ya ke kira da a sake fasalin yadda ake karɓar rance a ƙasar. Akan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da wani tsohon ɗan majalisar dokoki a ƙasar, Nasiru Garba Ɗantiye, ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana.

    game akan abuja garba bashi najeriya shugaban majalisar

    Claim Bakonmu a Yau

    In order to claim this podcast we'll send an email to with a verification link. Simply click the link and you will be able to edit tags, request a refresh, and other features to take control of your podcast page!

    Claim Cancel