A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban…

Yau ake fara gasar cin kofin duniya ta bana, inda ƙasashe 48 za su fafata domin samun zakarar bana. A karon farko ƙasashe uku ne ke daukar nauyin gasar, wato Amurka da Cnada da kuma Mexico kuma kalla yan wasa 1,248 da alkalan wasa 52 za su jagoranci wasanni 104 da za'a kwashe kwanaki 39 ana yi. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar da Bashir Ibrahim Idris ya yi da tsohon Sakataren hukumar kwallon kafar Najeriya Hon Sani Ahmed Toro.....

Asusun bada lamuni na duniya IMF ya ce sauye-sauyen da gwamnatin Najeriya ke yi na ƙarfafa tattalin arzikin ƙasar, sai dai kuma sun haifar da ƙarin ƴan Najeriya sama da miliyan 60 da suka faɗa cikin talauci. Ku danna alamar saurare domin jin tattaunawar Bashir Ibrahim Idris, da masanin tattalin arziki a Najeriya Samaila Abdullahi Muhammad kan wannan batu.

Yankin arewacin Najeriya na ci gaba da ɗanɗana kuɗar sa a hannun ƴan bindiga, waɗanda ke kai hari suna sace mutane da kuma hallaka su ba tare da ƙauƙautawa ba. ko a jiya sai da ƴan bindigar suka yi garkuwa da wata tawagar masu neman sulhu da su a jihar Zamfara, baya ga wasu ɗaruruwa da ke hannun su a jihohi da dama, a daidai lokacin da gwamnoni da ƴan majalisun yankin suka mayar da hankali a kan siyasa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Bello Bada na Jami'ar Usman Dan Fodio da ke Sokoto. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana...........

Gwamnatin jihar Lagos a Najeriya ta ƙaddamar da wani gagarumin samame kan mabarata da suka cika titunan birnin, inda aka cafke ɗimbin mabarata ciki har da masu fama da naƙasa da kuma waɗanda ke yi musu jagora, kazalika da ma waɗanda ke cikin ƙoshin lafiya. Kwamishin Ma'aikatar matasa da jin ɗadin jama'a na jihar Mobolaji Ogunlende, ya ce daga ƙarshen watan Mayun da ya gabata zuwa yau, sun cafke sama da mutane dubu 1 da 300 tare da hukunta aƙalla 450 daga cikinsu. Lura da cewa mafi yawan waɗanda suka riƙi bara a matsayin sana'a a birnin Lagos ƴan asalin Arewacin Najeriya ne, wannan ya sa Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da ɗaya daga cikin shugabannin al'ummar yankin da ke zaune a jihar, Alhaji Sa'adu Yusuf Ɗandare Gulma, ga kuma ƙarin bayanin da ya yi masa a game da wannan samame. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu.............

A Najeriya, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta ƙaddamar da bincike akan zargin fitar bayan sirri daga rumbun ajiyar bayananta na masu zaɓe, wanda ya jamnyo cece-kuce a ƴan kwanakin nan. Wannan ya biyo bayan wallafa bayan wani ɗan takara ne da ake zargin wani ma'aikacin INEC ya yi a dandalin sada zumunta a yayin zaɓwen fidda gwani na wata jam'iyyar siyasa a babban birnin tarayyar Najeriya Abuja. Akan haka Michael Kuduson ya tattauna da Dakta Umar Yakubu, shugaban wata ƙungiyar farar hula a Abuja babban birnin Najeriya.

Nijar da Jamhuriyar Benin sun amince da yin aiki a tare don yaƙi da ta'addanci da ke addabar ƙasashen biyu na Yammacin Afirka, yayin da a hannu ɗaya suka kafa wani kwamitin da zai bayar da shawarwari cikin kwanaki 15 a game da yadda za a sake buɗe iyakokin ƙasashen da ke rufe yau kusan shekaru uku. An dai cimma wannan matsaya ce a ziyarar da shugaban Benin Romuald Wadagni ya kai a birnin Yamai ranar talata, inda ya gana da takwaransa na Nijar Janar Abdourahman Tiani. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar da Abdulkarim Ibrahim Chikal ya yi da Sani Yahaya Djandjouna masanin siyasa ƙasa da ƙasa....

A yayin da ya yage kwana 9 a fara gasar lashe kofin duniya da ƙasashen Amurka da Canada da kuma Mexico za su karɓi baƙunci, har yanzu wasu ƙasashe na ci gaba da fuskantar ƙalubale wajen samun takardar izinin shiga ƙasashen. Ko a baya-bayan nan, anga yadda ƴan wasan tawagar ƙasar Afrika ta Kudu suka samu jinkiri wajen tafiya gasar sabida dalilai na Visa, bayaga ƙalubalen da ƙasashen Jamhuriyar Dimukaraɗiyyar Congo da Iran suma suka fuskanta. Kan wannan batu Khamis Saleh ya tattauna da Hon Sani Ahmed Toro, tsohon sakataren Hukumar Kwallon Ƙafara ta Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu..........

A Najeriya, jam'iyyun siyasa sun kammala zaɓen fidda ƴantakarar da za su tsaya musu a matakai daban-daban na zaɓukan da za a yi cikin shekara mai zuwa. To sai dai a ɓangaren adawa, mafi yawan jam'iyyun sun gudanar da zaɓukan ne a cikin yanayi na rabuwar kawuna sakamakon rikicin shugabanci. To akwai yiyuwar wannan rikici na cikin gida ya iya shafar ƙima da kwarjinin adawa a zaɓukan na baɗi? Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar da Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya yi wa Farfesa Usman Mohammed, masani siyasa a Najeriya.

Bisa ga dukkan alamu za a iya samun fahintar juna tsakanin Nijar da kuma maƙociyarta Jamhuriyar Benin, waɗanda ke takun-saka tun bayan kifar da gwamanatin dimokuraɗiyyar ta Mohamed Bazoum yau kusan shekaru uku kenan. Kasancewar Firaminsitan Nijar Mahamane Ali Lemine Zeine a wurin bikin rantsar da sabon shugaban Benin Romuald Wadagni, na ƙara nuni da cewa za a iya samun kusanci a tsakanin ɓangarorin biyu. A game da haka ne Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Adamu Muhammadu Ɗan Madawa, ɗaya daga cikin shugabannin ƴan Nijar mazauna Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraren zantawarsu...

A daidai lokacin da ake kan tattaunawa tsakanin Iran da Amurka don samar da yarjejeniyar kawo ƙarshen yakin da ake yi tsakaninsu, kafafen yaɗa labaran Iran sun ce akwai gagarumin cigaba a tattaunawar. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Malam Mubarak Abdul-Aziz, ɗan Najeriya mazauni Tehran, wanda ya yi masa ƙarin bayani a game da halin da jama'a ke ciki daidai wannan lokaci da ake dakon cimma yarjejeniya don kawo ƙarshen wannan yaƙi. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Jami'an Lafiya na ci gaba da ƙoƙarin daƙile yaɗuwar cutar Ebola da ta sake ɓulla a Jamhuriyar Congo, wadda kawo yanzu ta shiga maƙwafciyarta Uganda. Zuwa wannan lokacin dai, cutar wadda a wannan karon ta bayyana da wani sabon nau'in, ta laƙume rayukan mutane fiye da 100, yayin da wasu kusan dubu ɗaya suka kamu. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Nasiru Sani Gwarzo ƙwararre kan fannin kiwon lafiya da daƙile cutuka masu yaɗuwa a Najeriya, wanda ya yi tsokaci kan dalilan da suka sa wankin hula ke neman kai wa dare. Ku latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawarsu....................

A Najeriya jam'iyyar APC mai mulki ta kammala zaɓen fitar da ƴan takara a dukannin matakai, inda a ƙarshe magoya bayan jam'iyyar suka amince da Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda zai sake tsayawa takarar shugabancin ƙasar a shekara mai zuwa. An dai samu ƙorafe-ƙorafe da kuma taƙƙadama a tsakanin ƴantakara, ya yin da wasu ke zargin cewa an yi musu ba daidai ba. Abdoulkarim Ibrahim Shikak ya zanta da Hon Ishaq Muktar Yakasai, magoyi baya jam'iyyar ta APC kuma wanda ya taka wara domin haɗa kan magoya baya a lokacin zaɓukan. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu............

Kotu a Najeriya ta yi hukunci da ke cin karo da umarnin hukumar INEC da ta nemi dukkanin jam'iyyun siyasa su kammala miƙa mata sunayen ƴan takarar da suka tsaida kafin nan da ranar 31 ga watan da muke na Mayu, duk kuwa da tanadin dokar zaɓen ƙasar da ta sahalewa jam'iyyun kaiwa har nan da watan Satumba gabanin miƙa sunayen. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawar Abdoulkarim Ibrahim Shikal da masanin doka a Najeriya Barista El-zubair Abubakar kan wannan hukunci....

A wannan Alhamis 21 ga watan Mayu, Sashin Hausa na Radio France International RFI ke cika shekaru 19 da kafuwa, bayan fara yaɗa shirye-shiryensa a shekarar 2007, kuma dangane da wanna rana Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Umar Pate, ɗaya daga cikin masanan da ke bibiyar ayyukan wannan kafa a Najeriya.

Gwamnan jahar Borno Babagana Umara Zullum ya ce, gwamnati da jami'an tsaro na ƙoƙarin ceto daliban makaranta da aka sace a makarantar firamare a ƙauyen Mussa dake ƙaramar Hukumar Askira- Uba. Gwamna Zulum ya bayyana haka ne ya yin wata ziyarar jaje da ya kai Askira Uba dangane da iftila'in da ake dangantawa da Boko Haram. Ziyarar na zuwa ne yayin da aka shiga kwanaki na 5 da sace daliban ciki harda kanan yara. Shugabar kula da ilimi na ƙaramar Hukumar Askira-Uba, Hajiya Fatsuma Adamu Askira ta bayyana mana halin da ake ciki, a tattaunawarta da Ahmad Abba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta fara babban taronta karo na 79 jiya Litinin a birnin Geneva, wanda kuma za a ƙarƙare shi a ranar 23 ga watan Mayu da muke. Daga cikin muhimman batututwan da taron zai fi mayar da hankali a kai dai akwai giɓin kasafin kuɗin da ya kai Dala Biliyan 1 da Hukumar Lafiyar ta Duniya ke fuskanta, da kuma tasirin janyewa daga cikinta da Amurka ta yi. Kan wannan da kuma sauran batutuwa masu alaƙa, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Nasiru Sani Gwarzo, ƙwrarre kan sha'anin lafiya da ke Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

Yanzu haka na ci gaba da bayyana ra'ayoyi dangane da sanarwar da Amurka ta fitar da ke cewa ta kashe Abu Bilal Al-Minuki da ke matsayin jagora a ƙungiyar IS a Najeriya, labarin daga bisani hukumomin tsaron Najeriya suka tabbatar. To domin jin ƙarin bayani a game da wannan ɗan taliki da ake cewa an kashe, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Kabiru Adamu na Cibiyar da ke nazari kan sha'anin tsaro ta Beacon da ke Abuja, ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar...............

A zantawarsa da Radio France Internationale, da France 24 da kuma TV5 Monde a ƙarshen taron Afrika da Faransa da aka kammala birnin Nairobi na ƙasar Kenya, Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana matsayinsa a game da taɓarɓarewar sha'anin tsaro a Mali da kuma alaƙar Faransa da sauran ƙasashen Afirka ta fannin tsaro da aikin soji. To amma da farko shugaban ya fara amsa wata tambaya ce dangane da dalilan da suka sa Faransa ke ci gaba da taka rawa a wajen tafiyar da takardar kuɗin CFA. Ga dai tattaunawar. Latsa alamar sauti domin sauraren zanatawar.

A ranar Talata ne ake kammala taron shugabannin ƙasashen Afirka da Faransa da ya gudana a birnin Nairobi ta ƙasar Kenya, wanda ya mayar da hankali kan hanyoyin ci gaban tattalin arziki da noma da samar da abinci ga jama'ar nahiyar. Yaƙin Iran na ɗaya daga cikin abubuwan da ake ganin na maida hannun agogo baya wajen magance ƙarancin abinci, musamman rufe mahsigin Hormuz da ake amfani da ita wajen safarar takin zamani. Kan haka ne Nura Ado Suleiman ya zanta da ministan noman Najeriya Sanata Abubakar Kyari a wurin wannan taro, inda kuma ya ce su na ƙoƙarin magance matsalar. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

A jiya ne ake faro taron kwanaki biyu tsakanin Faransa da ƙasashen Afrika a birnin Nairobi, wanda shugaba Emmanuel Macron da takwaransa William Ruto ke jagoranta. Taron ya haɗa shugabannin ƙasashen Afrika, da Hamshaƙan ƴan Kasuwa, da sauran masu ruwa da tsaki domin tattaunawa kan nemawa nahiyar Afrika mafita wajen samun ci gaban Tattalin Arziƙi a fannonin da suka haɗa da, bunƙasa Masana'antu da Kimiyya da Fasaha da inganta Noma da Tsarin Kiwon Lafiya, da kuma samun wadatar makamashi. Danna alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar Nura Ado Suleiman da hadimin shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu Daniel Bwala.......

A ranar asabar da ta gabata ne, wasu masu fafufutuka da suka haɗa da ƴan siyasa, fararen hula, masana dokoki da dai sauransu da ke zaune a ƙetare, suka ƙaddamar da wani ƙawance da ake kira da suna ADS, (Alliance des Domocrates du Sahel) wanda babbar manufarsa ita ce sake dawo da tsarin dimokuraɗiyya a ƙasashen yankin Sahel da yanzu haka ke ƙarƙashin mulkin soji da suka hada da Burkina Faso, Mali da kuma Nijar. An dai ƙaddamar da wannan ƙawance ne a birnin Brussels na ƙasar Belgium, inda daga bisani Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Sakataren Yaɗa Labarai na ADS Boubacar Ɗan Zourmani, wanda ya yi masa ƙarin bayani a game da manufofinsu. Ga dai ƙarin bayaninsa.

Kotu a Najeriya yau ta ci gaba da sauraron shari'ar neman hana tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan tsayawa takarar zabe mai zuwa, kwana guda bayan wasu tarin magoya bayan sa sun bukaci ya shiga zaben mai zuwa. Dangane da matsayin dokar zabe a kan takarar ta Jonathan masanin shari'a, Farfesa Shehu Abdullahi Zuru na Jami'ar Baze dake Abuja, ya mana tsokaci a kai yayin zantawarsa da Bashir Ibrahim Idris. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

Wasu daga cikin Ƴan Majalisun Dattawan Najeriya sun buƙaci ɗaukar matakai maus tsauri a kan Afirka ta Kudu, ciki harda kwace lasisin kamfanonin su na MTN da DSTV saboda yadda ake kai wa ƴan ƙasar hari ake kuma kashe su. Majalisar ta yanke hukuncin tura tawaga Afirka ta Kudu domin tattaunawa da hukumomin ƙasar, yayin da shi ma bangaren gwamnati ya tura ministan harkokin waje. Ambasada Ibrahim Kazaure, tsohon Jakadan Najeriya a Saudi Arabia ya yi tsokaci a kai, a tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris.

Kamfanin mai na NNPC ya sanya hannu kan wata yarjejeniya da wasu kamfanonin ƙasar China guda biyu, Sanjiang Chemical Company Limited da kuma Fuzhou Industrial Park, domin farfaɗo da matatun mai na Warri da Port Harcourt. Wannan mataki ya zo ne bayan matatun man sun laƙume kimanin biliyan 3.2 na dala ba tare da an samu biyan buƙata ba. Injiniya Kailani Muhammad, tsohon babban jami'in kamfanin na NNPC ne, a tattaunawarsa da Shamsiyya Haruna, ya bayyana gamsuwa da wannan yarjejeniya da kasar China bisa wasu dalilai. Ku latsa alamaru sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa za ta fara kwashe ƴan ƙasarta da ke son komawa gida daga Afirka ta Kudu, matakin da ta ce ya zama dole saboda tsananin kyamar baƙi da kuma rahoton mutuwar wasu ƴan Najeriya biyu sakamakon hare-haren da ake kai wa ƴan cirani. Akalla 'yan Najeriya 130 ne suka riga suka yi rajista don neman a kwashe su zuwa gida, sakamakon fargabar makomarsu na rashin tabbas. Dakta Rakiya Sa'idu daga jami'ar Capetown, ta bayyana mana yadda ƴan siyasa ke amfani da lokacin zaɓe wajen rura wutar wannan matsala. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawar da Shamsiyya Haruna ta yi da ita............

Kamar dai kowace shekara, 3 ga watan Mayu ita ce ranar kare ƴancin aikin yaɗa labarai a duniya, inda rahotannin da ƙungiyoyin da ke fafutuka a wannan fage ke nuni da cewa an samu gagarumin koma-baya ta fannin aikin jarida a cikin shekarar da ta gabata. Dangane da wannan rana, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon shugaban ƙungiyar Ƴan Jarida ta Najeriya (NUJ) Honnorable Alhaji Muhammed Sani Zoro, wanda da farko ya fara yin tsokaci a game da irin sauye-sauyen da aka samu a aikin jarida saboda dalilai masu nasaba da zamani. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake jaddada aniyar sa ta samar da Yan Sandan jihohi domin samar da tsaro. Tinubu ya bayyana haka ne yayin ganawa da masu ruwa da tsaki na jihar Filato mai fama da tashin hankalin. Alhaji Isa Tafida Mafindi, wanda ya wallafa littafi a kan samar da Yan Sandan jihohi ya mana tsokaci a kai, yayin tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

Yan Najeriya na cigaba da bayyana fargaba dangane da makomar ƴan adawar ƙasar dangane da zabe mai zuwa , la'akari da cewar akasarin jami'iyyun adawar na fama da rikice-rikicen da ka iya hana su takara. Akan wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Alhaji Kabir Muhammad Baba, ɗan siyasa a jihar Bauchi. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar......

Ɗaruruwan ‘yan Afrika ta Kudu masu ƙyamar baƙi, sun gudanar da zanga-zanga jiya Talata a birnin Pretoria, bayan da suka bjirewa kiran da shugaban ƙasar Cyril Ramaphosa ya yi musu na dakatar da kai wa baƙi hare-hare gami da cin zarafinsu, inda a baya bayan wasu ‘yan Najeriya biyu suka rasa rayukansu. Cin zarafin baƙin da tsagerun ‘yan Afrika ta Kudun na baya bayan nan dai ya fara ne da shafar ‘yan ƙasashen Ghana, da Habasha da Zimbabwe kafin kai wa ga ‘yan Najeriya. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Kabiru Inuwa Dukawa, masanin siyasar ƙasa da ƙasa da ke Najeriya. Ku danna alamar sauraro domin jin cikakkiyar Hirar.

Wani rahoton masana na hukumomin Majalisar Ɗinkin Duniya da aka fitar a ƙarshen makon jiya, ya sanya Najeriya a cikin jerin ƙasashe 10 da suka fi fama da Yunwa a Duniya. A Najeriya rahoton ya ƙiyasta zuwa wannan shekara, aƙalla mutane miliyan 35 ke fuskantar haɗarin faɗawa cikin ƙangin Yunwa, saboda ƙarancin abincin da ake fama da shi a sassa da dama, musamman a yankunan karkara na arewacin ƙasar inda mafi rinjayen manoma suke. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Muhd Garba, malami a tsangayar koyar da Ilimin ayyukan Noma a Jami'ar Abubakar Tafawa Ɓalewa da ke garin Bauchi. Ku danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar tare da Nura Ado Sulaiman.

An shiga zaman zullumi a Mali bayan da ƙawancen ƙungiyar Abzinawa ƴan tawaye FLA da kuma kungiyoyin da ke ikirarin jihadi suka ƙaddamar da farmaki kan birane da dama na ƙasar tun a ranar asabar har zuwa jiya lahadi. Tuni dai aka tabbatar da mutuwar ministan tsaro Janar Sadio Camara da kuma wasu mutane da dama a wannan farmaki da ake kallo a matsayin mafi tsaruwa da kuma jajircewa daga waɗannan ƙungiyoyi da suka share tsawon shekaru suna fafatawa da dakarun gwamnati. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Malam Soumaila Amadou, mai sharhi kan lamurran yankin Sahel, ga kuma zantawarsu. Latsa alamar sauti don sauraron hirar Abdoulkarim Ibrahim da Soumala Amadou:

Kimanin gwamnonin jihohin Najeriya 20 sun amince su gina katafariyar ruga ta zamani a jihohinsu wadda za ta kunshi makarantu da asibitoci da kasuwanni har ma da wuraren kiwon dabbobi musamman shanu da zummar zaunar da Fulani makiyaya wuri guda ba tare da gararanba ba. Tuni masana suka ce wannan sabon tsarin zai yi tasiri wajen tabbatar da lafiyar dabbobin Najeriya tare da ruɓanya adadin madarar da suke samarwa a kullum. Jim kaɗan da kammala taro kan wannan shiri a birnin Lagos, Abdurrahman Gambo ya tattauna da Farfesa Abba Gambo, mai bai wa gwamnonin Najeriya shawara kan noma da kiwo. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

Wasu alƙaluma daga Hukumar Kula da Albarkatun Man Fetur na kan tudu da na cikin ruwa (NMDPRA) sun nuna cewa, adadin Iskar Gas ɗin da aka fitar daga Najeriya zuwa kasuwannin ƙetare ya kai kaso 62 cikin 100, cikin watanni uku na farkon wannan shekara. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Gas ɗin ya yi ƙaranci a Najeriyar, lamarin da ke taka rawa wajen raguwar hasken lantarkin da ake samu, fannin da kasonsa aƙalla 80 cikin 100 ya dogara da arziƙin na Gas. Don jin yadda masana ke kallon lamarin da kuma mafita, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Aminu Idris Harbau, ƙwararren kan tattalin arziki a Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraron hirar:

Najeriya da Morocco sun rattaba hannu kan wata yarjejeniyar shimfiɗa bututun Gas, aikin da zai laƙume kuɗin da yawansu ya kai Dala biliyan 25, kafin ƙarshen wannan shekara. Bayanai sun ce tsawon bututun Gas ɗin da za'a shimfiɗa ya kai kilomita dubu 6,900, wanda zai ratsa cikin Ruwa da Sahara, har ma ya tsallaka zuwa Turai. Kan wannan Shamsiyya Haruna ta tattauna da Dakta Abdullahi Auwal Aliyu, masanin tsaro a Najeriya, domin jin yiwuwar wannan aiki da kuma tasirin da zai yi. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar ta su.................

Hukumar Kula da kafafen Yaɗa Labarai a Najeriya NBC, ta gargaɗi masu gabatar da shirye-shirye a gidajen Radio da Talabijin da su guji bayyana ra'ayoyin ƙashin kansu, su kuma kaucewa yin katsalandan cikin bayanan waɗanda suka tattaunawa da su, da kuma yaɗa duk wani saƙo da ka iya haifar da rarrabuwar kai. Tuni dai wannan mataki ya gamu da caccakar ƙungiyoyin farar hula da kuma ɓangaren ‘yan adawa a Najeriyar. Kan haka, Nura Ado Suleiman ya tattauna Dakta Ruƙayya Yusuf Aliyu, Malama a tsangayar koyar da aikin Jarida na zamani a Jami'ar Bayero da ke Kano a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

Najeriya da kuma Turkiyya sun ƙulla yarjejeniyar tsaro a tsakaninsu, wadda a ƙarƙashinta matakin farko Najeriya za ta tura zatan sojoji 200 don samun horo na musamman a Turkiyya. Hakan dai na zuwa ne watanni kaɗan bayan da mahukuntan a birnin Abuja suka sanar da ƙulla irin wannan yarjejeniya da ke bai wa Amurka damar turo sojojinta zuwa Najeriya don yaƙi da ta'addanci? Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tsaro lamurran tsaro Dr Yahuza Getso, domin jin tasa fahintar a game da yadda alaƙar tsaron za ta kasance tsakanin Najeriya da kuma Turkiyya. Ga dai zantawarsu.

A ƙoƙarinta na ganin ta bunƙasa harkokin tattalin arzikinta, gwamnatin jihar Katsina ta ce ƙofofinta a buɗe suke ga masu zuba jari na ƙasashen ƙetare. A yayin wani taro na masu zuba jari da ya gudana a birnin Paris na Faransa, gwamnatin jihar Katsina ta ce akwai masu zuba jarin da suka nuna sha'awar zuba jari a ɓangaren noma da ma'adinai da kiwon lafiya a jihar. Domin jin irin matakan da suke ɗauka domin cimma wannan narasa, Khamis Saleh ya tattauna da mataimakin gwamnan jihar Kastina Malam Faruk Lawal Jobe. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Yayin da aka cika shekaru uku da fara yaƙin basasar ƙasar Sudan, Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla mutane miliyan 14 suka bar muhallansu, baya ga daruruwan da suka rasa rayukan su. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Abdulkadir Suleiman Muhammed na Jami'ar Abuja, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.

Ɗan takarar ƙawancen jam'iyyun da ke mara wa gwamnati baya a Jamhuriyar Benin ya yi nasarar lashe 94% na ƙuri'un da aka kaɗa a zaɓen shugabancin ƙasar da aka hana fitattun ƴan adawa tsayawa takara. Romuald Wadagni mai shekaru 49 a duniya, shi ne ministan kuɗi tsawon shekaru 10 kafin shugaba mai barin gado Patrice Talon ya gabatar da shi a matsayin wanda yake son gaje shi. Don jin yadda masu sharhi kan siyasar ƙasa da ƙasa musamman a Nahiyar Afrika ke kallon zaɓen na Jamhuriyar Benin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Janjouna Ali Mahamane Sani.

A cikin makon nan, gwamnatin Najeriya ta fitar da jerin sunayen mutane 48 da kuma wasu kamfanoni 12, waɗanda take tuhuma da hannu cikin ayyukan ta'addanci a ƙasar. Tuni dai wannan mataki ya haifar da muhawara a tsakanin ‘yan Najeriya waɗanda ke ci gaba da tofa albarkacin bakinsu a kan lamarin. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hira da Nura Ado Suleiman ya yi da Katfin Abdullahi Adamu Bakoji mai ritaya, masanin tsaro da ke Najeriya.

An tashi baram-baram tsakanin Amurka da Iran a tattaunawar da suka faro ranar Asabar a birnin Islamabad bisa shiga tsakanin Pakistan a ƙoƙarin kawo ƙarshen wannan yaƙi, tattaunawar da ke zuwa bayan cimma jituwar tsagaita wutar kwanaki 14 tsakanin ɓangarorin biyu. Tuni ƙasashe suka fara kiraye-kirayen ganin rashin cimma jituwar Amurkan da Iran bai taɓa yarjejeniyar da ke tsakaninsu ba Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hira da Dakta Dicko Abdourahmane malami a jami'ar Zinder Nijar....

‘Yan Sa'o'i bayan amincewa da yarjejeniyar tsagaita wutar kwanaki 14, Amurka da Iran sun zargi juna da karya yarjejeniyar, lamarin da ya kai ga Iran ta sake datse mashigin ruwan Hormuz jim kaɗan bayan buɗe shi da ta yi. Domin jin yiwuwar ɗorewar wannan yarjejeniya ta tsagaita wuta da kuma makomar ƙoƙarin da masu shiga tsakani ke yi, Nura Ado Suleiman ya tattauna da masanin Siyasar ƙasa da ƙasa, Dakta Riya'uddeen Zubairu Maitama na Jami'ar Bayero da ke Kano a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar ta su.............

Kotun musamman a Najeriya, ta ci gaba da zaman gudanar da ɗimbin shara'o'i na yanke hukunci da kuma sauraron ƙararraki kan waɗanda ake tuhuma da ayyukan ta'addanci da taimaka wa ƴan ta'addan. A daidai wannan lokaci kuma ɓangarori daban daban ke bayyana ra'ayoyinsu kan tsarin gudanar da shara'o'in lura da adadin masu laifukan da ke gurfana. Yayin da wasu ke ganin komai na tafiya daidai, wasu na ganin ana jan kafa, saɓanin taƙaita lokacin da ake buƙata. Tu latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Nura Ado Suleiman da Barista Umar Usman Ɗanbaito..........

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da ware Naira Tiriliyan 3 da Biliyan 300 domin biyan kamfanonin rarraba wutar lantarki basukan da suke bin gwamnatin ƙasar, da zummar kawo ƙarshen matsalar ƙarancin wutar da ‘yan Najeriya ke ciki. Bayanai dai sun nuna cewa bashin na sama da Naira Tiriliyan Ukun ya taru ne a tsakanin shekarar 2015 zuwa bara. Sai dai ɗaya daga cikin masu ruwa da tsaki kan sha'anin wutar lantarki a Najeriya, Comrade Musa Yunusa Ayiga ya bayyana shakku kan wannan yunƙuri. tattaunawarsa da Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Nura Ado Suleiman.............

Ana ci gaba da gudanar da bukukuwan Easter a sassan duniya, wadda Kiristoci suka yi imani da cewa a wannan rana ce aka gicceye Yesu Almasihu inda kwanaki uku bayan hakan ya tashi. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya tuntuɓi Reverand Andrew Doyu, domin jin ƙarin bayani a game da matsayin wannan rana da kuma muhimmancinta ga mabiya addinin Kirista. Shiga alamar sauti don saurarin cikakkiyar hirar...........

A wannan rana, ta biyu ga watan Afrilun shekarar 2026 da muke, wa'adin shugabancin hamɓararen shugaban ƙasar Jamhuriyar Nijar Muhammad Bazoum ke ƙarƙarewa da a ce yana kan karagar mulki. A irin wannan ranar ce dai ta watan Afrilun shekarar 2021, aka rantsar da Mohammed Bazoum a matsayin shugaban Jamhuriyar Nijar, bayan da ya lashe sama da kashi 55 na ƙuri'un zaɓen da aka yi a watan Fabrairun wannan shekara. Akan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Intinikar Alhassan, ɗaya daga cikin makusantan hamɓararren shugaban na Nijar. Ku latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu............

A Jamhuriyar Nijar, ra'ayoyi sun banbanta a kan shawarar da gwamnatin ƙasar ta yanke na kafa ƙungiyoyi waɗanda za ta bai wa horo tare da riƙe makamai don kare garuruwa daga hare-haren Ƴanbindiga. A cewar gwamnati, jami'an ƙungiyoyin kare kan, za su kasance sojoji, da ƴansanda da sauran jami'an tsaron da suka yi ritaya, waɗanda za a riƙa biyansu kuɗin alawus. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Mammane Wada na ƙungiyar Transparency International da ke bibiyar lamurra a ƙasar ta Nijar. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu............

Kwamitin da Sufeto Janar na Ƴansandan Najeriya Tunji Disu ya kafa domin bada shawarar yadda za'a kirkiro ƴansandan jihohi ya gabatar da shawarwarinsa ga kwamitin Majalisar tarayya dake yiwa kundin tsarin mulki kwaskwarima. Shugaban kwamitin Farfesa Olu Ogunsakin ya bayyana cewar sun bada shawarar mayar da kashi 60 na ƴansandan tarayya da ake da su yanzu zuwa sabuwar rundunar ƴansandan jihohin da za'a kirkiro a jihohi 36 da Abuja. Danna alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hirar Bashir Ibrahim Idriss da Sufet Muhammed Wakili mai riyata....

Yayinda ake cika wata guda curr da fara yaƙi tsakanin haɗin gwiwar Amurka da Isra'ila a gefe guda kuma da Iran, a yau ɓangarorin da ke rikici na ƙara zafafa hare-hare, a wani abu da duniya ke ci gaba da mamakinsa. Zuwa yanzu dai wannan yaƙi ya laƙume dubban rayuwa, inda kuma Iran ke zargin Amurka da shirya afka mata da sojoji ta ƙasa, yayinda wasu ƙasashe suka fara yunƙurin sulhunta tsakani. Shiga alamar sauti don sauraron karin bayani a hirar da Rukayya Abba Kabara ta yi da Bash M Bash....

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana fataucin bayi da aka share ɗaruruwan shekaru ana yi daga Afirka zuwa Turai da Amurka a matsayin ‘'cin zarafin bil Adama mafi girma'' da aka taɓa gani a tarihi. Ƙasashen duniya 123 ne suka kaɗa ƙuri'ar goyon bayan wannan ƙuduri, wasu uku wato Amurka, Isra'ila da Argentina suka ƙi amincewa yayin da wasu ƙasashe 52 suka yi ƙememe ta hanyar rowar ƙuri'unsu. To domin tuni a game da lokacin da aka fara ɗibar bayi daga Afirka da kuma yadda hakan ya shafi ci gaban nahiryar, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tarihi Dr Maman Kassou, malami a jami'ar Andre Salifou da ke Damagaram, ga kuma zantarwarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Farashin hajoji da sauran muhimman abubuwa na ci gaba da hauhawa a kasuwannin duniya sakamakon yadda yaƙin da ake yi a yankin Gabas ta Tsakiya ya hana fitar da mafi yawan man fetur da kamfanoni da masana'antu suka yi oda ya maƙale a Mashigin Ruwan Hormuz. To domin fahintar girman wannan matsala da kuma ɓangarorin da suka fi fama da ƙarancin makamashi a duniya saboda wannan rikici, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya tuntuɓi masani tattalin arziki Dr Isa Abdullahi, malami a jami'ar Tarayya da ke Kashere a jihar Gomben Najeriya, ga kuma zantawarsu. A latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawar