A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban…

Gwamnatin Jihar Benue a Najeriya, na neman amincewar gwamnatin tarayyar ƙasar wajen gina cibiyar sauya tunanin ‘yan bindigar da suka tuba, da ma sauran mutanen da wani yanayi ya sanya su taimaka wa ayyukan ta'addanci, ciki kuwa har da mata waɗanda ke yi wa ‘yan ta'addan aiki a bisa tilas bayan garkuwar da aka yi da su. Wannan na zuwa ne a yayin ake ci gaba da samun banbancin ra'ayi tsakanin ‘yan Najeriya a kan irin wannan yunƙuri. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Kabiru Adamu, shugaban kamfanin Beacon Consulting da ke bincike kan tsaro a nahiyar Afrika. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar..

A Najeriya, ƴan bindiga a ƴan kwanakin nan sun zafafa kai hare-hare yankunan jihohin Zamfara da kuma Kebbi. Na baya bayan nan shine wanda ya faru a garin Dutsen Dan Ajiya na karamar hukumar Anka ta jihar Zamfara, inda rahotanni suka ce sama da mutane 30 sun mutu, bayaga na Tungan Dutse da mutane 50 suka rasa ransu. Haka zalika, mayaƙan Lakurawa sun ƙara zafafa kai hare-hare a wasu sassa na jihar Kebbi, inda nan ma suka hallaka mutane da dama. Kan haka Khamis Saleh na zanta da Squadron Leader Aminu Bala Sokoto. Ku latsa alamar sauti don sauran cikakkiyar tattaunawar.

A ranar Alhamis, shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaddamar da fara aikin Kwamitin Zaman Lafiyar Duniya da ya kafa. Wakilai daga aƙalla ƙasashe 47 da kuma ƙungiyar Tarayyar Turai da Isra'ila ne suka halarci taron farkon na Kwamitin Zaman Lafiyar na Duniya a birnin Washington. Muhimman batutuwan da taron ya mayar da hankali kai sun haɗa da kafa Rundunar zaman lafiya a Gaza, da karɓe makamai daga hannun Hamas, da kuma sake gina Zirin na Gaza. Shiga alamar sauti, domin sauraron tattaunawar Nura Ado Suleiman da AbdulHakim Garba Funtua, masanin siyasar ƙasa da ƙasa.

Kotun ECOWAS ta koka kan alƙaluman da suka nuna cewar cikin shekaru 25, wato tun bayan da ta fara aiki a shekarar 2001, hukunce-hukunce gud 10 kaɗai Najeriya ta mutunta, 66 da ta yanke. Shugaban Kotun ta ECOWAS Ricardo Claudio ne ya bayyana alƙaluman yayin buɗe taron masu ruwa da tsaki da babbar ƙotun ƙungiyar ƙasashen ta Yammacin Afrika a Najeriya. Domin jin yadda masana ke kallon lamarin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Barista Abubakar Mujitafa Gagare, ƙwararren lauya da ke Najeriya. Latsa alamar sauti don jin yadda tattaunawar ta gudana...

Al'ummar Musulmai a sassan duniya, sun ɗauki azumin farko a bana, bayan da ƙasashen duniya ciki har da Saudiyya da Najeriya suka sanar da ganin jinjirin watan Ramadana. Azumin Ramadan lokaci ne da al'ummar musulmai ke amfani da shi wajen ƙara kusanci da mahallicinsu, da kuma ƙarfafa imani tare da nesantar aikata laifuffuka. A tattaunawar sa da Ahmad Alhassan, Imam Abubakar Muhammad malamin addinin musulunci ne a Najeriya, yayi mana ƙarin haske game da falalar azumin Ramadana. Latsa alamar sauti don sauraren hirarsu...

Masana Tarihi gami da Siyasar Duniya sun fara yin tsokaci kan matsayar da ƙungiyar ƙasashen Afrika AU ta tsaida na amincewa da ƙudurin bayyana cinikin bayi da kuma bautar da su gami da Mulkin Mallakar da Turawan yamma suka yi wa Nahiyar a matsayini kisan ƙare dangi da kuma laifukan take hakkin ɗan Adam. Shugabannin ƙasashen nahiyar ta Afrika sun cimma matsayar ce a Lahadin da ta gabata, yayin ƙarƙare taronsu na shekara karo na 39 a birnin Addis Ababa. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Tijjani Muhd Naniya, masanin tarihi da ke jami'ar Bayero a Kano, Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

A karon farko shugaban mulkin sojin Nijar Janar Abdulrahmane Tchiani ya kai ziyara Aljeriya, irinta ta farko da ya kai zuwa wata ƙasa da ba mamba ba a cikin ƙawancen AES, tun bayan ɗarewarsa karagar mulki ta hanyar juyin mulkin da ya kawo ƙarshen gwamnatin Mohamed Bazoum. Abba Sadiq, masanin siyasar yankin Saleh, ya ce dama alaƙa bata taɓa lalacewa tsakanin Nijar da Aljeriya. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsa da Ruƙayya Abba Kabara...

Wata cibiya da ke bibiyar ayyukan Kamfanonin sojojin haya a sassan Duniya, ta ce kusan mutane dubu 1 da 500, Rasha ta ɗiba daga ƙasashen Afrika aƙalla 35, a matsayin sojojin haya a yaƙin da take gwabzawa da Ukraine. Rahoton ya ƙara da cewar daga cikin jimillar ‘yan Afrikan da suka shigar wa Rasha yaƙin da take da Ukraine a tsakanin shekarar 2023 zuwa tsakiyar bara, 316 sun mutu. Don jin irin kallon da masana tsaro ke yi wa lamarin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Kabiru Adamu, shugaban kamfanin Beacon Consulting mai binciken tsaro a nahiyar Afrika. Latsa alamar sauti don jin yadda tattaunawarsu ta gudana...

A ranar Litinin da ta gabata, mahukuntan Najeriya suka buɗe iyakokinsu da Nijar da kuma Jamhuriyar Benin ta ɓangaren jihar Kebbi, matakin da ya maido da zirga-zirgar kasuwanci tsakanin ƙasashen uku. Gabanin buɗe iyakokin dai sai da aka gana tsakanin wakilan Najeriya da na Nijar, matakin da ya kawo ƙarshen katse jigilar manyan motocin dakon kaya fiye da Dubu Ɗaya da Ɗari Biyar, da suka shafe aƙalla wata guda a tsaye. Domin jin ƙarin bayani kan lamarin Nura Ado Suleiman ya tattauna da Alhaji Sani Shekarau, shugaban ƙungiyar manyan ‘yan kasuwa da ke jigilar kayayyaki zuwa ciki da wajen Jamhuriyar Nijar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

Ɗaruruwan ‘yan Najeriya a jiya Litinin, sun gudanar da zanga-zangar lumana a birnin Abuja, domin bayyana ɓacin ransu dangane da jan ƙafa a kan gyaran dokar zaɓe da majalisar ƙasar ke yi, musamman kan matakinta na ƙin amincewa da batun tilasta wa hukumar zaɓe sakin sakamako kai-tsaye daga rumfuna a shafinta na yanar gizo.Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Barista Ibrahim Bello Rigachikun, tsohon ɗan Majalisar Tarayya, kuma ƙwararren lauya a Najeriyar. Latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawar

Kungiyar IPOB da ke fafutukar neman ɓallewar Yankin Kudu Maso Gabashin ƙasar daga Najeriya, ta sanar da kawo ƙarshen tilasta wa jama'a zaman gida a kowace ranar litinin yau kusan shekaru biyar kenan. Matakin dakatar da tilasta zama gidan da ƙungiyar ta sanar a jiya lahadi, ya zo ne bayan da gwamnan jihar Anambra ya buƙaci jama'a su bijire sannan su ci gaba fita kowace litinin domin gudanar da harkokinsu na yau da kullum. Alhaji Ibrahim Abdulƙadir Ɗan-Ghali shi ne jagoran ƙawancen ƙungiyoyin ƴankasuwa ƴan asalin Arewacin Najeriya mazauna jihar Imo, ya bayyana wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal matsayinsu game da sanarwar ta IPOB. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Babban Sifeton Ƴansandan Najeriya Kayode Egbetokun, ya aike runduna ta musamman domin mara wa sojoji baya wajen tabbatar da tsaro a ƙaramar hukumar Kaiama da ke jihar Kwara, inda ‘yan ta'adda suka salwantar da rayukan mutane kusan 170. Yanzu haka dai ana dakon ganin tasirin matakan da haɗin gwiwar jami'an tsaron Najeriyar zai yi wajen murƙushe matsalar tsaron da ke daɗa ƙamari, lamarin da ke ta'azzara duk da jerin farmakin da jami'an tsaro ke kaiwa, tare da tarwatsa sansanonin ‘yan ta'adda a sassan arewacin ƙasar. Kan wannan lamari Nura Ado Suleiman ya tattauna da Kaftin Abdullahi Bakoji mai ritaya masanin tsaro a Najeriya.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta ware 4 ga watan kowane watan Fabarairu a matsayin ranar yaƙi da Cutar Daji ko kuma Cancer ta Duniya, wadda hukumar lafiya ta Duniya WHO ke jagorancin gangamin wayar da kai a kanta, gami da bayyana halin da ake dangane da kula da masu fama da ita. Wannan rana ta zo ne a daidai lokacin da wani sabon rahoton masana ya ce daga cikin kusan mutane miliyan 19 da suka kamu da cutar ta Daji a shekarar 2022, ana iya bayar da kariya ga aƙalla mutane miliyan 7 daga kamuwa da cutar in da an ɗauki matakan da suka dace. Domin jin ƙalubalen da ƙasashe masu tasowa kamar Najeriya ke fuskanta dangane da cutar, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Shehu Usman AbdulMumin Maƙarfi, ƙwararren Likita a Jihar Kaduna da ke Najeriya. Sai a latsa alamar sautin da ke sama domin sauraron bayanan Dakta Shehu Usmanu Maƙarfi....

Amurka ta sanar da tura wata tawagar sojinta zuwa Najeriya, abinda a karon farko ke tabbatar da isar dakarun nata ƙasar, tun bayan ƙarfafa yarjejeniyar tsaron da ƙasashen biyu suka yi, biyo bayan zargin da shugaba Donald Trump ya yi a shekarar bara, cewa ana kashe Kiristoci a Najeriyar. Kwamandan rundunar sojin Amurka da ke kula da Afirka, Janar Dagvin R.M. Anderson ya ce sun tura dakarun ne a bisa amincewar Najeriya. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Yahuza Ahmed Getso masanin tsaro a Najeriya. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.......

A Najeriya, alamu na nuni da cewa gwamnatin Anambra ta kama hanyar kawo ƙarshen barazanar ‘yan awaren IPOB da ke tilasta wa jama'a zaman gida a kowace ranar Litinin, bayan da a jiya aka buɗe kasuwanni a jihar, biyo bayan umarnin ga gwamna Charles Suludo ya bayar na ko dai su buɗe ko kuma ya rufe su a sauran kwanakin mako. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Alhaji Abdullahi Bebeji shugaban Ƴan Kasuwar da ke hada-hadar kayan Gwari a babbar kasuwar Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken bayani......

A Njeriya rahotanni daga Kaduna na nuni da cewar 80 daga cikin mutanen nan da aka bayyana cewar an sace a wata Majalimi'a da ke a Kurmin Wali sun kubuta daga masu garkuwa da su, sun dawo gida, bayan sun share tsawon lokaci suna tafiya a cikin Dokar Daji. To sai dai abin da ke ɗiga ayar tambaya shi ne yawansu su 80 su kuɓuta a hannun ƴan ta'adda abu ne da ke buƙatar bayani. Dangane da haka na samu zantawa da wani shugaban al'umma a Kurmin Wali wanda ya bayyana cewar akwai ƙamshin gaskiya a labarin kuɓutar mutanen amma ya bukaci a sakaya sunansa. A latsa alamar sauti domin sauraron cikakken zaantawar Faruk Muhammad Yabo da wani shugaban al'umar

A farkon makon nan, gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin maido da tsaffin sojoji bakin aiki, domin taimaka wa wajen samar da tsaro a yankunan da ke fuskantar barazanar ƴan ta'adda a sassan ƙasar. Sanar da matakin na zuwa ne bayan kafa wani kwamiti mai mambobi 18 da ministan tsaron na Najeriya Janar Chrisroper Musa mai ritaya ya jagoranci samarwa, wanda ya ce aikinsa shi ne tabbatar da ƙwato dukkanin yankunan da ke ƙarƙashin ikon ƴan ta'adda. Dangane da wannan Nura Ado Suleima ya tattauna da Dakta Auwal Aliyu Abdullahi, mai magana da yawun Kwamitin musamman da ke kula da walwalar tsaffin sojoji a Najeriya.

Yau ake cika shekaru biyu da ficewar ƙasashen Nijar da Mali da kuma Burkina Faso daga cikin ECOWAS, KO CEDAEO, biyo bayan matsin lambar ƙungiyar ta yi musu saboda juyin mulkin da sojojinsu suka yi, da kawar da matsalolin da suka zargi gwamnatociin da suka hamɓarar da gaza magancewa. Domin tsokaci kan halin da ƙasashen na AES ke ciki, shekaru biyu bayan matakan da mahukuntansu suka ɗauka, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Abdel Nasser Saidu ɗaya daga cikin wakilan kungiyoyin farraren fula a Nijar..

Wani sabon rahoton masana, ya nuna cewar yawan tallafin bashi da China ke bai wa ƙasashe marasa ƙarfi musamman na Afrika ya ragu matuƙa daga kashi 124 cikin shekaru 10 da suka gabata zuwa kashi 56. A cewar rahoton, wannan na zuwa ne , a yayin bashin da ƙasashen na Afrika suke biyan ƙasar ta Sin ke ci gaba da ƙaruwa, fiye da tallafin da suke samu daga gareta ba. Ga misali a tsakanin 2000 zuwa 2023 China ta tallafa wa ƙasashen Afrika 49 da bashin Dala biliyan 182, to amma a shekarar 2024, tallafin Dala Biliyan 2.1 kawai ta samar. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna na Farfesa Mansur Idris na Jami'ar Bayero da ke Kano. Shiga alamar sauti domin sautraron cikakkiyar tattaunawar.

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da yunkurin yi wa shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu juyin mulki a watan Oktoban shekarar bara, lamarin da ya kai ga cafke wasu jami'an soji da ake zargin da hannunsu a yunƙurin. A jiya Litinin ne dai Hedikwatar tsaron Najeriya ta hannun kakakinta Manjo Janar Sama'ila Uba ta tabbatar da lamarin, tare da sanar da miƙa rahoton bincikenta ga shugaban Najeriya. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da masanin tsaro a Najeriya Muhd Sani Ibrahim Makiga. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

A Najeriya babban abin da mafi yawan mutane ke neman ƙarin haske a kai su ne abubuwan da ke ƙunshe a yarjejeniyar tsaron da aka ƙulla tsakanin ƙasar da Amurka domin kawo ƙarshen ƴanbindigar da Amurkan ta ce suna yi wa Kiristoci kisan gilla. A game da wannan yarjejeniyar ce Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Yahuza Getso, masani tsaro da ke game da ayykan ƴanbingar da suka addabin jama'a, ga kuma yadda zantawarsu ta gudana. A latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar zantawar.

Amurka ta kawo ƙarshen tallafin da ta ke bayar wa a hukumar Lafiya ta Duniya WHO daga wannan Alhamis, 22 ga watan Janairun 2026, duk kuwa da kasancewarta jigo wajen samar da kuɗaɗen tafiyar da hukumar wadda ke samar da tallafin magunguna da sauran ɓangarorin lafiya ga ƙasashe da dama musamman masu tasowa. Donald Trump ya sanar da aniyar janyewar ƙasar daga hukumar koda yake tun a wancan lokaci ya ƙulla yarjejeniyar cewa sai bayan shekara guda ne ficewar za ta fara aiki a hukumance. Kan haka ne Faruk Muhammad Yabo ya tattauna da Dr Adam Mustapha na sashen nazarin ƙananan halittu a jami'ar Maiduguri ya yi mana tsokaci kan illar da matakin na Amurka ka iya haifarwa.

Mahukuntan soji a Burkina Faso sun bayyana mutukar jin ɗaɗinsu tare da mika godiya ga ƙasar Togo, dangane da namijin ƙoƙari na miƙa musu tsohon shugaban riƙon ƙwaryar ƙasar, laftanar kanar Henri Damiba, wanda su ke zargi da yunƙurin juyin mulki a lokuta da dama.Damiba zai fuskanci kotu domin amsa wannan tuhuma.... Abdoulaye Issa ya tattauna da Farfesa Ali Sakola Jika malami a jam'iar Ouagadougou.

Makomar ayyuka da tsarin haƙar ma'adanai na cikin batutuwan da a ‘yan kwanakin nan ya ɗauki hankali a Najeriya, inda a gwamnatin ƙasar ta musanta zargin cewa tana shirin kafa matatar zinare mallakinta a jihar Legas da ke kudancin ƙasar. Tun da fari, ƙungiyar dattawan arewacin Najeriya ce ta yi wannan ƙorafi cikin wata buɗaɗɗiyar wasiƙa, inda ta bayyana matakin a matsayin rashin adalci, la'akari da cewar yankunan arewa maso yammaci da tsakiyar Najeriya ne ke da arzikin na Zinare. Kan wannan da wasu batutuwan masu nasaba, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Injiniya Datti Yusuf Yahya ƙwararre kuma tsarawa da bayar da shawara kan ayyukan haƙar ma'adanai a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Yau Donald Trump ke cika shekara guda da komawa shugabancin Amurka, wa'adin da wasu ke ganin tamkar shugaban ya shafe shekara da shekaru bisa mulkin, la'akari da jerin matakan da ya riƙa aiwatarwa a matakin ƙasa da ƙasa da kuma cikin gida, ba tare da la'akari da caccakar da ake yi masa ba a gida da waje. Domin jin hasashen masana kan abinda ke tafe a ragowar shekaru uku da suka rage wa shugaban na Amurka Donald Trump, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta AbdulHakim Garba Funtua masanin siyasar ƙasa da ƙasa. Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawarsu...........

A daren jiya ne aka kammala gasar lashe kofin nahiyar Afrika ta AFCON da Morocco ta karɓi bakunci, inda Senegal ta samu nasarar lashe gasar a karo na biyu a tarihi. Masu sharhi kan lamuran wasanni na kallon gasar a matsayin wacce aka inganta, sai dai ba a rasa ƙalubale nan da can da aka samu ba. Khamis Saleh ya zanta da Aliyu Lawal Ibrahim wanda akafi sani da Ali Cairo, tsohon ko-odinetan hukumar CAF kuma tsohon sakataren tawagar ƴan ƙasa da shekaru 20 ta Najeriya, wanda ya halarci gasar, Ku latsa alamar sauti don sauraron yadda zantawarsu ta kasance...........

Gamayyar Ƙungiyoyin ma'aikatan lafiya a Najeriya sun sha alwashin ci gaba da yajin aikin da suka faro tun cikin watan Nuwamban bara, a faɗin ƙasar, duk da cewar gwamnati ta yi gargaɗin dakatar da biyansu albashi muddin basu koma bakin aiki ba. Tuni dai yajin aikin ma'aikatan lafiyar ya jefa masu jinya cikin mawuyacin hali la'akari da makwannin da aka shafe ba tare an cimma matsaya a tsakanin masu yajin aikin da mahukuntan ƙasar ba. Kan wannan Faruk Muhd Yabo ya tattauna da Dakta Shehu Usman AbdulMumin Maƙarfi, ƙwararren Likitia a Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraren yadda tattaunawarsu ta gudana...

Najeriya ta rasa damar kai wa matakin buga wasan ƙarshe na gasar cin kofin ƙasashen Afrika, bayan da ta yi rashin nasara da ƙwallaye 4-2, a karawar da ta yi da mai masaukin baƙi wato Morocco. An dai ƙarƙare wasan ne a matakin bugun daga kai sai mai tsaron raga wato Fanareti, bayan da aka buga mintuna 90 har da ƙarin lokaci na wasu minitunan 30 ba tare da ɓangarorin sun jefa wa junansu ƙwallo ba. Shiga alamar sauti domin sauron cikakkiyar hirar.....

Hedikwatar rundunar sojin Amurka mai kula da nahiyar Afirka, AFRICOM, ta sanar da miƙa wa gwamnatin Najeriya taimakon kayayyakin aikin soji, matakin da ke ƙarfafa yarjejeniyar tsaron da ke tsakaninsu don yaƙi da ta'addanci. Sai dai cikin sanarwar da ta wallafa a shafinta na X, rundunar sojin Amurkan ba ta yi ƙarin bayani kan nau'ika da kuma adadin makaman ba. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Kabiru Adamu shugaban kamfanin Beacon Consulting da ke bincike kan tsaro a nahiyar Afrika.

Gwamnatin Iran ta ce tabbas an buɗe hanyoyin tuntubar juna tsakaninta da Amurka, bayan da shugaba Donald Trump ya yi barazanar yin amfani da ƙarfi kan ƙasar matuƙar ta ci gaba da kashe masu zanga-zanga. Mahukuntan Iran dai na ƙoƙarin shawo kan ɗaya daga cikin bore mafi muni da suka taɓa faruwa a ƙasar. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon jakadan Najeriya a Iran Amabasada Abubakar Cika, ga kuma zantawarsu dangane da wannan tarzoma ta Iran. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

A yayin da Dalibai su ka koma makarantu a jihohi daban daban na tarayyar Najeriya, wata matsalar da ake fama da ita, ita ce ta wasu yankuna na jihohin kasar da kusan kashi 70 zuwa 80 na Daliban ba sa zuwa Makaranta saboda matsalolin tsaro. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hirar Faruk Yabo da Hon. Habibu Halilu Modachi

A Najeriya, gobe Alhamis 1 ga watan Janairu ne, za a fara aiwatar da sabuwar dokar haraji ta ƙasa, a cikin yanayi da dokar ke shan suka saboda dalilai da dama. Yayin da jama'a ke cewa sabon tsarin karɓar haraji na matsayin ƙarin nauyi ne ga al'umma, hakazalika wasu ƴan majalisa sun yi zargin cewa abin da suka amince da shi ya sha bambam da abin da gwamnati ke shirin aiwatarwa. A game da shirin aiwatar da dokar ne Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dakta Mahdi Shehu da ke fafutuka a Najeriya, ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

A jamhuriyar Nijar yanzu haka ana ci gaba da mahawara dangane da matakin da mahukuntan ƙasar suka ɗauka da ke shelanta kafa dokar-ta-ɓaci, wanda a ƙarƙashinta gwamnati za ta iya yin amfani da illahirin al'ummar ƙasar da kuma dukiyoyinsu a duk lokacin da ta ga ya dace don tunkarar barazanar tsaro. Maman Wada na ƙugiyar Transaparency International reshen Nijar Ga dai abin da ya shaida wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal. Shiga alamar sauti domin sauraron karin bayani.....

A Najeriya, ko baya ga farbaga dangane yadda Amurka ta fara kai hare-hare ta sama a kan waɗanda ta kira a matsayin ƴanta'adda a yankin arewacin ƙasar, wani abin tambaya shi ne halascin ɗaukar mataki bai wa wata ƙasa ta ƙetare damar yin amfani da sojojinta ba tare da amincewar majalisun dokokin ƙasar ba. Abdoulkarim Ibrahinm Shikal ya zanta da masani doka Barrister Modibbo Bakari Danna alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hirar.......

Da sanyin safiyar yau Juma'a aka wayi gari da sanarwar gwamnatin Najeriya da ke tabbatar da harin da Amurka ta kai a wasu yankunan ƙananan hukumomin Tambuwal da Tangaza, da ke jihar Sokoto a yankin arewa maso yammacin ƙasar. Ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Maitama Tuggar, ya ce Amurka ta kai hare-haren ne tare da haɗin gwiwar dakarun ƙasar, a wani ɓangare na ƙawancen da suka ƙulla da zummar murƙushe ta'addanci. Dangane da wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Yahuza Gesto masanin tsaro da ke tarayyar Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawar...

Shugaban Najeriya Bola Ahmad Tinibu ya ƙaddamar da ababen hawa na sufuri masu amfani da lantarki guda dubu 3 da 620 da gwamnatin jihar Borno ta tanadar domin sauƙaƙa sufuri a tsakanin al'ummarta. Motocin sun haɗa ne da Kekuna dubu 3 da babura masu ƙafa 3 ko kuma adaidaita sahu guda 500 sai kuma ƙanana da manyan Motocin safa ko kuma bas bas masu ɗaukar mutum 20 da 42 guda 100, kari ga wasu motoci 650 masu amfani da lantarki da gwamnati ta samar don sufuri. Dangane da wanna ne Faruk Muhammad Yabo ya tattauna da Dauda Iliya mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Borno a fannin watsa labarai inda ya fara da tambayarsa yadda ababen hawan suke da kuma yawansu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar...

Majalisar wakilan Najeriya ta gudanar da wasu sauye-sauye ga dokar zaɓen ƙasar yayin zaman da ta yi a jiya Alhamis. Kuma daga cikin batutuwan da suka fi ɗaukar hankali akwai ƙara yawan kuɗaɗen da doka ta ƙayyade ɗan takara zai iya kashewa a yaƙin neman zaɓe, da kuma tilasta amfani da na'urorin tantance masu kaɗa ƙuri'a, gami da watsa sakamakon zaɓe kai tsaye. Sauyin dai na nufin daga yanzu masu neman shugabancin ƙasa na iya kashe Naira biliyan 10, saɓanin Naira biliyan 5, yayin da aka ƙara kasafin ‘yan takarar gwamna daga Naira Biliyan 1 zuwa biliyan 3. Domin jin yadda masana doka ke kallon wannan mataki, Nura Ado Suleiman ya tuntuɓi Barista Al-Zubair Abubakar da ke Najeriya. Latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana...

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya maye gurbin Engr Faruk Ahmed da Aliko Dangote ya zarga da hana ruwa gudu wajen harkokin kula da kasuwancin mai da kuma bada lasisi ta NMDPRA, tare da shugaban hukumar NUPRC. Fadar shugaban Najeriya ta ce jami'an biyu sun sauka daga mukaman su ne bisa dalilai na ƙashin kan su. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ibrahim Garba Wala kan lamarin. Ku latsa alamar sauti don jin yadda tattaunawarsu ta gudana...

A farkon wannan Kotun Ƙolin Najeriya ta tabbatar wa shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ƙarfin ikon kafa dokoar ta ɓaci a kowace jiha da ke faɗin ƙasar, idan buƙatar hakan ta taso, domin tabbatar da zaman lafiya. Yayin yanke hukunci kan ƙarar da gwamnatocin jihohin da ke ƙarƙashin jam'iyyar PDP suka shigar, Kotun ta ce shugaban ƙasa na da ikon dakatarwar wucin gadi ga zaɓaɓɓun shugabannin jihar da dokar ta ɓacin ta shafa. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Barista Ibrahim Bello Rigachikun da ke Najeriya.

Ƙasashen AES da suka hada da Mali da Nijar da kuma Burkina Faso, sun ƙalubalanci Najeriya sakamakon saukar gaggawar da jirgin sojin ta da ya yi a Burkina. Waɗannan ƙasashe na zargin Najeriya da keta haddin sararin samaniyar yankin su. Domin tattauna wannan batu da kuma yunkurin juyin mulkin da ya gudana a Benin, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Amb Abubakar Cika, tsohon Jakadan Najeriya a Iran. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana...........

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya jinjinawa sojojin ƙasar saboda rawar da suka taka wajen murkushe yunkurin juyin mulkin da aka samu a Jamhuriyar Benin. Tinubu ya ce hare haren sojin sama da kuma tura sojojin ƙasa cikin ƙasar, sun bada gagarumar gudumawa wajen kawar da sojojin da suka sanar da kwace ikon. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Air Commodore Tijjani Baba Gamawa mai ritaya. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu................

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta sanar da shirin dawo da illahirin makarantun na tsangaya guda 157 da ke sassan ƙasar zuwa ƙarƙashin cikakkiyar kulawarta ma'aikatar ilmin ƙasar. Ƙarƙashin sabon tsarin, duknannin ɗaliban da ke cikin irin waɗannan makarantu ba za a kira su da suna jahilai ba. Khamis Saleh ya zanta da Imam Bukhari Maraban Jos, shugaban gamayyar makarantun tsangaya a jihar Kaduna, wanda kuma ke da masaniya dangane da tsarin, ga kuma zantawarsu.

Sabon ministan tsaron Najeriya Janar Christopher Musa mai ritaya ya sha alwashin murƙushe barazanar ƴan ta'adda tare da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali tsakanin jama'ar Najeriya, inda ya ce nan gaba kaɗan jama'a za su ga gagarumin sauyi. Janar Musa wanda ya yi rantsuwar kama aiki a cikin makon nan, ya sanar da wasu daga cikin tsare-tsaren da zai yi amfani da su a sabon salon yaƙi da ta'addancin da zai faro, ciki har da mayar da ilahirin sojoji bakin daga don fatattakar ɓatagari da kuma hana biyan ƴan ta'addan fansa dama kawo ƙarshen sulhu dasu. Dangane da wannan ne Azima Bashir Aminu ta tattaunawa da masanin tsaro Squadron Leader Aminu Bala Sokoto. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Babban Bankin Najeriya ya sanar da cire shingen kuɗaɗen da jama'a ke ajiyewa a bankuna da kuma ƙara yawan kuɗin da ake ɗauka a bankin. Bankin ya ce daga yanzu an ƙara yawan kuɗin da mutum ka iya cirewa daga naira 100,000 zuwa naira 500,000, yayin da bankin ya ci gaba da riƙe naira N100,000 a matsayin kuɗin da mutum guda ka iya cirewa a ATM a rana guda. Domin duba tasirin wannan mataki, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki Dakta Isa Abdullahi, na Jami'ar Kashere, da ke jihar Gombe a Najeriya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatar da sunan Janar Christopher Musa mai ritaya ga majalisar Dattawa domin amincewar ta ya zama ministan tsaro. Christopher Musa ya yi aiki a matsayin babban hafsan tsaron Najeriya daga ranar 23 ga watan Yunin 2023 zuwa 30 ga watan Octoban 2025, lokacin da shugaban ƙasar Bola Ahmad Tinubu ya yi masa ritaya. Idan majalisa ta amince, Janar Musa zai maye gurbin Badaru Abubakar da ya yi murabus a ranar Litinin. Bayanai sun nuna cewa fannonin da Musa ya fi ƙwarewa a kai shine fatattarkar ƴan ta'adda, da dubarun yaƙi, kasancewar ya yi aiki a matsayin jagoran rundunar sojojin Najeriya da ke kula da tsaron iyakokin Najeriya ta arewa maso gabashi da kuma yankin tafkin Chadi, haka nan ya kuma yi aiki a matsayin guda daga cikin dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya a Sierra Leone, da kuma wasu ayyukan a Amurka da Majalisar Ɗinkin Duniya.. Domin sanin tasirin wannan nadin da kuma kalubalen dake gaban Janar Musa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon kakakin rundunar sojin kasa ta Najeria, Janar Sani Usman Kukasheka mai ritaya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Ƴan Najeriya na ci gaba da neman bayani a kan yadda wasu kuɗaɗen da aka tara, da yawan su ya kai dala miliyan 30 domin samar da tsaro a makarantu suka shiga, sakamakon sake dawowar satar ɗalibai a yankin arewacin ƙasar. A ƙarƙashin wannan shirin da ya fara a shekarar 2014, kasashe da dama suka tallafawa Najeriya, cikin su har da ƙasar Norway da ta bada dala miliyan guda, da wata dala miliyan guda daga Bankin Raya ƙasashen Afirka na AfDB, sai kuma Fam miliyan guda daga gwamnatin Birtaniya. Gwamnatin Switzerland ta bada taimakon dala miliyan takwas, yayin da Amurka ta bada dala miliyan biyu, sai kuma Qatar da ta bada dala miliyan biyu, yayin da ƴan kasuwan Najeriya su kuma suka bada taimakon dala miliyan 10. Ganin yadda aka kasa samar da tsaron a makarantu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Abubakar sadiq Umar Gombe. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Kamar dai kowace shekara, 1 ga watan Disamba ita ce ranar da Hukumar Lafiya ta Duniya ta keɓe don yaƙi da cuta mai karya garkuwar jikin ɗan Adam wato HIV ko kuma SIDA. Bikin na bana ya zo ne a cikin wani yanayi da shugaba Donald Trump ya katse tallafin da Amurka ke bai wa ƙasashe masu tasowa ciki har da na ɓangaren yaƙi da wannan cuta. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Nasir Sani Gwarzo ƙwararren likitan yaƙi da annoba a Najeriya, wanda ya fara da bayyana halin da ake ciki game da yaƙi da HIV a ƙasar. Ga zantawarsu.

A tsakiyar wannan mako, shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya shelanta kafa dokar ta ɓaci kan sha'anin tsaro a faɗin ƙasar, matakin da a ƙarƙashi ya bayar da umarnin ɗaukar sabbin jami'an Ƴansanda dubu 50,000 domin murƙushe matsalolin tsaron da ke ta'azzara. Kan wannan, da wasu ƙarin matakai da ake shirin ɗauka a ƙarƙashin dokar ta ɓacin kan tsaro Nura Ado Suleiman ya tattauna da Kanal Muhd Sani Makiga mai ritaya, masanin tsaro a Tarayyar Najeriyar. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

A jiya ne sojoji suka hambarar da gwamnatin shugaba Umaro Sissiko Embalo, sakamakon rikicin zaɓen shugaban ƙasar da aka yi a ƙarshen mako, a daidai lokacin da ake shirin gabatar da sakamako yau Alhamis. Shugaban da madugun yan adawa duk sun yi iƙrarin nasara, a kasar da ta yi ƙaurin suna wajen juyin mulki. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Tukur Abdulkadir dangane da juyin mulkin, wanda shi ne na biyar a kasashen Afirka ta Yamma, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.

Gwamnatocin wasu jihohin dake arewacin Najeriya sun sanar da matakan rufe makarantun firamare da sakandare, wasu ma harda jami'oi, domin kaucewa matsalar garkuwa da daliban da ake samu, wanda ya kara ta'azzara a kasar. Domin duba tasirin matakin da kuma halin da yankin ya samu kan sa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Bello Bada na Jami'ar Usman Dan Fodio dake Sokoto. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bada umarnin ɗaukar sabbin ƴansanda dubu 30 da kuma janye masu gadin manyan mutane ba bisa ƙa'ida ba. Domin sanin tasirin wannan mataki da kuma yadda zai taimaka wajen inganta tsaro a ƙasar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon mataimakin Sifeto Janar na Ƴansandan Najeriya Malam Ahmad Abdurrahaman. Ku latsa alamar sauti donjin yadda zantawarsu ta gudana.............