Bakonmu a Yau

Follow Bakonmu a Yau
Share on
Copy link to clipboard

A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban…

Rfi - Azima Bashir Aminu


    • Oct 1, 2025 LATEST EPISODE
    • weekdays NEW EPISODES
    • 3m AVG DURATION
    • 996 EPISODES


    Search for episodes from Bakonmu a Yau with a specific topic:

    Latest episodes from Bakonmu a Yau

    Atiku Abubakar akan cikar Najeriya shekaru 65 da samun 'yancin kai

    Play Episode Listen Later Oct 1, 2025 3:49


    Yau Najeriya ke bikin cika shekaru 65 da samun yancin kai daga Turawan mulkin mallaka na Birtaniya. A irin wannan lokaci akan yi tilawa da kuma nazari dangane da ci gaban da kasar ta samu da kuma kalubalen dake gaban ta. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar dangane da halin da kasar ke ciki, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.

    akan atiku abubakar najeriya birtaniya bashir ibrahim idris
    Dalilan rikici tsakanin Ɗangote da masu ruwa da tsaki a harkar man Najeriya

    Play Episode Listen Later Sep 30, 2025 3:31


    A Najeriya, wani abu da ke neman ɗaure wa jama'a kai shi ne yadda ƙasa da shekara ɗaya da ƙddamar da ayyukanta, matatar mai ta Ɗangote ke fuskantar rigingimu daban daban, da suka haɗa da tsakaninta da dillalan mai masu zaman kansu, da ma'aikatan dakon mai wato NUPENG sai kuma wannan karo da PENGASSAN wato ƙungiyar manyan ma'aikatan mai da iskar gaz na ƙasar. A game da waɗannan rigingimu ne Abdoulkarim Ibrahim Ibrahim Shikal ya zanta da masani harkar mai a ƙasar wato Alhaji Ɗayyabu Yusuf Garga, domin sanin wasu daga cikin dalilan faruwar hakan. Ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

    Tattaunawa da Farfesa Ouba Ali Mahamman masanin siyasa game da zaɓen Kamaru

    Play Episode Listen Later Sep 29, 2025 3:34


    A ƙarshen makon da ya gabata aka fara yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a Kamaru, inda mutane 12 ciki har da shugaba mai-ci Paul Biya za su kara da juna a ranar 12 ga watan gobe na Oktoba idan Allah ya kai mu. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Farfesa Ouba Ali Mahamman, masani siyasar Kamaru da ke zaune a birnin Yaounde, wanda da farko ya bayyana bambancin da ke akwai tsakanin wannan zaɓe da kuma waɗanda aka saba yi shekarun baya a ƙasar. Ga dai abin da yake cewa. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

    Tattaunawa da Dakta Bolori akan rage kudin ruwa da babban bankin Najeriya ya yi

    Play Episode Listen Later Sep 26, 2025 3:33


    Babban bankin Najeriya CBN ya sanar da rage kuɗin ruwan da ake sanyawa masu karɓar bashi daga kaso 27.50 zuwa kaso 27 karon farko cikin shekaru huɗu. Wannan ci gaba na zuwa ne a dai-dai lokacin da hukumar tattara haraji ta Najeriya ke cewa ta sami ƙarin kuɗaɗen shiga da kaso 411%, amma hakan ba zai hana ci gaba da ciyo bashi da Najeriya ke yi ba.   A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara, Dr Ahmad Bolori masanin tattalin arziki a Najeriya ce, ragin kwabo 50 kachal yayi matuƙar kaɗan duk da cewa babu wani abu da talaka zai mora a wannan ci gaba. Ga dai yadda tattaunawar tasu ta kasance.

    Emmanuel Macron kan amincewa da ƙasar Falasɗinu da kuma yakin Ukraine da Rasha

    Play Episode Listen Later Sep 25, 2025 3:13


    Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce ƙasar Rasha ta yi rauni sosai a yaƙin da take gwabzawa da Ukraine. Macron ya bayyana haka ne a zantawa ta musamman da ya yi tashar talabijin ta France24 da Kuma RFI a gefen Babban Taron Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya a birnin New York, inda ya taɓo batutuwa da dama ciki har da amincewa da Palesdinu a matsayin ƙasa da daidai sauransu. Da farko dai Emmanuel Macron ya jinjina wa shugaba Amurka Donald Trump ne a game da ƙoƙarinsa don kawo ƙarshen rikicin Ukraine. Ku latsa alamar sauti don sauraron fassarar kalamansa...............

    Maitre Lirwanou Abdourahman kan ficewar Nijar Mali da Burkina Faso daga ICC

    Play Episode Listen Later Sep 24, 2025 3:32


    Burkina Faso, Mali da kuma Nijar sun sanar da janyewar ƙasashensu daga Kotun Hukunta Laifufuka ta Duniya da ke birnin Hague. A sanarwar haɗin-gwiwa da suka fitar cikin daren litinin da ta gabata, ƙasashen uku sun ce sun ɗauki matakin saboda sun lura cewa kotun ta rikiɗe domin zama ƴar amashin ƴan mulkin mallaka. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani dokokin ƙasa da ƙasa Maitre Lirwanou Abdourahman, domin jin ko wataƙila ya yarda da dalilan da wadannan ƙasashe suka gabatar. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

    mali ku burkina faso hague maitre daga duniya nijar najeriya amurka abdoulkarim ibrahim shikal
    Maitre Lirwanou Abdourahman kan janyewar ƙasashen AES daga kotun ICC

    Play Episode Listen Later Sep 24, 2025 3:32


    Burkina Faso da Mali da kuma Nijar sun sanar da janyewar ƙasashensu daga Kotun Hukunta Laifufuka ta Duniya da ke birnin Hague. A sanarwar haɗin-gwiwa da suka fitar cikin daren Litinin da ta gabata, ƙasashen uku sun ce sun ɗauki matakin ne saboda sun lura cewa kotun ta rikiɗe domin zama ƴar amashin ƴan mulkin mallaka. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani dokokin ƙasa da ƙasa Maitre Lirwanou Abdourahman, domin jin ko wataƙila ya yarda da dalilan da wadannan ƙasashe suka gabatar. Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawarsu.................

    Farfesa Tukur Abdulƙadir kan ƙarin ƙasashen da ke amincewa da Falasɗinu

    Play Episode Listen Later Sep 23, 2025 3:45


    Ƙasashen duniya na ci gaba da nuna amincewarsu da samar da ƴantacciyar ƙasar Falasɗinu, a wata guguwa wadda ba'a taɓa ganin irinta ba. Ƙasashen turai da ake ganin suna da ƙyakyawar alaƙa da Amurka irinsu su Burtaniya, Canada da kuma Australia a wannan Karo sun sanar da amincewar su da baiwa Falasɗinu damar zama ƙasa mai cin gashin kanta amma bisa wasu shariɗoɗi. A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara Farfesa Tukur Abdulƙadir ya ce har yanzu da sauran rina a kaba don kuwa amincewar waɗannan ƙasashe ƙadai a fatar baki bata wadatar ba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

    Tattaunawa da tsohon Jakadan Kamaru Ambasada Malam Mohamed Sani kan zaɓen ƙasar

    Play Episode Listen Later Sep 22, 2025 3:38


    A ƙarshen wannan mako ne za a ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a Kamaru, zaɓen da zai gudana a ranar 12 ga watan gobe na Oktoba. To sai dai yayin da jam'iyyar RDPC mai mulki ta bayyana Paul Biya a matsayin wanda zai tsaya mata takara, a nasu ɓangare kuwa, yanzu haka ƴan adawa, na ci gaba da tattaunawa don fitar da mutum ɗaya da zai tsaya zaɓen amadadinsu. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Ambasada Malam Mohamed Sani, tsohon jakada a lokacin mulkin Ahmadou Ahidjo, amma a yanzu yake zaune a ƙetare, inda ya bayyana yadda suke kallon wannan zaɓe.

    malam sani asar kamaru paul biya oktoba abdoulkarim ibrahim shikal
    Ambasada Mohamed Sani kan zaɓen shugaban ƙasa da za a yi a Kamaru

    Play Episode Listen Later Sep 22, 2025 3:38


    A ƙarshen wannan mako ne za a ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa da za a gudanar 12 ga watan gobe na Oktoba idan Allah ya kai mu a Kamaru. To sai dai yayin da jam'iyyar RDPC mai mulki ta bayyana Paul Biya a matsayin wanda zai tsaya mata takara, a nasu ɓangare kuwa, yanzu haka ƴan adawa, na ci gaba da tattaunawa don fitar da mutum ɗaya da zai tsaya musu takara a zaɓen. Kan haka Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Ambasada Malam Mohamed Sani, tsohon jakada a lokacin mulkin Ahmadou Ahidjo, amma a yanzu yake zaune a ƙetare, inda ya bayyana yadda suke kallon wannan zaɓe. Ƙu latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu............

    allah sani kamaru paul biya oktoba shugaban abdoulkarim ibrahim shikal
    Shugabannin ƙananan hukumomin Kwara sun sanar da rufe kasuwannin sayar da shanu

    Play Episode Listen Later Sep 19, 2025 3:06


    Shugabannin ƙananan hukumomi a yankin Kudancin jihar Kwara ta Najeriya sun sanar da rufe dukkannin kasuwannin sayar da shanu da aka fi sani da {Kara}. Mahukuntan sun ce sun ɗauki wannan mataki ne sakamakon tashin matsalolin tsaro da ake samu a kasuwannin. A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara shugaban ƙungiyar Miyetti Allah reshen jihar ta kwara, kuma guda daga cikin jagororin ƙungiyar kasuwannin kara na jihar Alhaji Shehu Garba ya ce sam basu yarda da wannan mataki ba. Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawar tasu....

    sanar rufe najeriya
    Hira da Issa Tchiroma Bakary game da zaɓen Kamaru da ƙoƙarin kawar da Paul Biya

    Play Episode Listen Later Sep 18, 2025 3:18


    Issa Tchiroma Bakary, wanda ya share tsohon shekaru 16 yana riƙe da muƙamin minista ƙarƙashin gwamnatin Paul Biya na Kamaru, a yanzu ya koma ɓangaren adawa inda yake ci gaba da jawarcin sauran ƴan siyasa na ƙasar. Tuni dai wani ƙawance da ya ƙunshi jam'iyyin adawa 11 ya bayyana goyon baya ga takararsa a zaɓen shugabancin ƙasar da za a yi ranar 12 ga watan gobe idan Allah ya kai mu. Radio France Internationale ya zanta da tsohon minista Issa Tchiroma, wanda da farko ya bayyana matsayinsa dangane da wannan goyon baya da ya samu, inda ya ci gaba da cewa.

    Dr. Musa Adamu game da yadda rashawa ke ci gaba da haɓaka a Najeriya

    Play Episode Listen Later Sep 17, 2025 3:03


    Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Nigeria wato ICPC, ta bayyana damuwa kan yadda matsalar rashawa ke ci gaba da haɓaka, duk kuwa da matakan da ta ke ɗauka. A cewar Shugaban hukumar ta ICPC, Dr Musa Adamu Aliyu, a yanzu sun karkata akalarsu ne zuwa ga ƙananan hukumomi, don daƙile matsalar cin hanci da ta yi katutu... Latsa alamar sauti don sauraron ƙarin bayanin da Dr Musa Adamu, ya yi wa wakilinmu Ibrahim Malam Goje........

    Isa Tafida Mafindi-Kan yadda talakawa zasu mori raba fetur da Ɗangote ya fara da motocinsa

    Play Episode Listen Later Sep 16, 2025 3:33


    Kamfanin Dangote ya fara aikin rarraba man fetur daga matatarsa zuwa sassan Najeriya domin saukakawa jama'a, a dai-dai lokacin da manyan dilallan man fetur ke adawa da matakin. Dashi Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki, Alahji Isa Tafida Mafindi a kan yadda talakawa zasu ci gajiyar wannan shirin. Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar.

    Uzairu Abdullahi kan buƙatun likitocin Najeriya masu neman ƙwarewa ga gwamnati

    Play Episode Listen Later Sep 15, 2025 3:29


    A makon da ya gabata ne likitoci da ke neman ƙawarewa a Najeriya suka gudanar da yajin aiki, domin nuna rashin amincewa dangane da yadda gwamnati ke jan ƙafa wajen ƙin biyansu haƙƙoƙinsu.To sai dai bayan da aka fara biyansu wasu daga cikin haƙƙoƙin, sun dakatar da yajin aikin tare da bai wa gwamnati ƙarin makonni biyu domin shafe musu hawayensu. Dr Uzairu Abdullahi, shi ne Editan Mujallar wallafa labarai ta ƙungiyar ya yi ƙarin bayani..... Latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawar da Abdoulkarim Ibrahim Shikal........

    abdullahi masu atun najeriya abdoulkarim ibrahim shikal
    Dr Mubarak Muhammad kan naɗin sabon firaministan Faransa Lecornu

    Play Episode Listen Later Sep 11, 2025 3:32


    Sabon firaministan Faransa Sebastien Lecornu ya karɓi ragamar tafiyar da mulkin daga hannun Francois Bayrou, wanda ƴan Majalisar dokokin ƙasar suka tsige a ranar Litinin ta gabata.Wannan dai shi ne Firaminista na 5 bayan da Emmanuel Macron ya karɓi ragamar mulki domin yin wa'adi na biyu, lamarin da ke nuni da cewa ƙasar na fama da rikici a fagen siyasa. Dr Mubarak Muhammad, mazauni Faransa kuma masani a game da salon siyasar ƙasar, ya bayyana wa Nura Ado Sulaiman mahangarsa a game da wannan batu. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tasu..................

    Mammane Wada kan yadda jamhuriyar Nijar ke ci gaba da shaƙe wuyan masu chachakarta

    Play Episode Listen Later Sep 10, 2025 3:33


    Gwamnatin mulkin sojin  Jamhuriyyar Nijar na ci gaba da kamen waɗanda ke sukar lamirinta da suka hadar da ƴan jarida da masu fafutuka har ma da ƴan siyasa. A wani rahoto da ta fitar a baya bayan nan kungiyar kare hakkin bil Adam Human Right Watch ta soki yadda sojojin da suka kwace muki a ƙasar ke tsare jama'a babu gaira babu dalili. Akan wanan abokin aiki Oumarou Sani ya tattaunawa da Mamane Wada shugaban kungiyar yaki da cin hanci da rashawa ga kuma yadda zantawarsu ta gudana.

    Mamane Wada akan yadda Gwamnatin sojin Nijar ke kama waɗanda ke sukar lamirinta

    Play Episode Listen Later Sep 10, 2025 3:33


    Gwamnatin mulkin sojin  Jamhuriyyar Nijar na ci gaba da kamen waɗanda ke sukar lamirinta da suka haɗar da ƴan jarida da masu fafutuka har ma da ƴan siyasa. A wani rahoto da ta fitar a baya bayan nan kungiyar kare haƙƙin bil Adam Human Right Watch ta soki yadda sojojin da suka ƙwace muki a ƙasar ke tsare jama'a babu gaira babu dalili. Akan wanan abokin aiki Oumarou Sani ya tattaunawa da Mamane Wada shugaban ƙungiyar yaƙi da cin hanci da rashawa ga kuma yadda zantawarsu ta gudana. Latsa alaamar sauti don sauraron yadda tattaunawar ta su ta gudana...........

    Nasiru Garba Ɗantiye kan ƙorafin shugaban majalisar wakilan Najeriya game da yawan ciwo bashi

    Play Episode Listen Later Sep 9, 2025 3:29


    Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya, Abbas Tajudeen, ya koka akan yadda bashi ya ke cigaba da yi wa ƙasar katutu, lamarin da ya ce yana barazana ga bunƙasar tattalin arziƙinta. Tajuddeen, wanda ya bayyana haka jiya Litinin a Abuja, ya ce bashin da ke kan Najeriya a yanzu ya kai wani matsayi mai ban tsoro, inda ya ke kira da a sake fasalin yadda ake karɓar rance a ƙasar. Akan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da wani tsohon ɗan majalisar dokoki a ƙasar, Nasiru Garba Ɗantiye, ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana.

    game akan abuja garba bashi najeriya shugaban majalisar
    Alhaji Dayyabu Garga akan batun fara yajin aikin ƙungiyar NUPENG a Najeriya

    Play Episode Listen Later Sep 8, 2025 3:33


    A wannan litinin, ƙungiyar NUPENG da ta haɗa direbobin motocin dakon mai da iskar gas a Najeriya ta fara yajin aiki, domin nuna rashin amincewa da yadda Ɗangote ke shirin yin amfani da motocinsa domin rarraba man fetur a sassan ƙasar. Shugabannin NUPENG, sun ce su ne ke da hurumin raba mai da kuma iskar gaz a Najeriya, a maimakon yadda Ɗangote ke shirin yin amfani da motoci dubu huɗu domin wannan aiki. Latsa alamar sauti domin sauraro.......

    akan najeriya
    Nijar a duk kullum za ta kare hakokin ƴan ƙasar mazauna ketare

    Play Episode Listen Later Sep 6, 2025 3:23


    Jamhuriyar Nijar a duk kullum za ta kare hakokin ƴan ƙasar mazauna ketare, Wasu daga ciki tarin matsalolli da ƴan Nijar mazauna ƙasashen ketare ke fuskanta sun hada da rashin takardun zama wadanan kasashe. Jakadan Nijar a Jamhuriyar Benin, Kadade Chaibou ya bayyana haka yayin zantawa da Abdoulaye Issa a ofishinsa dake birnin Kwatanu.

    asar wasu nijar jamhuriyar nijar abdoulaye issa
    Tattaunawa da Barr Al-Zubair kan jinkiri wajen gudanar da shara'o'i a Najeriya

    Play Episode Listen Later Sep 3, 2025 3:29


    Masu ruwa da tsaki kan sha'anin Shari'a a Najeriya sun sabunta ƙorafin da suke yi a kan matsalar jinkiri maras tushe, wajen gudanar da shara'o'i ko yanke hukunci kan waɗanda ake tuhuma da aikata manyan laifuka, musamman na ta'addanci. Ƙorafin ya sake bijirowa ne la'akari da yadda cikin ƙanƙanin lokaci mahukuntan ƙasar Finland suka zartas da hukunci kan Simon Ekpa, wani mai iƙirarin neman kafa ƙasar Biafra a Najeriya. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hirar....

    Muhammad Magaji kan ƙorafin manoma game da jinkirin raba kayayyyakin noma

    Play Episode Listen Later Sep 2, 2025 3:33


    Manoma a Najeriya na kokawa kan ƙarancin samun taimako daga gwamnati wajen sauƙaƙa musu ayyukan noma. Ƙorafi na baya bayan nan a Najeriyar shi ne jinkirin raba wasu kayayyakin noma ciki har da motocin Tantan aƙalla dubu biyu da gwamnatin Najeriyar ta sanar da sayowa yau fiye da watanni biyu, yayin da a gefe guda tuni daminar bana ta yi nisa. Kan wannan al'amari Nura Ado Suleiman ya tattauna da Alhaji Muhd Magaji, Sakataren tsare tsare na ƙungiyar manoman Najeriya.

    Fatima Baba Fugu akan 'yan Najeriya fiye da dubu 24 da suka ɓata

    Play Episode Listen Later Sep 1, 2025 3:34


    Ƙuniyar Agaji ta Red Cross ta ce yanzu haka akwai mutane sama da dubu 23 da suka ɓata a sassan Najeriya. A bayanin da ta fitar a jiya lahadi, ƙungiyar ta ce 68% na waɗanda suka ɓata dukanninsu mata ne, yayin da jihar Yobe ke matsayin jagora ta fannin yawan waɗanda lamarin ya fi shafa. Fatima Baba Fugu, tana aiki ne da sashen da ke haɗa waɗanda suka ɓata da iyalansu a ƙungiyar ta ICRC daga birnin Maiduguri jihar Borno, ta yi wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal ƙarin bayani a game da waɗannan alkaluma da ƙungiyar ta fitar.

    Dalilan PDP na baiwa kudancin Najeriya takarar shugaban ƙasa - Sen Ibrahim Tsauri

    Play Episode Listen Later Aug 28, 2025 3:33


    Taron Jam'iyyar PDP a ƙarshen makon da ya gabata, ya amince da bai wa yankin kudancin ƙasar damar gabatar da ɗan takarar zaɓen shugaban ƙaasr da za ayi a shekarar 2027, ya yin da ya haramtawa waɗanda suka fito daga arewacin ƙasar tsayawa takara. Tuni aka bayyana cewar wasu kusoshin jam'iyyar na zawarcin tsohon shugaban ƙasar Goodluck Jonathan da Peter Obi domin tsaya musu takara. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon Sakataren jam'iyyar, Sanata Umar Ibrahim Tsauri game da lamarin. Ku latsa alamar sauti don sauraron yadda zantawarsu ta gudana.................

    ku pdp peter obi tuni goodluck jonathan najeriya shugaban bashir ibrahim idris
    Janar Idris Bello Danbazau mai ritaya kan taron manyan hafsoshin tsaron Afrika

    Play Episode Listen Later Aug 27, 2025 3:33


    Manyan hafsoshin tsaron ƙasashen Afrika sun bayyana aniyar aiki tare a tsakaninsu domin tunƙarar matsalolin tsaron da suka addabi nahiyar, musamman ayyukan ta'addanci. Wannan ya biyo bayan taron da suka halarta a Najeriya. Dangane da wannan, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Janar Idris Bello Danbazau mai ritaya dangane don jin alfanun wannan sabin yunƙuri , ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana akai. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....

    afrika ku bello taron wannan najeriya bashir ibrahim idris
    Malam Isa Sunusi kan kisan da Isra'ila ta yi wa ƴan jaridu a Gaza

    Play Episode Listen Later Aug 26, 2025 3:46


    Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah wadai da kisan ƙarin ƴan jaridu 5 da Isra'ila ta yi a asibitin Khan Younes. Daraktan ƙungiyar a Najeriya, Malam Isa Sanusi ya buƙaci ƙasashen duniya da su tilastawa Isra'ila mutunta dokokin duniya wajen kare ƴan jaridun da ke gudanar da aikin su a ƙasar.  Ku latsa alamar sauti don jin yadda tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris ta gudana............

    Baba Ngelzerma kan rashin goyon bayan ta'addancin wasu ɗai-ɗaikun Fulani ke yi

    Play Episode Listen Later Aug 25, 2025 3:36


    Ƙungiyar Fulani ta Miyetti Allah a Najeriya, ta nesanta kan ta daga goyan bayan ayyukan ta'addancin da wasu ɗai-ɗaikun ƴaƴanta keyi, tare da bayyana cewar ita ta fi jin raɗaɗin matsalar. Shugaban ƙungiyar Baba Usman Ngelzerma ya ce aƙalla Fulani 20,000 aka kashe, yayin da suka yi asarar shanu sama da miliyan 4 ga ayyukan ta'addancin a shekaru 5 da suka gabata. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Bashir Ibrahim Idris.............

    baba ku bayan fulani wasu rashin najeriya shugaban bashir ibrahim idris
    Kafafen sadarwa sun zama babbar barazana ga zaman lafiyar Najeriya- Majalisa

    Play Episode Listen Later Aug 22, 2025 3:38


    Majalisar Dattawan Najeriya ta bayyana cewar ya zama dole ta yi dokokin da za su takaita yadda kafofin sada zumunta ke neman haifar da tashin hankali a cikin kasar. Shugaban masu rinjaye a Majalisar Bamidele Opeyemi ya bayyana haka, sakamakon zargin neman jefa kasar cikin tashin hankalin da matasa ke yi ta wadannan kafofi. Dangane da wannan yunkuri, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin harkar sadarwa,Malam Umar Saleh Gwani. Latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana...

    zaman najeriya shugaban bashir ibrahim idris
    Dr Abubakar Sadiq Muhammad kan matsalolin tsaro a Najeriya

    Play Episode Listen Later Aug 21, 2025 3:33


    Gwamnan Jihar Kaduna da ke Arewacin Najeriya, Uba Sani ya ce matakin soji kawai ba zai iya magance ayyukan ta'addancin da ake fuskanta a ƙasar ba. Gwamnan ya ce ya zama wajibi a magance matsalolin da ke haifar da matsalar baki ɗaya da suka haɗa da talauci da nuna banbanci da rashin shugabanci na gari da kuma bai wa matasa dama. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abubakar Sadiq Muhammad, tsohon malami a jami'ar Ahmadu Bello akan matsalar ta tsaro a ƙasar. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu...................

    ku sadiq abubakar najeriya bashir ibrahim idris
    Farfesa Balarabe Sani Garko kan rage farashin wanke ƙoda a wasu asibitocin Najeriya

    Play Episode Listen Later Aug 20, 2025 3:34


    Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya amince da rage farashin wankin ƙoda daga naira 50,000 zuwa naira 12,000 a manyan asibitocin tarayya a faɗin ƙasar. Daniel Bwala, mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan Bayanan da suka shafi tsare-tsaren gwamnati ne ya bayyana hakan a shafin sada zumuntansa na X, inda ya ce matakin zai sauƙaƙa wa dubban marasa lafiya masu fama da ciwon ƙoda. An fara aiwatar da wannan mataki a manyan asibitoci kamar FMC Ebute-Metta da ke Lagos da FMC da ke Jabi a Abuja da UCH Ibadan da FMC Owerri da UMTH Maiduguri, yayin da za a ƙara wasu kafin ƙarshen shekara domin samun damar amfani da su a duk faɗin ƙasar. Sai dai da safiyar Laraba bayan rahotannin RFI, Gwamnatin Najeriya ta ɗan daidaita jerin sunayen manyan asibitocin ƙasar da za su ci gajiyar sabon tallafin domin sauƙaƙawa majinyta wanke ƙoda, inda aka ƙara asibitin koyerwa na Malam Aminu Kano da ke jihar Kano. Cikin sanarwar da ma'aikatar lafiyar ƙasar ta fitar, ta ce za'a ci gaba da ƙara wasu asibitocin ne dama sannu a hankali, amma ba mantawa da wani sashin ƙasar akayi ba. Ga asibitocin da za su amfana da sabon ragin farashin ƙudin wankin ƙoda 1. Asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano 2. Asibitin koyarwa na Maiduguri 3. Asibitin koyarwa na Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi 4. Asibitin koyarwa na Jos 5- Babban Asibitin tarayya da ke Abuja 6. Cibiyar kula da lafiya ta tarayya da ke Ebute Metta a Lagos 7. Asibitin jami'ar Ibadan 8. Asibitin koyarwa na Benin. 9.Cibiyar lafiya ta tarayya da ke Yenagoa a Bayelsa 10.Asibitin koyarwa ta Owerri da ke Imo 11. Asibitin koyerwa na Abakaliki da ke Ebonyi.

    Farfesa Yusuf Abdu Misau akan rungumar abinicin da aka sauya wa halitta

    Play Episode Listen Later Aug 19, 2025 3:38


    Gwamnatin Najeriya ta bayyana shirin amfani da malaman addini wajen wayar da kan jama'a wajen rungumar amfani da abincin da aka sauyawa kwayar halitta da ake kira GMO. Shugaban hukumar kula da irin wadannan abinci Farfesa AbdullahI Mustapha ya bayyana haka a tattaunawarsa da RFI Hausa. Ganin yadda jama'a ke dari darin amfani da irin wannan abinci, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin kula da harkar lafiya, Farfesa Yusuf Abdu Misau, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana. 

    gmo akan noma abdu najeriya shugaban bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da Janar Kukasheka mai ritaya kan kama shugabannin ƙungiyar Ansaru

    Play Episode Listen Later Aug 18, 2025 3:36


    Gwamnatin Najeriya ta bayyana nasarar kama shugabannin ƙungiyar ƴan ta'adda da ake kira Ansaru mai alaƙa da Al'Qaeda, wadda tayi ƙaurin suna wajen kai munanan hare hare a jihohin Neja da kwara. Mai baiwa shugaban ƙasar Najeriya a kan harakokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu ya bada wannan sanarwar. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Tsofan kakakin runduna sojin Najeriya Janar Sani Usman Kukasheka ga kuma yadda zantawarsu ta gudana. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hira......

    kama shiga neja najeriya bashir ibrahim idris
    Alhaji Mustapha Yusuf Mai Kalwa kan faɗuwar farashin kayan abinci a Najeriya

    Play Episode Listen Later Aug 15, 2025 3:34


    Rahotanni daga sassan Najeriya na bayyana faɗuwar farashin kayan abinci, abinda zai taimakawa talakawa wajen samun sauki. Sai dai manoman ƙasar na ƙorafi a kan asarar da suka ce sun tafka. Domin tabbatar da samun saukin farashin, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da shugaban ƴan kasuwar hatsi ta duniya da ke Dawanau a jihar Kano, Alhaji Mustapha Yusuf Mai Kalwa. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattawaunawar tasu.............

    ku sai kano domin mustapha kayan najeriya bashir ibrahim idris
    Abdulhakeem Funtuwa kan yunkurin dakatar da yaƙin Ukraine wajen mantawa da Gaza

    Play Episode Listen Later Aug 14, 2025 3:27


    A ranar Jumma'a ake saran shugaban Amurka Donald Trump zai yi wata ganawa da takwaransa na Rasha Vladimir Putin dangane da yadda za'a kawo ƙarshen yaƙin da ake gwabzawa a Ukraine. Sai dai wasu da bayyana damuwa kan yadda shugabannin suka manta da batun tsagaita wuta a yaƙin Gaza, ganin yadda ake ci gaba da asarar rayukan ɗimɓin rayuka. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr. Abdulhakeem Garba Funtuwa dangane da yunkurin ƙasashe duniyar na samaun tsagaita wuta da kuma watsi da halin da ake ciki a Gaza.

    Ibrahim Wala kan bashin dala miliyan 300 da Najeriya ta ciwo daga Bankin Duniya

    Play Episode Listen Later Aug 13, 2025 3:38


    Bankin Duniya ya ce ya amince da buƙatar bai wa Najeriya dala miliyan 300, domin amfani da shi wajen inganta rayuwar mutanen da rikici ya raba da muhallansu a yankin arewacin ƙasar. Sanarwar Bankin ta ce za ayi amfani da kuɗaɗen ne wajen tallafawa irin waɗannan mutane da waɗanda suka basu matsuguni domin ganin sun koma masu dogaro da kan su, maimakon dogara da kayan agaji. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ibrahim Garba Wala, ɗaya daga cikin masu fafutukar kare hakkokin jama'a a Najeriya.   Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana................

    ku dala wala daga duniya najeriya bashir ibrahim idris
    Farfesa Bello Bada akan kisan ƴanbindiga 100 da sojin Najeriya suka yi

    Play Episode Listen Later Aug 12, 2025 3:29


    Sojojin Najeriya sun yi nasarar hallaka ƴanbindiga sama da 100 a ƙaramar hukumar Bukkuyum dake jihar Zamfara, sakamakon wasu hare haren sama da suka kaddamar a kan su. Rahotanni sun ce sojojin sun yi amfani da bayanan asiri ne wajen kai harin kan ƴanta'addan waɗanda aka ce yawansu ya kai 400 a dajin a Makakkari. Wannan na daga cikin nasarorin da sojojin Najeriya suka samu a ƴan kwanakin nan. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ad Farfesa Bello Bada na Jami'ar Usman Danfodio dake Sokoto, wanda ya ce wannan shi ne labarin da ƴan Najeriya ke farin cikin ji. Ga yadda tatatunawar su ta gudana a kai.

    Hira da Aissami Tchiroma kan shirin gwamnatin Nijar na ƙarbe mahaƙun zinari

    Play Episode Listen Later Aug 11, 2025 3:32


    Gwammatin Jamhuriya Nijar ta sanar da kwace kamfanonin hako zinari na ƙasashen ketare tare da mayer da su ƙarkashin kulawarta a cikin wani ƙudiri da shugaban mulkin sojin ƙasar Janar Abdurahmane Tiani ya sanya wa hannu a karshen mako. Haka ma gwamnatin ta hana fitar da ma'adinan ƙarkashin ƙasa zuwa waje ba tare da izini ba. Shiga alamar sauti domin sauraron karin bayani.......

    Ladan Abdullahi Garkuwa kan shirin Ɗangote na rarraba mai da motocinsa sassan Najeriya

    Play Episode Listen Later Aug 9, 2025 3:11


    A Najeriya, ga dukkan alamu an samu rarrabuwar kawuna tsakanin dillalan man fetur, sakamakon shirin Aliko Dangote na jigilar man daga matatarsa da ke Lagos zuwa gidajen mai a sassan ƙasar. Yayin da shugabannin dillalan ke adawa da shirin Dangoten, kananan dillalan sun bayyana gamsuwar su da shirin, kamar yadda za kuji a tattaunawar Bashir Ibrahim Idris da Alhaji Ladan Abdullahi Garkuwa.

    lagos shirin ladan abdullahi yayin sassan najeriya bashir ibrahim idris
    Jamilu Adamu kan manyan labaran jaridar Aminiya a wannan mako

    Play Episode Listen Later Aug 8, 2025 3:11


    Kamar yadda aka saba a duk ranar Juma'a, muna kawo muku wasu daga cikin manyan labarun da Jaridar Aminiya da ke Najeriya ta ƙunsa. A wannan karon Nura Ado Suleiman ya tattauna ne da Jamilu Adamu, Editan shafin labarun ban Al'ajabi na wannan jarida.

    Matsalolin tattalin arziki sun ka kawo ƙarshen matsayin matsakaitan mutane a Najeriya - Bincike

    Play Episode Listen Later Aug 7, 2025 3:31


    Matsalolin tattalin arziki a Najeriya ya taimaka wajen watsi da matsayin matsakaitan mutane da ke tsakanin al'umma, inda yanzu ake da attajirai ko matalauta kawai. Masanan na gabatar da dalilai daban daban da suka yi sanadiyar samun wannan matsala, wadda ta haifar da wagegen gibi a tsakanin al'umma. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Bashir Ibrahim Idris da Dr Abbati Bako.......

    ku kawo najeriya bashir ibrahim idris
    Dakta Shu'aibu Shinkafi kan tsanantar hare-haren 'yan bindiga a Zamfara

    Play Episode Listen Later Aug 6, 2025 3:28


    'Yan asalin jihar Zamfara da ke Najeriya, na ci gaba da bayyana matuƙar damuwarsu dangane da ƙaruwar hare-hare da kisan jama'a da 'yan bindiga ke yi. Mazauna wannan jiha da ke Arewa maso Yammacin ƙasar, sun buƙaci haɗin kai tsakanin gwamnatin jihar da ta Tarayya da zumar samar musu mafita ta dindindin. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Sulaiman Shu'aibu Shinkafi daga jihar. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

    yan haren shiga zamfara arewa najeriya bashir ibrahim idris
    Dakta Auwal Aliyu kan zanga-zangar tsaffin sojojin Najeriya

    Play Episode Listen Later Aug 5, 2025 3:36


    Wani adadi da dama na tsaffin sojojin Najeriya da suka ajiye aiki bisa raɗin kansu, sun mamaye gaban ginin Ma'aikatar Kudin ƙasar, inda suka gudanar da zanga-zanga kan rashin biyansu wani kason kuɗaɗensu na Fansho. Zanga-zangar ta safiyar jiya Litinin, na zuwa ne ‘yan kwanaki bayan makamanciyarta da tsaffin jami'an ‘Yansanda suka yi kan haƙƙoƙinsu. Domin gano bakin zaren warware matsalar tsaffin jami'an tsaron Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Auwal Aliyu Abdullahi, mai magana da yawun Kwamitin musamman da ke kula da walwalar tsaffin sojoji a Najeriya. Shiga alamar sauti domin sauraron ckakkiyar tattaunawar.

    Dakta Isa Sanusu kan kin hukunta ƴansanda da suka murƙushe zanga-zangar yunwa

    Play Episode Listen Later Aug 4, 2025 3:44


    Ƙungiyar kare hakkin bil'adama ta Human rights watch ta koka kan yadda har yanzu gwamnatin Najeriya ta gaza ɗaukar mataki kan ƴan sandan da aka zarga da kisan mutane lokacin zanga-zangar yunwa da ta faru a ƙasar a bara. Baya ga haka kuma ƙungiyar ta ce lokaci yayi da ya kamata gwamnatin Najeriya ta yiwa iyalan ɗan gwagwarmayar nan Abubakar Dadiyata bayanin halin da yake ciki shekaru 6 bayan ɓatansa Shiga alamar sauti don sauraron cikakken bayani....

    Tattaunawa da Barista Abdullahi Jalo kan taron jagororin Arewacin Najeriya

    Play Episode Listen Later Jul 31, 2025 3:08


    Jagororin yankin Arewacin Najeriya sun kammala taron yini biyu da duka gudanar a Kaduna, don bibiyar alkawurran da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya ɗaukar wa yankin a lokacin yaƙin neman zabe. Wannan dai na zuwa ne bayan da wasu suka yi zargin cewa an maida yankin saniyar ware duk kuwa da irin gudunmuwar da ya bayar a lokacin zaɓen baya.  Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Khamis Saleh da Barista Abdullahi Jalo...........

    A Najeriya duk da zambaɗawa wutar lantarki kuɗi har yanzu ba ta sauya zani ba

    Play Episode Listen Later Jul 30, 2025 1:28


    A Najeriya, duk yadda mahukunta ke tsawwala kudin wutar lantarki, tare da  bijirowa da dokokin da suke ganin za su inganta bangaren samar da wutar, har yanzu dai da sauran rina a kaba a game da ƙarancin wutar. Akan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da ɗan gwagwarmaya a jihar Kanon Najeriya, Kwamared Belllo Basi, ga kuma tattaunawarsu.

    akan zani zamba najeriya yanzu
    Hira da Sani Roufa'i kan cika shekaru biyu da yin juyin mulki a jamhuriya Nijar

    Play Episode Listen Later Jul 28, 2025 3:29


    Ranar 26 ga watan yuli ne aka cika shekaru biyu da kifar da gwamnatin Bazoum Mohamed a Nijar, albarkacin wannan rana shugaban ƙasar Abdurahmane Tchiani ya gabatar da jawabi inda ya bayyana halin da kasar ke ciki. Ra'ayoyi jama'a dai sun sha bamban a kan tafiyar ƙasar a yanzu. Shiga alamar sauti domin jin cikakkiyar hira da Ibrahim Tchillo ya yi da Sani Roufa'i masanin halayya zamantakewa a jamhuriya Nijar....

    Dr Abdulƙadir Suleiman kan dalilan da ya sanya duniya ta mance da yaƙin Sudan

    Play Episode Listen Later Jul 25, 2025 3:39


    Sama da shekaru biyu bayan ɓarkewar yakin basasar ƙasar Sudan, kasashen duniya sun kau da kan su, yayin da ake ci gaba da hallaka fararen hula. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abdulkadir Suleiman Muhammad, a kan dalilin da ya haifar da yaƙin da kuma yadda ƙasashen duniya suka juyawa ƙasar baya.  Latsa alamar sauti domin sauraren hirar...

    Farfesa Abba Gambo kan barazanar yunwa da mutane sama da miliyan 3 ke fuskanta

    Play Episode Listen Later Jul 23, 2025 3:39


    Ƙungiyar agaji ta ICRC ta bayyana cewar akwai yiwuwar fuskantar matsalar yunwa a arewa maso gabashin Najeriya sakamakon tashin hankalin da ya tilastawa manoma ƙauracewa gonakin su. Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawar Bashir Ibrahim Idris da Farfesa Abba Gambo...

    abba sama icrc gambo najeriya bashir ibrahim idris
    Abubakar Abdullahi mai ritaya kan zanga-zangar tsoffin 'yan sandan Najeriya

    Play Episode Listen Later Jul 22, 2025 3:37


    A ranar Litinin ne tsofaffin 'Yan Sandan  Najeriya da suka yi ritaya suka gudanar da zanga-zanga a biranen ƙasar da kuma Abuja, saboda gabatar da ƙorafi akan yadda ake biyan su fansho da kuma neman fitar da su daga tsarin da ake amfani da shi yanzu haka. Bayan kammala zanga zangar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da CSP Abubakar Abdullahi dashe mai ritaya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana a kai. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

    abuja bayan abubakar abdullahi shiga najeriya bashir ibrahim idris
    An ɗauki hanyar samun zaman lafiya a Jamhuriyar dimokaraɗiyar Congo

    Play Episode Listen Later Jul 21, 2025 3:34


    An fara samun haske a game da kawo ƙarshen rikicin gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo, inda a ranar Asabar makon da ya gabata a birnin Doha na Qatar ƙasar, da kungiyar yan tawayen M23 suka rattaba hannu akan wata yarjejeniyar tsagaita wuta da zumar kawo ƙarshen yakin da suke yi a tsakaninsu. A cikin yarjejeniyar, dukkannin bangarorin sun amince su tsagaita kai wa juna hare-hare tare da dakatar da farfagandar nuna ƙiyayya. Akan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da Dokta Abbati Bako, masanin dangantakar ƙasa da ƙasa daga jami'ar Bayero da ke Kano a Najeriya.

    Claim Bakonmu a Yau

    In order to claim this podcast we'll send an email to with a verification link. Simply click the link and you will be able to edit tags, request a refresh, and other features to take control of your podcast page!

    Claim Cancel