Bakonmu a Yau

Follow Bakonmu a Yau
Share on
Copy link to clipboard

A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban…

Rfi - Azima Bashir Aminu


    • Oct 27, 2025 LATEST EPISODE
    • weekdays NEW EPISODES
    • 3m AVG DURATION
    • 1,014 EPISODES


    Search for episodes from Bakonmu a Yau with a specific topic:

    Latest episodes from Bakonmu a Yau

    Tattaunawa da Fatima Dangote kan shirin faɗaɗa aikin matatar Ɗangote

    Play Episode Listen Later Oct 27, 2025 3:38


    Katafaren kamfanin Dangote, ya sanar da shirin faɗaɗa matatar sa mai samar da tacaccen gangar mai 650,000 zuwa miliyan guda da 400,000 a kowacce rana.  Shugaban rukunin kamfanin Dangote Alhaji Aliko Dangote ya ce za'a kwashe shekaru uku ana aikin faɗaɗa matatar wadda ya ce za ta zama mafi girma a duniya.  Dangane da wannan ci gaba ne kuma Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da babbar manajar rukunonin kamfanin, Fatima Aliko Dangote. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.....

    ku shirin dangote najeriya shugaban bashir ibrahim idris
    Usman Ture kan zaɓen shugaban ƙasar Cote d'Ivoire na gobe Asabar

    Play Episode Listen Later Oct 24, 2025 3:04


    A Cote d'Ivoire, a jajiberin zaɓen shugaban ƙasar, hukumomi sun ɗauki matakan da suka dace na ganin an gudanar da zaɓen ba tare da an fuskanci wata matsala ba. To domin jin ko a ina aka kwana ,Abdoulaye Issa ya tattauna da Usman Ture,wani ɗan ƙasar ta Cote d'ivoire da ya karɓi katinsa na zaɓe. Latsa alamar sauti domin jin yadda tattaunawarsu ta gudana...

    cote usman ture asar gobe shugaban abdoulaye issa
    Dr Isa Abdullahi kan tasirin ƙananan bankunan a Najeriya

    Play Episode Listen Later Oct 23, 2025 3:32


    Sannu a hankali ƙananan bankuna na bada gagarumar gudumawa wajen ci gaban tattalin arzikin Najeriya, la'akari da yadda jama'a ke komawa hada hada da su maimakon manyan bankunan da aka sani a baya. Ko a jiya Moniepoint ya sanar da samun jarin Dala miliyan 200 domin inganta harkokin sa. Domin sanin tasirin wadannan ƙananan bankunan, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki, Dr Isa Abdullahi na Jami'ar Kashere. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana..................

    ko ku domin dala abdullahi najeriya bashir ibrahim idris
    Sunusi Bature game da taron baje-kolin kafafen yaɗa labarai na-afrika karo na 14

    Play Episode Listen Later Oct 22, 2025 2:43


    An buɗe taron baje kolin kafafen yaɗa labarai na Afrika da ake kira AFRICAST karo 14 a birnin Lagos da ke Najeriya, inda masu ruwa da tsaki a harkar yaɗa labarai daga nahiyar da kuma sassan duniya ke halarta.Domin ƙara inganta ayyukan yaɗa labarai, wasu daga cikin mahalarta wannan taro na ganin cewa ya zama wajibi a samar da dokokin da za su sa-ido kan ayyukan kafafen sada zumunta da kuma sauran hanyoyin yaɗa labarai ta yanar gizo. Sanusi Bature Dawakin Tofa, shi ne mai magana da yawun gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Yusuf, kuma wanda ya wakilce shi a taron, a zantawarsa da Abdoulkarim Ibrahim Shikal, ya ce lalle akwai buƙatar samar da gyara a wannan fanni. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar...................

    game afrika lagos karo domin taron baje kolin najeriya abdoulkarim ibrahim shikal
    Gwamna Dikko Raɗɗa kan shirin bunƙasa lantarki a jihohin Kano da Jigawa da Katsina

    Play Episode Listen Later Oct 21, 2025 3:21


    Gwamnatocin jihohin Katsina da Kano da kuma Jigawa da ke arewa maso yammacin Najeriya sun kulla haɗakar inganta wutar lantarkin ga jihohin uku. Gwamnonin Kano, Jiagwa da Katsina sun shiga yarjejeniyar haɗin gwiwa kan bunƙasa wutar lantarki a jihohin uku da ke arawacin Najeriya, tare da zuba hannun jari a kamfanonin Future Energies Africa (FEA) da na rarraba wutar lantarki a jihohin uku wato KEDCO. Hakan ya fito fili ne bayan wani taro da gwamnonin jihohin uku da suka hada da Malam Umar Dikko Radda da Abba Kabir Yusuf da kuma Umar Namadi suka gudanar a ƙasar Morocco inda suka tattauna da kamfanin Future Energies Africa da Kedco da sauran masu ruwa da tsaki a harkar makamashi. A zantawarsa da RFI Hausa, Gwamnan jihar Katsina Malama Dikko Rada ya ce suna son fito da haryar yin haɗaka a fannin wutar lantarki tsakanin jihohin makwabtan juna ta hanyar zuba jari naira biliyan 50 domin samar da wutar da yankin ke bukata. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar................

    Birgediya Tukur Gusau akan jita-jitar yunƙurin juyin mulki a Najeriya

    Play Episode Listen Later Oct 20, 2025 3:08


    Babbar Cibiyar rundinonin sojin Najeriya ta yi watsi da rahotannin dake cewa an yi yunkurin juyin mulkin a kasar, abinda ya kai ga kama wasu hafsoshi guda 16. Daraktan yada labaran Cibiyar janar Tukur Gusau ya shaidawa Bashir Ibrahim Idris a zantawarsu cewar, sojojin da aka kama ana tuhumar su ne da laifin saba dokoki na soji amma ba juyin mulki ba. Ga yadda zantawarsu ta gudana. 

    ga akan urin najeriya jita bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da Isah Sunusi kan horon da Amnesty ta baiwa matasa a Najeriya

    Play Episode Listen Later Oct 17, 2025 3:39


    Ƙungiyar Amnesty International a Najeriya ta shirya wani taro a Lagos domin horar da matasa a kan yadda za su kare haƙƙoƙin jama'a a yankunan da suka fito.Taron wanda zai gudana a shiyoyin Najeriya guda 6 ya ƙunshi matasa daga shiyar kudu maso yammacin kasar. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Daraktan ƙungiyar a Najeriya, Malam Isa Sanusi. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.............

    lagos amnesty international amnesty taron isah najeriya matasa bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da Ambasada Ibrahim Kazaure kan zauya sheƙar wasu ƴan siyasa zuwa APC

    Play Episode Listen Later Oct 16, 2025 3:25


    Jiga-jigan Jam'iyyun adawa a Najeriya da suka haɗa da gwamnoni da ƴan majalisun tarayya da na jihohi na rige-rigen komawa jam'iyya mai mulki ta APC. Na baya-bayan nan da ya koma jam'iyyar ta APC shi ne gwamnan jihar Bayelsa yayinda na Taraba ke kan hanya, kan hakan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar PDP na ƙasa Ambasada Ibrahim Kazaure akan wannan lamari ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.......

    jam ku apc pdp taraba wasu bayelsa najeriya bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da Dr Abbati Bako game da buƙatar sauya lokacin zaɓe a Najeriya

    Play Episode Listen Later Oct 15, 2025 3:25


    Kwamitin Majalisun Najeriya da ke yiwa kundin tsarin mulki gyaran fuska ya bada shawarar sake dokar zaɓe ta yadda za a dinga gudanar da zaɓuɓɓuka a watan Nuwamba domin bada damar kammala shari'u kafin lokacin rantsar da waɗanda suka samu nasara. Domin sanin tasirin wannan shiri, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abbati Baƙo mai sharhin kan harkokin siyasa ga kuma yadda tattaunawarsu ta kasance. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar....

    game ku domin atar bako najeriya nuwamba bashir ibrahim idris
    Farfesa Haruna Jibril kan dalilan da suka tilasta ASUU tsunduma yajin aiki

    Play Episode Listen Later Oct 14, 2025 3:39


    Malaman Jami'o'in Najeriya sun kare matakin ƙungiyarsu na tsunduma yajin aikin gargaɗi na makwanni 2, inda suka zargi gwamnati da yaradara. Wannan kuwa na zuwa ne duk da gargaɗin da gwamnatin ƙasar ta yi na amfani da dokar nan ta babu aiki babu biya duk malamin da ya shiga yajin aiki na ASUU. Shugaban ƙungiyar Malaman reshen Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria, Farfesa Haruna Jibril ya yiwa Bashir Ibrahim Idris ƙarin bayani a tattaunawar da suka yi kamar haka... Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....

    ku suka jibril asuu haruna aiki wannan najeriya shugaban bashir ibrahim idris
    Malam Ibrahim Garba Wala game da afuwar Tunubu ga wasu Fursunoni

    Play Episode Listen Later Oct 13, 2025 3:29


    Ƴan Najeriya na ci gaba da bayyana ra'ayoyi dangane da wasu daga cikin mutanen da shugaban ƙasar Bola Tinubu ya yiwa afuwa a makon jiya, inda suke bayyana rashin dacewar afuwar da akan wasu waɗanda suka aikata manya laifuka. Daga cikin waɗanda ake muhawara a kan su akwai masu kisan kai da masu safarar ƙwayoyi da kuma masu safarar makamai. Domin tattauna wannan batu Bashir Ibrahim Idris, ya zanta da Ibrahim Garba Wala, guda cikin masu fafutukar kare haƙƙin Bil'Adama a Najeriya.......... Latsa alamar sauti domin sauraron zantawarsu................

    Tsohon Jakadan Kamaru a Faransa Ambasada Muhd kan zaɓen ƙasar ta Afrika

    Play Episode Listen Later Oct 10, 2025 3:32


    A ƙarshen wannan mako ne jama'ar ƙasar Kamaru za su kaɗa kuri'a a zaɓen shugaban ƙasa, inda ƴan takara 10 ke neman shugabanci, cikin su harda shugaba Paul Biya dake neman wa'adi na 8. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon Jakadan Kamaru a Faransa, Ambasada Muhammad Sani game da zaɓen. Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawarsu...

    afrika asar kamaru paul biya faransa bashir ibrahim idris
    Najeriya: 'Yansanda sun karɓi umarnin kotu na dena kama masu baƙi gilashin mota

    Play Episode Listen Later Oct 9, 2025 3:29


    Rundunar Ƴansandan Najeriya ta sanar da karɓar umarnin kotu na dakatar da kama motocin dake ɗauke da bakin gilashi, inda ta umarci jami'an ta da su dakatar da kamen har zuwa lokacin da za'a kammala shari'ar. Wannan ya biyo bayan rugawa kotu da wasu lauyoyi suka yi domin hana aiwatar da dokar da suka ce za ta take haƙƙin Bil Adama. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Barr Suleiman Muhammed, lauya mai zaman kansa. Ku latsa alamar sauti domin jin tattaunawarsu...

    ku mota kama masu kotu wannan najeriya bashir ibrahim idris
    Malam Ibrahim Garba Wala game da wanda ya dace ya maye gurbin Yakubu a INEC

    Play Episode Listen Later Oct 8, 2025 3:36


    Shugaban Hukumar zaɓen Najeriya Farfesa Mahmood Yakubu ya kawo ƙarshen aikin sa a INEC, inda ya miƙa ragamar tafiyar da hukumar ga May Agbamuche.Yayin miƙa ragamar aikin, Yakubu ya roƙi kwamishinonin hukumar da su bai wa Agbamuche haɗin kai wajen gudanar da ayyukan ta na riƙo zuwa lokacin da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai naɗa wanda zai maye gurbinsa.Tuni dai tambayoyi suka yawaita game da wanda zai maye gurbin Yabubu a matsayin shugaban hukumar ta INEC, dangane da wannan batu Bashir Ibrahim Idris ya tattaunawa da Malam Ibrahim Garba Wala. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar..........

    Tattaunawa da Abdulhakeem Garba Funtua kan cika shekaru 2 da yaƙin Gaza

    Play Episode Listen Later Oct 7, 2025 3:31


    Yau ake cika shekaru biyu cif da ƙazamin harin da Mayaƙan Hamas suka kai Isra'ila wanya ya hallaka Yahudawa fiye da dubu guda sanadiyyarsa ne kuma aka faro wannan yaƙi na Gaza da ya kashe Falasɗinawa fiye da dubu 60. Wannan yaƙi shi ne mafi muni da duniya ta gani a wannan ƙarnin wanda ya rushe fiye da kashi 90 na gine-ginen yankin. Dangane da wannan ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin siyasar ƙasashe don jin tasirin wannan yaƙi ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar...

    Tattaunawa da Alhaji Ouba Danlami game da babban zaɓen Kamaru

    Play Episode Listen Later Oct 6, 2025 3:38


    A Kamaru ana ci gaba da yaƙin neman zaɓen shugabancin ƙasar wanda za a gudanar ranar lahadi mai zuwa 12 ga wannan wata na Oktoba, inda ƴantakara 10 ke shirin fafatawa ciki har da shugaba mai-ci Paul Biya. Akwai dai waɗanda suka janye daga zaɓen don mara wa wasu ƴantakarar duk da cewa an tantance su, yayin da wasu suka yanke shawarar mara wa wasu ƴantakarar haka kawai saboda wasu dalilai. Alhaji Ouba Danlami, ya sha tsayawa takarar shugabancin  ƙasar a zaɓukan da suka gabata, to amma ban da wannan karo, ko saboda? Ga ƙarin bayanin da ya yi wa Ahmed Abba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar..

    Tattaunawa da AA Zaura kan rikicin matatar Dangote da PENGASSAN

    Play Episode Listen Later Oct 4, 2025 3:21


    Yayin da ake ci gaba da tsokaci a kan matsalolin da suka shafi matatar Dangote da ƙungiyar PENGASSAN, wani hamshaƙin Dan kasuwa, Alhaji Abdulsalam Abdulkarim Zaura, ya buƙaci gwamnatin Najeriya da ta shiga lamarin domin kawo ƙarshensa. Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawarsa da Bashir Ibrahim Idris....

    dangote yayin najeriya bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da tsohon shugaban EFCC Abdurrashid Bawa kan rashawa a Najeriya

    Play Episode Listen Later Oct 2, 2025 3:33


    Matsalar cin hanci da rashawa na ci gaba da yiwa Najeriya illa a ɓangarori daban-daban, lamarin da ke haifar da tarnaki wajen ci gaban ƙasar. A yayinda manazarta ke ci gaba da sharhi kan ci gaban da wannan ƙasa ta yammacin Afrika ta samu cikin shekaru 65 da samun ƴancin kai daga Ingila da kuma irin matsalolin da suka dabaibaye wannan ƙasa. Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon shugaban hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC a ƙasar Abdurrashid Bawa. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawarsu.

    afrika ku bawa efcc najeriya shugaban bashir ibrahim idris ingila
    Atiku Abubakar akan cikar Najeriya shekaru 65 da samun 'yancin kai

    Play Episode Listen Later Oct 1, 2025 3:49


    Yau Najeriya ke bikin cika shekaru 65 da samun yancin kai daga Turawan mulkin mallaka na Birtaniya. A irin wannan lokaci akan yi tilawa da kuma nazari dangane da ci gaban da kasar ta samu da kuma kalubalen dake gaban ta. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar dangane da halin da kasar ke ciki, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.

    akan atiku abubakar najeriya birtaniya bashir ibrahim idris
    Dalilan rikici tsakanin Ɗangote da masu ruwa da tsaki a harkar man Najeriya

    Play Episode Listen Later Sep 30, 2025 3:31


    A Najeriya, wani abu da ke neman ɗaure wa jama'a kai shi ne yadda ƙasa da shekara ɗaya da ƙddamar da ayyukanta, matatar mai ta Ɗangote ke fuskantar rigingimu daban daban, da suka haɗa da tsakaninta da dillalan mai masu zaman kansu, da ma'aikatan dakon mai wato NUPENG sai kuma wannan karo da PENGASSAN wato ƙungiyar manyan ma'aikatan mai da iskar gaz na ƙasar. A game da waɗannan rigingimu ne Abdoulkarim Ibrahim Ibrahim Shikal ya zanta da masani harkar mai a ƙasar wato Alhaji Ɗayyabu Yusuf Garga, domin sanin wasu daga cikin dalilan faruwar hakan. Ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

    Tattaunawa da Farfesa Ouba Ali Mahamman masanin siyasa game da zaɓen Kamaru

    Play Episode Listen Later Sep 29, 2025 3:34


    A ƙarshen makon da ya gabata aka fara yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a Kamaru, inda mutane 12 ciki har da shugaba mai-ci Paul Biya za su kara da juna a ranar 12 ga watan gobe na Oktoba idan Allah ya kai mu. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Farfesa Ouba Ali Mahamman, masani siyasar Kamaru da ke zaune a birnin Yaounde, wanda da farko ya bayyana bambancin da ke akwai tsakanin wannan zaɓe da kuma waɗanda aka saba yi shekarun baya a ƙasar. Ga dai abin da yake cewa. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

    Tattaunawa da Dakta Bolori akan rage kudin ruwa da babban bankin Najeriya ya yi

    Play Episode Listen Later Sep 26, 2025 3:33


    Babban bankin Najeriya CBN ya sanar da rage kuɗin ruwan da ake sanyawa masu karɓar bashi daga kaso 27.50 zuwa kaso 27 karon farko cikin shekaru huɗu. Wannan ci gaba na zuwa ne a dai-dai lokacin da hukumar tattara haraji ta Najeriya ke cewa ta sami ƙarin kuɗaɗen shiga da kaso 411%, amma hakan ba zai hana ci gaba da ciyo bashi da Najeriya ke yi ba.   A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara, Dr Ahmad Bolori masanin tattalin arziki a Najeriya ce, ragin kwabo 50 kachal yayi matuƙar kaɗan duk da cewa babu wani abu da talaka zai mora a wannan ci gaba. Ga dai yadda tattaunawar tasu ta kasance.

    Emmanuel Macron kan amincewa da ƙasar Falasɗinu da kuma yakin Ukraine da Rasha

    Play Episode Listen Later Sep 25, 2025 3:13


    Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce ƙasar Rasha ta yi rauni sosai a yaƙin da take gwabzawa da Ukraine. Macron ya bayyana haka ne a zantawa ta musamman da ya yi tashar talabijin ta France24 da Kuma RFI a gefen Babban Taron Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya a birnin New York, inda ya taɓo batutuwa da dama ciki har da amincewa da Palesdinu a matsayin ƙasa da daidai sauransu. Da farko dai Emmanuel Macron ya jinjina wa shugaba Amurka Donald Trump ne a game da ƙoƙarinsa don kawo ƙarshen rikicin Ukraine. Ku latsa alamar sauti don sauraron fassarar kalamansa...............

    Maitre Lirwanou Abdourahman kan ficewar Nijar Mali da Burkina Faso daga ICC

    Play Episode Listen Later Sep 24, 2025 3:32


    Burkina Faso, Mali da kuma Nijar sun sanar da janyewar ƙasashensu daga Kotun Hukunta Laifufuka ta Duniya da ke birnin Hague. A sanarwar haɗin-gwiwa da suka fitar cikin daren litinin da ta gabata, ƙasashen uku sun ce sun ɗauki matakin saboda sun lura cewa kotun ta rikiɗe domin zama ƴar amashin ƴan mulkin mallaka. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani dokokin ƙasa da ƙasa Maitre Lirwanou Abdourahman, domin jin ko wataƙila ya yarda da dalilan da wadannan ƙasashe suka gabatar. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

    mali ku burkina faso hague maitre daga duniya nijar najeriya amurka abdoulkarim ibrahim shikal
    Maitre Lirwanou Abdourahman kan janyewar ƙasashen AES daga kotun ICC

    Play Episode Listen Later Sep 24, 2025 3:32


    Burkina Faso da Mali da kuma Nijar sun sanar da janyewar ƙasashensu daga Kotun Hukunta Laifufuka ta Duniya da ke birnin Hague. A sanarwar haɗin-gwiwa da suka fitar cikin daren Litinin da ta gabata, ƙasashen uku sun ce sun ɗauki matakin ne saboda sun lura cewa kotun ta rikiɗe domin zama ƴar amashin ƴan mulkin mallaka. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani dokokin ƙasa da ƙasa Maitre Lirwanou Abdourahman, domin jin ko wataƙila ya yarda da dalilan da wadannan ƙasashe suka gabatar. Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawarsu.................

    Farfesa Tukur Abdulƙadir kan ƙarin ƙasashen da ke amincewa da Falasɗinu

    Play Episode Listen Later Sep 23, 2025 3:45


    Ƙasashen duniya na ci gaba da nuna amincewarsu da samar da ƴantacciyar ƙasar Falasɗinu, a wata guguwa wadda ba'a taɓa ganin irinta ba. Ƙasashen turai da ake ganin suna da ƙyakyawar alaƙa da Amurka irinsu su Burtaniya, Canada da kuma Australia a wannan Karo sun sanar da amincewar su da baiwa Falasɗinu damar zama ƙasa mai cin gashin kanta amma bisa wasu shariɗoɗi. A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara Farfesa Tukur Abdulƙadir ya ce har yanzu da sauran rina a kaba don kuwa amincewar waɗannan ƙasashe ƙadai a fatar baki bata wadatar ba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

    Tattaunawa da tsohon Jakadan Kamaru Ambasada Malam Mohamed Sani kan zaɓen ƙasar

    Play Episode Listen Later Sep 22, 2025 3:38


    A ƙarshen wannan mako ne za a ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a Kamaru, zaɓen da zai gudana a ranar 12 ga watan gobe na Oktoba. To sai dai yayin da jam'iyyar RDPC mai mulki ta bayyana Paul Biya a matsayin wanda zai tsaya mata takara, a nasu ɓangare kuwa, yanzu haka ƴan adawa, na ci gaba da tattaunawa don fitar da mutum ɗaya da zai tsaya zaɓen amadadinsu. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Ambasada Malam Mohamed Sani, tsohon jakada a lokacin mulkin Ahmadou Ahidjo, amma a yanzu yake zaune a ƙetare, inda ya bayyana yadda suke kallon wannan zaɓe.

    malam sani asar kamaru paul biya oktoba abdoulkarim ibrahim shikal
    Ambasada Mohamed Sani kan zaɓen shugaban ƙasa da za a yi a Kamaru

    Play Episode Listen Later Sep 22, 2025 3:38


    A ƙarshen wannan mako ne za a ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa da za a gudanar 12 ga watan gobe na Oktoba idan Allah ya kai mu a Kamaru. To sai dai yayin da jam'iyyar RDPC mai mulki ta bayyana Paul Biya a matsayin wanda zai tsaya mata takara, a nasu ɓangare kuwa, yanzu haka ƴan adawa, na ci gaba da tattaunawa don fitar da mutum ɗaya da zai tsaya musu takara a zaɓen. Kan haka Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Ambasada Malam Mohamed Sani, tsohon jakada a lokacin mulkin Ahmadou Ahidjo, amma a yanzu yake zaune a ƙetare, inda ya bayyana yadda suke kallon wannan zaɓe. Ƙu latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu............

    allah sani kamaru paul biya oktoba shugaban abdoulkarim ibrahim shikal
    Shugabannin ƙananan hukumomin Kwara sun sanar da rufe kasuwannin sayar da shanu

    Play Episode Listen Later Sep 19, 2025 3:06


    Shugabannin ƙananan hukumomi a yankin Kudancin jihar Kwara ta Najeriya sun sanar da rufe dukkannin kasuwannin sayar da shanu da aka fi sani da {Kara}. Mahukuntan sun ce sun ɗauki wannan mataki ne sakamakon tashin matsalolin tsaro da ake samu a kasuwannin. A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara shugaban ƙungiyar Miyetti Allah reshen jihar ta kwara, kuma guda daga cikin jagororin ƙungiyar kasuwannin kara na jihar Alhaji Shehu Garba ya ce sam basu yarda da wannan mataki ba. Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawar tasu....

    sanar rufe najeriya
    Hira da Issa Tchiroma Bakary game da zaɓen Kamaru da ƙoƙarin kawar da Paul Biya

    Play Episode Listen Later Sep 18, 2025 3:18


    Issa Tchiroma Bakary, wanda ya share tsohon shekaru 16 yana riƙe da muƙamin minista ƙarƙashin gwamnatin Paul Biya na Kamaru, a yanzu ya koma ɓangaren adawa inda yake ci gaba da jawarcin sauran ƴan siyasa na ƙasar. Tuni dai wani ƙawance da ya ƙunshi jam'iyyin adawa 11 ya bayyana goyon baya ga takararsa a zaɓen shugabancin ƙasar da za a yi ranar 12 ga watan gobe idan Allah ya kai mu. Radio France Internationale ya zanta da tsohon minista Issa Tchiroma, wanda da farko ya bayyana matsayinsa dangane da wannan goyon baya da ya samu, inda ya ci gaba da cewa.

    Dr. Musa Adamu game da yadda rashawa ke ci gaba da haɓaka a Najeriya

    Play Episode Listen Later Sep 17, 2025 3:03


    Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Nigeria wato ICPC, ta bayyana damuwa kan yadda matsalar rashawa ke ci gaba da haɓaka, duk kuwa da matakan da ta ke ɗauka. A cewar Shugaban hukumar ta ICPC, Dr Musa Adamu Aliyu, a yanzu sun karkata akalarsu ne zuwa ga ƙananan hukumomi, don daƙile matsalar cin hanci da ta yi katutu... Latsa alamar sauti don sauraron ƙarin bayanin da Dr Musa Adamu, ya yi wa wakilinmu Ibrahim Malam Goje........

    Isa Tafida Mafindi-Kan yadda talakawa zasu mori raba fetur da Ɗangote ya fara da motocinsa

    Play Episode Listen Later Sep 16, 2025 3:33


    Kamfanin Dangote ya fara aikin rarraba man fetur daga matatarsa zuwa sassan Najeriya domin saukakawa jama'a, a dai-dai lokacin da manyan dilallan man fetur ke adawa da matakin. Dashi Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki, Alahji Isa Tafida Mafindi a kan yadda talakawa zasu ci gajiyar wannan shirin. Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar.

    Uzairu Abdullahi kan buƙatun likitocin Najeriya masu neman ƙwarewa ga gwamnati

    Play Episode Listen Later Sep 15, 2025 3:29


    A makon da ya gabata ne likitoci da ke neman ƙawarewa a Najeriya suka gudanar da yajin aiki, domin nuna rashin amincewa dangane da yadda gwamnati ke jan ƙafa wajen ƙin biyansu haƙƙoƙinsu.To sai dai bayan da aka fara biyansu wasu daga cikin haƙƙoƙin, sun dakatar da yajin aikin tare da bai wa gwamnati ƙarin makonni biyu domin shafe musu hawayensu. Dr Uzairu Abdullahi, shi ne Editan Mujallar wallafa labarai ta ƙungiyar ya yi ƙarin bayani..... Latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawar da Abdoulkarim Ibrahim Shikal........

    abdullahi masu atun najeriya abdoulkarim ibrahim shikal
    Dr Mubarak Muhammad kan naɗin sabon firaministan Faransa Lecornu

    Play Episode Listen Later Sep 11, 2025 3:32


    Sabon firaministan Faransa Sebastien Lecornu ya karɓi ragamar tafiyar da mulkin daga hannun Francois Bayrou, wanda ƴan Majalisar dokokin ƙasar suka tsige a ranar Litinin ta gabata.Wannan dai shi ne Firaminista na 5 bayan da Emmanuel Macron ya karɓi ragamar mulki domin yin wa'adi na biyu, lamarin da ke nuni da cewa ƙasar na fama da rikici a fagen siyasa. Dr Mubarak Muhammad, mazauni Faransa kuma masani a game da salon siyasar ƙasar, ya bayyana wa Nura Ado Sulaiman mahangarsa a game da wannan batu. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tasu..................

    Mammane Wada kan yadda jamhuriyar Nijar ke ci gaba da shaƙe wuyan masu chachakarta

    Play Episode Listen Later Sep 10, 2025 3:33


    Gwamnatin mulkin sojin  Jamhuriyyar Nijar na ci gaba da kamen waɗanda ke sukar lamirinta da suka hadar da ƴan jarida da masu fafutuka har ma da ƴan siyasa. A wani rahoto da ta fitar a baya bayan nan kungiyar kare hakkin bil Adam Human Right Watch ta soki yadda sojojin da suka kwace muki a ƙasar ke tsare jama'a babu gaira babu dalili. Akan wanan abokin aiki Oumarou Sani ya tattaunawa da Mamane Wada shugaban kungiyar yaki da cin hanci da rashawa ga kuma yadda zantawarsu ta gudana.

    Mamane Wada akan yadda Gwamnatin sojin Nijar ke kama waɗanda ke sukar lamirinta

    Play Episode Listen Later Sep 10, 2025 3:33


    Gwamnatin mulkin sojin  Jamhuriyyar Nijar na ci gaba da kamen waɗanda ke sukar lamirinta da suka haɗar da ƴan jarida da masu fafutuka har ma da ƴan siyasa. A wani rahoto da ta fitar a baya bayan nan kungiyar kare haƙƙin bil Adam Human Right Watch ta soki yadda sojojin da suka ƙwace muki a ƙasar ke tsare jama'a babu gaira babu dalili. Akan wanan abokin aiki Oumarou Sani ya tattaunawa da Mamane Wada shugaban ƙungiyar yaƙi da cin hanci da rashawa ga kuma yadda zantawarsu ta gudana. Latsa alaamar sauti don sauraron yadda tattaunawar ta su ta gudana...........

    Nasiru Garba Ɗantiye kan ƙorafin shugaban majalisar wakilan Najeriya game da yawan ciwo bashi

    Play Episode Listen Later Sep 9, 2025 3:29


    Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya, Abbas Tajudeen, ya koka akan yadda bashi ya ke cigaba da yi wa ƙasar katutu, lamarin da ya ce yana barazana ga bunƙasar tattalin arziƙinta. Tajuddeen, wanda ya bayyana haka jiya Litinin a Abuja, ya ce bashin da ke kan Najeriya a yanzu ya kai wani matsayi mai ban tsoro, inda ya ke kira da a sake fasalin yadda ake karɓar rance a ƙasar. Akan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da wani tsohon ɗan majalisar dokoki a ƙasar, Nasiru Garba Ɗantiye, ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana.

    game akan abuja garba bashi najeriya shugaban majalisar
    Alhaji Dayyabu Garga akan batun fara yajin aikin ƙungiyar NUPENG a Najeriya

    Play Episode Listen Later Sep 8, 2025 3:33


    A wannan litinin, ƙungiyar NUPENG da ta haɗa direbobin motocin dakon mai da iskar gas a Najeriya ta fara yajin aiki, domin nuna rashin amincewa da yadda Ɗangote ke shirin yin amfani da motocinsa domin rarraba man fetur a sassan ƙasar. Shugabannin NUPENG, sun ce su ne ke da hurumin raba mai da kuma iskar gaz a Najeriya, a maimakon yadda Ɗangote ke shirin yin amfani da motoci dubu huɗu domin wannan aiki. Latsa alamar sauti domin sauraro.......

    akan najeriya
    Nijar a duk kullum za ta kare hakokin ƴan ƙasar mazauna ketare

    Play Episode Listen Later Sep 6, 2025 3:23


    Jamhuriyar Nijar a duk kullum za ta kare hakokin ƴan ƙasar mazauna ketare, Wasu daga ciki tarin matsalolli da ƴan Nijar mazauna ƙasashen ketare ke fuskanta sun hada da rashin takardun zama wadanan kasashe. Jakadan Nijar a Jamhuriyar Benin, Kadade Chaibou ya bayyana haka yayin zantawa da Abdoulaye Issa a ofishinsa dake birnin Kwatanu.

    asar wasu nijar jamhuriyar nijar abdoulaye issa
    Tattaunawa da Barr Al-Zubair kan jinkiri wajen gudanar da shara'o'i a Najeriya

    Play Episode Listen Later Sep 3, 2025 3:29


    Masu ruwa da tsaki kan sha'anin Shari'a a Najeriya sun sabunta ƙorafin da suke yi a kan matsalar jinkiri maras tushe, wajen gudanar da shara'o'i ko yanke hukunci kan waɗanda ake tuhuma da aikata manyan laifuka, musamman na ta'addanci. Ƙorafin ya sake bijirowa ne la'akari da yadda cikin ƙanƙanin lokaci mahukuntan ƙasar Finland suka zartas da hukunci kan Simon Ekpa, wani mai iƙirarin neman kafa ƙasar Biafra a Najeriya. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hirar....

    Muhammad Magaji kan ƙorafin manoma game da jinkirin raba kayayyyakin noma

    Play Episode Listen Later Sep 2, 2025 3:33


    Manoma a Najeriya na kokawa kan ƙarancin samun taimako daga gwamnati wajen sauƙaƙa musu ayyukan noma. Ƙorafi na baya bayan nan a Najeriyar shi ne jinkirin raba wasu kayayyakin noma ciki har da motocin Tantan aƙalla dubu biyu da gwamnatin Najeriyar ta sanar da sayowa yau fiye da watanni biyu, yayin da a gefe guda tuni daminar bana ta yi nisa. Kan wannan al'amari Nura Ado Suleiman ya tattauna da Alhaji Muhd Magaji, Sakataren tsare tsare na ƙungiyar manoman Najeriya.

    Fatima Baba Fugu akan 'yan Najeriya fiye da dubu 24 da suka ɓata

    Play Episode Listen Later Sep 1, 2025 3:34


    Ƙuniyar Agaji ta Red Cross ta ce yanzu haka akwai mutane sama da dubu 23 da suka ɓata a sassan Najeriya. A bayanin da ta fitar a jiya lahadi, ƙungiyar ta ce 68% na waɗanda suka ɓata dukanninsu mata ne, yayin da jihar Yobe ke matsayin jagora ta fannin yawan waɗanda lamarin ya fi shafa. Fatima Baba Fugu, tana aiki ne da sashen da ke haɗa waɗanda suka ɓata da iyalansu a ƙungiyar ta ICRC daga birnin Maiduguri jihar Borno, ta yi wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal ƙarin bayani a game da waɗannan alkaluma da ƙungiyar ta fitar.

    Dalilan PDP na baiwa kudancin Najeriya takarar shugaban ƙasa - Sen Ibrahim Tsauri

    Play Episode Listen Later Aug 28, 2025 3:33


    Taron Jam'iyyar PDP a ƙarshen makon da ya gabata, ya amince da bai wa yankin kudancin ƙasar damar gabatar da ɗan takarar zaɓen shugaban ƙaasr da za ayi a shekarar 2027, ya yin da ya haramtawa waɗanda suka fito daga arewacin ƙasar tsayawa takara. Tuni aka bayyana cewar wasu kusoshin jam'iyyar na zawarcin tsohon shugaban ƙasar Goodluck Jonathan da Peter Obi domin tsaya musu takara. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon Sakataren jam'iyyar, Sanata Umar Ibrahim Tsauri game da lamarin. Ku latsa alamar sauti don sauraron yadda zantawarsu ta gudana.................

    ku pdp peter obi tuni goodluck jonathan najeriya shugaban bashir ibrahim idris
    Janar Idris Bello Danbazau mai ritaya kan taron manyan hafsoshin tsaron Afrika

    Play Episode Listen Later Aug 27, 2025 3:33


    Manyan hafsoshin tsaron ƙasashen Afrika sun bayyana aniyar aiki tare a tsakaninsu domin tunƙarar matsalolin tsaron da suka addabi nahiyar, musamman ayyukan ta'addanci. Wannan ya biyo bayan taron da suka halarta a Najeriya. Dangane da wannan, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Janar Idris Bello Danbazau mai ritaya dangane don jin alfanun wannan sabin yunƙuri , ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana akai. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....

    afrika ku bello taron wannan najeriya bashir ibrahim idris
    Malam Isa Sunusi kan kisan da Isra'ila ta yi wa ƴan jaridu a Gaza

    Play Episode Listen Later Aug 26, 2025 3:46


    Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah wadai da kisan ƙarin ƴan jaridu 5 da Isra'ila ta yi a asibitin Khan Younes. Daraktan ƙungiyar a Najeriya, Malam Isa Sanusi ya buƙaci ƙasashen duniya da su tilastawa Isra'ila mutunta dokokin duniya wajen kare ƴan jaridun da ke gudanar da aikin su a ƙasar.  Ku latsa alamar sauti don jin yadda tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris ta gudana............

    Baba Ngelzerma kan rashin goyon bayan ta'addancin wasu ɗai-ɗaikun Fulani ke yi

    Play Episode Listen Later Aug 25, 2025 3:36


    Ƙungiyar Fulani ta Miyetti Allah a Najeriya, ta nesanta kan ta daga goyan bayan ayyukan ta'addancin da wasu ɗai-ɗaikun ƴaƴanta keyi, tare da bayyana cewar ita ta fi jin raɗaɗin matsalar. Shugaban ƙungiyar Baba Usman Ngelzerma ya ce aƙalla Fulani 20,000 aka kashe, yayin da suka yi asarar shanu sama da miliyan 4 ga ayyukan ta'addancin a shekaru 5 da suka gabata. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Bashir Ibrahim Idris.............

    baba ku bayan fulani wasu rashin najeriya shugaban bashir ibrahim idris
    Kafafen sadarwa sun zama babbar barazana ga zaman lafiyar Najeriya- Majalisa

    Play Episode Listen Later Aug 22, 2025 3:38


    Majalisar Dattawan Najeriya ta bayyana cewar ya zama dole ta yi dokokin da za su takaita yadda kafofin sada zumunta ke neman haifar da tashin hankali a cikin kasar. Shugaban masu rinjaye a Majalisar Bamidele Opeyemi ya bayyana haka, sakamakon zargin neman jefa kasar cikin tashin hankalin da matasa ke yi ta wadannan kafofi. Dangane da wannan yunkuri, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin harkar sadarwa,Malam Umar Saleh Gwani. Latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana...

    zaman najeriya shugaban bashir ibrahim idris
    Dr Abubakar Sadiq Muhammad kan matsalolin tsaro a Najeriya

    Play Episode Listen Later Aug 21, 2025 3:33


    Gwamnan Jihar Kaduna da ke Arewacin Najeriya, Uba Sani ya ce matakin soji kawai ba zai iya magance ayyukan ta'addancin da ake fuskanta a ƙasar ba. Gwamnan ya ce ya zama wajibi a magance matsalolin da ke haifar da matsalar baki ɗaya da suka haɗa da talauci da nuna banbanci da rashin shugabanci na gari da kuma bai wa matasa dama. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abubakar Sadiq Muhammad, tsohon malami a jami'ar Ahmadu Bello akan matsalar ta tsaro a ƙasar. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu...................

    ku sadiq abubakar najeriya bashir ibrahim idris
    Farfesa Balarabe Sani Garko kan rage farashin wanke ƙoda a wasu asibitocin Najeriya

    Play Episode Listen Later Aug 20, 2025 3:34


    Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya amince da rage farashin wankin ƙoda daga naira 50,000 zuwa naira 12,000 a manyan asibitocin tarayya a faɗin ƙasar. Daniel Bwala, mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan Bayanan da suka shafi tsare-tsaren gwamnati ne ya bayyana hakan a shafin sada zumuntansa na X, inda ya ce matakin zai sauƙaƙa wa dubban marasa lafiya masu fama da ciwon ƙoda. An fara aiwatar da wannan mataki a manyan asibitoci kamar FMC Ebute-Metta da ke Lagos da FMC da ke Jabi a Abuja da UCH Ibadan da FMC Owerri da UMTH Maiduguri, yayin da za a ƙara wasu kafin ƙarshen shekara domin samun damar amfani da su a duk faɗin ƙasar. Sai dai da safiyar Laraba bayan rahotannin RFI, Gwamnatin Najeriya ta ɗan daidaita jerin sunayen manyan asibitocin ƙasar da za su ci gajiyar sabon tallafin domin sauƙaƙawa majinyta wanke ƙoda, inda aka ƙara asibitin koyerwa na Malam Aminu Kano da ke jihar Kano. Cikin sanarwar da ma'aikatar lafiyar ƙasar ta fitar, ta ce za'a ci gaba da ƙara wasu asibitocin ne dama sannu a hankali, amma ba mantawa da wani sashin ƙasar akayi ba. Ga asibitocin da za su amfana da sabon ragin farashin ƙudin wankin ƙoda 1. Asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano 2. Asibitin koyarwa na Maiduguri 3. Asibitin koyarwa na Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi 4. Asibitin koyarwa na Jos 5- Babban Asibitin tarayya da ke Abuja 6. Cibiyar kula da lafiya ta tarayya da ke Ebute Metta a Lagos 7. Asibitin jami'ar Ibadan 8. Asibitin koyarwa na Benin. 9.Cibiyar lafiya ta tarayya da ke Yenagoa a Bayelsa 10.Asibitin koyarwa ta Owerri da ke Imo 11. Asibitin koyerwa na Abakaliki da ke Ebonyi.

    Farfesa Yusuf Abdu Misau akan rungumar abinicin da aka sauya wa halitta

    Play Episode Listen Later Aug 19, 2025 3:38


    Gwamnatin Najeriya ta bayyana shirin amfani da malaman addini wajen wayar da kan jama'a wajen rungumar amfani da abincin da aka sauyawa kwayar halitta da ake kira GMO. Shugaban hukumar kula da irin wadannan abinci Farfesa AbdullahI Mustapha ya bayyana haka a tattaunawarsa da RFI Hausa. Ganin yadda jama'a ke dari darin amfani da irin wannan abinci, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin kula da harkar lafiya, Farfesa Yusuf Abdu Misau, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana. 

    gmo akan noma abdu najeriya shugaban bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da Janar Kukasheka mai ritaya kan kama shugabannin ƙungiyar Ansaru

    Play Episode Listen Later Aug 18, 2025 3:36


    Gwamnatin Najeriya ta bayyana nasarar kama shugabannin ƙungiyar ƴan ta'adda da ake kira Ansaru mai alaƙa da Al'Qaeda, wadda tayi ƙaurin suna wajen kai munanan hare hare a jihohin Neja da kwara. Mai baiwa shugaban ƙasar Najeriya a kan harakokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu ya bada wannan sanarwar. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Tsofan kakakin runduna sojin Najeriya Janar Sani Usman Kukasheka ga kuma yadda zantawarsu ta gudana. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hira......

    kama shiga neja najeriya bashir ibrahim idris

    Claim Bakonmu a Yau

    In order to claim this podcast we'll send an email to with a verification link. Simply click the link and you will be able to edit tags, request a refresh, and other features to take control of your podcast page!

    Claim Cancel