A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban…
Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International a Najeriya ta yi zargin cewa jirgin sojin saman ƙasar ya yi ruwan bamai-bamai kan jami'an sakai tare da kashe akalla 20 da jikkata wasu da dama a ƙauyukan Maraya da Wabi da ke ƙaramar hukumar Maru na jihar Zamfara. Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar jiya Litinin, ta ce lamarin kai tsaye ya shafi jami'an sakai da suka taru domin tunkarar ƴan bindiga da suka kai hare-hare a ƙauyukan nasu ranar Asabar. A tattaunawarsa da Ahmad Abba, Daraktan Amnesty International a Najeriya, Malam Isa Sunusi, ya fara da bayani kan yadda lamarin ya auku.
Kwanaki biyar bayan da ambaliyar ruwa ta afka wa garin Mokwa na jihar Neja a tarayyar Najeriya, mahukunta a yankin sun ce adadin mutanen da aka tabbatar da cewa sun rasa rayukansu sun kai ɗari biyu. A cewa Sakataren ƙaramar hukumar ta Mokwa Dauda Liman Mokwa, yanzu ana kyautata zaton cewa akwai gawarwaki da dama da ba a kai ga gano su ba, ko dai a cikin ruwa ko kuma a ƙarƙashin gine-ginen da suka rufta. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawarsa da Abdulkarim Ibrahim Shikal..............
Yau Alhamis shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ke cika shekaru 2 a kan karagar mulki, bayan rantsuwar kama aikin da ya yi a rana mai kamar ta yau, cikin shekarar 2023. La'akari da yadda ra'ayoyi suka banbanta a tsakanin ƴan ƙasar a kan manufofi da sauran matakan wannan gwamnati.......ya sa muka nemi tsokacin Kwamrade Ishaq Ja'afar Ɗalhat Gandun Albasa, mai sharhi kan lamurran yau da kullum a Najeriyar. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Nura Ado Suleiman...........
Yayin ake ci gaba da bikin cika shekaru 50 da kafa Ƙungiyar Haɓaka Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika ECOWAS/CEDEAO, a wannan karo za mu yi dubi a game da wasu daga cikin muhimman ayyukan da ƙungiyar ta yi a fagen yaƙi da rashawa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna Dr Abdullahi Shehu, tsohon jakadan Najeriya a Rasha, kuma wanda ya jagora hukumar ta GIABA tsawon shekaru 8. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tasu...........
Ranar 28 ga watan Mayu, wato gobe Laraba kenan, Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afrika ECOWAS, ke cika shekaru 50 da kafuwa.An dai samar da ƙungiyar ne cikin watan Mayun shekarar 1975 a birnin Legas, inda a wacccan lokacin ta ƙunshi ƙasashe 15. A tsawon lokacin da ta shafe bayan kafuwarta, ECOWAS ta taka rawa muhimmiyar rawa ta fuskar tsaro, ciki kuwa har da kawo ƙarshen yaƙe-yaƙen da suka nemi wargaza ƙasashen Saliyo da Liberia. Kan haka ne kuma Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da, Air Comodore Tijjani Baba Gamawa ɗaya daga cikin sojojin da suka bayar da gudunmawa a waccan lokaci.
Gwamnmatin Jamhuriyar Nijar ta buƙaci ƴan asalin ƙasashen ƙetare da ke aiki a ɓangaren man fetur da su fice daga ƙasar kafin ranar 31 ga wannan wata na Mayu. Mafi yawan waɗanda matakin zai shafa ƴan ƙasar China ne da ke aikin haƙowa, da tacewa, sai kuma waɗanda ke fitar da mai ta bututu zuwa ƙetare. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Alhaji Nouhou Abdou Magaji da Abdoulkarim Ibrahim Shikal.....
Kungiyar kasashen Afirka ta Yamma ta ECOWAS ta bayyana shirin kafa sabuwar rundunar hadin kai wadda za ta dinga yaki da yan ta'addan da suka addabi yankin. Wannan na da cikin shirin shugabannin yankin na dakile ayyukan ta'addanci, da suka ƙi ci suka ƙi cinyewa.Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Janar Kape Alwali Kazir mai ritaya a dangane da wannan shiri.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
An gudanar da ƙwarya-ƙwaryar biki don murnar cika shekaru 18 da buɗe Sashen Hausa na Radio France International, inda aka samu halartar manyan baƙi da suka haɗa da sarakunan gargaji, ƴan siyasa da kuma masu sauraren rediyon da sauran kafafensa na yaɗa shirye-shirye. Ɗaya daga cikin manyan baƙi a taron shi ne Distinguished Senator Aliyu Ikra Bilbis wanda ya bayyana mahangarsa a game da waɗannan shekaru 18 na RFI Hausa. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Abdoulkarim Ibrahim Shikal..............
A yau 21 ga watan Mayun 2025, shekaru 18 kenan da Radio France International ya fara yaɗa shirye-shiryensa a cikin harshen Hausa, wanda kuma shi ne harshen na farko daga Afirka da RFI ta fara yaɗa shirye-shiryenta da shi. Malam Bashir Ibrahim Idris, shi ne Babban Editan RFI Hausa, ya yi muna ƙarin bayani a game da yadda rediyon ya fara da kuma irin ci gaba da ya samu a waɗannan shekaru. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawar da Ƙaribullah Abdulmajid Namadobi ya yi da shi...........
Aƙalla Direbobin manyan motoci uku sun mutu yayin da wasu da dama suka jikkata a wani saban harin da ƴanta'adda masu ikrarin jihadi suka kai kan ayarin motocinsu akan hanyar Burkina Faso zuwa Jamhuriyar a rana lahadin da ta gabata. Wanan ne karo na biyu cikin kasa da shekaru guda da ƴan bindigar ke farwa wadanan motoci tare da banka musu wuta.A kan wanan abokin aiki Oumar Sani ya tattauna da Gamatie Mahamadou Yansanbou, magatakarda kungiyar direbobin manyan motoci UTTAN a Jamhuriya Nijar ga kuma yadda zantawarsu ta gudana.Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar.
Da aalam dai har yanzu da sauran rina a kaba ga hukkumar JAMB, mai shirya jarabawar shiga manyan makarantu a Najeriya a game da matsalar da aka samu a lokacin jarabawar wannan shekarar sakamakon ƙorafin da wasu jihohin arewacin ƙasar ke yi akan ware wasu jihohi huɗu na kudu da hukumar ta yi don sake zana jarawabar. Tuni dai wasu suka yi barazanar zuwa kotu tare da kira ga gwamnati da ta saka baki a lamarin. Kan haka ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Barrister Abdullahi Jalo, masanin doka.
Babban Hafsan tsaron Najeriya, Laftanar Janar Christopher Musa ya ce baya ga amfani da makamai wajen tinkarar mayakan Boko Haram, farfado da Tafkin Chadi zai taimaka wajen samarwa jama'ar yankin sana'oi. Wannan ya biyo bayan ziyarar aikin da ya kai Maiduguri bayan kazaman hare haren da boko haram ta kai cibiyoyin soji.Dangane da wannan bukatar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da wani mutumin yankin, Farfesa Sheriff Muhammad Almuhajir.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Hukumar kula da jarabawar shiga manyan makarantu a Najeriya ta JAMB ta nemi gafarar jama'ar kasar saboda matsalolin da aka samu wajen jarabaswar bana, wadda ta kai ga dalibai sama da miliyan guda da rabi suka kasa samun makin da ake bukata. Shugaban hukumar Farfesa Ishaq Oloyede cikin hawaye ya nemi gafarar jama'a da kuma daukar alhakin lamarin.Dangane da wannan matsala, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Umar Saleh Gwani masanin harkar sadarwa.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Yayinda hare-haren ƙungiyar Boko Haram tsagin ISWAP ke ƙara tsananta musamman a Najeriya, rahotanni na cewa mayakan sun shafe ƙarshen makon jiya zuwa jiya Litinin suna kadammar da hare-hare a sassa na jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar.A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara, Farfesa Khalifa Dikwa masanin tsaro a Najeriya ya ce ba abin mamaki bane yadda ‘yan ta'addar suka sauya salon kai hare-harensu. Ku shiga alamar sauti domin sauraro karin bayani.....
Yayinda hare-haren ƙungiyar Boko Haram tsagin ISWAP ke ƙara tsananta musamman a Najeriya, rahotanni na cewa mayakan sun shafe ƙarshen makon jiya zuwa Litinin da ta gabata suna kadammar da hare-hare a sassa na jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar.A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara, Farfesa Khalifa Dikwa masanin tsaro a Najeriya ya ce ba abin mamaki bane yadda ‘yan ta'addar suka sauya salon kai hare-harensu. Shiga alamar sauti domin sauraron cikaken bayani.....
Wasu rahotanni a Najeriya na bayani akan karuwar samun mutanen dake fama da rashin lafiyar dake da nasaba da kwakwalwa, sakamakon yanayin rayuwar yau da kullum. Domin sanin tasirin matsalar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Balarabe Sani Garko na Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Gwamnonin Arewacin Najeriya tare da Sarakunan yankin sun gudanar da wani taro na musamman domin sake duba matsalolin tsaron da suka addabi yankin, a dai-dai lokacin da mayaƙan Boko Haram da ƴanbindiga ke ci gaba da hallaka jama'a ba tare da ƙaƙƙautawa ba. Bayan kammala taron, Bashir Ibrahim Idris ya tintibi Farfesa Bello Bada na Jami'ar Usman Dan Fodio da ke Sokoto. Kula latsa alamar sauti don sauraron yadda zantawarsu ta gudana akai...........
Dalilan da suka sanya 'yan Najeriya ke ƙara faɗawa cikin mawuyacin hali sanadiyyar talaucin da ya yi musu katutu. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziƙi a Najeriya Dr Kassim Garba Kurfi.Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawar...
Majalisar dokokin ƙungiyar ƙasashen ECOWAS ta gudanar da taron ta a Lome da ke ƙasar Togo, wanda ya mayar da hankali kan tsadar sufurin jiragen sama a yankin. Bayan taron, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Sanata Ali Muhammed Ndume, daya daga cikin shugabannin taron. Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar tattaunawar tasu.............
Yau manyan limaman dariƙar Katolika na duniya sama da 130 ke fara gudanar da zaɓen Fafaroma domin maye gurbin Francis da ya rasu a makon jiya.Domin sanin yadda ake gudanar da zaɓen, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Archpishop Ignatius Kaigama, daya daga cikin manyan limaman Katolika a Najeriya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana akai. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.....
Gwamnatin sojin Jamhuriyar Nijar ta bai wa hafsan sojojin ƙasar umarnin cewar babu wanda zai tafi ritaya a cikin wannan shekarar, sakamakon wasu matsalolin tsaron da kasar ke fuskanta. Dangane da wannan umarni, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Sani Yahya Janjuna, mai sharhi akan lamuran yau da kullum, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana akai.
Katafaren kamfanin sadarwar Meta da ya mallaki Facebook da WhatsApp ya yi barazamar ficewa daga Najeriya, saboda cin tararsa da hukumomin ƙasar suka yi na Dala miliyan 290, sakamako karya ƙa'idodin aikinsa. Najeriya ta samu kamfanin ne da laifin talla ba bisa ƙa'ida ba, da kuma rashin alkince bayanan asiri na jama'ar dake hulɗa da shi.Dangane da wannan dambarwa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hon Samaila Muhammed, masanin tallalin arziki da kuma sadarwa, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana akai.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar
Yau ɗaya ga watan Mayu take ranar Ma'aikata ta Duniya, ranar da ake duba gudummawa da sadaukarwar ma'aikata ga al'umma. A kan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da Dokta Aminu Idris Harbau, masanin tattalin arziki a jami'ar ilimi ta Sa'adatu Rimi da ke jihar Kano a Najeriya, wanda ya duba yadda wannan rana ta riski ma'aikata, tare da shawartar su a kan nema wa kansu mafita a yanayi da albashi ba zai wadata ba wajen tafiyar da rayuwa mai inganci.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakakkiyar hirarsu
A daidai lokacin da rikici tsakanin Mali da Algeria ke cigaba da ruruwa, Sarkin Morocco Mohammed VI ya gayyaci ministocin harkokin wajen ƙasashen Burkina Faso,Mali da kuma jamhuriya Nijar a fadarsa da ke birnin Rabat domin basu damar yin fanin da tashar ruwanta na Atlantic wajan jigilar kayakinsu.Ziyarar tasu dai na zuwa ne bayan da alaƙa tsakanin ƙasashen AES da Algeria, wacce ke zama babbar abokiyar hamayyar Morocco ta yi tsami. Latsa alamar sauti domin suraron karin bayani.....
Yau shugaban Amurka Donald Trump le cika kwanaki 100 a karagar mulkin ƙasar, tun bayan rantsar da shi a ranar 20 ga watan Janairun shekarar nan. A tsawon wannan lokaci, shugaban na Amurka ya ɗauki mabanbantan matakai da suak girgiza sassan duniya.Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Tukur Abdulkadir na Jami'ar Kaduna, don jin yadda masana ke kallon salon kamun ludayin Donald Trump ga kuma tattaunawarsu.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar..
Kungiyar Amnesty International ta tabbatar da mutuwar mutane 26 sakamakon harin ƴan bindiga a wurin hakar zinaren da ke jihar Zamfara. Daraktan ƙungiyar a Najeriya, Malam Isa Sanusi ne ya tabbatar da haka a tatatunawar da suka yi da Bashir Ibrahim Idris. Ku latsa alamar sautin don sauraron cikakkiyar tattaunawar tasu...........
‘Yan adawa a Najeriya sun zargi gwamnatin ƙasar ta jam'iyyar APC da yi musu rinto ta hanyar amfani da ƙarfin tattalin arziƙin ƙasa da ke hannunta da kuma wasu dabaru wajen sanya jiga-jigai daga ɓangaren su ‘yan adawar sauya sheka zuwa ga jam'iyya mai mulki. Wannan lamari ya maido da muhawara a tsakanin ‘yan Najeriya a kan dalilan da suke haddasa yawaitar sauyin shekar ‘yan siyasa daga ɓangaren adawa zuwa gwamnati.Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Kamilu Sani Fagge na jami'ar Bayero a Najeriya.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyarsu
Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya UNICEF, ya ce an samu ɓullar sabon nau'in cutar Polio a ƙananan hukumomi 18 da ke wasu jihohin Najeriya 9 ciki har da Kano. Rahoton ya ce zuwa yanzu an samu rahotanni daban daban aƙalla 18 kan ɓullar sabon nau'in cutar ta Shan Inna, kuma an tattara bayanan ne a cikin watanni uku da suka gabata zuwa yanzu.Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Sadiq Isa Abubakar, shugaban cibiyar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa na asibitin Malam Aminu Kano da kuma jami'ar Bayero.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu
Mazauna ƙauyuka da dama a wasu yankunan jihar Zamfara, ciki har da yankin Gusau ta Gabas, na rayuwa cikin tsananin fargabar fuskantar hare-haren ‘yan bindiga, muddin suka gaza biyan miliyoyin Nairar da ‘yan ta'addan ke tilasta musu bayar wa a matsayin musayar barinsu su zauna lafiya.Yayin ƙarin bayani a kan halin da suke ciki, da kuma ƙauyukan da ke cikin tashin hankalin, wani mazaunin ɗaya daga cikin yankunan, ya ce biyan maƙudan kuɗaɗen da suke yi ba ya kawar da barazanar da suke ciki.
Gwamnatin shugaba Donald Trump ta gabatar da ƙudurin daina ba da tallafi ga rundunonin wanzar da zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya, saboda gazawar da ta ce rundunonin na yi a ƙasashen Mali da Lebanon da kuma Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo.Amurka ce dai ke kan gaba wajen tallafa wa ayyukan wanzar da zaman lafiyar a sassan Duniya, inda take samar da kusan kaso 27 cikin 100 na kasafin da ake buƙata.akan haka ne, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Kamilu Sani Fagge.
Yanzu haka ana ci gaba da gudanar da bukukuwan Easter, waɗanda ke matsayin tunawa da ranar da aka gicciye Yesu Almasihu da kuma tashinsa bayan kwanaki uku. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Reverand Andrew Dayyu, wanda ya yi masa ƙarin bayani a game da abin da ake nufi da Easter da kuma muhimmancinta ga mabiyar addinin Kirista. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar zantawarsu.............
Dubban ‘yan Najeriya ne a cikin makon nan suka shiga cikin tashin hankali, sakamakon hasarar sama da Naira Tiriliyan 1 da suka tafka, a dalilin rushewar shafin CBEX, wanda ke hada-hadar kuɗaɗen Intanet. Shafin, ya ja hankalin mutane ne ta hanyar yi musu alƙawarin kason ribar 100 bisa 100 akan dukkanin adadin kuɗin da suka sanya cikinsa da zarar an cika kwanaki 30. Sai dai bayan ɗaukar wani ɗan lokaci, shafin tare da wakilansa da ke Najeriya suka yi layar zana.Kan wannan lamari, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Sagir Muhd mataimakin shugaban ƙungiyar ƙwararru kan na'ura mai ƙwaƙwalwa ta Najeriya......Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar
Gwamnatin Najeriya ta yi gargaɗin cewa jihohi 30 na ƙasar na fuskantar barazanar iftila'in ambaliyar ruwa yayin da daminar bana ta soma, kuma tuni ta fara shirin ƙaddamar da gangamin wayar da kan mutane game da illar ta da kuma hanyoyin rage kaifinta. To ko wace rawa hukumomi da al'umma za su taka dangane da rage mummanar illar da ambaliyar ke yi?Hauwa Halliru Gwangwazo ta tattauna da Umar Saleh Anka na ƙungiyar rajin kare muhalli a Najeriya.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar
A Gabon, ana ci gaba da yakin neman zabe a yau da ke jajuburin zaben Shugaban kasar,wanda ya hada 'yan takara takwas. Gwamnati ta ayyana ranar zaben gobe a matsayin ranar hutu, domin baiwa masu rajista a larduna damar yin balaguro. Ƴan adawa sun bayyana damuwarsu ganin ta yada shugaban majalisar sojin kasar ke amfani da kadarorin gwamanti a yakin zaben. A game da zaɓen, Abdoulaye Issa ya tattauna da Janjouna Ali Mahaman Sani, masanin siyasar ƙasar ta Gabon da kewaye.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu
A kasar Gabon, ana ci gaba da yakin neman zabe a yau da ke jajiberin zaɓen Shugaban ƙasar,wanda ya haɗa 'yan takara takwas. Gwamnati ta ayyana ranar zaben gobe a matsayin ranar hutu, domin baiwa masu rajista a larduna damar yin balaguro.Ƴan adawa sun bayyana damuwarsu ganin ta yada shugaban majalisar sojin kasar ke amfani da kadarorin gwamanti a yakin zaben.Abdoulaye Issa ya tattauna da Janjouna Ali Mahaman Sani, masani siyasar kasar ta Gabon da kewaye.Ga kuma yada zantawar tasu ta gudana.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
Rikici tsakanin Mali da Aljeriya na cigaba da ɗaukar saban salo, tun bayan da Aljeriya ta kakkaɓo wani jirgin sojin Mali mara matuƙi a kan iyakar ƙasashen biyu a farko makon jiya. Sai dai wani batu da ya baiwa kowa mamaki shi ne, yadda Nijar ta shigo cikin rikicin a matsayinta na mamba a ƙungiyar AES, wato saban kawance da ƙasashen Mali, Burkina Faso da Nijar suka kafa bayan ficewrasu daga ECOWAS.Umar Sani ya tattauna da Abdoul Moumouni Abass mai sharhi kan siyasar ƙasa da ƙasa.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
A Laraba 9 ga watan Afrilu, sabon harajin da ya kama daga kashi 10 zuwa sama, da shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaƙaba wa ƙasashen Afirka zai fara aiki, bayan da harajin da ya shafi sauran ƙasashe ya soma aiki a ranar 5 ga watan na Afrilu. Tun cikin makon jiya ne dai matakin na Trump ya soma tasiri a kasuwannin Turai da Asiya, a yayin da ƙasashen Afirka suka shiga zulumi dangane da makomarsu.Don jin tasirin da sabon harajin na Amurka zai yi a kan tattalin Arzikin arziƙin ƙasashen Afirka, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dr Ƙasim Garba Kurfi.A latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar zanatawar.
Ƙasashe da dama ciki har da na Ƙungiyar EU, sun alwashin mayar da martanin ƙaƙaba wa kayayyakin Amurka haraji, kamar yadda shugaba Trump ya ƙaddamar da sabon tsarin karɓar harajin da ya ce ya shafi duniya baki ɗaya.Sabon harajin dai ya kama ne daga kashi 10 zuwa sama, wanda ya shafi hajoji daga kowace ƙasa, matakin da Trump matakin ya ce ya ɗauka ne don kare buƙatun al'ummar Amurka. Don jin yadda masana ke kallon sabon yaƙin kasuwancin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta AbdulHakim Garba Funtua.
Kamar yadda wataƙila aka ji cikin labarun duniyar da suka gabata, shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu yayi tankaɗe da rairaya a fannin man fetur ɗin ƙasar inda ya sallami shugaban kamfanin NNPCL malam Mele Kyari da shugaba da mambobin majalisar aminattu na kamfanin. Nan take ne kuma shugaba Tinubun ya maye gurbin manyan jami'an da ya sallama. Ko yaya ƙwararru ke kallon wannan sauyi? Wakilinmu a Abuja Muhd Sani Abubakar ya tattauna da Injiniya Safiyya Sanusi, ƙwararriya a fannin man fetur da Iskar Gas.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirar
Gidajen man fetur a Najeriya na ci gaba da sauya farashi, bayan da matatar Dangote ta sanar da cewa yarjejeniyar da ke tsakaninta da NNPC wadda ke bayar da damar samun gurbataccen mai a farashin Naira ta kawo ƙarshe ba tare da an sabunta ta ba. Alhaji Abubakar Maigandi, shugaban ƙungiyar dillalan man fetur masu zaman kansu a Najeriya wato IPAM, ya ce tuni suka yi hasashen faruwar hakan bayan rugujewar waccan yarjejeniyar.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.
A farkon makon nan, Hukumar Zaɓen Najeriya INEC, ta ce ba a kammala cika ƙa'idojin da kundin tsarin mulki ya gindaya ba, a kan tsarin kiranyen da ake ƙoƙarin yi wa Sanata Natasha mai wakiltar yankin Kogi ta Tsakiya a zauren Majalisar Dattijai. INEC ta bayyana haka ne, bayan da ta fara nazari akan ƙorafe-ƙorafen da aka gabatar mata na nemn yi wa Sanata Natasha yankan ƙauna, wadda a kwanakin baya ta zargi shugaban Majalisar Dattawan Najeriyar Godswil Akpabio da cin zarafinta ta hanyar nemanta da lalata.Domin jin yadda tsarin na Kiranyen yake...Nura Ado Suleiman ya tattauna da Barista Abba Hikima, ƙwararren lauya a Najeriya.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
Gwamnatin Najeriya ta ɗauko hayar ƙwararrun sojoji daga wasu ƙasashen duniya, domin horas da sojojin ƙasar wajen yaƙi da ta'addanci, da kuma yin ƙundunbala wajen ceto mutanen da ‘yan ta'addan ke yin garkuwa da su. Ministan Tsaron Najeriya Badaru Abubakar ne ya sanar da matakin, a lokacin da yake ƙaddamar da aikin fara horas da kashin farko na sojojin Najeriyar a Kaduna. A kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Auwal Aliyu Abdullahi, mai magana da yawun Kwamitin musamman na kula da walwalar tsaffin sojoji a Najeriya.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawarsu.............
Sufeta Janar na ƴansandan Najeriya Kayode Egbetokun, ya jaddada umarnin Antoni Janar na ƙasar, kan haramcin holin waɗanda ake zargi da aikata laifuka da jami'an tsaro ke yi ga manema labarai, ba tare da an hukuncin kotu ba. Ya ce a lokuta da dama jam'an tsaro basa iya gabatar da hujjoji kan zarge-zagen a gaban kotu, duk da cewa an nuna wa duniya fuskokinsu, lamarin da ya ce ya sabawa dokokin kare hakkin ɗan adam. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tsakanin Khamis Saleh da Barista Al-Zubair Abubakar........
Yayin da ƙungiyar ECOWAS ke cika shekaru 50 a wannan mako, mun shirya muku rahotanni da hirarraki daban-daban dangane da gudunmawar da ƙungiyar ta bayar a cikin waɗannan shekaru. Daga cikin su akwai rawar da dakarun ECOMOG suka taka wajen magance rikice-rikice da aka samu a ƙasashen Liberia da Saliyo.Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Air Commodore Tijjani Baba Gamawa mai ritaya, ɗaya daga cikin sojojin da suka yi aikin samar da zaman lafiyar. ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
A ranar Larabar da ta gabata, matatar mai ta Ɗangote a Najeriya ta sanar da dakatar da sayar da mai da Naira ga 'yan kasuwa.Tuni dai lamarin ya haifar da fargaba a kan yiwuwar fukantar ƙarin farashin litar mai, bayan sauƙin da ‘yan Najeriya suka samu. Sai dai kamfanin ya ce matakin na wucin gadi ne, har sai an samu daidaito tsakaninsa da kamfanin NNPCL a kan adadin ɗanyen man da yake saye daga wurinsa da Naira.Kan wannan batu Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Aminu Idris Harbau, masanin tattalin arziƙi a Najeriya.Latsa alamar sauti don sauraren hirar:
Ƙungiyar Lauyoyin Najeriya ta bayyana rashin amincewar ta da matakin da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya ɗauka, na dakatar da gwamnan Jihar Rivers Siminalayi Fubara da majalisar dokokin jihar, tare da naɗa kantoman soji. Kungiyar tare da jam'iyyun adawa da kuma wasu masu sharhi na cewa matakin ya saba dokar ƙasa. Dangane da wannan matsayi, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin shari'a Barr Solomon Dalung. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu..........
Ƙasashe da hukumomi na ci gaba da yin tsokaci daban daban a kan halaka Falasɗinawa sama da 400 da Isra'ila ta yi jiya Talata a Gaza, lamarin da ya rusa yarjejeniyar tsagaita wutar da ta shafe watanni biyu tana aiki a yankin. Wani batu da ya ɗauki hankali bayan harin kuma shi ne, alwashin da Fira Ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya sha na amfani da ƙarfi fiye da na baya wajen ƙwato ragowar mutane kusan 60 da ƙungiyar Hamas ke riƙe da su a Zirin na Gaza. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Nura Ado Suleiman da Dakta AbdulHakim Garba Funtua kan wannan lamari......
Alƙaluma na nuni da cewa amfani da kuɗaɗen Crypto na daɗa samun karɓuwa a ƙasashen Yankin Kudu Da Saharar Afrika musamman ma Najeriya, inda a bara wani rahoto ya ce a tsakanin 2023 zuwa 2024, yawan kuɗaɗen Crypton da aka yi hada-hadarsu ya kai na Dalar Amurka biliyan 59. Wannan ya sa wasu ƙwararru bai wa mahukuntan Najeriyar shawarar, kamata yayi su rungumi sauyin domin amfana da shi a maimakon ƙoƙarin daƙile kasuwar Crypton, saboda illolin da suka ce na tattare da ita. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Nura Ado Suleiman da Dakta Ƙasim Garba Kurfi, masanin tattalin arziƙi a Najeriya..............
Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar sun ce an fara samun saukin karancin man fetur da aka fuskanta a kwanakin da suka gabata, abinda ya jefa jama'a da dama cikin halin kunchi. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Muhammadu Gamatche, shugaban gamayyar kungiyoyin masu motocin sufuri ta kasa a Nijar, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana
Kwanai bayan miƙa rahoton taron ƙasar da aka yi a Jamhuriyar Nijar, mutane na ci gaba da gabatar da ra'ayoyin su akai. Malam Sirajo Issa na ƙungiyar Mojen ya ce basa goyon bayan taron.
Gwamnatin Najeriya ta bai wa jihohin kasar Dala biliyan guda domin amfani da shi wajen magance matsalar da ake samu na mutuwar mata da jarirai lokacin haihuwa.Ministan lafiyar kasar Mohammed Pate ya sanar da haka.Domin jin tasirin da zai yi,Bashir Ibrahim Idriss ya tattauna da Farfesa Balarabe Sani Garko na Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.