Bakonmu a Yau

Follow Bakonmu a Yau
Share on
Copy link to clipboard

A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban…

Rfi - Azima Bashir Aminu


    • Jul 17, 2025 LATEST EPISODE
    • weekdays NEW EPISODES
    • 3m AVG DURATION
    • 945 EPISODES


    Search for episodes from Bakonmu a Yau with a specific topic:

    Latest episodes from Bakonmu a Yau

    Hira da Kwamared Umar Hamisu Ƙofar Na'isa kan matakin ladabtar da yansanda

    Play Episode Listen Later Jul 17, 2025 3:27


    Kamar yadda akaji a farkon Shirin, Hukumar kula da ƴansanda a Najeriya ta gurfanar da manyan jami'ai sama da 150 a gaban kwamitin ladabtarwa, bisa zarginsu da wulakanta aikin ɗansanda da kuma take hakkoki fararen hula a wasu lokutan. Bayanai sun ce an baiwa kwamitin kwanaki 10 ya gama binciken ƴansanda masu muƙamin ASP zuwa sama, ya kuma gabatar da rahoto wanda zai baiwa hukumomi damar ɗaukar matakin hukunci a kansu. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiya hirar.....

    Tattaunawa da Isma'ila Muhammed ɗan siyasa a Kamaru game da takarar Paul Biya

    Play Episode Listen Later Jul 15, 2025 3:32


    Shugaba Paul Biya na Kamaru mai shekaru 92 ya bayyana aniyar sake tsayawa takara don neman wa'adi na 8 na mulkin ƙasar da nufin ci gaba da yiwa ƙasar hidima. Shugaba Biya ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta. Sai dai ko yaya jama'ar Kamaru ke kallon wannan mataki, dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Isma'ila Muhammed ɗan siyasa a ƙasar ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar..

    Tattaunawa da makusancin Buhari, Faruk Adamu Aliyu kan rasuwar tsohon shugaban

    Play Episode Listen Later Jul 14, 2025 2:58


    A jiya Lahadi, 13 ga watan Yulin nan ne Allah ya yi wa tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari rasuwa yana da shekaru  82 a duniya. Bayan kasancewa shugaban gwamnatin sojin Najeriya daga shekarar 1983 zuwa da 1985, ya sake dawowa a matsayin farar hula, inda ya mulki ƙasar daga shekarar 2015 zuwa 2023. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Faruk Adamu Aliyu, ɗaya daga cikin makusantan Buhari akan wannan rasuwa da irin rayuwar da yayi. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....

    allah ku bayan buhari faruk muhammadu buhari yulin adamu najeriya shugaban bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da Alhaji Garba Suleiman Krako Madakin Saminaka kan ambaliyar Texas

    Play Episode Listen Later Jul 10, 2025 3:33


    Rahotanni daga Amurka na cewa an samu ƙaruwar yawan mutanen da suka rasa rayukansu a sakamakon Iftila'in Ambaliyar ruwan da ya afka wa Jihar Texas, inda zuwa yanzu adadin ya haura mutane 115, yayin da har aynzu aka gaza gano wasu aƙalla 160 da suka ɓace. Domin jin halin da ake ciki da kuma dalillan da suka haddasa aukuwar ambaliyar a Texas, Nura Ado Suleiman ya tattauna da mazaunin ƙasar ta Amurka, Alhaji Garba Suleiman Krako Madakin Saminaka. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....

    Tattaunawa da Dr Idris Harbau kan taron ƙasashen BRICS a Brazil

    Play Episode Listen Later Jul 9, 2025 3:34


    A ranar Litinin ƙasashe manbobin ƙungiyar BRICS suka kammala taronsu na 17 a Brazil, inda a cikin kwanaki biyu da suka shafe suna ganawa, jagororin ƙasashen suka tattauna a kan yadda manufofin shugaba Trump ke tasiri kan tattalin arziƙi da kasuwancin Duniya. Sai dai tun kafin kammala taron, shugaba Trump ɗin ya yi barazanar lafta harajin kashi 10 kan kayayyakin ƙasashen na BRICS, da ma duk wata ƙasa da ta goyi bayan matakan adawa da manufofin Amurka. Kan wannan batu, da kuma tasirin ƙungiyar ta BRICS Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Aminu Idris Harbau, masanin tattalin arziƙi da ke Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar..

    Tattaunawa da Sakataren ƙungiyar direbobin sufuri ta NURTW kan yawaitar haɗurra

    Play Episode Listen Later Jul 8, 2025 3:32


    Rahotanni daga Najeriya sun ce mutane da dama ne suka rasa rayukansu sakamakon haɗurran motoci da aka samu a ƙarshen mako cikin jihohin Kano da Jigawa da Bauchi da Lagos da kuma jihar Oyo baya ga Lagos da kuma jihar Kogi. Wannan na zuwa ne a dai dai lokacin hanyoyin motoci ke ci gaba da taɓarɓarewa, yayinda wasu direbobin ke tuƙi cikin yanayi na maye ko kuma saɓawa dokokin tuƙi. Dangane da wannan matsala da ke kaiwa ga asarar ɗimbin rayuka, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Adamu Idris Abdullahi Sakataren ƙungiyar direbobin sufuri ta NURTW da ke Abuja ga kuma yadda tattaunawarsu ta kasance. Sai ku latsa alamar sauti don saurare.

    Tattaunawa da Honourable Siraj Imam Ibrahim kan ambaliyar ruwan Kano

    Play Episode Listen Later Jul 7, 2025 3:37


    A ƙarshen makon da ya gabata aka samu ambaliyar ruwan sama a sassan birnin Kano, a dai dai lokacin da damina ta fara kankama a jihar. Wannan matsalar ta haifar da matsaloli ga mazauna da kuma baƙin da ke zuwa birnin. Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da shugaban ƙaramar hukumar Dala, Hon Siraj Ibrahim Imam, Kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.   Ku latsa alamar sauti son sauraron cikakkiyar Hirar.

    Dr Aliyu Bello kan ƙawancen 'yan adawa a Najeriya

    Play Episode Listen Later Jul 4, 2025 3:37


    A wannan mako ne yan adawan Najeriya suka kafa wani kawancen da suka ce zai tinkari Jam'iyyar APC a zabe mai zuwa, da zummar kawar da ita daga karagar mulki. Shirin Duniyarmu Ayau na RFI Hausa ya gudanar da mahawara tsakanin Sanata Ahmed Babba Kaita na sabuwar kawancen da kuma shugaban Jam'iyyar APC a Jihar Nasarawa Dr Aliyu Bello. Ga kadan daga cikin abinda shugaban APC ya fadi a cikin shirin da zai zo muku gobe da misalin karfe 5 na yamma.

    Emmanuel Shehu kan haɗakar jam'iyyun adawa a Najeriya da nufin tunkarar APC mai mulki

    Play Episode Listen Later Jul 3, 2025 3:27


    Wasu daga cikin jiga-jigan ƴan adawar Najeriya sun haɗa kansu wajen komawa jam'iyyar ADC domin shirin tunkarar gwamnatin APC mai mulki da suke zargi da rashin iya mulki, Yayin gabatar da sabbin shugabannin, ƴan adawar sun sha alwashin ceto talakan Najeriya daga halin ƙuncin da ya samu kansa. Sai dai wasu na cewa neman mulki ne kawai suke yi amma ba don talakan Najeriya ba. Bashir Ibrahim Idris ya tattauwa da shugaban cibiyar horar da ƴan Jaridu ta IIJ da ke Abuja, Dr Emman Shehu, kuma ga yadda zatawarsu ta gudanar.

    sai apc abuja adc akar yayin wasu najeriya bashir ibrahim idris
    Dr Yahuza Getso kan yadda jami'an sojoji suka hallaka Kachalla Ɗanbokolo a Zamfara

    Play Episode Listen Later Jul 2, 2025 3:36


    A Najeriya mayaƙan sa kai a jihar Zamfara sun yi nasarar hallaka wasu daga cikin manyan kwamandojin ƴan bindigar da suka hana zaman lafiya a jihar, cikinsu har da Kachalla Ɗanbokolo da wasu tarin magoya bayansu. Domin sanin tasirin wannan nasara ga jama'ar yankin, Bashir Ibrahim Idris ya tattauba da masanin harkar tsrao, Dr Yahuza Getso.   Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar

    suka domin yadda zamfara najeriya bashir ibrahim idris
    Muhammad Adamu Dansitta kan shirin gwamnatin Najeriya na dasa bishiyoyi biliyan 20

    Play Episode Listen Later Jul 1, 2025 3:02


    Gwamnatin Najeriya ta sha alwashin dasa itatuwa biliyan 20, a kokarin da take yi na magance gurgusowar hamada da tsananin zafi , har ma da sauyin yanayi. Mataimakin shugaban kasar Kashin Shetimma ne ya bayyana hakan, yayin da yake jawabi a wajen wani taroa  kasar Habasha. Game da tasirin wannan, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Muhammad Adamu Dansitta. Dannan alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar.

    game dasa shirin adamu najeriya bashir ibrahim idris
    Issof Emoud kan sabuwar Majalisar Tuntuɓa da gwamnatin sojin Nijar da kafa

    Play Episode Listen Later Jun 30, 2025 3:34


    Majalisar Tuntuɓa da gwamnatin sojin Jamhuriyar Nijar ta kafa ta conseil consultatif na fara aiki a ranar Asabar 28 ga watan Yunin wannan shekara ta 2025, Majalisar mai kunshe da mambobi 194 an ɗaura mata nauyin bayar da shawarwari kan harokin da su ka shafi cigaban ƙasa da  kuma gayyato majalisa zartaswa domin amsa tambayoyi idan hakan ta kama. A kan haka Oumar Sani ya  tattauna da Hon. Issouf Emoud ɗan majalisa mai wakilta jihar Agadas.

    kafa nijar jamhuriyar nijar majalisar
    Amb Abubakar Chika: cika shekaru 80 da sanya hannu kan yarjejeniyar samar da MDD

    Play Episode Listen Later Jun 26, 2025 3:35


    Yau ake cika shekaru 80 da rattaɓa hannu kan yarjejeniyar da ta samar da Majalisar Ɗinkin Duniya da aka gudanar a Birnin San Francisco da ke Amurka, a ranar 26 ga watan Yunin shekarar 1945. Bikin cika shekaru 80 din na zuwa ne a daidai lokacin da Majalisar mai wakilai 193 ke fuskantar kalubale da dama, waɗanda suka hada da makomar ta ko kuma ci gaban tasirinta baki ɗaya. Kan wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ambasada Abubakar Chika, tsohon jakadan Najeriya a Iran. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana..........

    iran ku bikin chika samar sanya duniya abubakar hannu yau najeriya amurka majalisar dinkin duniya majalisar bashir ibrahim idris
    Aliyu Dawobe kan janyewar wasu ƙungiyoyin agaji a Arewa maso Gabashin Najeriya

    Play Episode Listen Later Jun 25, 2025 3:47


    Ƙungiyar agaji ta ICRC wadda ke aiki a yankin arewa maso gabashin Najeriya, ta bayyana damuwa da janyewar wasu ƙungiyoyin agaji da ke bai wa ƴan gudun hijira tallafi a yankin. Babban jami'in yada labaran ƙungiyar a Najeriya, Aliyu Dawobe da ke ziyarar aiki a Lagos, ya mana ƙarin bayani dangane da halin da suke ciki.  Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Bashir Ibrahim Idris...........

    lagos ku maso icrc wasu arewa najeriya bashir ibrahim idris
    Janar Sani Usman Kukasheka kan rundunar tsaro ta haɗin gwiwar ƙasashen ECOWAS

    Play Episode Listen Later Jun 24, 2025 3:17


    Shugabannin ƙsashen Yammacin Afrika da ke ƙarƙarshin ƙungiyar ECOWAS sun sake bayyana damuwarsu dangane da ƙruwar matsalar tsaro a yankin. Yayin taron da suka gudanar a ƙarshen mako, shugaban ƙungiyar mai barin gado kuma shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake gabatar da buƙatarsa ta tabbatar da rundunar tsaro ta haɗin gwiwar da zata tinkari wannan matsalar. Bashir Ibrahim Idris ya tattaunawa da Janar Sani Usman Kukasheka mai ritaya,tsohon kakakin rundunar sojin Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu..........

    ku usman sani ecowas yayin najeriya bashir ibrahim idris
    Muhammad Ibrahim Sa'id kan yunƙurin kwaso ƴan Najeriya da ke Iran

    Play Episode Listen Later Jun 23, 2025 3:04


    Yanzu haka ƙasashe na ci gaba da ɗaukar matakan kwashe al'ummominsu daga Iran da kuma Isra'ila, saboda yadda yaƙi ya tsananta a tsakanin ƙasashen biyu. Bayanai na nuni da cewa ofishin jakadancin Najeriya da ke Iran, ya fara tsara yadda za su kwashe ƴan Najeriya da motoci zuwa Armenia kafin wataƙila a yi amafani da jiragen don dawo su gida. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Muhammad Ibrahim Sa'id, ɗan Najeriya da ke karatu a birnin Qoom mai tazarar kilomita 150 a kudancin Tehran. Ku latsa alamar sauti domin jin zantawarsu........

    iran armenia tehran ku isra urin najeriya yanzu abdoulkarim ibrahim shikal
    IPMAN ta yaba wa Dangote na fara rarraba man fetur da Disal zuwa sassan ƙasar

    Play Episode Listen Later Jun 19, 2025 3:21


    Ƙungiyar dillalan man fatir masu zaman kansu ta Najeriya IPMAN ta yaba da sabon shirin matan man Dangote na fara rarraba man fetur da Disal daga Lagos zuwa sassan ƙasar, sai dai ta ci gaba da nuna damuwa kan sabon harajin naira 12,500 da gwamnatin jihar Lagos ta sanya kan duk mota guda kafin bin titin Lekki da ke kaiwa matatar Dangote da sauran kamfanonin mai dake yankin, matakin da ya haifar da fargabar samun karin faranshin litar mai, masamman a arewacin ƙasar. Sai dai a tataunawarsa da Ahmad Abba, shugaban ƙungiyar IPMAN, Alhaji Abubakar Maigandi, ya ce bayan ɗan yajin aikin da derebobin dakon mai suka yi, gwamnatin Lagos ta sanya ranar Yau Alhamis, domin cimma matsaya kan wannan batu. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawarsu................

    Jaloud Sambo kan juya baya ga takarar Paul Biya da ƴan adawar Kamaru suka yi

    Play Episode Listen Later Jun 18, 2025 3:34


    A yayin da guguwar siyasa ke kaɗawa a Jamhuriyar Kamaru, alamu na nuni da cewa jiga-jigan jam'iyyu da suka daɗe suna ƙawance da jam'iyyar MPRC  mai mulkin ƙasar za su yi wata tafiya ta daban saɓanin ta shugaba Paul Biya ba. Bisa ga dukkannin alamu, ƙusoshin ƴan siyasa daga arewacin Kamaru da suka shafe shekaru a tafiyar kuma ke riƙe da manyan makamai irin su Isa Ciroma Bakari da Bello Buba Maigari sun fara tunanin yin watsi da tafiyar shugaba Biya, kamar yadda ake raɗe-raɗi. Akan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da Jaloud Sambo, shugaban ƴaƴan jam'iyyar adawa ta MPSC da ke zaune a ƙasashen waje.......

    Tattaunawa da Dr Awwal Abdullahi kan kashe-kashen jihar Benue

    Play Episode Listen Later Jun 17, 2025 7:52


    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya umarci jami'an tsaro da su kawo karshen kashe-kashen da ake yi a jihar Benue ta tsakiya, inda rahotanni ke cewa fiye da mutane 200 ne suka mutu a wasu jerin hare-hare da aka kai Yelewata a baya-bayan nan. Kiran na zuwa bayan da daruruwan mutane suka gudanar da zanga-zanga a Makurdi babban birnin jihar domin nuna adawa da kashe-kashen.  A tattaunarsa da Ahmed Abba, Dr. Awwal Abdullahi Aliyu, masanin harkokin tsaro, kuma babban magatakardar ƙungiyar tsoffin sojojin Najeriya, ya fara da bayyana dalilan da ke haddasa rikicin. Shiga alamar sauti domin jin cikakken bayani.....

    Alhaji Abubakar Cika kan rikicin Isra'ila da Iran

    Play Episode Listen Later Jun 16, 2025 3:37


    A wannan litinin an shiga rana ta huɗu da fara yaƙi gadan-gadan tsakanin Isra'il ta Iran, inda kowanne daga cikin ƙsashen biyu ke amfani da manyan makamai don kai wa farmaki a kan manyan biranen ƙasashensu. Domin yin dubi a game da wannan rikici da ake ganin cewa muddun ba a dakatar da shi ba zai shafar ƙasashe da dama, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon jakadan Najeriya a Iran. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hira da Ambasada Alhaji Abubukar Cika.....

    iran isra domin abubakar shiga najeriya abdoulkarim ibrahim shikal
    Farfesa Kamilu Sani Fagge kan bikin ranar dimokaraɗiyar Najeriya

    Play Episode Listen Later Jun 12, 2025 3:37


    Yau Najeriya ke bikin Ranar Dimokaraɗiya, wadda gwamnatin ƙasar ta ware domin girmamawa a ranakun 12 ga watan Yunin kowace shekara, don tunawa da soke zaɓe na makamancin lokacin da gwamnatin mulkin soji ta yi a shekarar 1993. La'akari da cewa zuwa yanzu Najeriyar ta cika shekaru 26 kenan cif a ƙarƙashin mulkin Dimokaraɗiya, ya sanya Nura Ado Suleiman tattaunawa da Farfesa Kamilu Sani Fagge na Jami'ar Bayero da ke Kano. Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar tattaunawasu..............

    Sarkin Hausawan Mokwa kan makomar al'ummar da ambaliya ta shafa

    Play Episode Listen Later Jun 11, 2025 3:03


    Bayanai daga Najeriya na cewa wasu daga cikin al'ummar da ibtila'in ambaliyar garin Mokwa ta jihar Neja ya shafa sun bijirewa yunƙurin mahukunta na kwashe su daga inda lamarin ya auku.Sai dai wani  jagoron al'umma a yankin ya musanta labarin, yana mai cewa jama'a a shirye suke duk lokacin da gwamnati ta shirya kwashe su. Ku latsawa alamar sauti domin jin karin bayani.....

    Dr Mustapha Karkarna kan tanon duniya game da barazanar da Tekuna ke fuskanta

    Play Episode Listen Later Jun 10, 2025 3:39


    Yayin da aka buɗe babban taro kan alkinta tekunan duniya a birnin Nice na Faransa, Majalisar Ɗinkin Duniya ta buƙaci a sake rattaba hannu kan sabbin yarjejeniyoyi da za su mayar da hankali kan alkinta tekuna da kuma kare hallittun ƙarƙashin ruwa. To sai dai duk da kasancewar Nahiyar Africa yankin da yafi fama da matsalolin muhalli ciki har da gurgusowar tekun, da alama taron bai yiwa yankin tanadin komai ba. Kan haka muka tattauna da Dr Mustapha Zakari Karkarna. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Rukayya Abba Kabara................

    Malaman makarantu sun sake tsunduma yajin aiki a Nijar

    Play Episode Listen Later Jun 9, 2025 3:26


    Gamayyar ƙungiyoyin malaman makarantu da ke koyarwa a matakai daban daban a Jamhuriyar Nijar, sun sanar da shiga yajin aikin kwanki 5 a jere daga wannan litinin, tare da barazanar da baiwa kowane ɗalibi maki ɗari bisa ɗari na jarabawar da aka yi masa. Malaman suna wannan yajin aiki  ne don neman gwamnati ta biya musu buƙatunsu da suka haɗa da: ɗaukar malaman kwantaragi a matsayin ma'aikata na dindindin, tare da biyan wasu kuɗaɗensu na alawus da suka maƙale a hannun gwamnati. A game da wannan batu, Ibrahim Malam Tchillo, ya zanta da shugaban ƙungiyar ASO EPT, mai fafutar samar da ilimi mai nagarta ga al'ummar Nijar wato Ibrahim Babaye Sani.Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana..................

    sake ku aiki nijar jamhuriyar nijar
    Badaru Abubakar kan yadda ƴan Boko Haram suka ƙara ƙaimi wajen kai hare-hare

    Play Episode Listen Later Jun 8, 2025 3:24


    Matsalar tsaro na ci gaba da addabar ƙasashen da ke yankin Sahel, lamarin da ke ƙara maida hannun agogo baya wajen yaƙi da ta'addanci da su ke yi. A wata zantawa da ministan tsaron Najeriya Mohammed Badaru Abubakar, ya ce ƴan ta'addan rinsu Boko Haram sun sauya salon kai hare-haren ta'addancinsu ne, sai dai ya ce a yanzu dakurun sojojin Najeriya sun gano salon kuma suna samun galaba akan ƴan ta'addan, lamarin da ya ce nan ba da jimawa za a kawo ƙarshen matalar. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsa da Aminu Sani Sado..........

    Dr. Kabir Adamu kan kiran da Janar Christopher ya yi na gine iyakokin Najeriya

    Play Episode Listen Later Jun 5, 2025 6:39


    Babban hafsan tsaron sojin Najeriya Janar Christopher Musa, ya yi kira da a gina katanga a ɗaukacin iyakokin ƙasar domin kawo karshen matsalolin tsaro da ƙasar ke fuskanta. Janar Musa ya bayyana hakan ne yayin wani taro kan tsaro da aka gudanar a Abuja babban birnin ƙasar, inda ya bayyana katange iyakokin ƙasar a matsayin mai matuƙar muhimmanci, yana mai misali da yadda ƙasashen Pakistan da Saudiya suka katange iyakokinsu da Afghanistan da Iraq a matsayin abin koyi. Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawar Ahmad Abba da Dr. Kabir Adamu, shugaban kamfanin tsaro na Beacon Security and Intelegence a Najeriya........

    Najeriya na shirin shigar da shanu daga Denmark

    Play Episode Listen Later Jun 4, 2025 3:34


    Gwamnatin tarayyar Najeriya ta sanar da shirinta na shigar da wasu shanu daga ƙasar Denmark, a ƙoƙarinta na rage kashe kuɗaɗen shigar da madara da kuma wadatarta a ƙasar, wanda yawansu ya kai dala biliyan 1.5 duk shekara. Duk da ikirarin kasancewarta ƙasar da ta fi kowacce yawan shanu a nahiyar Africa, amma Najeriya na samar da tan dubu 700 na madara duk shekara ne, ƙasa da tan miliyan 1.6 da ƴan ƙasar ke buƙata. To sai dai a zantawarsa da RFI Hausa, sakataren Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Najeriya Baba Usman Ngerzelma ya ce babu buƙatar ɗaukar wannan mataki da za'a mayar da hankali kan shanun da ake da su a ƙasar.Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Rukayya Abba Kabara..........

    Ƙungiyar Amnesty ta zargi sojojin Najeriya da kashe ƴan-sa-kai a Zamfara

    Play Episode Listen Later Jun 3, 2025 3:18


    Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International a Najeriya ta yi zargin cewa jirgin sojin saman ƙasar ya yi ruwan bamai-bamai kan jami'an sakai tare da kashe akalla 20 da jikkata wasu da dama a ƙauyukan Maraya da Wabi da ke ƙaramar hukumar Maru na jihar Zamfara. Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar jiya Litinin, ta ce lamarin kai tsaye ya shafi jami'an sakai da suka taru domin tunkarar ƴan bindiga da suka kai hare-hare a ƙauyukan nasu ranar Asabar.  A tattaunawarsa da Ahmad Abba, Daraktan Amnesty International a Najeriya, Malam Isa Sunusi, ya fara da bayani kan yadda lamarin ya auku.

    Har yanzu akwai sauran gawarwakin da ba a gano ba - Dauda Mokwa

    Play Episode Listen Later Jun 2, 2025 3:01


    Kwanaki biyar bayan da ambaliyar ruwa ta afka wa garin Mokwa na jihar Neja a tarayyar Najeriya, mahukunta a yankin sun ce adadin mutanen da aka tabbatar da cewa sun rasa rayukansu sun kai ɗari biyu. A cewa Sakataren ƙaramar hukumar ta Mokwa Dauda Liman Mokwa, yanzu ana kyautata zaton cewa akwai gawarwaki da dama da ba a kai ga gano su ba, ko dai a cikin ruwa ko kuma a ƙarƙashin gine-ginen da suka rufta. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawarsa da Abdulkarim Ibrahim Shikal..............

    ku gano neja dauda najeriya akwai yanzu
    Kwamrade Ishaq Ja'afar kan cikar gwamnatin Tinubu shekaru biyu kan karaga

    Play Episode Listen Later May 29, 2025 3:33


    Yau Alhamis shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ke cika shekaru 2 a kan karagar mulki, bayan rantsuwar kama aikin da ya yi a rana mai kamar ta yau, cikin shekarar 2023. La'akari da yadda ra'ayoyi suka banbanta a tsakanin ƴan ƙasar a kan manufofi da sauran matakan wannan gwamnati.......ya sa muka nemi tsokacin Kwamrade Ishaq Ja'afar Ɗalhat Gandun Albasa, mai sharhi kan lamurran yau da kullum a Najeriyar. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Nura Ado Suleiman...........

    Dr Abdullahi Shehu kan rawar da ECOWAS ta taka wajen yaƙi da rashawa

    Play Episode Listen Later May 28, 2025 3:31


    Yayin ake ci gaba da bikin cika shekaru 50 da kafa Ƙungiyar Haɓaka Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika ECOWAS/CEDEAO, a wannan karo za mu yi dubi a game da wasu daga cikin muhimman ayyukan da ƙungiyar ta yi a fagen yaƙi da rashawa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna Dr Abdullahi Shehu, tsohon jakadan Najeriya a Rasha, kuma wanda ya jagora hukumar ta GIABA tsawon shekaru 8.  Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tasu...........

    ku taka rasha ecowas abdullahi yayin najeriya bashir ibrahim idris
    Air Comodore Tijjani Baba Gamawa kan bikin cikar ECOWAS shekaru 50 da kafuwa

    Play Episode Listen Later May 27, 2025 3:06


    Ranar 28 ga watan Mayu, wato gobe Laraba kenan, Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afrika ECOWAS, ke cika shekaru 50 da kafuwa.An dai samar da ƙungiyar ne cikin watan Mayun shekarar 1975 a birnin Legas, inda a wacccan lokacin ta ƙunshi ƙasashe 15. A tsawon lokacin da ta shafe bayan kafuwarta, ECOWAS ta taka rawa muhimmiyar rawa ta fuskar tsaro, ciki kuwa har da kawo ƙarshen yaƙe-yaƙen da suka nemi wargaza ƙasashen Saliyo da Liberia. Kan haka ne kuma Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da, Air Comodore Tijjani Baba Gamawa ɗaya daga cikin sojojin da suka bayar da gudunmawa a waccan lokaci.

    baba liberia bikin ecowas mayu legas comodore bashir ibrahim idris
    Alhaji Nouhou Magaji kan ƙorar ma'aikatan ƙetare a ɓangaren man fetur da Nijar ta yi

    Play Episode Listen Later May 26, 2025 3:29


    Gwamnmatin Jamhuriyar Nijar ta buƙaci ƴan asalin ƙasashen ƙetare da ke aiki a ɓangaren man fetur da su fice daga ƙasar kafin ranar 31 ga wannan wata na Mayu. Mafi yawan waɗanda matakin zai shafa ƴan ƙasar China ne da ke aikin haƙowa, da tacewa, sai kuma waɗanda ke fitar da mai ta bututu zuwa ƙetare.  Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Alhaji Nouhou Abdou Magaji da Abdoulkarim Ibrahim Shikal.....

    china ku orar mafi mayu nijar abdoulkarim ibrahim shikal
    Janar Alwali Kazir kan matakin ECOWAS na samar da rundunar yaki da ta'addanci

    Play Episode Listen Later May 23, 2025 3:38


    Kungiyar kasashen Afirka ta Yamma ta ECOWAS ta bayyana shirin kafa sabuwar rundunar hadin kai wadda za ta dinga yaki da yan ta'addan da suka addabi yankin. Wannan na da cikin shirin shugabannin yankin na dakile ayyukan ta'addanci, da suka ƙi ci suka ƙi cinyewa.Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Janar Kape Alwali Kazir mai ritaya a dangane da wannan shiri.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

    samar ecowas yaki shiga yamma wannan afirka bashir ibrahim idris
    Senator Ikra Bilbis kan cika shekaru 18 da fara watsa shirye-shiryen RFI Hausa

    Play Episode Listen Later May 22, 2025 3:39


    An gudanar da ƙwarya-ƙwaryar biki don murnar cika shekaru 18 da buɗe Sashen Hausa na Radio France International, inda aka samu halartar manyan baƙi da suka haɗa da sarakunan gargaji, ƴan siyasa da kuma masu sauraren rediyon da sauran kafafensa na yaɗa shirye-shirye. Ɗaya daga cikin manyan baƙi a taron shi ne Distinguished Senator Aliyu Ikra Bilbis wanda ya bayyana mahangarsa a game da waɗannan shekaru 18 na RFI Hausa. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Abdoulkarim Ibrahim Shikal..............

    senators ku hausa najeriya sashen hausa abdoulkarim ibrahim shikal
    Malam Bashir Ibrahim Idris kan cika shekaru 18 da kafuwar RFI Hausa

    Play Episode Listen Later May 21, 2025 3:39


    A yau 21 ga watan Mayun 2025, shekaru 18 kenan da Radio France International ya fara yaɗa shirye-shiryensa a cikin harshen Hausa, wanda kuma shi ne harshen na farko daga Afirka da RFI ta fara yaɗa shirye-shiryenta da shi. Malam Bashir Ibrahim Idris, shi ne Babban Editan RFI Hausa, ya yi muna ƙarin bayani a game da yadda rediyon ya fara da kuma irin ci gaba da ya samu a waɗannan shekaru. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawar da Ƙaribullah Abdulmajid Namadobi ya yi da shi...........

    ku malam rfi hausa najeriya afirka bashir ibrahim idris
    Gamatie Mahamadou Yansanbou-Kan ta'addancin masu ikirarin jihadi kan ayarin motocin dakon kaya

    Play Episode Listen Later May 20, 2025 3:35


    Aƙalla Direbobin manyan motoci uku sun mutu  yayin da wasu da dama suka jikkata a wani saban  harin da ƴanta'adda masu ikrarin jihadi suka kai kan ayarin motocinsu akan hanyar Burkina Faso zuwa Jamhuriyar a rana lahadin da ta gabata. Wanan ne karo na biyu cikin kasa da shekaru guda da ƴan bindigar ke farwa wadanan motoci tare da banka musu wuta.A kan wanan abokin aiki Oumar  Sani ya tattauna da Gamatie Mahamadou Yansanbou, magatakarda kungiyar direbobin manyan motoci UTTAN a Jamhuriya Nijar ga kuma yadda zantawarsu ta gudana.Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar.

    Abdullahi Jalo akan ƙorafin arewa a game da jarabawar JAMB

    Play Episode Listen Later May 19, 2025 3:24


    Da aalam dai har yanzu da sauran rina a kaba ga hukkumar JAMB, mai shirya jarabawar shiga manyan makarantu a Najeriya a game da matsalar da aka samu a lokacin jarabawar wannan shekarar sakamakon ƙorafin da wasu jihohin arewacin ƙasar ke yi akan ware wasu jihohi huɗu na kudu da hukumar ta yi don sake zana jarawabar. Tuni dai wasu suka yi barazanar zuwa kotu tare da kira ga gwamnati da ta saka baki a lamarin. Kan haka ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Barrister Abdullahi Jalo, masanin doka.

    game akan jalo abdullahi jamb tuni arewa najeriya bashir ibrahim idris
    Farfesa Sheriff Almuhajir kan makomar yankin Tafkin Chadi a ɓangaren tsaro

    Play Episode Listen Later May 16, 2025 3:39


    Babban Hafsan tsaron Najeriya, Laftanar Janar Christopher Musa ya ce baya ga amfani da makamai wajen tinkarar mayakan Boko Haram, farfado da Tafkin Chadi zai taimaka wajen samarwa jama'ar yankin sana'oi. Wannan ya biyo bayan ziyarar aikin da ya kai Maiduguri bayan kazaman hare haren da boko haram ta kai cibiyoyin soji.Dangane da wannan bukatar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da wani mutumin yankin, Farfesa Sheriff Muhammad Almuhajir.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

    Umar Saleh Gwani kan faɗuwar jarabawar JAMB a Najeriya

    Play Episode Listen Later May 15, 2025 3:35


    Hukumar kula da jarabawar shiga manyan makarantu a Najeriya ta JAMB ta nemi gafarar jama'ar kasar saboda matsalolin da aka samu wajen jarabaswar bana, wadda ta kai ga dalibai sama da miliyan guda da rabi suka kasa samun makin da ake bukata. Shugaban hukumar Farfesa Ishaq Oloyede cikin hawaye ya nemi gafarar jama'a da kuma daukar alhakin lamarin.Dangane da wannan matsala, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Umar Saleh Gwani masanin harkar sadarwa.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

    umar saleh shiga jamb najeriya shugaban hukumar bashir ibrahim idris
    Farfesa Khalifa Dikwa kan karuwar hare-haren Boko Haram a Borno

    Play Episode Listen Later May 14, 2025 3:40


    Yayinda hare-haren ƙungiyar Boko Haram tsagin ISWAP ke ƙara tsananta musamman a Najeriya, rahotanni na cewa mayakan sun shafe ƙarshen makon jiya zuwa jiya Litinin suna kadammar da hare-hare a sassa na jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar.A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara, Farfesa Khalifa Dikwa masanin tsaro a Najeriya ya ce ba abin mamaki bane yadda ‘yan ta'addar suka sauya salon kai hare-harensu. Ku shiga alamar sauti domin sauraro karin bayani.....

    Farfesa Khalifa Dikwa kan karuwar hare-haren Boko Haram a Borno

    Play Episode Listen Later May 14, 2025 3:40


    Yayinda hare-haren ƙungiyar Boko Haram tsagin ISWAP ke ƙara tsananta musamman a Najeriya, rahotanni na cewa mayakan sun shafe ƙarshen makon jiya zuwa Litinin  da ta gabata suna kadammar da hare-hare a sassa na jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar.A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara, Farfesa Khalifa Dikwa masanin tsaro a Najeriya ya ce ba abin mamaki bane yadda ‘yan ta'addar suka sauya salon kai hare-harensu. Shiga alamar sauti domin sauraron cikaken bayani.....

    Dakta Garko akan ƙaruwar masu matsalar ƙwaƙalwa a Najeriya

    Play Episode Listen Later May 13, 2025 3:35


    Wasu rahotanni a Najeriya na bayani akan karuwar samun mutanen dake fama da rashin lafiyar dake da nasaba da kwakwalwa, sakamakon yanayin rayuwar yau da kullum. Domin sanin tasirin matsalar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Balarabe Sani Garko na Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana. 

    akan domin masu alwa wasu najeriya bashir ibrahim idris
    Farfesa Bello Bada kan matsalar tsaro a Arewacin Najeriya

    Play Episode Listen Later May 12, 2025 3:27


    Gwamnonin Arewacin Najeriya tare da Sarakunan yankin sun gudanar da wani taro na musamman domin sake duba matsalolin tsaron da suka addabi yankin, a dai-dai lokacin da mayaƙan Boko Haram da ƴanbindiga ke ci gaba da hallaka jama'a ba tare da ƙaƙƙautawa ba. Bayan kammala taron, Bashir Ibrahim Idris ya tintibi Farfesa Bello Bada na Jami'ar Usman Dan Fodio da ke Sokoto. Kula latsa alamar sauti don sauraron yadda zantawarsu ta gudana akai...........

    bello boko haram bada kula bayan sokoto najeriya bashir ibrahim idris
    Dr Kassim Kurfi kan dalilan da suke sanya 'yan Najeriya ƙara talaucewa

    Play Episode Listen Later May 9, 2025 3:37


    Dalilan da suka sanya 'yan Najeriya ke ƙara faɗawa cikin mawuyacin hali sanadiyyar talaucin da ya yi musu katutu. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziƙi a Najeriya Dr Kassim Garba Kurfi.Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawar...

    sanya kassim bola ahmed tinubu najeriya bashir ibrahim idris
    Sanata Ali Ndume kan taron da majalisar dokokin ECOWAS tayi a Lome

    Play Episode Listen Later May 8, 2025 3:23


    Majalisar dokokin ƙungiyar ƙasashen ECOWAS ta gudanar da taron ta a Lome da ke ƙasar Togo, wanda ya mayar da hankali kan tsadar sufurin jiragen sama a yankin. Bayan taron, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Sanata Ali Muhammed Ndume, daya daga cikin shugabannin taron. Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar tattaunawar tasu.............

    ku togo bayan ecowas taron lome najeriya majalisar bashir ibrahim idris
    Archbishop Kaigama akan yadda ake zaɓen Fafaroma a dariƙar Katolika

    Play Episode Listen Later May 7, 2025 3:36


    Yau manyan limaman dariƙar Katolika na duniya sama da 130 ke fara gudanar da zaɓen Fafaroma domin maye gurbin Francis da ya rasu a makon jiya.Domin sanin yadda ake gudanar da zaɓen, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Archpishop Ignatius Kaigama, daya daga cikin manyan limaman Katolika a Najeriya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana akai. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.....

    archbishop akan domin yadda yau najeriya bashir ibrahim idris
    Babu sojan da zai yi ritaya a wannan shekarar a Jamhuriyar Nijar

    Play Episode Listen Later May 6, 2025 3:26


    Gwamnatin sojin Jamhuriyar Nijar ta bai wa hafsan sojojin ƙasar umarnin cewar babu wanda zai tafi ritaya a cikin wannan shekarar, sakamakon wasu matsalolin tsaron da kasar ke fuskanta. Dangane da wannan umarni, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Sani Yahya Janjuna, mai sharhi akan lamuran yau da kullum, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana akai.

    babu wannan sojan jamhuriyar nijar bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da Hon Samaila Muhammed kan barazanar Meta na ficewa daga Najeriya

    Play Episode Listen Later May 5, 2025 3:30


    Katafaren kamfanin sadarwar Meta da ya mallaki Facebook da WhatsApp ya yi barazamar ficewa daga Najeriya, saboda cin tararsa da hukumomin ƙasar suka yi na Dala miliyan 290, sakamako karya ƙa'idodin aikinsa. Najeriya ta samu kamfanin ne da laifin talla ba bisa ƙa'ida ba, da kuma rashin alkince bayanan asiri na jama'ar dake hulɗa da shi.Dangane da wannan dambarwa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hon Samaila Muhammed, masanin tallalin arziki da kuma sadarwa, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana akai.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar

    whatsapp ku muhammed dala daga najeriya bashir ibrahim idris
    Dr. Harbau: Yadda ma'aikata za su nema wa kansu mafita

    Play Episode Listen Later May 1, 2025 3:24


    Yau ɗaya ga watan Mayu take ranar Ma'aikata ta Duniya, ranar da ake duba gudummawa da sadaukarwar ma'aikata ga al'umma. A kan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da Dokta Aminu Idris Harbau, masanin tattalin arziki a jami'ar ilimi ta Sa'adatu Rimi da ke jihar Kano a Najeriya, wanda ya duba yadda wannan rana ta riski ma'aikata, tare da shawartar su a kan nema wa kansu mafita a yanayi da  albashi ba zai wadata ba wajen tafiyar da rayuwa mai inganci.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakakkiyar hirarsu

    Morocco ta baiwa ƙasashen AES damar yin amfani da tashar ruwanta

    Play Episode Listen Later Apr 30, 2025 3:38


    A daidai lokacin da rikici tsakanin Mali da Algeria ke cigaba da ruruwa, Sarkin Morocco Mohammed VI ya gayyaci ministocin harkokin wajen  ƙasashen Burkina Faso,Mali da kuma  jamhuriya  Nijar a fadarsa da ke birnin Rabat domin basu damar yin fanin da tashar ruwanta na Atlantic wajan jigilar kayakinsu.Ziyarar tasu dai na zuwa ne bayan da alaƙa tsakanin ƙasashen AES da Algeria, wacce ke zama babbar abokiyar hamayyar Morocco ta yi tsami. Latsa alamar sauti domin suraron karin bayani.....

    Claim Bakonmu a Yau

    In order to claim this podcast we'll send an email to with a verification link. Simply click the link and you will be able to edit tags, request a refresh, and other features to take control of your podcast page!

    Claim Cancel