Bakonmu a Yau

Follow Bakonmu a Yau
Share on
Copy link to clipboard

A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban…

Rfi - Azima Bashir Aminu


    • May 20, 2026 LATEST EPISODE
    • weekdays NEW EPISODES
    • 3m AVG DURATION
    • 1,139 EPISODES


    Search for episodes from Bakonmu a Yau with a specific topic:

    Latest episodes from Bakonmu a Yau

    Hajiya Fatsuma Adamu shugabar makarantar da Boko Haram ta sace ɗalibai a Askira-Uba

    Play Episode Listen Later May 20, 2026 3:22


    Gwamnan jahar Borno Babagana Umara Zullum ya ce, gwamnati da jami'an tsaro na ƙoƙarin ceto daliban makaranta da aka sace a makarantar firamare a ƙauyen Mussa dake ƙaramar Hukumar Askira- Uba. Gwamna Zulum ya bayyana haka ne ya yin wata ziyarar jaje da ya kai Askira Uba dangane da iftila'in da ake dangantawa da Boko Haram. Ziyarar na zuwa ne yayin da aka shiga kwanaki na 5 da sace daliban ciki harda kanan yara. Shugabar kula da ilimi na ƙaramar Hukumar Askira-Uba, Hajiya Fatsuma Adamu Askira ta bayyana mana halin da ake ciki, a tattaunawarta da Ahmad Abba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

    Tattaunawa da Dakta Nasiru Sani Gwarzo kan giɓin kasafin da WHO ke fuskanta

    Play Episode Listen Later May 19, 2026 3:40


    Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta fara babban taronta karo na 79 jiya Litinin a birnin Geneva, wanda kuma za a ƙarƙare shi a ranar 23 ga watan Mayu da muke. Daga cikin muhimman batututwan da taron zai fi mayar da hankali a kai dai akwai giɓin kasafin kuɗin da ya kai Dala Biliyan 1 da Hukumar Lafiyar ta Duniya ke fuskanta, da kuma tasirin janyewa daga cikinta da Amurka ta yi. Kan wannan da kuma sauran batutuwa masu alaƙa, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Nasiru Sani Gwarzo, ƙwrarre kan sha'anin lafiya da ke Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

    ku sani daga duniya mayu najeriya amurka majalisar dinkin duniya
    Dr Kabiru Adamu kan kisan jagoran ƙungiyar IS Abu Bilal Al-Minuki

    Play Episode Listen Later May 18, 2026 3:35


    Yanzu haka na ci gaba da bayyana ra'ayoyi dangane da sanarwar da Amurka ta fitar da ke cewa ta kashe Abu Bilal Al-Minuki da ke matsayin jagora a ƙungiyar IS a Najeriya, labarin daga bisani hukumomin tsaron Najeriya suka tabbatar. To domin jin ƙarin bayani a game da wannan ɗan taliki da ake cewa an kashe, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Kabiru Adamu na Cibiyar da ke nazari kan sha'anin tsaro ta Beacon da ke Abuja, ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar...............

    beacon ku bilal abuja adamu kisan najeriya amurka yanzu abdoulkarim ibrahim shikal
    Zantawa da Macron a ƙarshen taron ci gaban Afirka

    Play Episode Listen Later May 14, 2026 10:04


    A zantawarsa da Radio France Internationale, da France 24 da kuma TV5 Monde a ƙarshen taron Afrika da Faransa da aka kammala birnin Nairobi na ƙasar Kenya, Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana matsayinsa a game da taɓarɓarewar sha'anin tsaro a Mali da kuma alaƙar Faransa da sauran ƙasashen Afirka ta fannin tsaro da aikin soji. To amma da farko shugaban ya fara amsa wata tambaya ce dangane da dalilan da suka sa Faransa ke ci gaba da taka rawa a wajen tafiyar da takardar kuɗin CFA. Ga dai tattaunawar. Latsa alamar sauti domin sauraren zanatawar.

    Sanata Abubakar Kyari kan makomar noma a Najeriya

    Play Episode Listen Later May 13, 2026 3:28


    A ranar Talata ne ake kammala taron shugabannin ƙasashen Afirka da Faransa da ya gudana a birnin Nairobi ta ƙasar Kenya, wanda ya mayar da hankali kan hanyoyin ci gaban tattalin arziki da noma da samar da abinci ga jama'ar nahiyar. Yaƙin Iran na ɗaya daga cikin abubuwan da ake ganin na maida hannun agogo baya wajen  magance ƙarancin abinci, musamman rufe mahsigin Hormuz da ake amfani da ita wajen safarar takin zamani. Kan haka ne Nura Ado Suleiman ya zanta da ministan noman Najeriya Sanata Abubakar Kyari a wurin wannan taro, inda kuma ya ce su na ƙoƙarin magance matsalar. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

    iran kenya nairobi noma hormuz abubakar shiga najeriya talata afirka faransa kyari
    Abubuwan da taron Faransa da ƙasashen Afirka ke son cimma

    Play Episode Listen Later May 12, 2026 3:41


    A jiya ne ake faro taron kwanaki biyu tsakanin Faransa da ƙasashen Afrika a birnin Nairobi, wanda shugaba Emmanuel Macron da takwaransa William Ruto ke jagoranta. Taron ya haɗa shugabannin ƙasashen Afrika, da Hamshaƙan ƴan Kasuwa, da sauran masu ruwa da tsaki domin tattaunawa kan nemawa nahiyar Afrika mafita wajen samun ci gaban Tattalin Arziƙi  a fannonin da suka haɗa da, bunƙasa Masana'antu da Kimiyya da Fasaha da inganta Noma da Tsarin Kiwon Lafiya, da kuma samun wadatar makamashi. Danna alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar Nura Ado Suleiman da hadimin  shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu Daniel Bwala.......

    Boubacar Ɗan Zourmani akan makasudin ƙafa kungiyar ƙawancen ADS

    Play Episode Listen Later May 11, 2026 3:26


    A ranar asabar da ta gabata ne, wasu masu fafufutuka da suka haɗa da ƴan siyasa, fararen hula, masana dokoki da dai sauransu da ke zaune a ƙetare, suka ƙaddamar da wani ƙawance da ake kira da suna ADS, (Alliance des Domocrates du Sahel) wanda babbar manufarsa ita ce sake dawo da tsarin dimokuraɗiyya a ƙasashen yankin Sahel da yanzu haka ke ƙarƙashin mulkin soji da suka hada da Burkina Faso, Mali da kuma Nijar. An dai ƙaddamar da wannan ƙawance ne a birnin Brussels na ƙasar Belgium, inda daga bisani Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Sakataren Yaɗa Labarai na ADS Boubacar Ɗan Zourmani, wanda ya yi masa ƙarin bayani a game da manufofinsu. Ga dai ƙarin bayaninsa.

    Tattaunawa kan ci gaba da shari'ar neman hana Jonathan tsayawa takara a Najeriya

    Play Episode Listen Later May 8, 2026 3:30


    Kotu a Najeriya yau ta ci gaba da sauraron shari'ar neman hana tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan tsayawa takarar zabe mai zuwa, kwana guda bayan wasu tarin magoya bayan sa sun bukaci ya shiga zaben mai zuwa. Dangane da matsayin dokar zabe a kan takarar ta Jonathan masanin shari'a, Farfesa Shehu Abdullahi Zuru na Jami'ar Baze dake Abuja, ya mana tsokaci a kai yayin zantawarsa da Bashir Ibrahim Idris. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

    Ambasada Kazaure kan kiran wasu ƴanmajalisar Najeriya na kwace lasisin MTN da DSTV

    Play Episode Listen Later May 7, 2026 3:37


    Wasu daga cikin Ƴan Majalisun Dattawan Najeriya sun buƙaci ɗaukar matakai maus tsauri a kan Afirka ta Kudu, ciki harda kwace lasisin kamfanonin su na MTN da DSTV saboda yadda ake kai wa ƴan ƙasar hari ake kuma kashe su. Majalisar ta yanke hukuncin tura tawaga Afirka ta Kudu domin tattaunawa da hukumomin ƙasar, yayin da shi ma bangaren gwamnati ya tura ministan harkokin waje. Ambasada Ibrahim Kazaure, tsohon Jakadan Najeriya a Saudi Arabia ya yi tsokaci a kai, a tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris.

    saudi arabia kiran mtn dstv kudu wasu najeriya afirka majalisar bashir ibrahim idris
    Hira da Kailani Muhammad kan baiwa China ragamar farfaɗo da matatun man Najeriya

    Play Episode Listen Later May 6, 2026 3:48


    Kamfanin mai na NNPC ya sanya hannu kan wata yarjejeniya da wasu kamfanonin ƙasar China guda biyu, Sanjiang Chemical Company Limited da kuma Fuzhou Industrial Park, domin farfaɗo da matatun mai na Warri da Port Harcourt. Wannan mataki ya zo ne bayan matatun man sun laƙume kimanin biliyan 3.2 na dala ba tare da an samu biyan buƙata ba. Injiniya Kailani Muhammad, tsohon babban jami'in kamfanin na NNPC ne, a tattaunawarsa da Shamsiyya Haruna, ya bayyana gamsuwa da wannan yarjejeniya da kasar China bisa wasu dalilai. Ku latsa alamaru sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

    Dr Rakiya Sa'idu kan halin da ƴan Najeriya da ke Afirka ta Kudu ke ciki

    Play Episode Listen Later May 5, 2026 3:29


    Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa za ta fara kwashe ƴan ƙasarta da ke son komawa gida daga Afirka ta Kudu, matakin da ta ce ya zama dole saboda tsananin kyamar baƙi da kuma rahoton mutuwar wasu ƴan Najeriya biyu sakamakon hare-haren da ake kai wa ƴan cirani. Akalla 'yan Najeriya 130 ne suka riga suka yi rajista don neman a kwashe su zuwa gida, sakamakon fargabar makomarsu na rashin tabbas. Dakta Rakiya Sa'idu daga jami'ar Capetown, ta bayyana mana yadda ƴan siyasa ke amfani da lokacin zaɓe wajen rura wutar wannan matsala. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawar da Shamsiyya Haruna ta yi da ita............

    cape town ku kudu ciki akalla najeriya rakiya afirka
    Alhaji Muhammed Sani Zoro tsohon shugaban NUJ kan ranar ƴan jarida ta duniya

    Play Episode Listen Later May 4, 2026 3:38


    Kamar dai kowace shekara, 3 ga watan Mayu ita ce ranar kare ƴancin aikin yaɗa labarai a duniya, inda rahotannin da ƙungiyoyin da ke fafutuka a wannan fage ke nuni da cewa an samu gagarumin koma-baya ta fannin aikin jarida a cikin shekarar da ta gabata. Dangane da wannan rana, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon shugaban ƙungiyar Ƴan Jarida ta Najeriya (NUJ) Honnorable Alhaji Muhammed Sani Zoro, wanda da farko ya fara yin tsokaci a game da irin sauye-sauyen da aka samu a aikin jarida saboda dalilai masu nasaba da zamani. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

    ku muhammed kamar sani zoro duniya mayu shugaban abdoulkarim ibrahim shikal
    Tinubu ya ce babu gudu ba ja da baya kan samar da ƴan sandan jihohi

    Play Episode Listen Later May 1, 2026 3:35


    Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake jaddada aniyar sa ta samar da Yan Sandan jihohi domin samar da tsaro. Tinubu ya bayyana haka ne yayin ganawa da masu ruwa da tsaki na jihar Filato mai fama da tashin hankalin. Alhaji Isa Tafida Mafindi, wanda ya wallafa littafi a kan samar da Yan Sandan jihohi ya mana tsokaci a kai, yayin tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

    babu samar baya bashir ibrahim idris
    Fargaba ta mamaye zukatan ƴan Najeriya dangane da makomar adawa a ƙasar

    Play Episode Listen Later Apr 30, 2026 3:34


    Yan Najeriya na cigaba da bayyana fargaba dangane da makomar ƴan adawar ƙasar dangane da zabe mai zuwa , la'akari da cewar akasarin jami'iyyun adawar na fama da rikice-rikicen da ka iya hana su takara. Akan wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Alhaji Kabir Muhammad Baba, ɗan siyasa a jihar Bauchi. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar......

    akan asar shiga bauchi najeriya bashir ibrahim idris
    Dakta Kabiru Inuwa Dukawa kan yadda ƙin jinin baƙi a Afrika ta Kudu ke ƙaruwa

    Play Episode Listen Later Apr 29, 2026 3:32


    Ɗaruruwan ‘yan Afrika ta Kudu masu ƙyamar baƙi, sun gudanar da zanga-zanga jiya Talata a birnin Pretoria, bayan da suka bjirewa kiran da shugaban ƙasar Cyril Ramaphosa ya yi musu na dakatar da kai wa baƙi hare-hare gami da cin zarafinsu, inda a baya bayan wasu ‘yan Najeriya biyu suka rasa rayukansu. Cin zarafin baƙin da tsagerun ‘yan Afrika ta Kudun na baya bayan nan dai ya fara ne da shafar ‘yan ƙasashen Ghana, da Habasha da Zimbabwe kafin kai wa ga ‘yan Najeriya. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Kabiru Inuwa Dukawa, masanin siyasar ƙasa da ƙasa da ke Najeriya. Ku danna alamar sauraro domin jin cikakkiyar Hirar.

    Dakta Muhammad Garba kan matsanancin halin yunwa da ake ciki a Najeriya

    Play Episode Listen Later Apr 28, 2026 3:40


    Wani rahoton masana na hukumomin Majalisar Ɗinkin Duniya da aka fitar a ƙarshen makon jiya, ya sanya Najeriya a cikin jerin ƙasashe 10 da suka fi fama da Yunwa a Duniya.  A Najeriya rahoton ya ƙiyasta zuwa wannan shekara, aƙalla mutane miliyan 35 ke fuskantar haɗarin faɗawa cikin ƙangin Yunwa, saboda ƙarancin abincin da ake fama da shi a sassa da dama, musamman a yankunan karkara na arewacin ƙasar inda mafi rinjayen manoma suke. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Muhd Garba, malami a tsangayar koyar da Ilimin ayyukan Noma a Jami'ar Abubakar Tafawa Ɓalewa da ke garin Bauchi. Ku danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar tare da Nura Ado Sulaiman.

    Soumaila Amadou akan harin ta'addancin Mali da ya kashe ministan tsaro

    Play Episode Listen Later Apr 27, 2026 3:26


    An shiga zaman zullumi a Mali bayan da ƙawancen ƙungiyar Abzinawa ƴan tawaye FLA da kuma kungiyoyin da ke ikirarin jihadi suka ƙaddamar da farmaki kan birane da dama na ƙasar tun a ranar asabar har zuwa jiya lahadi. Tuni dai aka tabbatar da mutuwar ministan tsaro Janar Sadio Camara da kuma wasu mutane da dama a wannan farmaki da ake kallo a matsayin mafi tsaruwa da kuma jajircewa daga waɗannan ƙungiyoyi da suka share tsawon shekaru suna fafatawa da dakarun gwamnati. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Malam Soumaila Amadou, mai sharhi kan lamurran yankin Sahel, ga kuma zantawarsu. Latsa alamar sauti don sauraron hirar Abdoulkarim Ibrahim da Soumala Amadou:

    mali fla akan sahel amadou tuni abdoulkarim ibrahim shikal
    Gwamnonin Najeriya 20 sun amince da gina katafariyar rugar zamani

    Play Episode Listen Later Apr 24, 2026 3:31


    Kimanin gwamnonin jihohin Najeriya 20 sun amince su gina katafariyar ruga ta zamani a jihohinsu wadda za ta kunshi makarantu da asibitoci da kasuwanni har ma da wuraren kiwon dabbobi musamman shanu da zummar zaunar da Fulani makiyaya wuri guda ba tare da gararanba ba. Tuni masana suka ce wannan sabon tsarin zai yi tasiri wajen tabbatar da lafiyar dabbobin Najeriya tare da ruɓanya adadin madarar da suke samarwa a kullum. Jim kaɗan da kammala taro kan wannan shiri a birnin Lagos, Abdurrahman Gambo ya tattauna da Farfesa Abba Gambo, mai bai wa gwamnonin Najeriya shawara kan noma da kiwo. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

    Dakta Harbau akan yawan iskar gas da Najeriya ta fitar

    Play Episode Listen Later Apr 23, 2026 3:20


    Wasu alƙaluma daga Hukumar Kula da Albarkatun Man Fetur na kan tudu da na cikin ruwa (NMDPRA) sun nuna cewa, adadin Iskar Gas ɗin da aka fitar daga Najeriya zuwa kasuwannin ƙetare ya kai kaso 62 cikin 100, cikin watanni uku na farkon wannan shekara. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Gas ɗin ya yi ƙaranci a Najeriyar, lamarin da ke taka rawa wajen raguwar hasken lantarkin da ake samu, fannin da kasonsa aƙalla 80 cikin 100 ya dogara da arziƙin na Gas. Don jin yadda masana ke kallon lamarin da kuma mafita, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Aminu Idris Harbau, ƙwararren kan tattalin arziki a Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraron hirar:

    Dr Auwal Aliyu kan yarjejeniyar shimfiɗa bututun Gas tsakanin Najeriya da Morocco

    Play Episode Listen Later Apr 22, 2026 3:27


    Najeriya da Morocco sun rattaba hannu kan wata yarjejeniyar shimfiɗa bututun Gas, aikin da zai laƙume kuɗin da yawansu ya kai Dala biliyan 25, kafin ƙarshen wannan shekara. Bayanai sun ce tsawon bututun Gas ɗin da za'a shimfiɗa ya kai kilomita dubu 6,900, wanda zai ratsa cikin Ruwa da Sahara, har ma ya tsallaka zuwa Turai. Kan wannan Shamsiyya Haruna ta tattauna da Dakta Abdullahi Auwal Aliyu, masanin tsaro a Najeriya, domin jin yiwuwar wannan aiki da kuma tasirin da zai yi. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar ta su.................

    Tattaunawa da Dr Ruƙayya Yusuf Aliyu kan gargaɗin NBC ga kafofin yaɗa labarai

    Play Episode Listen Later Apr 21, 2026 3:36


    Hukumar Kula da kafafen Yaɗa Labarai a Najeriya NBC, ta gargaɗi masu gabatar da shirye-shirye a gidajen Radio da Talabijin da su guji bayyana ra'ayoyin ƙashin kansu, su kuma kaucewa yin katsalandan cikin bayanan waɗanda suka tattaunawa da su, da kuma yaɗa duk wani saƙo da ka iya haifar da rarrabuwar kai. Tuni dai wannan mataki ya gamu da caccakar ƙungiyoyin farar hula da kuma ɓangaren ‘yan adawa a Najeriyar. Kan haka, Nura Ado Suleiman ya tattauna Dakta Ruƙayya Yusuf Aliyu, Malama a tsangayar koyar da aikin Jarida na zamani a Jami'ar Bayero da ke Kano a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

    Tattaunawa da Dr Yahuza Getso kan yarjejeniyar tsaro tsakanin Najeriya da Turkiya

    Play Episode Listen Later Apr 20, 2026 3:27


    Najeriya da kuma Turkiyya sun ƙulla yarjejeniyar tsaro a tsakaninsu, wadda a ƙarƙashinta matakin farko Najeriya za ta tura zatan sojoji 200 don samun horo na musamman a Turkiyya. Hakan dai na zuwa ne watanni kaɗan bayan da mahukuntan a birnin Abuja suka sanar da ƙulla irin wannan yarjejeniya da ke bai wa Amurka damar turo sojojinta zuwa Najeriya don yaƙi da ta'addanci? Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tsaro lamurran tsaro Dr Yahuza Getso, domin jin tasa fahintar a game da yadda alaƙar tsaron za ta kasance tsakanin Najeriya da kuma Turkiyya. Ga dai zantawarsu.

    ga hakan abuja najeriya amurka abdoulkarim ibrahim shikal
    Yadda gwamnatin Katsina ta gudanar da taron masu zuba jari a Faransa

    Play Episode Listen Later Apr 17, 2026 3:30


    A ƙoƙarinta na ganin ta bunƙasa harkokin tattalin arzikinta, gwamnatin jihar Katsina ta ce ƙofofinta a buɗe suke ga masu  zuba jari na ƙasashen ƙetare. A yayin wani taro na masu zuba jari da ya gudana a birnin Paris na Faransa, gwamnatin jihar Katsina ta ce akwai masu zuba jarin da suka nuna sha'awar zuba jari a ɓangaren noma da ma'adinai da kiwon lafiya a jihar. Domin jin irin matakan da suke ɗauka domin cimma wannan narasa, Khamis Saleh ya tattauna da mataimakin gwamnan jihar Kastina Malam Faruk Lawal Jobe. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

    Farfesa Abdulƙadir Suleiman akan cika shekaru 3 da yaƙin Sudan

    Play Episode Listen Later Apr 16, 2026 3:24


    Yayin da aka cika shekaru uku da fara yaƙin basasar ƙasar Sudan, Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla mutane miliyan 14 suka bar muhallansu, baya ga daruruwan da suka rasa rayukan su. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Abdulkadir Suleiman Muhammed na Jami'ar Abuja, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.

    sudan abdul akan abuja suleiman adir yayin majalisar dinkin duniya bashir ibrahim idris
    Yadda masana ke kallon zaɓen Jamhuriyar Benin

    Play Episode Listen Later Apr 15, 2026 3:38


    Ɗan takarar ƙawancen jam'iyyun da ke mara wa gwamnati baya a Jamhuriyar Benin ya yi nasarar lashe 94% na ƙuri'un da aka kaɗa a zaɓen shugabancin ƙasar da aka hana fitattun ƴan adawa tsayawa takara. Romuald Wadagni mai shekaru 49 a duniya, shi ne ministan kuɗi tsawon shekaru 10 kafin shugaba mai barin gado Patrice Talon ya gabatar da shi a matsayin wanda yake son gaje shi. Don jin yadda masu sharhi kan siyasar ƙasa da ƙasa musamman a Nahiyar Afrika ke kallon zaɓen na Jamhuriyar Benin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Janjouna Ali Mahamane Sani.

    Gwamnatin Najeriya ta fitar da sunayen mutane 48 da ke daukar nauyin ta'addanci

    Play Episode Listen Later Apr 14, 2026 3:12


    A cikin makon nan, gwamnatin Najeriya ta fitar da jerin sunayen mutane 48 da kuma wasu kamfanoni 12, waɗanda take tuhuma da hannu cikin ayyukan ta'addanci a ƙasar. Tuni dai wannan mataki ya haifar da muhawara a tsakanin ‘yan Najeriya waɗanda ke ci gaba da tofa albarkacin bakinsu a kan lamarin. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hira da Nura Ado Suleiman ya yi da Katfin Abdullahi Adamu Bakoji mai ritaya, masanin tsaro da ke Najeriya.

    shiga tuni najeriya
    Abubuwan da suka haifar da saɓani a tattaunawar Amurka da Iran

    Play Episode Listen Later Apr 13, 2026 3:32


    An tashi baram-baram tsakanin Amurka da Iran a tattaunawar da suka faro ranar Asabar a birnin Islamabad bisa shiga tsakanin Pakistan a ƙoƙarin kawo ƙarshen wannan yaƙi, tattaunawar da ke zuwa bayan cimma jituwar tsagaita wutar kwanaki 14 tsakanin ɓangarorin biyu. Tuni ƙasashe suka fara kiraye-kirayen ganin rashin cimma jituwar Amurkan da Iran bai taɓa yarjejeniyar da ke tsakaninsu ba Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hira da Dakta Dicko Abdourahmane malami a jami'ar Zinder Nijar....

    Riya'uddeen Zubairu Maitama kan yarjejeniyar tsagaita wutar Amurka da Iran

    Play Episode Listen Later Apr 9, 2026 3:24


    ‘Yan Sa'o'i bayan amincewa da yarjejeniyar tsagaita wutar kwanaki 14, Amurka da Iran sun zargi juna da karya yarjejeniyar, lamarin da ya kai ga Iran ta sake datse mashigin ruwan Hormuz jim kaɗan bayan buɗe shi da ta yi. Domin jin yiwuwar ɗorewar wannan yarjejeniya ta tsagaita wuta da kuma makomar ƙoƙarin da masu shiga tsakani ke yi, Nura Ado Suleiman ya tattauna da masanin Siyasar ƙasa da ƙasa, Dakta Riya'uddeen Zubairu Maitama na Jami'ar Bayero da ke Kano a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar ta su.............

    Barista Umar Ɗanbaito kan shari'ar waɗanda ake zargi da ta'addanci a Najeriya

    Play Episode Listen Later Apr 8, 2026 3:34


    Kotun musamman a Najeriya, ta ci gaba da zaman gudanar da ɗimbin shara'o'i na yanke hukunci da kuma sauraron ƙararraki kan waɗanda ake tuhuma da ayyukan ta'addanci da taimaka wa ƴan ta'addan. A daidai wannan lokaci kuma ɓangarori daban daban ke bayyana ra'ayoyinsu kan tsarin gudanar da shara'o'in lura da adadin masu laifukan da ke gurfana. Yayin da wasu ke ganin komai na tafiya daidai, wasu na ganin ana jan kafa, saɓanin taƙaita lokacin da ake buƙata.   Tu latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Nura Ado Suleiman da Barista Umar Usman Ɗanbaito..........

    Comrade Musa Ayiga kan shirin Tinubu na biyan bashin lantarki na sama da Tiriliyan 3

    Play Episode Listen Later Apr 7, 2026 3:40


    Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da ware Naira Tiriliyan 3 da Biliyan 300 domin biyan kamfanonin rarraba wutar lantarki basukan da suke bin gwamnatin ƙasar, da zummar kawo ƙarshen matsalar ƙarancin wutar da ‘yan Najeriya ke ciki. Bayanai dai sun nuna cewa bashin na sama da Naira Tiriliyan Ukun ya taru ne a tsakanin shekarar 2015 zuwa bara. Sai dai ɗaya daga cikin masu ruwa da tsaki kan sha'anin wutar lantarki a Najeriya, Comrade Musa Yunusa Ayiga ya bayyana shakku kan wannan yunƙuri. tattaunawarsa da Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Nura Ado Suleiman.............

    Tattaunawa da Reverand Andrew akan bukukuwan Easter

    Play Episode Listen Later Apr 6, 2026 3:22


    Ana ci gaba da gudanar da bukukuwan Easter a sassan duniya, wadda Kiristoci suka yi imani da cewa a wannan rana ce aka gicceye Yesu Almasihu inda kwanaki uku bayan hakan ya tashi. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya tuntuɓi Reverand Andrew Doyu, domin jin ƙarin bayani a game da matsayin wannan rana da kuma muhimmancinta ga mabiya addinin Kirista. Shiga alamar sauti don saurarin cikakkiyar hirar...........

    akan shiga reverand abdoulkarim ibrahim shikal
    Intinikar Alhassan kan ƙarewar wa'adin gwamnatin Bazoum da aka hamɓarar

    Play Episode Listen Later Apr 2, 2026 3:35


    A wannan rana, ta biyu ga watan Afrilun shekarar 2026 da muke, wa'adin shugabancin hamɓararen shugaban ƙasar Jamhuriyar Nijar Muhammad Bazoum ke ƙarƙarewa da a ce yana kan karagar mulki. A irin wannan ranar ce dai ta watan Afrilun shekarar 2021, aka rantsar da Mohammed Bazoum a matsayin shugaban Jamhuriyar Nijar, bayan da ya lashe sama da kashi 55 na ƙuri'un zaɓen da aka yi a watan Fabrairun wannan shekara. Akan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Intinikar Alhassan, ɗaya daga cikin makusantan hamɓararren shugaban na Nijar. Ku latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu............

    Mammane Wada kan shirin Nijar na kafa ƙungiyoyin samar da tsaro da basu makamai

    Play Episode Listen Later Apr 1, 2026 3:31


    A Jamhuriyar Nijar, ra'ayoyi sun banbanta a kan shawarar da gwamnatin ƙasar ta yanke na kafa ƙungiyoyi waɗanda za ta bai wa horo tare da riƙe makamai don kare garuruwa daga hare-haren Ƴanbindiga. A cewar gwamnati, jami'an ƙungiyoyin kare kan, za su kasance sojoji, da ƴansanda da sauran jami'an tsaron da suka yi ritaya, waɗanda za a riƙa biyansu kuɗin alawus. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Mammane Wada na ƙungiyar Transparency International da ke bibiyar lamurra a ƙasar ta Nijar. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu............

    Tattaunawa akan shirin samar da ƴansandan jihohi a Najeriya

    Play Episode Listen Later Mar 31, 2026 3:32


    Kwamitin da Sufeto Janar na Ƴansandan Najeriya Tunji Disu ya kafa domin bada shawarar yadda za'a kirkiro ƴansandan jihohi ya gabatar da shawarwarinsa ga kwamitin Majalisar tarayya dake yiwa kundin tsarin mulki kwaskwarima. Shugaban kwamitin Farfesa Olu Ogunsakin ya bayyana cewar sun bada shawarar mayar da kashi 60 na ƴansandan tarayya da ake da su yanzu zuwa sabuwar rundunar ƴansandan jihohin da za'a kirkiro a jihohi 36 da Abuja. Danna alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hirar Bashir Ibrahim Idriss da Sufet Muhammed Wakili mai riyata....

    akan abuja shirin samar najeriya shugaban majalisar
    Darusan da aka koya a kwanaki 30 na yakin Gabas ta Tsakiya

    Play Episode Listen Later Mar 30, 2026 3:35


    Yayinda ake cika wata guda curr da fara yaƙi tsakanin haɗin gwiwar Amurka da Isra'ila a gefe guda kuma da Iran, a yau ɓangarorin da ke rikici na ƙara zafafa hare-hare, a wani abu da duniya ke ci gaba da mamakinsa. Zuwa yanzu dai wannan yaƙi ya laƙume dubban rayuwa, inda kuma Iran ke zargin Amurka da shirya afka mata da sojoji ta ƙasa, yayinda wasu ƙasashe suka fara yunƙurin sulhunta tsakani. Shiga alamar sauti don sauraron karin bayani a hirar da Rukayya Abba Kabara ta yi da Bash M Bash....

    Tattaunawa da Dr Maman Kassou na jami'ar Andre Salifou a Nijar kan cinikin bayi

    Play Episode Listen Later Mar 26, 2026 3:34


    Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana fataucin bayi da aka share ɗaruruwan shekaru ana yi daga Afirka zuwa Turai da Amurka a matsayin ‘'cin zarafin bil  Adama mafi girma'' da aka taɓa gani a tarihi. Ƙasashen duniya 123 ne suka kaɗa ƙuri'ar goyon bayan wannan ƙuduri, wasu uku wato Amurka, Isra'ila da Argentina suka ƙi amincewa yayin da wasu ƙasashe 52 suka yi ƙememe ta hanyar rowar ƙuri'unsu. To domin tuni a game da lokacin da aka fara ɗibar bayi daga Afirka da kuma yadda hakan ya shafi ci gaban nahiryar, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tarihi Dr Maman Kassou, malami a jami'ar Andre Salifou da ke Damagaram, ga kuma zantarwarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.

    argentina isra ku maman adama bayi duniya nijar turai afirka amurka majalisar damagaram abdoulkarim ibrahim shikal
    Yadda rikicin Gabas ta Tsakiya ke tasiri akan farashin kayayyaki a duniya

    Play Episode Listen Later Mar 25, 2026 3:38


    Farashin hajoji da sauran muhimman abubuwa na ci gaba da hauhawa a kasuwannin duniya sakamakon yadda yaƙin da ake yi a yankin Gabas ta Tsakiya ya hana fitar da mafi yawan man fetur da kamfanoni da masana'antu suka yi oda ya maƙale a Mashigin Ruwan Hormuz. To domin fahintar girman wannan matsala da kuma ɓangarorin da suka fi fama da ƙarancin makamashi a duniya saboda wannan rikici, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya tuntuɓi masani tattalin arziki Dr Isa Abdullahi, malami a jami'ar Tarayya da ke Kashere a jihar Gomben Najeriya, ga kuma zantawarsu. A latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawar

    iran akan duniya yadda amurka abdoulkarim ibrahim shikal
    Yaƙin da ake a Iran ya ritsa da ɗimbin ƴan ƙasashen waje da ke karatu a ƙasar

    Play Episode Listen Later Mar 24, 2026 0:59


    Yanzu haka yaƙin da ake fama da shi a yanzu Gabas ta Tsakiya ya rutsa da ɗimbin ƴan kasashen waje musamman ɗalibai da ke karatu a ƙasar Iran. To sai dai yayin da wasu ƙasashe suka fara kwashe mutane zuwa gida ko kuma wasu ƙasashe, amma har yanzu Najeriya ba su samu irin wannan tallafi daga gwamnatinsu ba. A game da haka ne Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Muhammad Umar Nuruddeen, ɗaya daga cikin ɗaliban ƴan Najeriya wadanda adadinsu ya zarta 500, wanda ya fara da yin bayani a game da yadda rikicin ya tarar da su Ku latsa alamar sauti da ke sama domin jin wannan tattaunawa.................................

    iran ku asar waje najeriya amurka yanzu abdoulkarim ibrahim shikal
    Ambasada Cika akan iƙirarin Trump na tattaaunawa da Iran

    Play Episode Listen Later Mar 24, 2026 3:37


    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ba dan tattaunawar da gwamnatinsa ta yi da wani babban jami'in ƙasar Iran ba, to lalle da babu makawa ya ƙaddamar da farmaki domin rusa cibiyoyin samar da wutar lantarki na ƙasar. Trump ya ce ya jinkirta kai farmaki har tsawon kwanaki biyar, tare da yiyuwar hakan ya kasance damar cimma yarjejeniya da Iran a cewarsa. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon jakadan Najeriya a Iran Ambasada Alhaji Abubakar Cika, domin jin tasa fahintar a game da dalilan jinkirta kai wannan hari. Ga kuma abin da yake cewa.

    donald trump iran ga akan najeriya abdoulkarim ibrahim shikal
    Barrister Modibbo Bakary kan wa'adin Tunibu ga masu riƙe da muƙaman siyasa

    Play Episode Listen Later Mar 23, 2026 3:36


    A Najeriya, 31 ga wannan watan na  Maris ita ce ranar da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya bai wa masu riƙe da naɗaɗɗun muƙaman siyasa su yi marubus muddun suna son tsayawa takara a zaɓuka masu zuwa, kamar dai yadda dokokin zaɓe suka tanada. To domin jin ƙarin bayani a game da wannan doka, da irin mutanen da ya kamata su yi marabus da kuma tasirin dokar wajen samar da ingantaccen zaɓe, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Barrister Modibbo Bakary, ƙwararren lauya da ke birnin Abuja, ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.

    ku aman barrister abuja masu bakary bola ahmed tinubu najeriya abdoulkarim ibrahim shikal
    Hukumar ƙwallon ƙafar AFCON ta ƙwace nasarar da Senegal ta miƙawa Morocco

    Play Episode Listen Later Mar 19, 2026 3:28


    Hukumar kwallon ƙafar Afrika ta sanar da ƙwace Kambun da Senegal ta lashe a gasar neman kofin nahiyar da aka kammala cikin watan Janairun da gabata tare da miƙa shi A a hannun ƙasar Moroko. Wannan dai mataki ne da ya yi matuƙar girgizar masu shawar harkar ƙwallon ƙafa ba wai a nahiyar Afrika ba har da sauran sassan duniya. To sai tuni Senegal ta buƙaci a gudanar da bincike bisa zargin cewa akwai yiyuwar an bayar da rashawa ne don ƙwace wannan galaba.   A game da wannan mataki ne Michael Kuduson ya zanta da Aliyu Awwal Ibrahim, Sakataren tawagar ƙwallon ƙafar Najeriya ƴan ƙasa da shekaru 20. Ga kuma zantawarsu. A latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar tattaunawar.

    Tattaunawa da Abdulaziz Abdulaziz game da ziyarar Tinubu a Birtaniya

    Play Episode Listen Later Mar 18, 2026 3:36


    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya fara ziyarar aiki a Birtaniya inda ya samu kyakkyawar tarba daga hukumomin ƙasar. Wannan ziyara na zuwa ne a dai dai lokacin da Najeriyar ke fuskantar matsalolin tsaro iri-iri. Dangane da ziyarar ta Tinubu da kuma alfanunta ga ƙasar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai taimakawa shugaban kan harkokin tsaro Malam Abdulaziz Abdulaziz kuma ga yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

    game ku abdul aziz bola ahmed tinubu wannan najeriya birtaniya bashir ibrahim idris
    Dakta Yahuza Getso kan dawowar hare-haren Boko Haram a jihar borno

    Play Episode Listen Later Mar 17, 2026 3:32


    A baya-bayan nan ƙungiyar ta'addanci ta Boko Haram ta tsananta kai hare-hare jihar Borno da maƙwabtanta wanda ya sabbaba asarar ɗimbin rayuka kama daga na jami'an tsaro da kuma fararen hula. Kafin yanzu anga lafawar hare-haren ƙungiyar, sai dai a baya-bayan nan ta dawo da hare-hare ba ƙaƙƙautawa inda ko a tsakanin ranakun Lahadi zuwa yau Talata ta kashe mutane da dama a jihar ta Borno wadda ta shafe shekaru aƙalla 17 tana fama da matsalolin tsaro. Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tsaro Dakta Yahuza Ahmed Getso. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.

    ku boko haram haren borno najeriya talata bashir ibrahim idris
    Amurka na ci gaba da lallshn ƙawanta wajen samun buɗe mashigin Hormuz

    Play Episode Listen Later Mar 16, 2026 3:39


    Shugaban Amurka Donalad Trump, ya ce yanzu haka ya samu tabbaci daga wasu ƙasashen duniya cewa za su taimaka don tabbatar da cewa an ci gaba da zirga-zirgar jiragen ruwa a Mashigin Ruwan Hormuz. Domin jin irin sarƙaƙiyar da ke tattare da irin wannan aiki, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tsaro Air Commodore Tijjani Ahmed Baba Gamawa mai ritaya, ga kuma zantawarsu. A lasa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

    gaba hormuz domin amurka abdoulkarim ibrahim shikal
    Dr Kasim Garba Kurfi kan makomar tattalin arzikin Najeriya a yaƙin Gabas ta Tsakiya

    Play Episode Listen Later Mar 12, 2026 3:31


    Ana saran Najeriya ta shiga cikin jerin ƙasashen da za su amfana da yaƙin Iran wajen samun maƙudan kuɗaɗe ta hanyar cinikin man fetur da ake nema ruwa a jallo. Sai dai masana na bayyana cewar wasu matsalolin cikin gida na iya rage tasirin samun kuɗaɗen da ake hasashe.   Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Bashir Ibrahim Idris da DR. Kasim Garba Kurfi, masanin tattalin.......

    iran ku sai kasim garba najeriya bashir ibrahim idris
    Yara sama da miliyan 6 ne ke fama da tamowa a Arewacin Najeriya - ICRC

    Play Episode Listen Later Mar 11, 2026 3:38


    Ƙungiyar agaji ta ICRC ta ce aƙalla yara ƙanana da ke ƙasa da shekaru 5 miliyan 6 da dubu 400 ke fama da tamowa a yankunan arewa maso gabashin Najeriya da ya kwashe shekaru 15 ya na fama da rikice rikicen Boko Haram da arewa maso yamma da ke fama da rikicin ƴan bindiga, sai kuma arewa ta tsakiya da ke fama da rikicin manoma da makiyaya. Mai magana da yawun ƙungiyar Usman Kundili Bukar ya bayyana haka a tattaunarsa da Bashir Ibrahim Idris. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu.......

    sama ku fama boko haram icrc najeriya bashir ibrahim idris
    Tattaunawa da Dr Isa Abdullahi illar yaƙin Amurka a Iran ga tattalin arziƙin duniya

    Play Episode Listen Later Mar 10, 2026 3:13


    Ƙasashen duniya sun fara jin raɗaɗin yaƙin Iran sakamakon tashin farashin man fetur a kasuwannin duniya, wanda ya shafi harkokin yau da kullum. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Isa Abdullahi, masanin tattalin arziki a kan lamarin, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

    iran ku duniya abdullahi amurka bashir ibrahim idris
    Dr. Yahuza Getso kan harin da mayaƙan Boko Haram suka kai jihar Borno

    Play Episode Listen Later Mar 9, 2026 3:39


    Rundunar sojin Najeriya ƙarkashin dakarun ‘Operation HADIN KAI', ta musanta rahotanni da ke cewa mayaƙan Boko Haram sun kashe sojoji 40, a wani mummunan hari da suka kai Jihar Barno.  Sanarwar mai magana da yawun rundunar Lt. Col. Sani Uba, na zuwa ne, bayan da rahotanni suka ce, mayakan Boko Haram da aka tarwatsa su daga dajin Sambisa, suka sake haɗa kai tare da afkawa ƙauyukan Konduga da Ngoshe da Mainok da Jakana, inda bayanai suka ce sun kashe wani adadi mai yawa na sojoji da fararen hula a Ngoshe tare da sace da dama. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawar Ahmed Abba da Dakta Yahuza Getso matsanin tsaro a Najeriya.........

    Tattaunawa da Dakta Bashir Nuhu Mabai kan sake ta'azzarar yaƙin Iran da Amurka

    Play Episode Listen Later Mar 5, 2026 3:40


    Masana siyasar Duniya gami da rikicin Yankin Gabas ta Tsakiya, na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu kan yaƙin da ya shiga rana ta shida tsakanin Iran da Amurka, wadda ke taimaka wa Isra'ila. Ya zuwa jiya Laraba dai Isra'ilar ta yi iƙirarin kai wa Iran hare-hare sama da dubu 5, yayin da ita ma Amurka ke ci gaba kai wa Iran ɗin farmaki ta sama, da zummar rusa duk wani ƙarfi da ya rage wa gwamnatin ƙasar. Kan wannan, da kuma yadda yaƙin ke daɗa rincaɓewa da shafar ƙasashen Yankin Gabas ta Tsakiya, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Bashir Nuhu Mabai, Malami a Jami'ar Dutsinma da ke Katsina a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

    iran sake isra ku bashir duniya katsina najeriya masana malami amurka
    Ana zaman ɗar-ɗar a Iraqi da sauran ƙasashen yankin Gulf saboda hare-haren Iran

    Play Episode Listen Later Mar 4, 2026 3:35


    Iran ta ci gaba da kai munanan hare-hare kan Isra'ila da muradun Amurka a Gabas ta Tsakiya.To sai dai ƙasashen yankin Gulf na zarginta da faɗaɗa hare-haren kan fararen hula da ababen more rayuwa kamar Otel-otel da filayen jiragen sama da kuma cibiyoyin makamashi. Ko a jiya, dakarun juyin juya halin Iran sun yi ikirarin tarwatsa cibiyoyi da dama a yankin kurdawa, wadanda ta ce mayakanta na shirin yi mata kutse domin kai mata hare-hare. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....

    Tattaunawa da Farfesa Tukur AbdulƘadir kan fargabar tsanantar yaƙin Iran

    Play Episode Listen Later Mar 3, 2026 3:38


    Ga dukkanin alamu akwai yiwuwar yaƙi tsakanin Iran da kuma haɗin gwiwar Amurka da Isra'ila ya ɗauki tsawon lokaci saɓanin zaton da ake yi na ya kasance gajere, wannan kuwa ya biyo bayan jawabin shugaban Amurka Donald Trump a daren jiya da ke cewa mai yiwuwa a shafe makwanni 4 zuwa 5 suna kai hare-hare kan Iran. Wannan na zuwa ne a yayin da yaƙin da ya rincaɓe, ke ci gaba da shafar ƙasashe da dama a Yankin Gabas ta Tsakiya. Domin jin yadda masana siyasar ƙasa da ƙasa ke kallon lamarin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Tukur AbdulƘadir na Jami'ar Jihar Kaduna a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar..

    Claim Bakonmu a Yau

    In order to claim this podcast we'll send an email to with a verification link. Simply click the link and you will be able to edit tags, request a refresh, and other features to take control of your podcast page!

    Claim Cancel