A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban…

Farashin hajoji da sauran muhimman abubuwa na ci gaba da hauhawa a kasuwannin duniya sakamakon yadda yaƙin da ake yi a yankin Gabas ta Tsakiya ya hana fitar da mafi yawan man fetur da kamfanoni da masana'antu suka yi oda ya maƙale a Mashigin Ruwan Hormuz. To domin fahintar girman wannan matsala da kuma ɓangarorin da suka fi fama da ƙarancin makamashi a duniya saboda wannan rikici, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya tuntuɓi masani tattalin arziki Dr Isa Abdullahi, malami a jami'ar Tarayya da ke Kashere a jihar Gomben Najeriya, ga kuma zantawarsu. A latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawar

Yanzu haka yaƙin da ake fama da shi a yanzu Gabas ta Tsakiya ya rutsa da ɗimbin ƴan kasashen waje musamman ɗalibai da ke karatu a ƙasar Iran. To sai dai yayin da wasu ƙasashe suka fara kwashe mutane zuwa gida ko kuma wasu ƙasashe, amma har yanzu Najeriya ba su samu irin wannan tallafi daga gwamnatinsu ba. A game da haka ne Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Muhammad Umar Nuruddeen, ɗaya daga cikin ɗaliban ƴan Najeriya wadanda adadinsu ya zarta 500, wanda ya fara da yin bayani a game da yadda rikicin ya tarar da su Ku latsa alamar sauti da ke sama domin jin wannan tattaunawa.................................

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ba dan tattaunawar da gwamnatinsa ta yi da wani babban jami'in ƙasar Iran ba, to lalle da babu makawa ya ƙaddamar da farmaki domin rusa cibiyoyin samar da wutar lantarki na ƙasar. Trump ya ce ya jinkirta kai farmaki har tsawon kwanaki biyar, tare da yiyuwar hakan ya kasance damar cimma yarjejeniya da Iran a cewarsa. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon jakadan Najeriya a Iran Ambasada Alhaji Abubakar Cika, domin jin tasa fahintar a game da dalilan jinkirta kai wannan hari. Ga kuma abin da yake cewa.

A Najeriya, 31 ga wannan watan na Maris ita ce ranar da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya bai wa masu riƙe da naɗaɗɗun muƙaman siyasa su yi marubus muddun suna son tsayawa takara a zaɓuka masu zuwa, kamar dai yadda dokokin zaɓe suka tanada. To domin jin ƙarin bayani a game da wannan doka, da irin mutanen da ya kamata su yi marabus da kuma tasirin dokar wajen samar da ingantaccen zaɓe, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Barrister Modibbo Bakary, ƙwararren lauya da ke birnin Abuja, ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Hukumar kwallon ƙafar Afrika ta sanar da ƙwace Kambun da Senegal ta lashe a gasar neman kofin nahiyar da aka kammala cikin watan Janairun da gabata tare da miƙa shi A a hannun ƙasar Moroko. Wannan dai mataki ne da ya yi matuƙar girgizar masu shawar harkar ƙwallon ƙafa ba wai a nahiyar Afrika ba har da sauran sassan duniya. To sai tuni Senegal ta buƙaci a gudanar da bincike bisa zargin cewa akwai yiyuwar an bayar da rashawa ne don ƙwace wannan galaba. A game da wannan mataki ne Michael Kuduson ya zanta da Aliyu Awwal Ibrahim, Sakataren tawagar ƙwallon ƙafar Najeriya ƴan ƙasa da shekaru 20. Ga kuma zantawarsu. A latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar tattaunawar.

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya fara ziyarar aiki a Birtaniya inda ya samu kyakkyawar tarba daga hukumomin ƙasar. Wannan ziyara na zuwa ne a dai dai lokacin da Najeriyar ke fuskantar matsalolin tsaro iri-iri. Dangane da ziyarar ta Tinubu da kuma alfanunta ga ƙasar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai taimakawa shugaban kan harkokin tsaro Malam Abdulaziz Abdulaziz kuma ga yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

A baya-bayan nan ƙungiyar ta'addanci ta Boko Haram ta tsananta kai hare-hare jihar Borno da maƙwabtanta wanda ya sabbaba asarar ɗimbin rayuka kama daga na jami'an tsaro da kuma fararen hula. Kafin yanzu anga lafawar hare-haren ƙungiyar, sai dai a baya-bayan nan ta dawo da hare-hare ba ƙaƙƙautawa inda ko a tsakanin ranakun Lahadi zuwa yau Talata ta kashe mutane da dama a jihar ta Borno wadda ta shafe shekaru aƙalla 17 tana fama da matsalolin tsaro. Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tsaro Dakta Yahuza Ahmed Getso. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Shugaban Amurka Donalad Trump, ya ce yanzu haka ya samu tabbaci daga wasu ƙasashen duniya cewa za su taimaka don tabbatar da cewa an ci gaba da zirga-zirgar jiragen ruwa a Mashigin Ruwan Hormuz. Domin jin irin sarƙaƙiyar da ke tattare da irin wannan aiki, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tsaro Air Commodore Tijjani Ahmed Baba Gamawa mai ritaya, ga kuma zantawarsu. A lasa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Ana saran Najeriya ta shiga cikin jerin ƙasashen da za su amfana da yaƙin Iran wajen samun maƙudan kuɗaɗe ta hanyar cinikin man fetur da ake nema ruwa a jallo. Sai dai masana na bayyana cewar wasu matsalolin cikin gida na iya rage tasirin samun kuɗaɗen da ake hasashe. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Bashir Ibrahim Idris da DR. Kasim Garba Kurfi, masanin tattalin.......

Ƙungiyar agaji ta ICRC ta ce aƙalla yara ƙanana da ke ƙasa da shekaru 5 miliyan 6 da dubu 400 ke fama da tamowa a yankunan arewa maso gabashin Najeriya da ya kwashe shekaru 15 ya na fama da rikice rikicen Boko Haram da arewa maso yamma da ke fama da rikicin ƴan bindiga, sai kuma arewa ta tsakiya da ke fama da rikicin manoma da makiyaya. Mai magana da yawun ƙungiyar Usman Kundili Bukar ya bayyana haka a tattaunarsa da Bashir Ibrahim Idris. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu.......

Ƙasashen duniya sun fara jin raɗaɗin yaƙin Iran sakamakon tashin farashin man fetur a kasuwannin duniya, wanda ya shafi harkokin yau da kullum. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Isa Abdullahi, masanin tattalin arziki a kan lamarin, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

Rundunar sojin Najeriya ƙarkashin dakarun ‘Operation HADIN KAI', ta musanta rahotanni da ke cewa mayaƙan Boko Haram sun kashe sojoji 40, a wani mummunan hari da suka kai Jihar Barno. Sanarwar mai magana da yawun rundunar Lt. Col. Sani Uba, na zuwa ne, bayan da rahotanni suka ce, mayakan Boko Haram da aka tarwatsa su daga dajin Sambisa, suka sake haɗa kai tare da afkawa ƙauyukan Konduga da Ngoshe da Mainok da Jakana, inda bayanai suka ce sun kashe wani adadi mai yawa na sojoji da fararen hula a Ngoshe tare da sace da dama. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawar Ahmed Abba da Dakta Yahuza Getso matsanin tsaro a Najeriya.........

Masana siyasar Duniya gami da rikicin Yankin Gabas ta Tsakiya, na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu kan yaƙin da ya shiga rana ta shida tsakanin Iran da Amurka, wadda ke taimaka wa Isra'ila. Ya zuwa jiya Laraba dai Isra'ilar ta yi iƙirarin kai wa Iran hare-hare sama da dubu 5, yayin da ita ma Amurka ke ci gaba kai wa Iran ɗin farmaki ta sama, da zummar rusa duk wani ƙarfi da ya rage wa gwamnatin ƙasar. Kan wannan, da kuma yadda yaƙin ke daɗa rincaɓewa da shafar ƙasashen Yankin Gabas ta Tsakiya, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Bashir Nuhu Mabai, Malami a Jami'ar Dutsinma da ke Katsina a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

Iran ta ci gaba da kai munanan hare-hare kan Isra'ila da muradun Amurka a Gabas ta Tsakiya.To sai dai ƙasashen yankin Gulf na zarginta da faɗaɗa hare-haren kan fararen hula da ababen more rayuwa kamar Otel-otel da filayen jiragen sama da kuma cibiyoyin makamashi. Ko a jiya, dakarun juyin juya halin Iran sun yi ikirarin tarwatsa cibiyoyi da dama a yankin kurdawa, wadanda ta ce mayakanta na shirin yi mata kutse domin kai mata hare-hare. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....

Ga dukkanin alamu akwai yiwuwar yaƙi tsakanin Iran da kuma haɗin gwiwar Amurka da Isra'ila ya ɗauki tsawon lokaci saɓanin zaton da ake yi na ya kasance gajere, wannan kuwa ya biyo bayan jawabin shugaban Amurka Donald Trump a daren jiya da ke cewa mai yiwuwa a shafe makwanni 4 zuwa 5 suna kai hare-hare kan Iran. Wannan na zuwa ne a yayin da yaƙin da ya rincaɓe, ke ci gaba da shafar ƙasashe da dama a Yankin Gabas ta Tsakiya. Domin jin yadda masana siyasar ƙasa da ƙasa ke kallon lamarin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Tukur AbdulƘadir na Jami'ar Jihar Kaduna a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar..

Iran ta kai jerin hare-hare kan sansanonin sojin Amurka da wasu muhimman wurare biranen Dubai da Abu Dhabi a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, sai kuma Doha a Qatar da kuma Manama a Baharain, domin ɗaukar fansa kan farmakin da haɗin gwiwar Amurka da Isra'ila suka ƙaddamar kanta tun daga ranar Asabar. Baya ga harba makamai masu linzami kan Isra'ila, Iran ta tsananta kai hare-haren kan sansanonin sojin Amurka ne bayan mutuwar jagoranta Ayatollah Khamenei. Domin jin halin da ake ciki da sauran batutuwa masu alaƙa da yaƙin da ya ɓarke, Nura Ado Suleiman ya tattauna Dakta Ibrahim Adamu, masanin Yankin Gabas ta Tsakiya da ke Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Wani rahoton bincike da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya wallafa, ya bayyana cewa an hare-haren ta'addanci a yankunan da ke iyakokin ƙasashen Najeriya, Benin, da kuma jamhuriyar Nijar sun ƙaru da aƙalla kaso 86 bisa 100, sakamakon yunƙurin da ‘yan ta'addan masu alaƙa da Al-Qa'eeda da IS ke yi na karɓe iko da hanyoyin da ratsa yankunan. Rahoton ya ƙara da cewar matsalar wadda ta yi ƙamari a tsakanin shekarar 2024 zuwa bara, ta yi sanadin mutuwar aƙalla mutane dubu 1000. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Kaftin Abdullahi Adamu Bakoji mai ritaya, masanin tsaro a Najeriya. Latsa alamar sauti domin sauraren tataunawarsu...

A Najeriya, Matatar Man Dangote mafi girma a Afirka ta cimma matsaya da wasu manyan kamfanonin dallancin Mai guda 12 domin rarraba man fetir kimanin lita miliyan 60 zuwa 65 a kowace rana. Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya bayyana haka cikin wata sanarwar, da ya ce gagarumin mataki ne na wadata kasar da mai da kuma dogaro da kai a bangaren makashi. Domin sanin tasirin matakin, Ahmad Abba ya tattauna da Dr. Kasum Garba Kurfi, masanin tattalin arziki a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

Shugabannin ƙasashen ƙungiyar Tarayyar Turai EU, sun sha alwashin babu gudu babu ja da baya, kan ci gaba da taimaka wa Ukraine a yaƙin da take yi da Rasha. A yayin da ita kuma Rashar ta lashi takobin ci gaba da yaƙi har ta cimma nasarar da take nema, bayan da ta amince cewar zuwa yanzu ta gaza cimma muradunta a maƙwafciyar tata. Waɗannan ɓangarori sun bayyana matsayarsu ce bayan cika shekaru huɗu cif da ɓarkewar yaƙi tsakanin Rasha da Ukraine, a rana mai kamar ta jiya Talata, 24 ga watan Fabarairun shekarar 2022. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Tukur Abdulƙadir na Jami'ar Jihar Kaduna da ke Najeriya, wanda ya yi tsokaci kan yadda lamura ke warwara. Ku latsa alamar sauti don jin yadda tattaunawarsu ta gudana...............

Gwamnatin Jihar Benue a Najeriya, na neman amincewar gwamnatin tarayyar ƙasar wajen gina cibiyar sauya tunanin ‘yan bindigar da suka tuba, da ma sauran mutanen da wani yanayi ya sanya su taimaka wa ayyukan ta'addanci, ciki kuwa har da mata waɗanda ke yi wa ‘yan ta'addan aiki a bisa tilas bayan garkuwar da aka yi da su. Wannan na zuwa ne a yayin ake ci gaba da samun banbancin ra'ayi tsakanin ‘yan Najeriya a kan irin wannan yunƙuri. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Kabiru Adamu, shugaban kamfanin Beacon Consulting da ke bincike kan tsaro a nahiyar Afrika. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar..

A Najeriya, ƴan bindiga a ƴan kwanakin nan sun zafafa kai hare-hare yankunan jihohin Zamfara da kuma Kebbi. Na baya bayan nan shine wanda ya faru a garin Dutsen Dan Ajiya na karamar hukumar Anka ta jihar Zamfara, inda rahotanni suka ce sama da mutane 30 sun mutu, bayaga na Tungan Dutse da mutane 50 suka rasa ransu. Haka zalika, mayaƙan Lakurawa sun ƙara zafafa kai hare-hare a wasu sassa na jihar Kebbi, inda nan ma suka hallaka mutane da dama. Kan haka Khamis Saleh na zanta da Squadron Leader Aminu Bala Sokoto. Ku latsa alamar sauti don sauran cikakkiyar tattaunawar.

A ranar Alhamis, shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaddamar da fara aikin Kwamitin Zaman Lafiyar Duniya da ya kafa. Wakilai daga aƙalla ƙasashe 47 da kuma ƙungiyar Tarayyar Turai da Isra'ila ne suka halarci taron farkon na Kwamitin Zaman Lafiyar na Duniya a birnin Washington. Muhimman batutuwan da taron ya mayar da hankali kai sun haɗa da kafa Rundunar zaman lafiya a Gaza, da karɓe makamai daga hannun Hamas, da kuma sake gina Zirin na Gaza. Shiga alamar sauti, domin sauraron tattaunawar Nura Ado Suleiman da AbdulHakim Garba Funtua, masanin siyasar ƙasa da ƙasa.

Kotun ECOWAS ta koka kan alƙaluman da suka nuna cewar cikin shekaru 25, wato tun bayan da ta fara aiki a shekarar 2001, hukunce-hukunce gud 10 kaɗai Najeriya ta mutunta, 66 da ta yanke. Shugaban Kotun ta ECOWAS Ricardo Claudio ne ya bayyana alƙaluman yayin buɗe taron masu ruwa da tsaki da babbar ƙotun ƙungiyar ƙasashen ta Yammacin Afrika a Najeriya. Domin jin yadda masana ke kallon lamarin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Barista Abubakar Mujitafa Gagare, ƙwararren lauya da ke Najeriya. Latsa alamar sauti don jin yadda tattaunawar ta gudana...

Al'ummar Musulmai a sassan duniya, sun ɗauki azumin farko a bana, bayan da ƙasashen duniya ciki har da Saudiyya da Najeriya suka sanar da ganin jinjirin watan Ramadana. Azumin Ramadan lokaci ne da al'ummar musulmai ke amfani da shi wajen ƙara kusanci da mahallicinsu, da kuma ƙarfafa imani tare da nesantar aikata laifuffuka. A tattaunawar sa da Ahmad Alhassan, Imam Abubakar Muhammad malamin addinin musulunci ne a Najeriya, yayi mana ƙarin haske game da falalar azumin Ramadana. Latsa alamar sauti don sauraren hirarsu...

Masana Tarihi gami da Siyasar Duniya sun fara yin tsokaci kan matsayar da ƙungiyar ƙasashen Afrika AU ta tsaida na amincewa da ƙudurin bayyana cinikin bayi da kuma bautar da su gami da Mulkin Mallakar da Turawan yamma suka yi wa Nahiyar a matsayini kisan ƙare dangi da kuma laifukan take hakkin ɗan Adam. Shugabannin ƙasashen nahiyar ta Afrika sun cimma matsayar ce a Lahadin da ta gabata, yayin ƙarƙare taronsu na shekara karo na 39 a birnin Addis Ababa. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Tijjani Muhd Naniya, masanin tarihi da ke jami'ar Bayero a Kano, Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

A karon farko shugaban mulkin sojin Nijar Janar Abdulrahmane Tchiani ya kai ziyara Aljeriya, irinta ta farko da ya kai zuwa wata ƙasa da ba mamba ba a cikin ƙawancen AES, tun bayan ɗarewarsa karagar mulki ta hanyar juyin mulkin da ya kawo ƙarshen gwamnatin Mohamed Bazoum. Abba Sadiq, masanin siyasar yankin Saleh, ya ce dama alaƙa bata taɓa lalacewa tsakanin Nijar da Aljeriya. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsa da Ruƙayya Abba Kabara...

Wata cibiya da ke bibiyar ayyukan Kamfanonin sojojin haya a sassan Duniya, ta ce kusan mutane dubu 1 da 500, Rasha ta ɗiba daga ƙasashen Afrika aƙalla 35, a matsayin sojojin haya a yaƙin da take gwabzawa da Ukraine. Rahoton ya ƙara da cewar daga cikin jimillar ‘yan Afrikan da suka shigar wa Rasha yaƙin da take da Ukraine a tsakanin shekarar 2023 zuwa tsakiyar bara, 316 sun mutu. Don jin irin kallon da masana tsaro ke yi wa lamarin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Kabiru Adamu, shugaban kamfanin Beacon Consulting mai binciken tsaro a nahiyar Afrika. Latsa alamar sauti don jin yadda tattaunawarsu ta gudana...

A ranar Litinin da ta gabata, mahukuntan Najeriya suka buɗe iyakokinsu da Nijar da kuma Jamhuriyar Benin ta ɓangaren jihar Kebbi, matakin da ya maido da zirga-zirgar kasuwanci tsakanin ƙasashen uku. Gabanin buɗe iyakokin dai sai da aka gana tsakanin wakilan Najeriya da na Nijar, matakin da ya kawo ƙarshen katse jigilar manyan motocin dakon kaya fiye da Dubu Ɗaya da Ɗari Biyar, da suka shafe aƙalla wata guda a tsaye. Domin jin ƙarin bayani kan lamarin Nura Ado Suleiman ya tattauna da Alhaji Sani Shekarau, shugaban ƙungiyar manyan ‘yan kasuwa da ke jigilar kayayyaki zuwa ciki da wajen Jamhuriyar Nijar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

Ɗaruruwan ‘yan Najeriya a jiya Litinin, sun gudanar da zanga-zangar lumana a birnin Abuja, domin bayyana ɓacin ransu dangane da jan ƙafa a kan gyaran dokar zaɓe da majalisar ƙasar ke yi, musamman kan matakinta na ƙin amincewa da batun tilasta wa hukumar zaɓe sakin sakamako kai-tsaye daga rumfuna a shafinta na yanar gizo.Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Barista Ibrahim Bello Rigachikun, tsohon ɗan Majalisar Tarayya, kuma ƙwararren lauya a Najeriyar. Latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawar

Kungiyar IPOB da ke fafutukar neman ɓallewar Yankin Kudu Maso Gabashin ƙasar daga Najeriya, ta sanar da kawo ƙarshen tilasta wa jama'a zaman gida a kowace ranar litinin yau kusan shekaru biyar kenan. Matakin dakatar da tilasta zama gidan da ƙungiyar ta sanar a jiya lahadi, ya zo ne bayan da gwamnan jihar Anambra ya buƙaci jama'a su bijire sannan su ci gaba fita kowace litinin domin gudanar da harkokinsu na yau da kullum. Alhaji Ibrahim Abdulƙadir Ɗan-Ghali shi ne jagoran ƙawancen ƙungiyoyin ƴankasuwa ƴan asalin Arewacin Najeriya mazauna jihar Imo, ya bayyana wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal matsayinsu game da sanarwar ta IPOB. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Babban Sifeton Ƴansandan Najeriya Kayode Egbetokun, ya aike runduna ta musamman domin mara wa sojoji baya wajen tabbatar da tsaro a ƙaramar hukumar Kaiama da ke jihar Kwara, inda ‘yan ta'adda suka salwantar da rayukan mutane kusan 170. Yanzu haka dai ana dakon ganin tasirin matakan da haɗin gwiwar jami'an tsaron Najeriyar zai yi wajen murƙushe matsalar tsaron da ke daɗa ƙamari, lamarin da ke ta'azzara duk da jerin farmakin da jami'an tsaro ke kaiwa, tare da tarwatsa sansanonin ‘yan ta'adda a sassan arewacin ƙasar. Kan wannan lamari Nura Ado Suleiman ya tattauna da Kaftin Abdullahi Bakoji mai ritaya masanin tsaro a Najeriya.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta ware 4 ga watan kowane watan Fabarairu a matsayin ranar yaƙi da Cutar Daji ko kuma Cancer ta Duniya, wadda hukumar lafiya ta Duniya WHO ke jagorancin gangamin wayar da kai a kanta, gami da bayyana halin da ake dangane da kula da masu fama da ita. Wannan rana ta zo ne a daidai lokacin da wani sabon rahoton masana ya ce daga cikin kusan mutane miliyan 19 da suka kamu da cutar ta Daji a shekarar 2022, ana iya bayar da kariya ga aƙalla mutane miliyan 7 daga kamuwa da cutar in da an ɗauki matakan da suka dace. Domin jin ƙalubalen da ƙasashe masu tasowa kamar Najeriya ke fuskanta dangane da cutar, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Shehu Usman AbdulMumin Maƙarfi, ƙwararren Likita a Jihar Kaduna da ke Najeriya. Sai a latsa alamar sautin da ke sama domin sauraron bayanan Dakta Shehu Usmanu Maƙarfi....

Amurka ta sanar da tura wata tawagar sojinta zuwa Najeriya, abinda a karon farko ke tabbatar da isar dakarun nata ƙasar, tun bayan ƙarfafa yarjejeniyar tsaron da ƙasashen biyu suka yi, biyo bayan zargin da shugaba Donald Trump ya yi a shekarar bara, cewa ana kashe Kiristoci a Najeriyar. Kwamandan rundunar sojin Amurka da ke kula da Afirka, Janar Dagvin R.M. Anderson ya ce sun tura dakarun ne a bisa amincewar Najeriya. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Yahuza Ahmed Getso masanin tsaro a Najeriya. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.......

A Najeriya, alamu na nuni da cewa gwamnatin Anambra ta kama hanyar kawo ƙarshen barazanar ‘yan awaren IPOB da ke tilasta wa jama'a zaman gida a kowace ranar Litinin, bayan da a jiya aka buɗe kasuwanni a jihar, biyo bayan umarnin ga gwamna Charles Suludo ya bayar na ko dai su buɗe ko kuma ya rufe su a sauran kwanakin mako. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Alhaji Abdullahi Bebeji shugaban Ƴan Kasuwar da ke hada-hadar kayan Gwari a babbar kasuwar Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken bayani......

A Njeriya rahotanni daga Kaduna na nuni da cewar 80 daga cikin mutanen nan da aka bayyana cewar an sace a wata Majalimi'a da ke a Kurmin Wali sun kubuta daga masu garkuwa da su, sun dawo gida, bayan sun share tsawon lokaci suna tafiya a cikin Dokar Daji. To sai dai abin da ke ɗiga ayar tambaya shi ne yawansu su 80 su kuɓuta a hannun ƴan ta'adda abu ne da ke buƙatar bayani. Dangane da haka na samu zantawa da wani shugaban al'umma a Kurmin Wali wanda ya bayyana cewar akwai ƙamshin gaskiya a labarin kuɓutar mutanen amma ya bukaci a sakaya sunansa. A latsa alamar sauti domin sauraron cikakken zaantawar Faruk Muhammad Yabo da wani shugaban al'umar

A farkon makon nan, gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin maido da tsaffin sojoji bakin aiki, domin taimaka wa wajen samar da tsaro a yankunan da ke fuskantar barazanar ƴan ta'adda a sassan ƙasar. Sanar da matakin na zuwa ne bayan kafa wani kwamiti mai mambobi 18 da ministan tsaron na Najeriya Janar Chrisroper Musa mai ritaya ya jagoranci samarwa, wanda ya ce aikinsa shi ne tabbatar da ƙwato dukkanin yankunan da ke ƙarƙashin ikon ƴan ta'adda. Dangane da wannan Nura Ado Suleima ya tattauna da Dakta Auwal Aliyu Abdullahi, mai magana da yawun Kwamitin musamman da ke kula da walwalar tsaffin sojoji a Najeriya.

Yau ake cika shekaru biyu da ficewar ƙasashen Nijar da Mali da kuma Burkina Faso daga cikin ECOWAS, KO CEDAEO, biyo bayan matsin lambar ƙungiyar ta yi musu saboda juyin mulkin da sojojinsu suka yi, da kawar da matsalolin da suka zargi gwamnatociin da suka hamɓarar da gaza magancewa. Domin tsokaci kan halin da ƙasashen na AES ke ciki, shekaru biyu bayan matakan da mahukuntansu suka ɗauka, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Abdel Nasser Saidu ɗaya daga cikin wakilan kungiyoyin farraren fula a Nijar..

Wani sabon rahoton masana, ya nuna cewar yawan tallafin bashi da China ke bai wa ƙasashe marasa ƙarfi musamman na Afrika ya ragu matuƙa daga kashi 124 cikin shekaru 10 da suka gabata zuwa kashi 56. A cewar rahoton, wannan na zuwa ne , a yayin bashin da ƙasashen na Afrika suke biyan ƙasar ta Sin ke ci gaba da ƙaruwa, fiye da tallafin da suke samu daga gareta ba. Ga misali a tsakanin 2000 zuwa 2023 China ta tallafa wa ƙasashen Afrika 49 da bashin Dala biliyan 182, to amma a shekarar 2024, tallafin Dala Biliyan 2.1 kawai ta samar. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna na Farfesa Mansur Idris na Jami'ar Bayero da ke Kano. Shiga alamar sauti domin sautraron cikakkiyar tattaunawar.

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da yunkurin yi wa shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu juyin mulki a watan Oktoban shekarar bara, lamarin da ya kai ga cafke wasu jami'an soji da ake zargin da hannunsu a yunƙurin. A jiya Litinin ne dai Hedikwatar tsaron Najeriya ta hannun kakakinta Manjo Janar Sama'ila Uba ta tabbatar da lamarin, tare da sanar da miƙa rahoton bincikenta ga shugaban Najeriya. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da masanin tsaro a Najeriya Muhd Sani Ibrahim Makiga. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

A Najeriya babban abin da mafi yawan mutane ke neman ƙarin haske a kai su ne abubuwan da ke ƙunshe a yarjejeniyar tsaron da aka ƙulla tsakanin ƙasar da Amurka domin kawo ƙarshen ƴanbindigar da Amurkan ta ce suna yi wa Kiristoci kisan gilla. A game da wannan yarjejeniyar ce Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Yahuza Getso, masani tsaro da ke game da ayykan ƴanbingar da suka addabin jama'a, ga kuma yadda zantawarsu ta gudana. A latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar zantawar.

Amurka ta kawo ƙarshen tallafin da ta ke bayar wa a hukumar Lafiya ta Duniya WHO daga wannan Alhamis, 22 ga watan Janairun 2026, duk kuwa da kasancewarta jigo wajen samar da kuɗaɗen tafiyar da hukumar wadda ke samar da tallafin magunguna da sauran ɓangarorin lafiya ga ƙasashe da dama musamman masu tasowa. Donald Trump ya sanar da aniyar janyewar ƙasar daga hukumar koda yake tun a wancan lokaci ya ƙulla yarjejeniyar cewa sai bayan shekara guda ne ficewar za ta fara aiki a hukumance. Kan haka ne Faruk Muhammad Yabo ya tattauna da Dr Adam Mustapha na sashen nazarin ƙananan halittu a jami'ar Maiduguri ya yi mana tsokaci kan illar da matakin na Amurka ka iya haifarwa.

Mahukuntan soji a Burkina Faso sun bayyana mutukar jin ɗaɗinsu tare da mika godiya ga ƙasar Togo, dangane da namijin ƙoƙari na miƙa musu tsohon shugaban riƙon ƙwaryar ƙasar, laftanar kanar Henri Damiba, wanda su ke zargi da yunƙurin juyin mulki a lokuta da dama.Damiba zai fuskanci kotu domin amsa wannan tuhuma.... Abdoulaye Issa ya tattauna da Farfesa Ali Sakola Jika malami a jam'iar Ouagadougou.

Makomar ayyuka da tsarin haƙar ma'adanai na cikin batutuwan da a ‘yan kwanakin nan ya ɗauki hankali a Najeriya, inda a gwamnatin ƙasar ta musanta zargin cewa tana shirin kafa matatar zinare mallakinta a jihar Legas da ke kudancin ƙasar. Tun da fari, ƙungiyar dattawan arewacin Najeriya ce ta yi wannan ƙorafi cikin wata buɗaɗɗiyar wasiƙa, inda ta bayyana matakin a matsayin rashin adalci, la'akari da cewar yankunan arewa maso yammaci da tsakiyar Najeriya ne ke da arzikin na Zinare. Kan wannan da wasu batutuwan masu nasaba, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Injiniya Datti Yusuf Yahya ƙwararre kuma tsarawa da bayar da shawara kan ayyukan haƙar ma'adanai a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Yau Donald Trump ke cika shekara guda da komawa shugabancin Amurka, wa'adin da wasu ke ganin tamkar shugaban ya shafe shekara da shekaru bisa mulkin, la'akari da jerin matakan da ya riƙa aiwatarwa a matakin ƙasa da ƙasa da kuma cikin gida, ba tare da la'akari da caccakar da ake yi masa ba a gida da waje. Domin jin hasashen masana kan abinda ke tafe a ragowar shekaru uku da suka rage wa shugaban na Amurka Donald Trump, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta AbdulHakim Garba Funtua masanin siyasar ƙasa da ƙasa. Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawarsu...........

A daren jiya ne aka kammala gasar lashe kofin nahiyar Afrika ta AFCON da Morocco ta karɓi bakunci, inda Senegal ta samu nasarar lashe gasar a karo na biyu a tarihi. Masu sharhi kan lamuran wasanni na kallon gasar a matsayin wacce aka inganta, sai dai ba a rasa ƙalubale nan da can da aka samu ba. Khamis Saleh ya zanta da Aliyu Lawal Ibrahim wanda akafi sani da Ali Cairo, tsohon ko-odinetan hukumar CAF kuma tsohon sakataren tawagar ƴan ƙasa da shekaru 20 ta Najeriya, wanda ya halarci gasar, Ku latsa alamar sauti don sauraron yadda zantawarsu ta kasance...........

Gamayyar Ƙungiyoyin ma'aikatan lafiya a Najeriya sun sha alwashin ci gaba da yajin aikin da suka faro tun cikin watan Nuwamban bara, a faɗin ƙasar, duk da cewar gwamnati ta yi gargaɗin dakatar da biyansu albashi muddin basu koma bakin aiki ba. Tuni dai yajin aikin ma'aikatan lafiyar ya jefa masu jinya cikin mawuyacin hali la'akari da makwannin da aka shafe ba tare an cimma matsaya a tsakanin masu yajin aikin da mahukuntan ƙasar ba. Kan wannan Faruk Muhd Yabo ya tattauna da Dakta Shehu Usman AbdulMumin Maƙarfi, ƙwararren Likitia a Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraren yadda tattaunawarsu ta gudana...

Najeriya ta rasa damar kai wa matakin buga wasan ƙarshe na gasar cin kofin ƙasashen Afrika, bayan da ta yi rashin nasara da ƙwallaye 4-2, a karawar da ta yi da mai masaukin baƙi wato Morocco. An dai ƙarƙare wasan ne a matakin bugun daga kai sai mai tsaron raga wato Fanareti, bayan da aka buga mintuna 90 har da ƙarin lokaci na wasu minitunan 30 ba tare da ɓangarorin sun jefa wa junansu ƙwallo ba. Shiga alamar sauti domin sauron cikakkiyar hirar.....

Hedikwatar rundunar sojin Amurka mai kula da nahiyar Afirka, AFRICOM, ta sanar da miƙa wa gwamnatin Najeriya taimakon kayayyakin aikin soji, matakin da ke ƙarfafa yarjejeniyar tsaron da ke tsakaninsu don yaƙi da ta'addanci. Sai dai cikin sanarwar da ta wallafa a shafinta na X, rundunar sojin Amurkan ba ta yi ƙarin bayani kan nau'ika da kuma adadin makaman ba. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Kabiru Adamu shugaban kamfanin Beacon Consulting da ke bincike kan tsaro a nahiyar Afrika.

Gwamnatin Iran ta ce tabbas an buɗe hanyoyin tuntubar juna tsakaninta da Amurka, bayan da shugaba Donald Trump ya yi barazanar yin amfani da ƙarfi kan ƙasar matuƙar ta ci gaba da kashe masu zanga-zanga. Mahukuntan Iran dai na ƙoƙarin shawo kan ɗaya daga cikin bore mafi muni da suka taɓa faruwa a ƙasar. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon jakadan Najeriya a Iran Amabasada Abubakar Cika, ga kuma zantawarsu dangane da wannan tarzoma ta Iran. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

A yayin da Dalibai su ka koma makarantu a jihohi daban daban na tarayyar Najeriya, wata matsalar da ake fama da ita, ita ce ta wasu yankuna na jihohin kasar da kusan kashi 70 zuwa 80 na Daliban ba sa zuwa Makaranta saboda matsalolin tsaro. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hirar Faruk Yabo da Hon. Habibu Halilu Modachi

A Najeriya, gobe Alhamis 1 ga watan Janairu ne, za a fara aiwatar da sabuwar dokar haraji ta ƙasa, a cikin yanayi da dokar ke shan suka saboda dalilai da dama. Yayin da jama'a ke cewa sabon tsarin karɓar haraji na matsayin ƙarin nauyi ne ga al'umma, hakazalika wasu ƴan majalisa sun yi zargin cewa abin da suka amince da shi ya sha bambam da abin da gwamnati ke shirin aiwatarwa. A game da shirin aiwatar da dokar ne Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dakta Mahdi Shehu da ke fafutuka a Najeriya, ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.