A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban…

Tawagar ƙasar Spain ta lashe gasar kofin duniya karo na biyu a tarihi, bayan da doke Argentina da ke kare kambun a wasan ƙarshe da suka gudanar a daren jiya. Ita kuma Ingila ta ƙare a matsayi na 3 ne a gasar, inda ta lashe kyautar tagulla da ke zama kyauta ta farko da ta lashe a kofin duniya cikin shekaru 60, ya yin da Faransa ta ƙare a matsayi na 4. Shiga alamar sauti don sauraron hirar da Khamis Saleh ya yi da tsohon ɗan wasan tawagar Super Eagles ta Najeriya Coach Garba Lawal......

Ƙungiyar Greenpeace dake kare muhalli a duniya ta buƙaci dakatar da shirin gina sabuwar matatar man Dangote da za ta laƙume Dala biliyan 17 a ƙasar Kenya, saboda yadda aikin zai yiwa muhalli da sauran hallitun ruwa illa. uni wannan kira ya haifar da mahawara, la'akari da yadda sabuwar matatar za ta taimakawa al'ummar Gabashin Afirka baki ɗaya. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Kabir Muhammad Baba, masanin tattalin arziki. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

Matsalar tsaro ta hare-haren da ‘yan ta'adda kan kai wa makarantu ko ɗalibai a sassan Najeriya, na ci gaba da ci wa al'ummar ƙasar tuwo a ƙwarya, la'akari da cewar ko a baya bayan nan, ‘yan bindiga sun kai hari tare da sace wasu ɗaliban wata Sakandare a ƙaramar hukumar Dekina da ke jihar Kogi. Wannan ya zo ne bayan hare-haren da a makwannin baya makarantun suka fuskanta a jihohin Oyo da kuma Borno. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da shugaban ƙungiyar Malaman Makarantu ta Najeriya, Comrade Audu Titus Amba. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Majalisar Wakilan Najeriya ta yi kira ga rundunar sojin saman ƙasar da ta buɗe ɓangaren hanyar Maiduguri zuwa Kano da ta toshe a anguwar Ngomari-Pompomari da ke wajen birnin Maiduguri kusan shekaru 10 wanda ke haddasa asarar ɗumbin rayuka. Ɗan Majalisa mai wakiltar Jere a jihar Borno, Hon. Satomi da ya gabatar da ƙudirin gaban Majalisar a makon jiya, ya yi wa Ahmed Abba ƙarin bayani dangane da girman matsalar da toshe hanyar ya haifar da kuma ƙoƙarin da gwamnati ke yi wajen ceto ɗalibai da malamai da Boko Haram ta yi garkuwa da su a Askira-Uba na jihar Borno. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana.

Al'ummar yankunan ƙananan hukumomin Faskari da Ɗandume da ke jihar Katsina, na ƙoƙawa kan yadda ƴan ta'adda ke amfani da ranakun kasuwa wajen tare hanyar da ta tashi daga Ɗandume ta wuce zuwa Kadisau ta dangane da Sheme, inda su ke kwace musu ababen hawa da garkuwa da mutane harma a wasu lokuta da salwantar da rayukansu. Haka nan a wasu lokuta ƴan ta'addan na kuma bin manoma gonakinsu don kwace musu babura da kuma shanun huɗa. Khamis Saleh ya zanta da ɗaya daga cikin mazauna wannan yankin da wannan matsala ta daɗe tana ci musu tuwo a ƙwarya.

Yayin da ake ci gaba da jinjina wa rundunar sojin Najeriya saboda nasarar ceto ɗalibai da malamai 44 da ƴanbindiga suka yi garkuwa da su a jihar Oyo, wasu na gani cewa ya kamata mahukunta su ƙara azama don ceto ɗaruruwan mutanen da ake ci gaba da yin garkuwa da su a sasan ƙasar. Ko a jiya lahadi ɗimbin mutane ne suka gudanar da zanga-zangar neman gaggauta ceto ɗalibai da dama da ake yin garkuwa da su a jihar Borno ciki har da waɗanda aka sace rana ɗaya da na jihar Oyo. Abdoulkarim Ibrahinm Shikal ya zanta da Ibrahim Garba Wala da ke bin diddigin wannan batu na taɓarɓarewar tsaro a Najeriya, ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....

Cikin makon nan, kasuwar hada-hadar hannayen jarin Najeriya, ta kafa tarihin zama mafi ƙarfi gami da bunƙasa a faɗin Duniya, bayan zarta mai riƙe da kambun a baya bayan nan, wato takwararta ta Korea ta Kudu. Rahoton kamfanin Bloomberg ya nuna cewa, zuwa yanzu Kasuwar ta Najeriya ta samu tagomashi ne da kaso 67 cikin 100, yayin da ta Korea ta Kudu ke da kaso 66. Domin jin ƙarin bayanin kan dalilan samun wannan nasara, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Ƙasim Garba Kurfi, ɗaya daga cikin masu ruwa da tsaki a kasuwar hada-hadar hannayen jarin ta Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawar...

Najeriya na tattaunawa da China wajen ganin ta samu goyon bayan da ya dace a fasahar zamani da kuma makamai domin shawo kan matsalolin tsaro da suka addibi ƙasar. Sabon jakadan Najeriya a ƙasar China Janar Abdurrahman Bello Dambazau mai ritaya ya bayyana haka a tattaunawar da suka kayi da Bashir Ibrahim Idris. Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirar.

A wannan Laraba ake fara taron tuntuɓa tsakanin ƙasashen ƙungiyar AES wato Mali, Nijar da Burkina Faso da kuma ƙasar Rasha a gefe guda a Yamai fadar gwamnatin Nijar, inda ake sa ran za su tattauna batutuwan da suka shafi tsaro, tattalin arziki da kuma makamashi. Wannan ne karo na biyu da ake gudanar taron bayan makamancinsa da aka yi a birnin Moscow na Rasha a watan Afrilun 2025, kuma ya na zuwa a daidai lokacin da mayaƙa masu ikirarin jihadi suka zafafa kai hare-hare a waɗannan ƙasashen na Sahel. A kan wannan Oumarou Sani ya tattauna da Dakta Sani Gambo malami a jami'ar Andre Salifou da ke Zinder a Jamhuriyar Nijar, game da ci gaban da hakan zai kawo ga ƙasashen biyu. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

A Najeriya, daidai lokacin da ake neman sanin matsayin shugaba Bola Tinubu dangane da zargin kafawa da kuma tafiyar da wata ma'aikatar jabu a ƙarƙshin gwamnatin tarayya, sai kuma ga wasu bayanai daga Asusun Lamuni na Duniya IMF da ke cewa gwamnatin ta kashe sama da Naira triliyan 8 waɗanda sam kasafin kuɗin ƙasar bai san da su ba. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hira da Abdoulklarim Ibrahim Shikal ya yi da Kwamrad Nasiru Kura mai fafutukar yaƙi da rashawa a ƙasar..........

Ƙungiyar Amnesty International a Najeriya ta zargi gwamnatin shugaba Bola Ahmad Tinubu da gaza kare ƴan Najeriya daga matsaloli na ta'addanci da na tattalin arziki da ake fama da shi. Ruƙayya Abba Kabara ta tattauna da daraktan Amnesty a Najeriya, Malam Isa Sanusi kan rahoton nasu. Latsa alamar sauti don sauraren sa....

Babban Bankin Najeriya na CBN ya sanar da soke lasisin wasu ƙananan bankuna 46 saboda saɓawa ƙa'idar aiki. Waɗannan bankuna sun haɗa da guda 12 a Kano da wasu takwas a Lagos, baya ga wasu ɗaiɗaikun jihohi. Domin sanin tasirin wannan mataki, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Isa Abdullahi, masanin tattalin arziki, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.

Kotun Ƙolin Amurka ta yi watsi da buƙatar shugaba Donald Trump ta soke dokar da ke bai wa waɗanda aka haifa a ƙasar ƴancin zama ƴan ƙasa kai-tsaye. Kotun ta tananata cewa, duk wanda aka haifa a Amurka na da ƴancin mallakar shaidar zama ɗan ƙasa. Trump ya ruga kotun kolin ne bayan rashin nasara a ƙananan kotunan ƙasar. Kan haka, Abdurrahman Gambo Ahmad ya tattauna da Muhammad Sani Sufyan, mazaunin Amurka wanda kuma ke sharhi kan siyasar ƙasar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

An shiga wani yanayi na fargaba da tsananin tashin hankali a Afirka ta Kudu, yayin da yau wa'adin ranar 30 ga watan nan na Yuni ke cika, game da zanga-zangar da wasu ƙungiyoyin ƙyamar baki suka shirya don tilasta wa baƙin da ba su da takardu barin ƙasar. Ko da yake hukumar 'yansandan ƙasar ta ce ta tura ɗimbin jami'an tsaro zuwa yankunan da ake sa ran za su fuskanci tashin hankali, kamar su Pretoria, Johannesburg, da KwaZulu-Natal. Shamsiyya Haruna ta tattauna da Hajiya Rakiya Sa'idu, wata yar Najeriya da ke aiki a jami'ar Cape Town a Afirka ta Kudun, dangane da halin da suke ciki.

Mahukunta a Faransa, sun ce yanzu haka suna kan yin nazari domin ɗaukar matakin da ya dace bayan da Burkina Faso ta sanar da katse duk wata hulɗar diflomasiyya da ƙasar, inda ta zargi Faransa da taimaka wa masu tayar da ƙayar baya da ke neman wargaza sha'anin tsaro da na zamantakewar al'ummarta. A game da wannan batu ne Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Malam Soumaila Amadou, wanda ke bin diddigin wannan takun-saka da aka jima ana yi tsakanin Faransa da kuma ƙasashen da ta yi mulkin mallaka a Yankin Sahel. Ga dai zantawarsu.

A Najeriya ra'ayoyi sun sha bambam a tsakanin al'umma dangane da shirin bai wa jihohi damar kafa rundunar ƴansanda don inganta sha'anin tsaro a ƙasar. Tuni dai Majalisun Tarayyar Ƙasar biyu suka amince da daftarin dokar da ke bayar da damar ɗaukar wannan mataki, kamar dai yadda gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta buƙata. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon Kwamishinan Ƴansanda CP Muhammed Indabawa mai ritaya, domin jin yadda masana aikin ɗansanda ke kallon matakin. Latsa alamar sauti don sauraren zantawarsu...

Fulani makiyaya a Najeriya sun koka dangane da irin tsangwama da kuma barazanar da suke fuskanta a kudancin ƙasar, sakamakon matsalar tsaro da kuma garkuwa da mutane da ake fama da shi. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da shugaban ƙungiyar Miyetti Allah, Baba Usman Ngelzerma. Ku danna alamar sauraro domin jin cikakkiyar tattaunawar.

Yau ake cika shekaru 10 da ficewar Birtaniya daga cikin kungiyar ƙasashen Turai domin cin gashin kan ta wajen gudanar da harkokin mulki da kuma kasuwancin ta ba tare da sanya hannun ƙungiyar EU ba. Bayan share shekaru ana tattaunawa, Birtaniya ta fita a hukumance a ranar 31 ga Janairun 2020. Wannan mataki na Birtaniya ya canza taswirar siyasa, tattalin arziki, da dangantakar kasuwanci ta duniya baki ɗaya Domin duba tasirin wannan mataki da kuma nasarar da za'a ce ƙasar ta samu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Abdulhakeem Garba Funtua, mai sharhi kan harkokin siyasar duniya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

An fara tattaunawa tsakanin Benin da kuma Jamhuriyar Nijar da nufin sake buɗe iyakar ƙasashen biyu, sai dai mahukuntan birnin Yamai sun gindaya sharuɗɗa biyu kafin sake buɗe iyakar. Ministan cikin gida kuma jagoran tawagar Nijar a tattaunawar, ya ce na farko dole ne a ƙulla yarjejeniyar tsaro wadda a ƙarƙashinta ba ɗaya daga cikin ƙasashen biyu da za ta bari a yi amfani da ita domin kai wa ɗaya hari, sai kuma a kafa wata cibiyar musayar bayanan sirri ta haɗi-gwiwa da za ta bai wa Nijar damar sa-ido a game da kai-da-kawon sojojin ƙetare a kusa da iyakarta da Benin. Dangane da wannan Oumarou Sani ya tattaunawa da Alhassane Intchinicar guda daga cikin waɗanda suka jima suna fafutukar ganin a sake buɗe iyakar ga kuma yadda zantawarsu ta gudana.

Gobe ne hukumar zaɓe a Najeriya ke gudanar da zaɓen gwamnan Ekiti da ke yankin kudanci, inda ƴan takara 13 za su fafata. Ana kallon wannan zaɓen a matsayin zakaran gwajin dafi ga sabon shugaban hukumar zaɓen Farfesa Joash Amiputan. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai magana da yawun hukumar Hajiya Zainab Abubakar. Latsa alamar sauti don sauraren yadda zantawarsu ta gudana...

Ƙungiyar Kare Hakkin Bil'adama ta Amnesty International ta bukaci gwamnatin Najeriya da ta dauki matakai na gaggawa don kare dalibai da kuma ceto wadanda har yanzu suke hannun masu garkuwa da mutane. Ƙungiyar ta jaddada cewa gazawar hukumomi wajen kawo ƙarshen hare-hare da sace-sacen dalibai na nuna cewa rayuwar yara na cikin matsananciyar barazana. Ƙungiyar ta bukaci Shugaba Tinubu da ya dauki matakin gaggawa na kawo karshen satar yara da kai hari makarantu, tana mai cewa iyaye sun gaji da romon bakar da ake musu. Amnesty ta zargi gwamnatin da kasa kare kananan hukumomi, musamman a jihar Zamfara da sauran yankunan Arewa daga hare-haren yan bindiga. Kungiyar ta nuna damuwa kan yadda tsadar rayuwa da matsalar tsaro ke raba iyalai da muhallansu, lamarin da ke jefa yara da dama cikin yunwa da rashin ilimi. Kan wannan ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Daraktan Ƙungiyar a Najeriya Isah Sunusi. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Gwamnatin Jihar Filato da ke Najeriya ta bayyana matuƙar damuwar ta dangane da yadda ta ce wasu na amfani da hukuncin wata kotu dangane da baiwa wasu Hausawa takardar zama ƴan ƙasa domin haifar da tashin hankali a tsakanin al'ummar da suka kwashe shekaru da dama su na zaman lafiya da juna. Gwamnatin ta ja kunnen al'umma inda ta ce waɗanda ba su gamsu da hukuncin ba na da hurumin ɗaukaka ƙara kamar yadda dokokin ƙasa da suka tanada. Bashir Ibrahim Idris ya tuntuɓi kwamishiniyar yaɗa labaran jihar da ta gabatar da sanawar, Joyce Ramnap kuma ga yadda zantawarsu ta gudanar a kai.

Wata babbar kotu a Najeriya, ta bai wa hukumar zaɓe ta INEC umarnin soke wasu jam'iyyun adawa har guda biyar, saboda saɓawa dokokin zaɓen shekarar 2023 na ƙasa samun kashi 25 na ƙuri'un da aka kaɗa. Jam'iyyun sun haɗa da ADC da AA da APP da ZLP da Acoord Party. Tuni wannan hukunci ya haifar da mahawara da kuma zargin yunƙrin haa 'yan adawa shiga zaɓe mai zuwa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Abubakar Sadiq Gombe, shugaban Jam'iyyar adawa ta SDP. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

A Najeriya, mutuwar tsohon kakakin rundunar sojin ƙasar Janar Abubakar Rabe mai ritaya a hannun ƴan bindiga, lamari ne da ya yi matuƙar ɗaga hankulan jama'a, tare da ƙara haifar da shakkun game da yiyuwar cewa anya kuwa za a iya magance matsalar tsaro a ƙasar? An dai gaza ceto janar Rabe daga hannun ƴanbindigar, duk da cewa ya share kusan makonni biyu a hannunsu. Shiga alamar sauti don sauraron hirar da Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya yi da Air Commodore Ahmed Tijjani Baba Gama mai ritaya......

Wasu fitattun mutane a Najeriya, da suka haɗa da tsohon shugaban hukumar zaɓe Farfesa Attahiru Jega, da tsohon jakadan ƙasar a Majalisar Dinkin Duniya Farfesa Ibrahim Gambari, sun yi gargaɗi a game da irin barazanar da ƙasar ke fuskanta sakamakon rashin tsaro, da yadda ake yi wa tsarin gudanar da zaɓuka na ƙasar karen-tsaye. Kan wannan na gana da guda daga cikin masu ruwa da tsakin da suka yi wannan jan hankali, wato Hussaini Abdu na ƙungiyar Action Aid. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Yau ake fara gasar cin kofin duniya ta bana, inda ƙasashe 48 za su fafata domin samun zakarar bana. A karon farko ƙasashe uku ne ke daukar nauyin gasar, wato Amurka da Cnada da kuma Mexico kuma kalla yan wasa 1,248 da alkalan wasa 52 za su jagoranci wasanni 104 da za'a kwashe kwanaki 39 ana yi. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar da Bashir Ibrahim Idris ya yi da tsohon Sakataren hukumar kwallon kafar Najeriya Hon Sani Ahmed Toro.....

Asusun bada lamuni na duniya IMF ya ce sauye-sauyen da gwamnatin Najeriya ke yi na ƙarfafa tattalin arzikin ƙasar, sai dai kuma sun haifar da ƙarin ƴan Najeriya sama da miliyan 60 da suka faɗa cikin talauci. Ku danna alamar saurare domin jin tattaunawar Bashir Ibrahim Idris, da masanin tattalin arziki a Najeriya Samaila Abdullahi Muhammad kan wannan batu.

Yankin arewacin Najeriya na ci gaba da ɗanɗana kuɗar sa a hannun ƴan bindiga, waɗanda ke kai hari suna sace mutane da kuma hallaka su ba tare da ƙauƙautawa ba. ko a jiya sai da ƴan bindigar suka yi garkuwa da wata tawagar masu neman sulhu da su a jihar Zamfara, baya ga wasu ɗaruruwa da ke hannun su a jihohi da dama, a daidai lokacin da gwamnoni da ƴan majalisun yankin suka mayar da hankali a kan siyasa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Bello Bada na Jami'ar Usman Dan Fodio da ke Sokoto. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana...........

Gwamnatin jihar Lagos a Najeriya ta ƙaddamar da wani gagarumin samame kan mabarata da suka cika titunan birnin, inda aka cafke ɗimbin mabarata ciki har da masu fama da naƙasa da kuma waɗanda ke yi musu jagora, kazalika da ma waɗanda ke cikin ƙoshin lafiya. Kwamishin Ma'aikatar matasa da jin ɗadin jama'a na jihar Mobolaji Ogunlende, ya ce daga ƙarshen watan Mayun da ya gabata zuwa yau, sun cafke sama da mutane dubu 1 da 300 tare da hukunta aƙalla 450 daga cikinsu. Lura da cewa mafi yawan waɗanda suka riƙi bara a matsayin sana'a a birnin Lagos ƴan asalin Arewacin Najeriya ne, wannan ya sa Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da ɗaya daga cikin shugabannin al'ummar yankin da ke zaune a jihar, Alhaji Sa'adu Yusuf Ɗandare Gulma, ga kuma ƙarin bayanin da ya yi masa a game da wannan samame. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu.............

A Najeriya, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta ƙaddamar da bincike akan zargin fitar bayan sirri daga rumbun ajiyar bayananta na masu zaɓe, wanda ya jamnyo cece-kuce a ƴan kwanakin nan. Wannan ya biyo bayan wallafa bayan wani ɗan takara ne da ake zargin wani ma'aikacin INEC ya yi a dandalin sada zumunta a yayin zaɓwen fidda gwani na wata jam'iyyar siyasa a babban birnin tarayyar Najeriya Abuja. Akan haka Michael Kuduson ya tattauna da Dakta Umar Yakubu, shugaban wata ƙungiyar farar hula a Abuja babban birnin Najeriya.

Nijar da Jamhuriyar Benin sun amince da yin aiki a tare don yaƙi da ta'addanci da ke addabar ƙasashen biyu na Yammacin Afirka, yayin da a hannu ɗaya suka kafa wani kwamitin da zai bayar da shawarwari cikin kwanaki 15 a game da yadda za a sake buɗe iyakokin ƙasashen da ke rufe yau kusan shekaru uku. An dai cimma wannan matsaya ce a ziyarar da shugaban Benin Romuald Wadagni ya kai a birnin Yamai ranar talata, inda ya gana da takwaransa na Nijar Janar Abdourahman Tiani. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar da Abdulkarim Ibrahim Chikal ya yi da Sani Yahaya Djandjouna masanin siyasa ƙasa da ƙasa....

A yayin da ya yage kwana 9 a fara gasar lashe kofin duniya da ƙasashen Amurka da Canada da kuma Mexico za su karɓi baƙunci, har yanzu wasu ƙasashe na ci gaba da fuskantar ƙalubale wajen samun takardar izinin shiga ƙasashen. Ko a baya-bayan nan, anga yadda ƴan wasan tawagar ƙasar Afrika ta Kudu suka samu jinkiri wajen tafiya gasar sabida dalilai na Visa, bayaga ƙalubalen da ƙasashen Jamhuriyar Dimukaraɗiyyar Congo da Iran suma suka fuskanta. Kan wannan batu Khamis Saleh ya tattauna da Hon Sani Ahmed Toro, tsohon sakataren Hukumar Kwallon Ƙafara ta Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu..........

A Najeriya, jam'iyyun siyasa sun kammala zaɓen fidda ƴantakarar da za su tsaya musu a matakai daban-daban na zaɓukan da za a yi cikin shekara mai zuwa. To sai dai a ɓangaren adawa, mafi yawan jam'iyyun sun gudanar da zaɓukan ne a cikin yanayi na rabuwar kawuna sakamakon rikicin shugabanci. To akwai yiyuwar wannan rikici na cikin gida ya iya shafar ƙima da kwarjinin adawa a zaɓukan na baɗi? Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar da Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya yi wa Farfesa Usman Mohammed, masani siyasa a Najeriya.

Bisa ga dukkan alamu za a iya samun fahintar juna tsakanin Nijar da kuma maƙociyarta Jamhuriyar Benin, waɗanda ke takun-saka tun bayan kifar da gwamanatin dimokuraɗiyyar ta Mohamed Bazoum yau kusan shekaru uku kenan. Kasancewar Firaminsitan Nijar Mahamane Ali Lemine Zeine a wurin bikin rantsar da sabon shugaban Benin Romuald Wadagni, na ƙara nuni da cewa za a iya samun kusanci a tsakanin ɓangarorin biyu. A game da haka ne Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Adamu Muhammadu Ɗan Madawa, ɗaya daga cikin shugabannin ƴan Nijar mazauna Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraren zantawarsu...

A daidai lokacin da ake kan tattaunawa tsakanin Iran da Amurka don samar da yarjejeniyar kawo ƙarshen yakin da ake yi tsakaninsu, kafafen yaɗa labaran Iran sun ce akwai gagarumin cigaba a tattaunawar. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Malam Mubarak Abdul-Aziz, ɗan Najeriya mazauni Tehran, wanda ya yi masa ƙarin bayani a game da halin da jama'a ke ciki daidai wannan lokaci da ake dakon cimma yarjejeniya don kawo ƙarshen wannan yaƙi. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Jami'an Lafiya na ci gaba da ƙoƙarin daƙile yaɗuwar cutar Ebola da ta sake ɓulla a Jamhuriyar Congo, wadda kawo yanzu ta shiga maƙwafciyarta Uganda. Zuwa wannan lokacin dai, cutar wadda a wannan karon ta bayyana da wani sabon nau'in, ta laƙume rayukan mutane fiye da 100, yayin da wasu kusan dubu ɗaya suka kamu. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Nasiru Sani Gwarzo ƙwararre kan fannin kiwon lafiya da daƙile cutuka masu yaɗuwa a Najeriya, wanda ya yi tsokaci kan dalilan da suka sa wankin hula ke neman kai wa dare. Ku latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawarsu....................

A Najeriya jam'iyyar APC mai mulki ta kammala zaɓen fitar da ƴan takara a dukannin matakai, inda a ƙarshe magoya bayan jam'iyyar suka amince da Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda zai sake tsayawa takarar shugabancin ƙasar a shekara mai zuwa. An dai samu ƙorafe-ƙorafe da kuma taƙƙadama a tsakanin ƴantakara, ya yin da wasu ke zargin cewa an yi musu ba daidai ba. Abdoulkarim Ibrahim Shikak ya zanta da Hon Ishaq Muktar Yakasai, magoyi baya jam'iyyar ta APC kuma wanda ya taka wara domin haɗa kan magoya baya a lokacin zaɓukan. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu............

Kotu a Najeriya ta yi hukunci da ke cin karo da umarnin hukumar INEC da ta nemi dukkanin jam'iyyun siyasa su kammala miƙa mata sunayen ƴan takarar da suka tsaida kafin nan da ranar 31 ga watan da muke na Mayu, duk kuwa da tanadin dokar zaɓen ƙasar da ta sahalewa jam'iyyun kaiwa har nan da watan Satumba gabanin miƙa sunayen. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawar Abdoulkarim Ibrahim Shikal da masanin doka a Najeriya Barista El-zubair Abubakar kan wannan hukunci....

A wannan Alhamis 21 ga watan Mayu, Sashin Hausa na Radio France International RFI ke cika shekaru 19 da kafuwa, bayan fara yaɗa shirye-shiryensa a shekarar 2007, kuma dangane da wanna rana Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Umar Pate, ɗaya daga cikin masanan da ke bibiyar ayyukan wannan kafa a Najeriya.

Gwamnan jahar Borno Babagana Umara Zullum ya ce, gwamnati da jami'an tsaro na ƙoƙarin ceto daliban makaranta da aka sace a makarantar firamare a ƙauyen Mussa dake ƙaramar Hukumar Askira- Uba. Gwamna Zulum ya bayyana haka ne ya yin wata ziyarar jaje da ya kai Askira Uba dangane da iftila'in da ake dangantawa da Boko Haram. Ziyarar na zuwa ne yayin da aka shiga kwanaki na 5 da sace daliban ciki harda kanan yara. Shugabar kula da ilimi na ƙaramar Hukumar Askira-Uba, Hajiya Fatsuma Adamu Askira ta bayyana mana halin da ake ciki, a tattaunawarta da Ahmad Abba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta fara babban taronta karo na 79 jiya Litinin a birnin Geneva, wanda kuma za a ƙarƙare shi a ranar 23 ga watan Mayu da muke. Daga cikin muhimman batututwan da taron zai fi mayar da hankali a kai dai akwai giɓin kasafin kuɗin da ya kai Dala Biliyan 1 da Hukumar Lafiyar ta Duniya ke fuskanta, da kuma tasirin janyewa daga cikinta da Amurka ta yi. Kan wannan da kuma sauran batutuwa masu alaƙa, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Nasiru Sani Gwarzo, ƙwrarre kan sha'anin lafiya da ke Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

Yanzu haka na ci gaba da bayyana ra'ayoyi dangane da sanarwar da Amurka ta fitar da ke cewa ta kashe Abu Bilal Al-Minuki da ke matsayin jagora a ƙungiyar IS a Najeriya, labarin daga bisani hukumomin tsaron Najeriya suka tabbatar. To domin jin ƙarin bayani a game da wannan ɗan taliki da ake cewa an kashe, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Kabiru Adamu na Cibiyar da ke nazari kan sha'anin tsaro ta Beacon da ke Abuja, ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar...............

A zantawarsa da Radio France Internationale, da France 24 da kuma TV5 Monde a ƙarshen taron Afrika da Faransa da aka kammala birnin Nairobi na ƙasar Kenya, Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana matsayinsa a game da taɓarɓarewar sha'anin tsaro a Mali da kuma alaƙar Faransa da sauran ƙasashen Afirka ta fannin tsaro da aikin soji. To amma da farko shugaban ya fara amsa wata tambaya ce dangane da dalilan da suka sa Faransa ke ci gaba da taka rawa a wajen tafiyar da takardar kuɗin CFA. Ga dai tattaunawar. Latsa alamar sauti domin sauraren zanatawar.

A ranar Talata ne ake kammala taron shugabannin ƙasashen Afirka da Faransa da ya gudana a birnin Nairobi ta ƙasar Kenya, wanda ya mayar da hankali kan hanyoyin ci gaban tattalin arziki da noma da samar da abinci ga jama'ar nahiyar. Yaƙin Iran na ɗaya daga cikin abubuwan da ake ganin na maida hannun agogo baya wajen magance ƙarancin abinci, musamman rufe mahsigin Hormuz da ake amfani da ita wajen safarar takin zamani. Kan haka ne Nura Ado Suleiman ya zanta da ministan noman Najeriya Sanata Abubakar Kyari a wurin wannan taro, inda kuma ya ce su na ƙoƙarin magance matsalar. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

A jiya ne ake faro taron kwanaki biyu tsakanin Faransa da ƙasashen Afrika a birnin Nairobi, wanda shugaba Emmanuel Macron da takwaransa William Ruto ke jagoranta. Taron ya haɗa shugabannin ƙasashen Afrika, da Hamshaƙan ƴan Kasuwa, da sauran masu ruwa da tsaki domin tattaunawa kan nemawa nahiyar Afrika mafita wajen samun ci gaban Tattalin Arziƙi a fannonin da suka haɗa da, bunƙasa Masana'antu da Kimiyya da Fasaha da inganta Noma da Tsarin Kiwon Lafiya, da kuma samun wadatar makamashi. Danna alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar Nura Ado Suleiman da hadimin shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu Daniel Bwala.......

A ranar asabar da ta gabata ne, wasu masu fafufutuka da suka haɗa da ƴan siyasa, fararen hula, masana dokoki da dai sauransu da ke zaune a ƙetare, suka ƙaddamar da wani ƙawance da ake kira da suna ADS, (Alliance des Domocrates du Sahel) wanda babbar manufarsa ita ce sake dawo da tsarin dimokuraɗiyya a ƙasashen yankin Sahel da yanzu haka ke ƙarƙashin mulkin soji da suka hada da Burkina Faso, Mali da kuma Nijar. An dai ƙaddamar da wannan ƙawance ne a birnin Brussels na ƙasar Belgium, inda daga bisani Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Sakataren Yaɗa Labarai na ADS Boubacar Ɗan Zourmani, wanda ya yi masa ƙarin bayani a game da manufofinsu. Ga dai ƙarin bayaninsa.

Kotu a Najeriya yau ta ci gaba da sauraron shari'ar neman hana tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan tsayawa takarar zabe mai zuwa, kwana guda bayan wasu tarin magoya bayan sa sun bukaci ya shiga zaben mai zuwa. Dangane da matsayin dokar zabe a kan takarar ta Jonathan masanin shari'a, Farfesa Shehu Abdullahi Zuru na Jami'ar Baze dake Abuja, ya mana tsokaci a kai yayin zantawarsa da Bashir Ibrahim Idris. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...

Wasu daga cikin Ƴan Majalisun Dattawan Najeriya sun buƙaci ɗaukar matakai maus tsauri a kan Afirka ta Kudu, ciki harda kwace lasisin kamfanonin su na MTN da DSTV saboda yadda ake kai wa ƴan ƙasar hari ake kuma kashe su. Majalisar ta yanke hukuncin tura tawaga Afirka ta Kudu domin tattaunawa da hukumomin ƙasar, yayin da shi ma bangaren gwamnati ya tura ministan harkokin waje. Ambasada Ibrahim Kazaure, tsohon Jakadan Najeriya a Saudi Arabia ya yi tsokaci a kai, a tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris.

Kamfanin mai na NNPC ya sanya hannu kan wata yarjejeniya da wasu kamfanonin ƙasar China guda biyu, Sanjiang Chemical Company Limited da kuma Fuzhou Industrial Park, domin farfaɗo da matatun mai na Warri da Port Harcourt. Wannan mataki ya zo ne bayan matatun man sun laƙume kimanin biliyan 3.2 na dala ba tare da an samu biyan buƙata ba. Injiniya Kailani Muhammad, tsohon babban jami'in kamfanin na NNPC ne, a tattaunawarsa da Shamsiyya Haruna, ya bayyana gamsuwa da wannan yarjejeniya da kasar China bisa wasu dalilai. Ku latsa alamaru sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa za ta fara kwashe ƴan ƙasarta da ke son komawa gida daga Afirka ta Kudu, matakin da ta ce ya zama dole saboda tsananin kyamar baƙi da kuma rahoton mutuwar wasu ƴan Najeriya biyu sakamakon hare-haren da ake kai wa ƴan cirani. Akalla 'yan Najeriya 130 ne suka riga suka yi rajista don neman a kwashe su zuwa gida, sakamakon fargabar makomarsu na rashin tabbas. Dakta Rakiya Sa'idu daga jami'ar Capetown, ta bayyana mana yadda ƴan siyasa ke amfani da lokacin zaɓe wajen rura wutar wannan matsala. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawar da Shamsiyya Haruna ta yi da ita............

Kamar dai kowace shekara, 3 ga watan Mayu ita ce ranar kare ƴancin aikin yaɗa labarai a duniya, inda rahotannin da ƙungiyoyin da ke fafutuka a wannan fage ke nuni da cewa an samu gagarumin koma-baya ta fannin aikin jarida a cikin shekarar da ta gabata. Dangane da wannan rana, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon shugaban ƙungiyar Ƴan Jarida ta Najeriya (NUJ) Honnorable Alhaji Muhammed Sani Zoro, wanda da farko ya fara yin tsokaci a game da irin sauye-sauyen da aka samu a aikin jarida saboda dalilai masu nasaba da zamani. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.