Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Follow Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Share on
Copy link to clipboard

Shiri ne na musamman, da kan tattaunawa da bangarori daban-daban na Al’umma da ke sauraren Shirye shiryen RFI Hausa daga kowane kusurwa na fadin duniya, kan muhimman batutuwa, da suka shafi siyasa Tattalin’ariziki, al’adu da dai sauransu…

Rfi - Salissou Hamissou


    • May 20, 2025 LATEST EPISODE
    • weekdays NEW EPISODES
    • 13m AVG DURATION
    • 318 EPISODES


    Search for episodes from Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare with a specific topic:

    Latest episodes from Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

    Ra'ayoyin masu saurare kan bikin cika shekara 53 da haɗewar Kamaru

    Play Episode Listen Later May 20, 2025 10:30


    A wannan talata, al'ummar Kamaru na bikin cika shekaru 53 da haɗewar yankunan da ke amfani da Faransanci da masu amfani da harshen Ingilishi, waɗanda kafin nan suna zaune da juna ne a ƙarƙashin tsarin tarayya. To sai dai a daidai yayin da ake wannan biki, yanzu haka akwai masu gwagwarmaya da makamai don samar wa yankunan da ke turancin Ingilishi ƴanci.Shin ko me za ku ce a game da wannan haɗewa?Ko waɗanne matakai ku ke ganin cewa sun dace a ɗauka domin dawo da yarda a tsakanin bangarorin biyu?Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a

    Ra'ayoyi kan matakin Ghana na kama masu bace-barace

    Play Episode Listen Later May 19, 2025 10:08


    Matsalar barace-barace a kan titunan manyan birane a Yammavin Afirka sai daɗa yin ƙamari take, to sai dai bisa ga dukan alamu mahukunta a ƙasar Ghana sun ƙuduri aniyar kawo ƙarshen wannan ɗabi'a. Domin a cikin makon jiya, jami'an tsaro sun cafke mabarata sama da dubu biyu a birnin Accra kawai, kuma yawancinsu ƴan asalin ƙasashen Najeriya, Nijar, Burkina Faso da Mali ne.Shin ko akwai dalilan da za su sa jama'a su mayar da bara a matsayin sana'a?Ko waɗanne matakai ya kamata a ɗauka domin kawo ƙarshen wannan ɗabi'a ta bara?Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a.

    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta

    Play Episode Listen Later May 16, 2025 10:23


    A duk ranar Juma'a, RFI Hausa na bai wa jama'a damar tofa albarkacin bakinsu kan abubuwan da ke ci musu tuwo a kwarya kama daga siyasa, tattalin arziki, zamantakewa, harkokin yau da kullum da dai saurarensu. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin tare da Shamsiyya Haruna...

    Ra'ayoyin masu sauraro kan matakin Nijar na hana fitar da dabbobi zuwa ƙetare

    Play Episode Listen Later May 15, 2025 10:24


    Makonni kaɗan gabanin bukukuwan Sallar Layyah, mahukuntan jamhuriyar Nijar sun bayar da umurnin hana fitar da dabbobi zuwa ƙetare. Ga alama dai an ɗauki matakin ne don hana tashin farashin dabbobi a wannan lokaci, yayin da wasu ke cewa matakin zai iya cutar da tattalin arzikin ƙasar.Abin tambayar shine, menene amfani ko kuma illar wannan mataki ga ƙasar?Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.

    Ra'ayoyin Masu Saurare kan yadda ƴanbindiga suka tsananta kai hare-hare

    Play Episode Listen Later May 14, 2025 9:49


    Hare-haren ƴanbindiga na ci gaba da ɗaukar sabon salo a Najeriya, inda a baya-bayan nan suka tsananta kai farmaki hatta akan sansanonin soji, kusan a iya cewa haka take a sauran yankin sahel musamman Burkina Faso, lamarin da kanyi sanadin mutuwar jami'an tsaro masu tarin yawa.  Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a kan wannan maudu'in.......

    Ra'ayoyi kan kula da lafiyar kwakwaluwa

    Play Episode Listen Later May 13, 2025 10:28


    Shin ko kun san muhimmancin kula da lafiyar ƙwaƙwalwa kuwa? Wannan tambaya ce mai matuƙar muhimmanci, lura da cewa yanzu haka akwai ɗimɓin mutane da ke fama da wannan matsala a sassan duniya. Yayin da wasu ke kira wannan lalura a matsayin hauka, masana kuwa na cewa hatta shiga yanayi na damuwa ko da ƙuncin rayuwa na iya haddasa wannan matsalar.Shin ko wace irin kulawa ku ke bai wa lafiyar ƙwaƙwalwa?Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a.

    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta

    Play Episode Listen Later May 9, 2025 10:12


    A duk ranar Juma'a, RFI Hausa na bai wa jama'a damar tofa albarkacin bakinsu kan abubuwan da ke ci musu tuwo a kwarya kama daga siyasa, tattalin arziki, zamantakewa, harkokin yau da kullum da dai saurarensu. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin tare da Shamsiyya Haruna...

    juma masu najeriya
    Ra'ayoyin Masu Saurare kan ficewar Meta daga Najeriya

    Play Episode Listen Later May 5, 2025 9:34


    Kamfanin Meta da ya mallaki Facebook, Instagram da Whatsapp ya yi barazanar ficewa daga Najeriya bayan da aka lafta masa biyan tarar dala miliyan 290 saboda karya ƙa'ida. To sai dai gwamnatin Najeriya ta ce ko da kamfanin ya janeye daga ƙasar, to dole ne sai ya biya wannan tarar. Za mu so jin ra'ayoyinku a game da wannan takun-saka tsakanin Najeriya da kuma wannan shahrarran kamfani na sadarwa. Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a.

    Ra'ayin jama'a kan batutuwan da ke ci musu tuwo a kwarya

    Play Episode Listen Later May 2, 2025 9:31


    Shirin ra'ayoyin masu saurare na wannan rana ta Juma'a bisa al'ada ya kan baiwa masu saurare damar fadin albarkacin bakinsu kan batutuwan da ke ci musu tuwo a kwarya. Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Shamsiyya Haruna

    Ra'ayoyin masu sauraro kan bikin ranar ma'aikata a sassan duniya

    Play Episode Listen Later May 1, 2025 8:55


    Kamar dai kowace shekara, yau 1 ga watan Mayu, ita ce Ranar Ma'aikata ta Duniya, bikin da a bana ana iya cewa ana gudanar da shi ne a cikin wani yanayi na tsadar rayuwa a mafi yawan ƙasashen duniya. Abin tambayar shine, shin ko a cikin wanne yanayi ake gudanar da bukukuwan na bana, musamman a kasashen Afirka?Waɗanne irin manyan buƙatu ma'akata suke son cimma wa?Shiga alamar sauti, diomin sauraron ciakken shirin.

    Ra'ayoyi masu saurare kan alakar Morocco da ƙasashen AES

    Play Episode Listen Later Apr 30, 2025 9:33


    Bisa ga dukan alamu Maroko na ƙara samun kusanci da ƙasashen Burkina Faso, Mali da kuma Jamhuriyar Nijar a daidai lokacin da alaƙa ke ƙara yin tsami tsakanin waɗannan kaasashen da Aljeriya. Ministocin Harkokin Wajen ƙasashen uku sun ziyarci Maroko tare da ƙulla yarjejeniyar da ke ba su damar yin amfani da tashoshin ruwa ƙasar, alhali ba ɗaya daga cikinsu da ke da iyaka da Marokon.Ko yaya ku ke kallon wannan alaƙa tsakanin Maroko da AES, yayin da suka juya wa makociyarsu Aljeriya baya?Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a.

    Yadda ake zargin gwamnatin Najeriya da shaƙe wuya ƴan adawa

    Play Episode Listen Later Apr 29, 2025 10:00


    Shirin ra'ayoyin ku masu saurare na wannan rana ya mayar da hankali ne kan yadda wasu fitattun mutane mambobin kungiyar farar hula a Najeriya suka nuna takaicinsu kan yadda gwamnatin mai ci ke neman mayar da kasar tsarin jam'iyya daya. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Oumarou Sani

    Ra'ayoyin masu sauraren shirye-shiryen RFI

    Play Episode Listen Later Apr 25, 2025 10:07


    A duk ranar Juma'a, RFI Hausa na bai wa jama'a damar tofa albarkacin bakinsu kan abubuwan da ke ci musu tuwo a kwarya kama daga siyasa, tattalin arziki, zamantakewa, harkokin yau da kullum da dai saurarensu. Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a.

    Ra'ayoyin masu saurare kan rigakadin cutar Polio a Najeriya

    Play Episode Listen Later Apr 24, 2025 9:49


    Yayin da a yau aka ƙaddamar da makon rigakafi a duniya, Hukumomi a Najeriya da kuma Unicef, sun yi gargaɗin cewa yanzu haka nau'ukan cutar shan'inna har guda 17 da suka yaɗu a cikin jihohi 8 na ƙasar. Wannan dai babban ƙalubale ne ga sha'anin kiwon lafiya, bayan da aka shelanta kawo ƙarshen cutar tun 2020.Shin ko meye dalilan sake ɓullar wannan cuta a Najeriya?Waɗanne matakai ya kamata a ɗauka domin shawo kanta?Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin masu saurare.

    Halin da wasu ƴan Najeriya suka shiga bayan da kamfanin CBEX ya tsere da kudadensu

    Play Episode Listen Later Apr 17, 2025 9:27


    Shirin ra'ayoyin masu saurare na wannan mako ya mayar da hankali ne kan yadda wani kamfanin hada-hadar kudi ta Internet a Najeriya mai suna CBEX ya tsere da kudaden jama'a. Danna alamar sauarre domin jin cikakken shirin tare da Nasiru Sani

    Yadda ƴan Najeriya suka shiga halin fargaba a game da yiwuwar ambaliyar ruwa a jihohi 30

    Play Episode Listen Later Apr 16, 2025 10:01


    Shirin ra'ayoyin masu saurare na wannan mako ya mayar da hankali ne kan gargaɗin gwamnatin Najeriya na yiwuwar samun ambaliyar ruwa a jihohi 30 a daminar bana. Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Abida Shu'aibu.

    Gagarin da ilimin yara mata ya shiga sakamakon ta'addanci a Najeriya

    Play Episode Listen Later Apr 15, 2025 10:54


    Shirin ra'ayoyin masu saurare na wannan rana ya mayar da hankali ne kan yadda kungiyoyin ta'addanci ke kawowa ilimin yara mata tsaiko a Najeriya. Danna alamar sauarre don jin cikakken shirin tare da Nasiru Sani.

    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwan da ke ci musu tuwo a ƙwarya

    Play Episode Listen Later Mar 14, 2025 10:13


    Yau ta ke ranar jin ra'ayoyin ku masu saurare kan batutuwan da ke ci muku tuwo a ƙwarya, kama daga fannin siyasa, ilimi, lafiya, tattalin arziƙi da dai sauransu. Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi...

    Kan yadda EFCC ta kwato Naira tiriliyan guda daga hannun ɓarayin gwamnati

    Play Episode Listen Later Mar 11, 2025 9:54


    Hukumar Yaƙi da Rashawa a Najeriya EFCC, ta ce a cikin shekarar ta 2024 da ta gabata, ta yi nasarar ƙwato kusan Naira tiriliyan ɗaya daga hannun barayi da masu handame dukiyar al'umma. EFCC ta ce ko a gaban kotu ma, ta samu nasarori sama da sau dubu huɗu akan masu cin rashawa da kuma ƴan damfara cikin shekarar da ta gabata.Abin tambayar shine, ko aikin hukumar na gamsar da 'yan Najeriya?Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakakken shirin.

    Kan yadda direbobin manyan motoci ke fuskantar kisa daga 'yan awaren Biafara

    Play Episode Listen Later Mar 4, 2025 10:26


    Ƙungiyar direbobin motoci a Najeriya, ta buƙaci mahukunta su ɗauki matakan kawo ƙarshen kisan da ƴan awaren Biafra ke yi wa direbobin manyan motoci a duk lokacin da suke ratsa yankin kudu maso gabashin ƙasar. Ƙungiyar ta ce an kashe mambobinta sama da 50, kuma 20 daga cikinsu an kashe su ne a shekarar 2024, sannan aka kwashe kayayyaki da kuma ƙona motocinsu.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.

    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwan da ke ci muku tuwo a ƙwarya

    Play Episode Listen Later Feb 28, 2025 10:18


    A yau Juma'a kamar yadda aka saba, masu sauraro ko kuma bibiyarmu a shafukan sada zumunta, kan aiko da saƙonnin ra'ayoyi kan batutuwa da dama, kama daga wanda ke ci musu tuwo a ƙwarya a fannoni daban-daban na rayuwa, da kuma fannin tattalin arziki, da tsaro, da lafiya, da siyasa da sauransu.

    Ra'ayoyin masu saurare kan yawaitar masu ta'ammali da ƙwayoyi a Arewacin Najeriya

    Play Episode Listen Later Feb 27, 2025 10:24


    Aƙalla 40% na mazauna yankin arewa maso yammacin Najeriya ne ka tu'ammuli da miyagun ƙwayoyi, kuma kusan 28 cikin ɗari suna zaune ne a jihar Kaduna kamar dai yadda rahoton hukumomin da yaƙi da wannan matsala ya nuna.  Hakazalika, mutum 1 cikin 7 a yankin arewa maso yammacin ƙasar suna tu'ammali da miyagun ƙwayoyin a cewar rahoton.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin...

    kaduna masu najeriya
    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbata

    Play Episode Listen Later Feb 21, 2025 9:47


    A yau Juma'a kamar yadda aka saba, masu sauraro ko kuma bibiyarmu a shafukan sada zumunta, kan aiko da saƙonnin ra'ayoyi kan batutuwa da dama, kama daga wanda ke ci musu tuwo a ƙwarya a fannoni daban-daban na rayuwa, da kuma fannin tattalin arziki, da tsaro, da lafiya, da siyasa da sauransu. Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin...

    Ra'ayoyin masu saurare kan tarar da za a ci masu satar lantarki a Najeriya

    Play Episode Listen Later Feb 20, 2025 9:36


    Hukumar Ƙayyade Farashin Wutatar Lantarki a Najeriya, sanar da sabon tsarin biyan tara a kan waɗanda ke satar makamashin lantarki a ƙasar. Tarar ta kama daga Naira dubu 100 zuwa dubu 300 daidai da irin salon da mutum ya yi wajen sada gidansa da wannan makamashi.

    naira masu najeriya hukumar
    Ra'ayoyin masu saurare kan saukar farashin kayan abinci a Najeriya

    Play Episode Listen Later Feb 19, 2025 9:54


    Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa a Najeriya, ta ce farashin kayan abinci ya sauka a cikin watan Janairun da ya gabata da 10% idan aka kwatanta da na wata Disamba. To waɗannan dai bayanai da hukuma ta fitar, saboda haka za mu so jin ra'ayoyinku a game da wannan rahoto.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin tare da Abida Shu'abu Baraza...

    kayan masu baraza najeriya hukumar
    Ra'ayoyin masu saurare kan kashe maƙudan kuɗaɗe don inganta lantarki a Najeriya

    Play Episode Listen Later Feb 18, 2025 10:39


    Alƙalumma na nuni da cewa a cikin shekaru 10 da suka gabata, an kashe aƙalla Naira Tiriliyan 7 da bilyan 200 a matsayin tallafi da nufin inganta sanar da wutar lantarki a Najeriya. To sai dai a zahirin ana cewa har yanzu wannan ɓangare na ci gaba fama da matsaloli masu tarin yawa, yayin da a ɗaya ɓangare farashin wutar ya ninka ninkin ba ninkin.

    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta

    Play Episode Listen Later Feb 7, 2025 11:09


    A yau Juma'a kamar yadda aka saba, masu sauraro ko kuma bibiyarmu a shafukan sada zumunta, kan aiko da saƙonnin ra'ayoyi kan batutuwa da dama, kama daga wanda ke ci musu tuwo a ƙwarya a fannoni daban-daban na rayuwa, da kuma fannin tattalin arziki, da tsaro, da lafiya, da siyasa da sauransu. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi mabanbanta...

    Shirin ra'ayoyin ku masu sauraro a yau.

    Play Episode Listen Later Feb 3, 2025 9:49


    a yau shirin namu na ra'ayoyin ku masu sauraro ya yi dubu ne akan Shin ko menene ra'ayin ku a game da batun tattaunawa da 'yan bindiga.

    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta

    Play Episode Listen Later Jan 31, 2025 9:36


    A yau juma'a kamar yadda aka saba kuna aiko mana da saƙonnin ra'ayoyinku kan abubuwan da ke ci muku tuwo a ƙwarya a fannoni daban-daban na rayuwa, kama daga fannin tattalin arziki, tsaro, lafiya, siyasa da sauransu. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi mabanbanta...

    masu najeriya
    Ra'ayoyin masu saurare kan shirin samar da lantarki ga gidaje 300M a Afirka

    Play Episode Listen Later Jan 30, 2025 9:36


    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sake jaddada aniyarsa ta inganta samar da wutar lantarki a faɗin ƙasar. Tinubu ya bayyana haka ne wajen taron ƙasashen Afirka wanda ya mayar da hankali akan yadda za a samar wa aƙalla mutane miliyan 300 wutar lantarki a nahiyar baki ɗaya. Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin...

    Ra'ayoyin masu saurare kan cikar wa'adin ficewar ƙasashen AES daga ECOWAS

    Play Episode Listen Later Jan 29, 2025 9:42


    Yau 29 ga watan Janairu wa'adin farko da kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso suka bayar na ficewa daga kungiyar ECOWAS ya cika, abinda ke tabbatar da raba garin bangarorin biyu dangane da cikar wannan wa'adi, Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi...

    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta

    Play Episode Listen Later Jan 24, 2025 10:23


    A yau juma'a kamar yadda aka saba kuna aiko mana da saƙonnin ra'ayoyinku kan abubuwan da ke ci muku tuwo a ƙwarya a fannoni daban-daban na rayuwa, kama daga fannin tattalin arziki, tsaro, lafiya, siyasa da sauransu. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi mabanbanta...

    masu nijar najeriya
    Yadda aka fara samun saukin farashin kayayyakin abinci a Najeriya

    Play Episode Listen Later Jan 23, 2025 10:05


    Rahotanni daga wasu sassan Najeriya ciki har da babbar kasuwar kayan abinci dangin hatsi ta Dawanau da ke Kano na cewa an fara samun sauƙin farashin kayayyakin abincin, idan aka kwatanta da yadda al'amarin yake a watannin baya. Lamarin dai ya haifar da muhawara akan dalillan da suka janyo saukin farashin kayana abincin da ɗorewar hakan.Abin tambayar shine, ko al'umma sun gamsu da wannan rahoto, ko kuma har yanzu anan nan a gidan jiya?Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.

    Ra'ayoyin masu saurare kan ficewar Amurka daga WHO

    Play Episode Listen Later Jan 22, 2025 9:41


    A ƙasar Amurka, bayan rantsar da shi a matsayin sabon shugaba ƙasa na 47, Donald Trump, ya rattaba hannu kan wasu gomman dokokin zartawa na ikon shugaban ƙasa, ciki har da janye ƙasarsa daga Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), kamar yadda ya yi a wa'adin mulkinsa na farko, kafin magabacinsa Joe Biden ya maido da ƙasar ciki. Wasu na ganin wannan mataki zai yi illa ƙwarai ga ɗorewar hukumar wajen gudanar da ayyukan ta a duniya, duba da kaso mai tsoka da Amurka ke bayarwa wajen gudanar da ayyukan WHO ɗin.Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi...

    Ra'ayoyin masu saurare kan sabuwar dokar Nijar na hukunta baƙi marasa takardu

    Play Episode Listen Later Jan 15, 2025 9:23


    A wannan makon ne gwamnatin sojin Nijar ta gabatar da wata sabuwar doka da ke tilastawa baƙi da ke neman zuwa ƙasar da su tabbatar sun samu takardun izini da suka dace, tare da gargadi ga su ma ƴan ƙasar da su yi hattara wajen ƙarbar baƙunci baƙi da ke shiga ƙasar ba bisa ƙa'ida ba. Sabuwar dokar ta soji ta tanadi hukunci mai tsauri ga waɗanda suka saɓa umarnin a bangarorin baƙi da su kansu ƴan ƙasar, wanda ya ƙunshi hukuncin ɗauri a gidan yari da kuma tara.Gwamnati da wasu ƴan ƙasar na cewa anyi hakan ne saboda dalilai na tsaro, yayin da wasu ke danganta hakan da tsoro da fargaba, to ku ya kuka kalli wannan mataki?Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin.....

    Ra'ayoyin masu saurare kan hare-haren soji da ke kashe fararen hula bisa kuskure

    Play Episode Listen Later Jan 14, 2025 10:06


    A baya-bayan hare-haren sojojin Najeriya kan ƴan ta'adda na shafar fararen hula musamman ƴan sa kai da ke taimakawa wajen yaƙar matsalolin tsaro. Matsalar na ƙara yawaita inda a kwanan nan sojojin suka kai hari a jihohin Sokoto da Zamfara wanda ya halaka fararen hula fiye da 100, yayin da a kowane lokaci sojojin kan musanta hakan , daga baya kuma su ce za su gudanar da bincike.Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi...

    Ra'ayoyin masu saurare kan sallamar tuɓaɓɓun ƴan Boko Haram da aka yi a Nijar

    Play Episode Listen Later Jan 13, 2025 9:40


    A wani yanayi da ba safai aka saba gani ba, mahukuntan Nijar sun sallami tuɓaɓɓun mayaƙan Boko Haram aƙalla 124 ciki har da ƙananan yara 44, waɗanda aka basu horan sauya ɗabi'u don komawa rayuwar fararen hula. Wannan shi ne karon farko da ake ganin irin hakan, tun bayan makamancin yunƙurin da hamɓararren shugaban ƙasar Bazoum Muhammad ya yi watanni ƙalilan gabanin hamɓarar da shi.Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi a cikin shirin...

    Yadda ake rige-rigen neman aiki a hukumar kwastam da ke Najeriya

    Play Episode Listen Later Jan 9, 2025 10:21


    Kamar yadda labari ya karaɗe kafafen yada labarai, ƙaasa da mako guda bayan da hukumar kwastan a Najeriya ta sanar da buɗe shafin yanar gizo don aikewa da takardun neman ɗaukar jami'ai kimanin dubu 4, sama da masu neman wannan aiki dubu dari 5 ne suka gabatar da buƙatunsu. Wannan al'amari ne da ke faruwa a kowace ma'aikata a duk lokacin da aka sanar da buƙatar ɗaukar ma'aikata.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Abida Shu'aibu Baraza.

    Kan yadda aka gudanar da bikin rantsuwar sabon shugaban Ghana

    Play Episode Listen Later Jan 8, 2025 9:53


    A wannan talatar ce aka rantsar da John Mahama a matsayin shugaban Ghana, cikin yanayi na tarin kalubale da suka hada da na matsin tattalin arziki biyo bayan lashe zaben da aka yi cikin kwanciyan hankali da lumana. Masu bibiyar siyasa a kasar sunyi ittifakin cewa duk da cewa Mahaman ya taba jagorancin kasar, ya dawo ne a lokacin da lamura suka sauya ainun.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Abida Shu'aibu Baraza.

    Kan yadda duniya ta yi bankwana da shekarar 2024

    Play Episode Listen Later Dec 31, 2024 10:29


    A yayin da ake bankwana da shekarar 2024 shuwagabanni daga kasashen Duniya na fuskantar tarin kalubale da suka hada da rikice-rikice,yake-yake harma da wasu matsalolin da suka shafi sauyin yanayi da matsin tattalin Arziki da sauran su. Wasu abubuwa ne baza ku iya mantawa  ba kuke tsoron dakon su zuwa sabuwar shekara?Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin, tare da Hauwa Garba Aliyu Zaria.

    duniya yadda shiga wasu najeriya amurka
    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta

    Play Episode Listen Later Dec 27, 2024 9:18


    A yau juma'a kamar yadda aka saba kuna aiko mana da saƙonnin ra'ayoyinku kan abubuwan da ke ci muku tuwo a ƙwarya a fannoni daban-daban na rayuwa, kama daga fannin tattalin arziki, tsaro, lafiya, siyasa da sauransu. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi mabanbanta...

    Ra'ayoyin masu saurare: harin soji kan Lakurawa ya hallaka mutane fiye da 10

    Play Episode Listen Later Dec 26, 2024 9:30


    Ana fargabar al'umma da dama sun mutu wasu kuma sun jikkata sakamakon wani hari da jirgin yaƙi na soji ya kai kan Lakurawa a wasu ƙauyuka da ke Sokoton Najeriya. Ana kallon wannan harin a matsayin na kuskure kuma ba wannan ne karon farko da hakan ke faruwa ba a arewaci da wasu Najeriya.Latsa alamar sauti domin sauraren mababanta ra'ayoyi a cikin shirin da Abida Shu'aibu Baraza ta jagoranta...

    Ra'ayoyin masu saurare kan rasa rayuka da aka yi yayin turmutsitsi a Najeriya

    Play Episode Listen Later Dec 23, 2024 10:47


    Aƙalla mutane 60 suka rasa rayukansu a sassan Najeriya, yayin turmutsitsin karɓar tallafin abinci da kuma taron bikin ƙarshen shekara na yara a jihohin Anambra, da Oyo da kuma birnin Abuja. A yayin da ‘yan Najeriyar ke tofa albarkacinsu kan lamarin wasu na ɗora laifin aukuwar haɗurran akan gazawar mahukunta wajen samar da tsarin bai wa mutane kariya yayin taruka, yayin da wasu ke ganin ɗaiɗaikun masu raba tallafin ke da alhaki la'akari da cewar suna yin hakan ne ba tare da tsari ko sanin hukuma ba.Wannna shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin...

    Ra'ayoyin masu saurare kan kasafin kuɗin 2025 da shugaban Najeriya ya gabatar

    Play Episode Listen Later Dec 19, 2024 11:39


    A ranar Laraba ne shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatar da kasafin kudin ƙasar na shekarar 2025 na naira Tiriliyan 47.9. Sai dai wani batu da ya haifar da muhawara a tsakanin ‘yan Najeriya dangane da kasafin kuɗin na baɗi, shi ne yadda aƙalla kaso 30 zuwa 32 na yawan kuɗaɗen za su tafi a biyan basuka ko kuma kudin ruwan basukan, kwatankwacin naira tiriliyan 15 da biliyan 800, adadin da ya zarce yawan kudaden da aka warewa tsaro, ilimi, lafiya da manyan ayyuka.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin tare da Kabiru Mohammed Dan Bauchi...

    Ra'ayoyin masu sauraren Rfi biyo bayan lashe kyautar gwarzon ɗan wasan Afrika na 2024 daga Lookman

    Play Episode Listen Later Dec 17, 2024 10:23


    A bikin da aka gudanar a birnin Marrakech na Morocco, Lookman ya shiga gaban ƴan wasan irinsu Simon Adingra na Ivory Coast da Achraf Hakimi na Morocco da Serhou Guirassy na Guinea sai kuma mai tsaron gidan Afrika ta Kudu Ronwen Williams.Tauraruwar Lookman wanda ke wasa a ƙungiyar Atalanta na haskawa a bana, musamman idan aka yi la'akari da bajintar da ya nuna wajen zamowa ɗan wasa na farko tun daga shekarar 1975 da ya zura kwallaye uku a raga cikin mintina 26.Masu saurare sun bayyana fatan da suke da shi a cikin wannan shiri..........

    Ra'ayoyin masu saurare kan shirin maja tsakanin Atiku da Obi a zaɓen 2027

    Play Episode Listen Later Dec 12, 2024 10:22


    Tsohon mataimakain shugaban Najeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a zaben 2023 da ya gabata Atiku Abubakar da kuma ɗan takarar LP a 2023 Peter Obi na shirin haɗewa domin kawar da gwamnatin APC wadda a cewarsu ta gaza, lamarin da ke zuwa tun kafin kakar zaɓen na shekarar 2027. Sai dai a martaninta, jam'iyyar APC ta ce babu wata haɗaka da za ta iya taka wa shugaba mai ci birki.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin...

    Ra'ayoyin masu saurare kan haramcin fitar da masara daga Najeriya

    Play Episode Listen Later Dec 11, 2024 10:30


    Kamar yadda aka saba, RFI Hausa na bai wa masu saurare damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwa da dama da ke ci musu tuwo a ƙwarya. Majalisar dattawar Najeriya ta amince da wani kuɗirin doka da ya haramta fitar da duk wata masara mai yawa da ba'a sarrafa ta ba daga ƙasar zuwa ƙasashen waje, kuma ta tanadi hukuncin ɗaurin shekara guda ga duk wanda ya yi kunnen ƙashi.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau.Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyin mabanbanta..

    kamar daga masu wannan najeriya majalisar
    Ra'ayoyin masu saurare kan kifar da gwamnatin Al-Assad na Syria

    Play Episode Listen Later Dec 10, 2024 9:12


    A ƙarshen makon da ya gabata ne ƴan tawaye suka kifar da gwamnatin shugaba Bashar al-Assad na Syria da zuri'arsa suka shafe shekaru 50 su na mulki a ƙasar. Rahotanni dai na cewa Al-Assad da iyalansa sun tsere daga ƙasar inda ake kyautata zaton cewa Rasha ta basu mafaka, lamarin da ƙasar Rashan ta musanta,  yayin da ƙasashen duniya ke tofa albarkacin bakinsu.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin tare da Hauwa Aliyu..

    Ra'ayoyin Masu Saurare kan zaɓen Ghana

    Play Episode Listen Later Dec 9, 2024 9:35


    Mataimakin shugaban ƙasa kuma ɗan takarar jam'iyya mai mulki a Ghana, Mahamudu Bawumia ya amince da shan kaye a zaɓen ƙasar, inda ya taya tsohon shugaban ƙasa John Mahama murnar lashe zaɓen. Wannan ya biyo bayan zaɓen shugaban ƙasar da aka yi a Asabar ɗin ƙarshen mako 7 ga watan Disamba, wanda rahotanni suka tabbatar da cewa ya gudana cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya.Shin ya ku ka kalli yadda zaɓen na Ghana ya gudana?Me za ku ce kan yadda Bawumia ya amince da shan kaye tun kafin a fitar da sakamakon zaɓen?Wane darasi ku ke ganin ƴan siyasa a yankunanku za su koya daga zaɓen Ghana?Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin

    Ra'ayoyin masu saurare kan caccakar tsarin zaɓen Kamaru

    Play Episode Listen Later Dec 6, 2024 9:34


    A Jamhuriyar Kamaru, wani babban limamin cocin Katolika a Duwala, Archbishop Samuel Kleda  ya caccaki tsarin zaben ƙasar, wanda ya ce an tsara shi ne don bai  wa shugaba mai ci damar ci gaba da yin kane-kane kan madafun iko, yana mai cewa akwai buƙatar gyara in dai dimokaradiyyar ake so. Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi...

    Ra'ayoyin masu sauraro kan kame mafi girma da EFCC ta yi a Najeriya

    Play Episode Listen Later Dec 4, 2024 9:42


    A Najeriya, kwanan nan ne kotu ta karbe wani rukuni mai ƙunshe da gidaje 753 mallakin wani tsohon gwamnan babban bankin ƙasar, nasara mafi girma da hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa ta'annati ta taɓa samu a cikin sama da shekaru 21 da kafuwarta. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin tare da Oumaru Sani:

    Claim Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

    In order to claim this podcast we'll send an email to with a verification link. Simply click the link and you will be able to edit tags, request a refresh, and other features to take control of your podcast page!

    Claim Cancel