Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Follow Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Share on
Copy link to clipboard

Shiri ne na musamman, da kan tattaunawa da bangarori daban-daban na Al’umma da ke sauraren Shirye shiryen RFI Hausa daga kowane kusurwa na fadin duniya, kan muhimman batutuwa, da suka shafi siyasa Tattalin’ariziki, al’adu da dai sauransu…

Rfi - Salissou Hamissou


    • Sep 30, 2025 LATEST EPISODE
    • weekdays NEW EPISODES
    • 12m AVG DURATION
    • 362 EPISODES


    Search for episodes from Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare with a specific topic:

    Latest episodes from Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

    Ra'ayoyin masu saurare game da dambarwar ƙungiyar PENGASSAN da Ɗangote

    Play Episode Listen Later Sep 30, 2025 9:56


    A Najeriya ana ci gaba da kai ruwa rana tsakanin matatar Dangote da kungiyar manyan ma'aikatan man fetur da iskar gas wato PENGASSAN. Tun daga lokacin da matatar Dangote ta fara aiki kawo yanzu, an samu takaddama irir-iri daga kungiyoyin da ke da alaka da man fetur da kuma iskar gas. Ko me yasa takun saka tsakanin Dangote da masu ruwa da tsaki a harkar mai, yaki ci yaki cinyewa? Me ku ke ganin ummul aba'isin wannan dambarwa da take bullowa daga kusurwa-kusurwa, wanda ake ganin zai haifar da tashin farashin mai a Najeriya? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai........ Ku latsa alamar sauti don sauraren ra'ayoyin na ku.....................

    Ra'ayoyin masu saurare game da yaƙin neman zaɓen Kamaru

    Play Episode Listen Later Sep 29, 2025 10:10


    An ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen shugabancin ƙasar Kamaru, inda mutane 12 ciki har da shugaba mai-ci Paul Biya za su kara da juna a ranar 12 ga watan gobe na Oktoba idan Allah ya kai mu. Yayin da Paul Biya ke fatan sake samun yardar al'umma don ci gaba da mulki karo 8, a nasu ɓangare kuwa 'yan adawa na kallon zaɓen a matsayin wata dama don samar da sauyi a ƙasar. Shin me za ku ce a game da wannan yaƙin neman zabe? Ko wane fata ku ke yi wa al'ummar Kamaru? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin....

    Ra'ayoyi kan shirin Amurka na hana ƴan Najeriya masu rashawa shiga ƙasar

    Play Episode Listen Later Sep 25, 2025 9:55


    Shirin Ra'ayoyin mai Saurare na wannan ranar Alhamis 25 ga watan Satumbar 2025, wanda Oumar Sani ya gabatar, ya tattauna ne kan matakin gwamnatin Amurka na hana duk wani ɗan Najeriya ciki har da jami'an gwamnati da aka samu da hannu da rashawa bisar da za ta ba su damar shiga ƙasar.

    shirin asar shiga masu najeriya amurka alhamis
    Ra'ayoyin masu saurare kan ficewar ƙasashen AES daga kotun ICC

    Play Episode Listen Later Sep 24, 2025 10:09


    Burkina Faso, Mali da kuma Nijar sun sanar da janyewa daga Kotun Hukunta Laifuka ta Duniya da ke birnin Hague, bisa zargin kotun da kasancewa ƴar amshin ƴan mulkin mallaka. To sai dai wasu na ganin cewa shugabannin ƙasashen uku sun ɗauki matakin ne don kauce wa bincike ko tuhuma daga wannan kotu. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacinku a yau cikin shirin na Ra'ayoyinku masu saurare. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

    Ra'ayoyin masu saurare kan ɗage haramcin shigar da siminti a Nijar

    Play Episode Listen Later Sep 22, 2025 10:38


    Gwamnatin Jamhuriya Nijar ta ɗage haramcin shigar da siminti a ƙasar, sakamakon yadda ake fama da ƙamfarsa, lamarin da ya haifar da tsadarsa a kasuwa. Wani lokaci a can baya ne dai mahukunta suka sanar da haramta shigar da simintin don kare kamfanonin da ke sarrafa shi a cikin gida, amma kuma aka wayi gari na cikin gidan sun gaza wadatar da masu buƙatar sa domin yin gini. Shin ko me za ku ce a game da cire haramcin? Wannan shine maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwan dake ci musu tuwo a ƙwarya

    Play Episode Listen Later Sep 19, 2025 10:49


    Yau juma'a, rana ce da sashen Hausa na RFI ke bai wa masu sauraro damar faɗin albarkacin bakinsu, kan batutuwan dake ci musu tuwo a ƙwarya, kama daga tattalin arziƙi, ilimi, lafiya, zamantakewa, siyasa da dai sauransu. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin tare Nasiru Sani...

    Ra'ayoyin masu saurare kan umarnin gwamnatin Neja na duba khuɗubobi kafin yaɗa su

    Play Episode Listen Later Sep 18, 2025 10:41


    A Najeriya, gwamnatin Neja ta umarci ilahirin limaman masallatan Juma'a a faɗin jihar da su riƙa miƙa mata bayanan da ke ƙunshe a cikin huɗubar da za su gabatar don tantancewa, matakin da Gwamna Muhammadu Umar Bago ke cewa yunƙuri ne na kaucewa duk wata barazana ta cusa ƙiyayya ko kuma haddasa rikici da malaman ka iya yi. Yaya kuke kallo wannan mataki na Gwamnan jihar Neja? Shin kuna ganin akwai buƙatar shigowar gwamnati don daidaita yadda malamai ke gudanar da khuɗubobi da sauran karatuttuka? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Ku latsa alamar sauti domin sauraren shirin....

    Ra'ayoyin masu saurare game da yadda ICPC ke sanya ido kan kuɗaɗen ƙananan hukumomi

    Play Episode Listen Later Sep 17, 2025 10:11


    Hukukumar Yaƙi da Rasha ta ICPC a Najeriya, ta ce yanzu haka tana ƙara sa-ido dangane da yadda ake kashe kuɗaɗe mallakin ƙananan hukumomi a ƙasar. Wannan na zuwa ne a dai-dai lokacin da gwamnatin tarayya ke shan matsin lamba domin ganin ta aiwatar da hukuncin Kotun Ƙoli wanda ya buƙaci a zuba wa ƙananan hukumomin kuɗadensu kai-tsaye a maimakon bi ta hannun gwamnonin jihohi. Ko me za ku ce a game da jan ƙafa wajen aiwatar da wannan umarni da kotu ta bayar tun watan Yulin shekara ta 2024 da ta gabata? Wace irin rawa ya dace ICPC ta taka don kare dukiyar ƙananan hukumomi a Najeriya? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakin ku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi mabanbanta...

    Ra'ayoyin Masu Sauraro kan janye yajin aikin Likitoci masu neman ƙwarewa a Najeriya

    Play Episode Listen Later Sep 15, 2025 9:24


    Shirin Ra'ayoyin Mai Sauraro na wannan Litinin tare da Nasiru Sani ya tattauna ne kan janye yajin aikin gargaɗi na kwanaki biyar da ƙugiyar likitoci masu neman ƙwarewa a Najeriya ta sanar a ƙarshen mako, kwanaki bayan fara ta a ranar Juma'ar da ta gabata, inda ta ƙara wa'aɗin makwanni  biyu don a biya musu buƙatunsu. Daga cikin buƙatun ƙungiyar da take nema gwamnati ta biya akwai abinda ya shafi albashi da alawus-alawus da kuma walwalar mambobinta. Ku latsa alamar sauti domin sauraron ra'ayoyin wasu daga cikin masu sauraro da suka aikoma ta manhajarmu ta Whatsapp

    Ra'ayoyin masu saurare kan matakin Najeriya na haramta zirga-zirgar jiragen ruwa marasa lasisi

    Play Episode Listen Later Sep 11, 2025 9:42


    A yunƙurin rage yawaitar haɗura akan ruwa, Hukumar Kula da Zirga-zirga a kan Kogunan Najeriya ta haramta yin amfani da jiragen ruwa a kan kogunan ƙasar sai tare da samun izini daga gare ta. Wasu daga cikin matakan da hukumar ta sanar sun haɗa da hana yin lodin fasinja sai a tashoshin da ta amince da su, sai tilasta wa fasinja yin amfani da rigar kariya, da mallakar takardar shaidar ƙwarewa ga illahirin matuƙan jiragen da dai sauransu. Anya waɗannan matakai za su taimaka don rage afkuwar haɗurra a kan kogunan Najeriya? Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Nasiru Sani.

    Ra'ayoyin masu saurare kan ƴancin faɗar albarkacin baki a Nijar

    Play Episode Listen Later Sep 10, 2025 8:32


    A Jamhuriyar Nijar, batun ƴancin faɗin albarkacin baki, aikin jarida ko kafa ƙungiyoyi da sunan yi fafutuka na ci gaba da fuskantar barazana. Bayan rusa ilahirin jam'iyyun siyasa, daga bisani an ci gaba da kama ƴan jarida da masu fafutukar kare hakkin bil adama, tare da jefa ƙungiyoyin kwadago a cikin fargaba ta hanyar farawa da rusa kungiyoyin alƙalai na ƙasar. Ku latsa alamar sauti don jin ra'ayoyin jama'a kan wannan batu.

    ku baki bayan masu nijar jamhuriyar nijar
    Ra'ayoyin masu sauraren kan rikicin NUPENG da Dangote a Najeriya

    Play Episode Listen Later Sep 8, 2025 10:03


    A Najeriya, an shiga takun-saƙa tsakanin Ƙungiyar NUPENG ta direbobin motocin dakon mai da iskar gas da kuma Ɗangote wanda ya sanar da sayo motoci dubu 4 da zai yi amfani da su don rarraba man fetur a sassan ƙasar. Yayin da NUPENG ke cewa magoya bayanta ne ke da hurumin raba mai da iskar gas a ƙasar, sai dai manazarta na cewa Ɗangote, na da damar raba hajarsa sakamakon sakin mara da aka yi wa ɓangaren kasuwanci a ƙarƙashin dokokin Najeriya. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi....

    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa daban-daban

    Play Episode Listen Later Sep 5, 2025 10:32


    Kamar yadda aka saba kowacce ranar Juma'a mukan baku dama don bayyana mana ra'ayoyinku game da batutuwa daban-daban da suka shafin fannonin rayuwa daban-daban don kira ga masu ruwa da tsaki da su kawo ɗauki. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Hauwa Aliyu Garba

    Ra'ayoyin masu saurare kan kama Simon Ekpa mai fafutukar kafa ƙasar Biafra

    Play Episode Listen Later Sep 3, 2025 10:06


    Kotun ƙasar Finland ta ɗaure Simon Ekpa mai fafutukar kafa ballewar Biafra daga Najeriya shekaru 6 a gidan yari, saboda samun sa da laifufukan ta'addanci.   Wannan hukunci na zuwa ne a daidai lokacin ake ci gaba da tsare ɗaruruwan mutane a gidajen yarin Najeriya bisa zargin aikata ta'addanci, amma kotuna sun gaza hukuntar da su. Shin ko me za ku ce a game da wannan hukunci da kotun ƙasar Finland ta yanke? Meye ra'ayoyinku a game da gazawar kotunan Najeriya wajen hukunta waɗanda ake tuhuma da aikata irin waɗannan laifuka a cikin gida? Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu

    Ra'ayoyin masu saurare kan taron manyan hafsoshin tsaron Afrika

    Play Episode Listen Later Aug 27, 2025 9:40


    Hafsoshin tsaro na ƙasashen Afirka a taron da suka yi a birinin Abujan Najeriya, sun ƙuduri aniyar haɗa gwiwa don tunkarar ƙalubalen tsaro da nahiyar ke fuskanta. Wannan taro dai ya samu halartar wakilan ƙasashe sama da 50, waɗanda suka yi imani da cewa la'akari da girman matsalar, akwai buƙatar ƙasashen su yi aiki a tare don tunkarar ta. Shin ko meye ra'ayoyinku a game da wannan yunƙuri na ƙasashen Afirka? Waɗannan shawarwari za ku bayar domin samun nasarar wannan fata? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin....

    Ra'ayoyin masu sauraren kan yadda ɗimbin mutane suka rasa ayyukansu a Nijar

    Play Episode Listen Later Aug 25, 2025 11:02


    A jamhuriyar Nijar, dubban mutane ne suka rasa ayyukansu yayin da ɗimbin ƴan gudun hijira suka daina samun tallafi, bayan da mahukunta suka kori mafi yawan ƙungiyoyin agaji daga gudanar da ayyukansu a cikin ƙasar. Bayan korar waɗannan ƙungiyoyi da ke taimaka wa ƴan gudun hijira, a mafi yawan yankuna har yanzu gwamnatin ta gaza samar da tsarin da zai maye gurbin waɗannan ƙungiyoyi don agaza wa jama'a. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin....

    Ra'ayoyin masu sauraro kan batutuwa da dama

    Play Episode Listen Later Aug 22, 2025 6:15


    Yau Juma'a rana ce da mukan baiwa masu saurarenmu damar tofa albarkacin bakinsu a cikin shirinmu kan abubuwan da ke ci musu tuwo a kwarya. Danna alamar saurare domin jin cikaken shirin tare da Nasiru Sani

    Ra'ayoyin masu saurare kan alfanun sulhu da 'yanbindiga ko akasanin haka a Najeriya

    Play Episode Listen Later Aug 21, 2025 10:12


    A Najeriya muhawara ta ɓarke game da buƙatar sulhu da ƴan ta'adda maimakon amfani da ƙarfin Soji, kodayake an samu mabanbantan ra'ayoyi daga ɓangaren masana a fannin na tsaro lura da yadda suka ce irin wannan sulhu ya gaza amfanarwa a yankuna da dama duk da cewa anga alfanunsa a wasu yankunan. Yaya kuke kallon wannan batu? Shin kuna ganin sulhu ko kuwa amfani da ƙarfin soji shi ne mafi  a'ala wajen yaƙi matsalolin tsaron Najeriyar? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkaci bakinku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin tare da Abida Shu'aibu Baraza....

    Ra'ayoyin masu saurare kan shirin rungumar GMO a Najeriya

    Play Episode Listen Later Aug 19, 2025 10:24


    Lura da yadda jama'a ke ɗari-ɗari a game da kayan abincin da aka sauya wa ƙwayoyin halitta da ake kira GMO, wannan ya sa mahukunta a Najeriya ke neman yin amfani da malaman addini domin gamsar da jama'a su rungumi irin wannan abinci. Abin neman sani a nan shi ne, shin ko kun fahinci abin da ake kira GMO? Ko a shirye ku ke domin karɓar nau'in abincin da aka canza wa ƙwayoyin halitta? Anya yin amfani da malaman addini zai sa jama'a su amince da shi a Najeriya? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

    Ra'ayoyin masu saurare kan kama jagororin ƙungiyar Ansaru a Najeriya

    Play Episode Listen Later Aug 18, 2025 10:19


    Mai Bai wa Shugaban Najeriya Shawara kan Sha'anin Tsaro Nura Ribaɗo ya tabbatar da kama jagororin ƙungiyar Ansaru da ake kira Ƴan Mahmuda su biyu, waɗanda suka jima suna addabar yankunan ƙasar. Ana dai bayyana wannan ƙungiya a matsayin babbar barazana ga matsalar tsaron ƙasar, saboda alaƙarta kai-tsaye da Alqa'ida. Shin ko wane sauyi wannan kame zai samar ta fannin tsaro a Najeriya? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta

    Play Episode Listen Later Aug 15, 2025 9:43


    Yau take ranar bayyana ra'ayoyinku kan batutuwa da suke ci muku tuwo a ƙwarya, kama daga siyasa, tattalin arziƙi, zamantewa da sauran abubuwan daban daban na rayuwa. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyin...

    Ra'ayoyin masu saurare kan yajin aikin lauyoyi a Nijar

    Play Episode Listen Later Aug 14, 2025 9:17


    Lauyoyi a Jamhuriyar Nijar sun tsunduma yajin aikin kwanaki biyu daga yau Alhamis, domin nuna rashin amincewa da rusa ƙungiyoyin alƙalai da sauran ma'aikatan shari'a da gwamnatin ƙasar ta yi. Kafin rusa waɗannan ƙungiyoyi, tuni aka rusa ƙungiyoyin jami'an kare gandun daji da na kwastam da kuma illahirin jam'iyyun siyasar ƙasar. Shin, ko me za ku ce a game da wannan mataki na gwamnatin Nijar ta ɗauka? A irin wannan yanayi, ko meye makomar ƴancin gudanar da ƙungiyoyi a ƙasar? Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi...

    shin masu nijar jamhuriyar nijar alhamis
    Ra'ayoyin masu sauraro kan yadda Bankin Duniya ya rantawa Najeriya dala miliyan 300

    Play Episode Listen Later Aug 13, 2025 10:16


    Bankin Duniya ya amince ya ranta wa Najeriya dala miliyan 300 kwatankwacin naira biliyan 460 don tallafa wa mutanen da suka ƙaurace wa matsugunansu saboda matsaloli a sassa daban daban na Arewacin ƙasar. Yanzu haka akwai mutane sama da milyan 3 da rabi da ke rayuwa a wannan yanayi, kuma mafi yawansu sun dogara da tallafi ne domin rayuwa. Shin ko waɗanne matakai suka kamata a ɗauka don tabbatar da cewa an yi amfani da kuɗaɗen ta hanyoyin da suka dace? Sai ku bayyana ra'ayoyinku a lambarmu ta Whatsapp da kuma shafinmu na Facebook.

    Ra'ayoyin masu saurare kan yadda ake samun ambaliyar ruwa a irin wannan lokaci

    Play Episode Listen Later Aug 12, 2025 10:52


    Kusan a kowacce shekara, dai-dai wannan lokaci ne ake samun faruwar ambaliya sakamakon saukar ruwan sama mai yawa da ke haddasa asarar rayuka da kuma dukiyoyi masu tarin yawa. A daidai wannan lokaci, ko wane hali ake ciki a yankunanku dangane da batun ambaliya? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a wannan rana. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

    Ra'ayoyin masu saurare kan matakin Nijar na ƙwace kamfanonin haƙar zinare

    Play Episode Listen Later Aug 11, 2025 10:24


    Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta sanar da ƙwace ilahirin kamfanonin haƙo zinare tare da shelanta cewa sun zama mallakin ƙasar, yayin da a ɗaya ɓangare ta hana fitar da duk wani nau'in dutse mai ƙima zuwa ƙetare sai tare da izinin hukuma. Hakan na zuwa ne watanni bayan ta ƙwace kamfanonin haƙo uranium matsayin mallakin ƙasar. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

    Waɗanne abubuwa ne suka fi ci muku tuwa a ƙwarya

    Play Episode Listen Later Aug 8, 2025 10:15


    Shirin ra'ayoyin ku masu saurare na wannan rana kamar yadda aka saba ya baku damar fadɗn albakacin bakinku kan abubuwan da suka fi ci muku tuwo a ƙwarya a fannin lafiya, jagoranci, siyasa da kuma zamantakewa. Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Nasiru Sani

    Ra'ayoyin masu saurare kan kalaman Falana game da matakan tattalin arziƙin Tinubu

    Play Episode Listen Later Aug 7, 2025 10:22


    Bisa ga al'ada, ana cewa al'umma ta kasu ne zuwa rukuni uku, wato attajirai, da matsakaita sai kuma matalauta. To sai dai a cewar shahrarren lauya kuma mai fafutuka Femi Falana, a Najeriya mutane na rayuwa ne a ɗaya daga cikin rukuni biyu kawai: wato gungun attajirai ko kuma na talakawa, wannan kuwa sakamakon ɓullo da sabuwar siyasar tattalin arziki maras alfanu a ƙasar.

    Ra'ayoyin masu saurare kan zanga-zangar neman korar 'yan Najeriya daga Ghana

    Play Episode Listen Later Jul 31, 2025 9:59


    A ƴan kwanakin nan an samu ɓarkewar zanga-zangar a Ghana, inda ƴan ƙasar ke zargin ƴan Najeriya da ke can da aikata laifuka kisan gilla da karuwanci, lamarin da ya sa masu zanga-zangar neman a koresu daga ƙasarsu. Haka nan masu zanga-zangar sun yi ikirarin cewa ƴan kasuwan Najeriya  sun mamaye musu kasuwanni tare da karya dokokin kasuwanci a ƙasar. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

    Ra'ayoyin masu saurare kan karrama 'yan wasan Super Falcons da Tinubu yayi

    Play Episode Listen Later Jul 29, 2025 10:35


    Tarihi dai ya maimaita kansa, inda tawagar Super Falcons ta Najeriya ta lashe gasar WAFCON karo na 10, bajintar da ba tawagar da ta taɓa yi. Sakamakon haka ne shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karrama ƴan wasan da lambar girmamawa ta ƙasa OON, da dala dubu dari-dari ($100,000) kowacce, da kuma gidaje a Abuja. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

    Ra'ayoyin masu saurare kan bikin cika shekaru biyu da juyin mulkin Nijar

    Play Episode Listen Later Jul 28, 2025 10:16


    A ranar Asabar da ta gabata, 26 ga watan Yuli Jamhuriyar Nijar ta yi bikin cika shekaru biyu a kasancewa a ƙarƙashin mulkin soji, wadanda suka hambarar da gwamnatin Mohamed Bazoum kuma suke cigaba da tsare  shi ba tare da gurfanar da shi ba. A waje daya kuma a karon farko a jawabin da ya  gabatar jagoran gwamnatin sojin Janar Abdourahmane Tchiani ya ce ya san halin ƙunci da jama'a ke ciki. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi mabanbanta...

    Yau take ranar jin ra'ayoyin ku masu saurare kan batutuwa mabanbanta

    Play Episode Listen Later Jul 25, 2025 9:46


    A duk ranar Juma'a, RFI Hausa na bai wa jama'a damar tofa albarkacin bakinsu kan abubuwan da ke ci musu tuwo a ƙwarya kama daga siyasa, tattalin arziki, zamantakewa, harkokin yau da kullum da dai saurarensu. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi mabanbanta...

    Ra'ayoyin masu saurare kan rahoton NBS na ƙaruwar tattalin arziƙin Najeriya

    Play Episode Listen Later Jul 23, 2025 9:52


    Hukumar ƙididdiga ta Najeriya ta ce tattalin arzikin ƙasar ya samu ƙarin tagomashi da kashi 3 da ɗigo 13 a rubu'in farko na wannan shekarar ta 2025, saɓanin kashi 2 da ɗigo 27 yake a daidai wannan lokaci a shekarar 2024.   Wannan na zuwa ne yayin da talauci ke ci gaba da ta'azzara a tsakanin al'ummar ƙasar, kuma manoma sun gaza yin noma yadda ya kamata saboda matsalar ta'addanci. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

    masu wannan najeriya hukumar
    Ra'ayoyin masu saurare kan zanga-zangar 'yansanda a Najeriya

    Play Episode Listen Later Jul 22, 2025 9:53


    A babban birnin Tarayyar Najeriya, Abuja, ɗaruruwan ƴansanda da suka yi ritaya kuma bisa ga dukkan alamu da yawun waɗanda suke bakin aiki a yanzu ne suka gudanar da zanga-zangar neman a cire su daga tsarin fanshon adashen gata, wanda suka ce babu abin da ya yi face jefa su cikin baƙin talauci bayan shafe shekaru suna wa ƙasar hidima. Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi....

    abuja masu najeriya tarayyar najeriya
    Yadda Isra'ila ke kashe Falasɗinawa masu jiran tallafin abinci

    Play Episode Listen Later Jul 21, 2025 9:29


    Shirin ra'ayoyin ku masu sauraro na wannan rana ya mayar da hankali ne kan yadda Isra'ila ta mayar da guraren rabon abincin tallafi a Gaza tarkon mutuwa. Ku danna alamar sauraro domin jin cikakken shirin tare da Hauwa Aliyu.

    Ra'ayoyin masu saurare kan rashin yiwa yara rigakafin cutuka a Najeriya a 2024

    Play Episode Listen Later Jul 16, 2025 9:43


    Wani sabon rahoton Asusun kula da ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya ya ce ƙananan yara  sama da miliyan 14 ne a fadin duniya ba su samu alluran rigakafin cutukkan da ke addabar yara a shekarar 2024 ba, kuma sama da miliyan biyu daga cikin wannan adadi a Najeriya suke. Rashin wannan rigakafi  na iya jefa waɗannan yara cikin hatsarin kamuwa da cutukan da ake iya samun kariya daga gare su. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

    duniya wani masu rashin najeriya majalisar
    Shugaban Kamaru Paul Biya zai sake tsayawa takarar shugabancin ƙasar karo na 8

    Play Episode Listen Later Jul 15, 2025 9:57


    Shugaban Kamaru Paul Biya ya bayyana aniyar sa ta sake tsayawa takarar shugabancin ƙasar a karo na 8 yana mai shekaru 92 da haihuwa, inda ya yi iƙirarin cewa matasa da mata ne zai fi bai wa fifiko idan ya samu ya zarce. Wani saƙo da Biya mai shekaru 92 ya wallafa a shafinsa na Twitter ne ke sanar da wannan mataki wanda ya kawar da jita-jitar da ke nuna cewa shugaban a wannan karon bashi da sha'awar tsayawa takara don neman wa'adi na gaba. Fiye da shekaru 40 kenan Paul Biya ke jagorancin Kamaru kasancewarsa shugaba na biyu da ya jagoranci ƙasar tun bayan samun ƴancinta daga Faransa wato bayan murabus ɗin shugaba Amadou Ahidjo. Idan har Paul Biya ya yi nasarar lashe zaɓen da zai bashi damar sake yin shekaru 7 a karagar mulki, kenan shugaban mafi daɗewa kan mulki, zai tasamma shekaru 100 na rayuwarsa a karagar mulki karon farko da ake ganin irin hakan a tarihi. Shiga alamar sauti, domin sauraro cikakken shirin tare da Abida Shu'aibu Baraza.

    Ra'ayoyin masu saurare kan mutanen da 'yanbindiga suka kashe a cikin watanni 6

    Play Episode Listen Later Jul 9, 2025 10:12


    A Najeriya, wasu alƙaluman hukumar kare hakkin ɗan adam ta ƙasar sun ce adadin mutanen da ƴanbindiga suka kashe a cikin watanni shida na farkon wannan shekarar ya zarce na ilahirin shekarar da ta gabata, inda a watan da ya gabata kawai mutane  606 ne masu ɗauke da makamai suka halaka. Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi...

    suka masu najeriya cikin
    Ra'ayoyin masu saurare kan yadda ambaliya ke yin ɓarna a wasu biranen Afrika

    Play Episode Listen Later Jul 7, 2025 10:33


    Ambaliyar ruwa na ci gaba da yin ɓarna a wasu biranen ƙasashen Afrika, inda ko a baya-bayan nan ta laƙume rayuka fiye da 600 a ƙaramar hukumar Mokwa ta jihar Nejan Najeriya yayin da tituna suka fara cika da ruwa a wasu ƙananan hukumomin jihar Kano, baya ga babban birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar da aka samu iftila'in ambaliyar a kwanakin baya.   Ya ya matsalar ta ke a yankunan ku, ko wani mataki kuke ɗauka don ganin kun kare kanku daga iftila'in ambaliyar ruwan yayin da daminar bana ta sauka? Shin ko akwai wasu matakai da gwamnatocinku ke ɗauka?

    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta

    Play Episode Listen Later Jul 4, 2025 10:32


    A duk ranar Juma'a, RFI Hausa na bai wa jama'a damar tofa albarkacin bakinsu kan abubuwan da ke ci musu tuwo a kwarya kama daga siyasa, tattalin arziki, zamantakewa, harkokin yau da kullum da dai saurarensu. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

    Yadda wasu fitattun ƴansiyasa a Najeriya suka kafa wani sabon ƙawance

    Play Episode Listen Later Jul 3, 2025 10:05


    Wasu fitattun ƴansiyasa a Najeriya, sun sanar da kafa wani sabon ƙawance da zummar ƙwace mulki daga hannu shugaba Bola Tinubu a shekara ta 2027. To sai dai abin lura a nan shi ne, waɗanda suka ƙulla ƙawancen mutane ne da suka taɓa riƙe muhimman muƙamai ƙarƙashin gwamnatoci daban-daban ciki har da ta APC. Abin tambayar shine, ko waɗanne irin alƙawura ne da za su sake gabatar wa 'yan ƙasar domin samun ƙuri'aunsu? Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.

    Ra'ayoyin masu saurare kan kashe 'yan ta'adda da jami'ai su ka yi a Najeriya

    Play Episode Listen Later Jul 2, 2025 10:01


    A Najeriya, ga alama sabon salon da hukumomin tsaro na tarayya da kuma na jihar Zamfara su ɓullo da su, sun fara yin tarisi a yaki da ayyukan ƴanbindiga da suka addabi jama'ar yankin. Bayanai sun ce farmakin da ƴan sa-kai suka kai ƙarshen makon jiya, ya yi sanadiyyar mutuwar ƴanbidigar kusan 200 ciki har da manyan kwamandojin Bello Turji. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyin jama'a mabanbanta...

    masu zamfara najeriya
    Kan tsagaita wuta tsakanin Iran da Isra'ila

    Play Episode Listen Later Jun 25, 2025 9:44


    Shirin na yau ya baku damar tofa albarkacin bakinku game da tsagita wuta da aka yi tsakanin Iran da Isra'ila bayan kwashe kusan kwanaki 12 ana gwabza yaƙi. Ku danna alamar sauraro domin jin cikakken shirin tare da Abida Shu'aibu Baraza.

    Ra'ayoyin masu sauraron kan shawarar gina katanga kan iyakokin Najeriya

    Play Episode Listen Later Jun 5, 2025 10:22


    Babban hafsan sojojin Najeriya ya bayar da shawarar gina katanga kan iyakokin ƙasar da maƙotanta don magance matsalolin tsaro da Najeriya ke fama da su. Janar Christopher Musa ya bayar da misali da ƙasashen Pakistan da kuma Saudiyya, waɗanda ya ce sun gina irin wannan katanga tsakaninsu da maƙota saboda dalilai na tsaro.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.

    Ra'ayoyin jama'a kan Gasar Zakarun Turai ta bana da PSG ta lashe

    Play Episode Listen Later Jun 3, 2025 8:38


    Karon farko a tarihi, ƙungiyar Paris Saint Germain ta Farnasa ta yi nasarar lashe kofin gasar Zakarun Turai ta wannan kaka bayan da ta doke Inter Milan ta Italiya, inda ta zama ta biyu da ta taɓa cin wannan kofidaga Faransa. Wani abin lura a game da wannan wasa, shi yadda PSG ta lallasa abokiyar karawarta da ci 5 da banza.Me za ku ce a game da wannan nasara da PSG ta samu?Ko meye ra'ayoyinku a game da yadda gasar ta Zakarun Turai ta wannan kaka ta gudana?

    Ra'ayoyin masu saurare kan bikin cika shekara 53 da haɗewar Kamaru

    Play Episode Listen Later May 20, 2025 10:30


    A wannan talata, al'ummar Kamaru na bikin cika shekaru 53 da haɗewar yankunan da ke amfani da Faransanci da masu amfani da harshen Ingilishi, waɗanda kafin nan suna zaune da juna ne a ƙarƙashin tsarin tarayya. To sai dai a daidai yayin da ake wannan biki, yanzu haka akwai masu gwagwarmaya da makamai don samar wa yankunan da ke turancin Ingilishi ƴanci.Shin ko me za ku ce a game da wannan haɗewa?Ko waɗanne matakai ku ke ganin cewa sun dace a ɗauka domin dawo da yarda a tsakanin bangarorin biyu?Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a

    Ra'ayoyi kan matakin Ghana na kama masu bace-barace

    Play Episode Listen Later May 19, 2025 10:08


    Matsalar barace-barace a kan titunan manyan birane a Yammavin Afirka sai daɗa yin ƙamari take, to sai dai bisa ga dukan alamu mahukunta a ƙasar Ghana sun ƙuduri aniyar kawo ƙarshen wannan ɗabi'a. Domin a cikin makon jiya, jami'an tsaro sun cafke mabarata sama da dubu biyu a birnin Accra kawai, kuma yawancinsu ƴan asalin ƙasashen Najeriya, Nijar, Burkina Faso da Mali ne.Shin ko akwai dalilan da za su sa jama'a su mayar da bara a matsayin sana'a?Ko waɗanne matakai ya kamata a ɗauka domin kawo ƙarshen wannan ɗabi'a ta bara?Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a.

    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta

    Play Episode Listen Later May 16, 2025 10:23


    A duk ranar Juma'a, RFI Hausa na bai wa jama'a damar tofa albarkacin bakinsu kan abubuwan da ke ci musu tuwo a kwarya kama daga siyasa, tattalin arziki, zamantakewa, harkokin yau da kullum da dai saurarensu. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin tare da Shamsiyya Haruna...

    Ra'ayoyin masu sauraro kan matakin Nijar na hana fitar da dabbobi zuwa ƙetare

    Play Episode Listen Later May 15, 2025 10:24


    Makonni kaɗan gabanin bukukuwan Sallar Layyah, mahukuntan jamhuriyar Nijar sun bayar da umurnin hana fitar da dabbobi zuwa ƙetare. Ga alama dai an ɗauki matakin ne don hana tashin farashin dabbobi a wannan lokaci, yayin da wasu ke cewa matakin zai iya cutar da tattalin arzikin ƙasar.Abin tambayar shine, menene amfani ko kuma illar wannan mataki ga ƙasar?Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.

    Ra'ayoyin Masu Saurare kan yadda ƴanbindiga suka tsananta kai hare-hare

    Play Episode Listen Later May 14, 2025 9:49


    Hare-haren ƴanbindiga na ci gaba da ɗaukar sabon salo a Najeriya, inda a baya-bayan nan suka tsananta kai farmaki hatta akan sansanonin soji, kusan a iya cewa haka take a sauran yankin sahel musamman Burkina Faso, lamarin da kanyi sanadin mutuwar jami'an tsaro masu tarin yawa.  Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a kan wannan maudu'in.......

    Ra'ayoyi kan kula da lafiyar kwakwaluwa

    Play Episode Listen Later May 13, 2025 10:28


    Shin ko kun san muhimmancin kula da lafiyar ƙwaƙwalwa kuwa? Wannan tambaya ce mai matuƙar muhimmanci, lura da cewa yanzu haka akwai ɗimɓin mutane da ke fama da wannan matsala a sassan duniya. Yayin da wasu ke kira wannan lalura a matsayin hauka, masana kuwa na cewa hatta shiga yanayi na damuwa ko da ƙuncin rayuwa na iya haddasa wannan matsalar.Shin ko wace irin kulawa ku ke bai wa lafiyar ƙwaƙwalwa?Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a.

    Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta

    Play Episode Listen Later May 9, 2025 10:12


    A duk ranar Juma'a, RFI Hausa na bai wa jama'a damar tofa albarkacin bakinsu kan abubuwan da ke ci musu tuwo a kwarya kama daga siyasa, tattalin arziki, zamantakewa, harkokin yau da kullum da dai saurarensu. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin tare da Shamsiyya Haruna...

    juma masu najeriya

    Claim Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

    In order to claim this podcast we'll send an email to with a verification link. Simply click the link and you will be able to edit tags, request a refresh, and other features to take control of your podcast page!

    Claim Cancel