Shiri ne na musamman, da kan tattaunawa da bangarori daban-daban na Al’umma da ke sauraren Shirye shiryen RFI Hausa daga kowane kusurwa na fadin duniya, kan muhimman batutuwa, da suka shafi siyasa Tattalin’ariziki, al’adu da dai sauransu…

Tawagar ƙasar Spain ta lashe gasar kofin duniya karo na biyu a tarihi, bayan ta doke Argentina da ke kare kambun a wasan ƙarshe da suka gudanar a daren jiya. Ita kuma Ingila ta ƙare a matsayi na 3 ne inda ta lashe kyautar tagulla da ke zama kyauta ta farko da ta lashe a kofin duniya cikin shekaru 60, ya yin da Faransa ta ƙare a matsayi na 4. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Yau juma'a, rana ce da sashen Hausa na RFI ke bai wa masu sauraro damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwan da ke ci musu tuwo a ƙwarya, kama daga tsaro, tattalin arziƙi, siyasa, zamantakewa, da dai sauransu. Latsa alamar sauti don sauraren ra'ayoyi mabanbanta...

Kamar yadda aka saba, yau rana ce da sashen Hausa na RFI ke bai wa masu sauraro damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwan da ke ci musu tuwo a ƙwarya, kama daga tsaro, siyasa, tattalin arziƙi da dai sauransu. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Majalisar dattijan Najeriya ta bukaci gwamnatin kasar da ta dakatar da shirin yin afuwa ko kuma sauya ɗabi'un tubabbun ƴan ta'adda a wani yunƙuri na dawo da su cikin al'umma, wanda ta ce ba ya taimakawa ƙoƙarin da ƙasar ke yi wajen yaƙi da ta'addancin da ya yi mata katutu. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Mai Alfarma Sarkin Musulmin Najeriya Muhammadu Sa'ad Abubakar na uku, ya ce mutunta addinan juna, daina furta kalaman ƙiyayya ko tsatsauran ra'ayi, abubuwa ne da za su iya taimakawa ta fannin kyautata zamantakewa a tsakanin al'umma. Wannan dai gargaɗi ne da ke ƙunshe a sanarwar da aka fitar bayan ganawar da aka yi a babban masallacin birnin Abuja tsakanin mai alfarma Sarkin Musulmin da kuma tawagar manyan jami'an Fadar Vatican ƙarƙashin jagorancin Archibishop Paul Richard Gallaghera. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Yau juma'a, kamar yadda aka saba, rana ce da sashen Hausa na RFI ke bai wa masu sauraro damar faɗin albarkacin bakin su kan batutuwan da ke ci musu tuwo a ƙwarya, kama daga tsaro, tattalin arziƙi, siyasa, da dai sauransu. Latsa alamar sauti don sauraren ra'ayoyi mabanbanta...

Birane da dama da ke gaɓar ruwan tekun ƙasashen Yammacin Afrika sun fuskanci ambaliyar ruwa wadda ta haddasa asarar rayuka da kuma salwatar dukiyoyi masu tarin yawa. Birnin Accra na ƙasar Ghana da Abidjan Ivory Coast, a can ne aka samu asarar rayuka, yayin ambaliyar ta haddasa ɓarna ga gidaje da kadarori a biranen Lagos, Cotonou, Lome da sauransu. Lura da abin da ya faru a waɗannan birane da kuma yadda damina ke ci gaba da sauka, shin ko akwai waɗansu matakai da ku ke saboda kasancewa a cikin shirin ko-ta-kwana? Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Bayan cikar wa'adin ranar 30 ga watan jiya da suka bai wa ƴan-ci rani don ficewa daga ƙasar, daga ƙarshe dai masu adawa da zaman baƙi a Afirka ta Kudu sun ƙaddamar da zanga-zangar neman ala dole sai sun fice daga ƙasar. Masu tarzomar dai na kallon ƴan asalin ƙasashen ƙetare a matsayin waɗanda suka mamaye gurabobin aiki, lamarin da ya jefe ɗimbin Ƴan Afirka ta Kudu cikin yanayin zaman kashe wando. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Duk da cewa an samu faɗuwar farashin ɗanyan man fetur a kasuwar duniya sakamakon sulhun tsakanin Amurka da Iran, amma har yanzu ana ci gaba da fama da tsadar wannan makamashi a mafi yawan ƙasashen duniya. A Najeriya tuni Hukumar kare masu amfani da kayan masarufi ta ƙasar ta yi gargaɗin cewa ko dai dillalan mai su karya farashi ko kuma ta ɗauki matakan ladaftarwa a kansu. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Ƙasashen Afrika 9 daga cikin 10 da ke halartar gasar cin kofin duniya ne suka samu nasarar tsallakawa zuwa zagayen ƙasashen 32 na wannan gasa da ke gudana a ƙasashen Amurka da Canada da kuma Mexico. Wannan dai shi ke matsayin babban tagomashi da nahiyar ta Afrika ta taɓa samu a irin wannan gasa ta cin kofin duniya. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Yau juma'a kamar yadda aka saba, rana ce da sashen Hausa na RFI ke bai wa masu sauraro damar faɗin albarkacin bakinsu kan batutuwan da ke ci musu tuwo a ƙwarya, kama daga siyasa, tsaro, tattalin arziƙi, zamantakewa da dai sauransu. Latsa alamar sauti don sauraren ra'ayoyi mabanbanta...

Yayin da damina ta fara kankama a Tarayyar Najeriya, wani abu da ake fargaba shi ne yadda matsalar tsaro ke iya haddasa tarnaki ga aikin gona hatta ma a wannan shekara. Kusan a kowace rana za a samu labarin cewa an kai hare-hare kan manoma da kan yi sanadiyyar kisa, yin garkuwa domin neman kuɗin fansa, yayin da a wasu lokuta ake tilasta wa manoman biyan haraji kafin ba su damar shiga gonakinsu. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Tawagar da Majalisar Ɗinkin Duniya ta tura zuwa Najeriya don gudanar da bincike a game da zargin kisa, yin garkuwa da mutane da kuma tilasta wa wasu barin muhallansu saboda dalilai na addini, ta ce wannan ba gaskiya ba ne. Jagorar tawagar Farfesa Nazila Ghanea, a ƙarshen ziyarar gani da ido ta kai a ƙasar, ta ce mutane na yin waɗannan zarge-zarge ne saboda gazawar gwamnati wajen ba su kariya da kuma gaza hukunta waɗanda ke aikata laifukan. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Yayin da ake shirin gudanar da zaɓuka cikin watan Fabarairun shekaru mai zuwa a Najeriya, wani abu da ke faruwa shi ne taƙaddamar ƴan siyasa a gaban kotunan ƙasar. Kusan a kowane mako, za a ji cewa kotu ta yanke hukunci kan jam'iyyun siyasa, lamarin da ke iya nisantar da su daga tsayawa takara a waɗannan zaɓuka. Wannan ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Nijar da Jamhuriyar Benin sun amince da yin aiki a tare don yaƙi da ta'addanci da ke addabar ƙasashen biyu na Yammacin Afirka, yayin da a hannu ɗaya suka kafa wani kwamitin da zai bayar da shawarwari cikin kwanaki 15 a game da yadda za a sake buɗe iyakokin ƙasashen da ke rufe yau kusan shekaru uku. An dai cimma wannan matsaya ce a ziyarar da shugaban Benin Romuald Wadagni ya kai a birnin Yamai ranar talata, inda ya gana da takwaransa na Nijar Janar Abdourahman Tiani. Dangane da hakan ne muka baku damar tofa albarkacin bakin ku ta cikin shirin Ra'ayoyinku Masu Sauraro. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

A yau take Sallah Babba! Ranar da ɗaukacin Musulmi a faɗin duniya ke murnar zagayowar Sallar layya. Wannan biki na zuwa ne a daidai lokacin da lamura suka yi tsauri, musamman ta ɓangaren tattalin arziƙi. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.

Kamar yadda aka saba a kowace ranar alhamis, shirin Rayuwata na bai wa masu sauraro damar bayyana ra'ayoyinsu kan maudu'an da shirin ya tattauna a wannan mako. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Bayan share kusan shekara ɗaya ana taƙaddama tsakanin gwamnatin Nijar da kamfanin mai na CNPCN na ƙasar China, ɓangarorin biyu sun cimma yarjejeniya da ke bai wa Nijar damar ƙarin jari da kuma faɗa-a-ji a harkar man fetur. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Yanzu haka ƙasashe masu tasowa na ci gaba da ƙoƙarin cike giɓin da aka samu bayan da Donald Trump ya janyewa tallafin da Amurka ke bai wa Hukumar Lafiya don yaƙi da wasu curutuka a duniya. A jawabinsa gaban Taron Hukumar Lafiya WHO da ke a birnin Geneva, shugaban Ghana John Dramani Mahama ya ce ya kamata Afirka ta samar da tsarin kula da lafiyar al'ummarta a maimakon barin lamarin a hannun hukumar WHO. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Gwamnatin Nijar ta fitar da wani daftari da ke ƙara adadin jihohi zuwa 19 ta hanyar ƙirƙiro sabbin 11 a maimakon 8 da ake da su a kasar yau kusan shekaru 30 kenan. Gwamnatin ta ce za ta ƙirƙiri sabbin jihohi da kuma gundumomi ne domin samar da ci gaba da ta hanyar ƙara matso da jama'a zuwa kusa da hukuma. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

A taron Afirka da Faransa da aka kammala jiya talata a ƙasar Kenya, Faransa ta sanar da shirin saka jarin Euro bilyan 23 don ƙarfafa kasuwanci tsakanin ɓangarorin biyu. Shugaba Emmanuel Macron ne ya sanar da haka, yana mai cewa daga yanzu ɓangarorin biyu za su gudanar da mu'amala ce irin ta ba ni gishiri in ba ka manda a maimakon bai Afirka tallafi kamar yadda ake yi a baya. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Yau juma'a sashen Hausa na RFI na bai wa masu sauraro damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwan da ke ci musu tuwo a ƙwarya, kama daga fannin siyasa, tattalin arziƙi, tsaro, da dai sauransu. Latsa alamar sauti don sauraren ra'ayoyi mabanbanta...

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta bayar da umarnin garƙame masallatai, da zarar an kammala sallolin farilla, tare da tabbatar da cewa an hana jama'a kwana a wuraren ibada ciki har da makarantun Islamiyya. Tuni ministan cikin gida ya sanar da gwamnoni, shugabannin ƙananan hukumomi da sarakunan gargajiya matakin a hukumance, saboda dalilai na tsaro. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Rahoton shekara-shekara da ƙungiyar kare ƴan jarida ta Reporters Without Borders ta fitar, na nuni da cewa an samu gagarumin koma-baya ta fannin ƴancin aikin yaɗa labarai a cikin ƙasashe 100 daga cikin 180 na duniya. RSF ta fitar da rahoton ne a jajibirin ranar ƴancin aikin jarida da ake gudanarwa ranar 3 ga watan Mayun kowace shekara. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

A kowace ranar Jumma'a filin ra'ayoyin 'Masu Sauraro kan bada damar tsokaci kan bututuwa da ke ci wa mai sauraro tuwo a kwarya. Ku latsa alamar sautin domin jin wasu daga cikin ra'ayoyin da wasu masu sauraro suka aiko mana.

A Najeriya, yayin da ƙasar ke ci gaba da ɗaura ɗamarar tunkarar zaɓukan gama-gari a shekara mai zuwa, yanzu haka ana ci gaba da mahawara dangane da abubuwan da ke ƙunshe a dokar zaɓe ta 2026 wadda a ƙarƙashinta ne komai zai gudana. Dokar dai na ƙunshe da sauye-sauye da dama saɓanin waɗanda aka sha jarrabawa a zaɓukan da suka gabata. Saboda haka za mu so jin ra'ayoyinku a game da alfahu ko rashin alfanunta wajen samar da tsaftaccen zaɓe a Najeriya. Latsa alamar sauti don jin ra'ayoyi mabanbanta...

A ranar Laraba ne aka fara shari'ar wasu mutane da ake zargi da hannu a wani yunƙurin kifar da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu gaban wata babbar kotu da ke Abuja. Gwamnatin Najeriya ta shigar da tuhume-tuhume guda 13 kan mutane shida, waɗanda suka haɗa da Janar mai ritaya, wani Kaftin ɗin sojan ruwa mai ritaya, da kuma wani sufeton ɗansanda. Karon farko kenan da aka ga shari'ar zargin yunkurin juyin mulki a kotun farar hula, sabanin yadda aka saba gani a bariki ko kuma kotun soji. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.

Yau juma'a, rana ce da sashen Hausa na RFI ke bai wa masu sauraro damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwan da ke ci musu tuwo a ƙwarya, kama daga tattalin arziƙin, siyasa, zamantakewa da dai sauransu. Latsa alamar sauti don sauraren ra'ayoyi mabambanta...

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ware sama da Naira tiriliyan uku domin biyan bashin da ke wuyan ƙasar a ɓangaren wutar lantarki. Sanarwa daga fadar shugaba Bola Tinubu ta ce an ɗauki matakin ne bayan an yi bitar illahirin bashin da ke wuyan gwamnati tsakanin 2015-2025 wannan bashi biyan wannan bashi zai bayar da damar shawo kan mafi yawan matsalolin da ke haifar da ƙarancin wutar lantarki a Najeriya. Shin ko meye ra'ayoyinku a game da wannan mataki? Ko wataƙila hakan zai kai ga ƙara ingantar samar da wutar lantarki a Najeriya? Ku danna alamar sauraro domin jin cikakken shirin tare na Nasiru Sani

Majalisun dokokin Kamaru sun amince da dokar da ke bai wa shugaba Paul Biya damar ƙirƙiro muƙamin mataimakin shugaban ƙasa da ke iya maye gurbin shugaban idan buƙatar hakan ta taso. Wasu dai na kallon hakan a matsayin yunƙurin da Biya ke yi domin tsara wanda zai gaje shi, a daidai lokacin da ake gaba da ɗiga ayar tambaya dangane da yanayi lafiyar shugaban mai shekaru 93 a duniya. Ku danna alamar sauraro dimin jin cikakke shirin tare da Nasiru Sani.

An shiga mako na huɗu da barkewar rikicin Yankin Gabas ta Tsakiya, inda ɓangarorin da ke hannu a rikicin ke ci gaba da kai wa juna hare-hare tare da kashe mutane da kuma lalata cibiyoyin makamashi. Tuni dai hakan ya haifar da tashin goron zabi ga farshin abubuwa da dama sanadiyar hauhawar farashin mai a kasuwar duniya. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabiru Yusuf

Hukumar kwallon ƙafar Afrika ta sanar da ƙwace Kambun da Senegal ta lashe a gasar neman kofin nahiyar da aka kammala cikin watan Janairun da gabata tare da miƙa shi ga ƙasar Moroko. Wannan dai mataki ne da ya yi matuƙar girgizar masu shawar harkar ƙwallon ƙafa a sassan duniya, inda tuni Senegal a buƙaci a gudanar da bincike bisa zargin cewa akwai yiyuwar an bayar da rashawa ne don ƙwace wannan galaba. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabiru Yusuf.

Yanzu haka farashin ɗanyen man fetur na ci gaba da hauhawa sakamakon yaƙin da Amurka da Isra'il suka ƙaddamar kan Iran, inda yanzu haka ake sayar da gangar mai fiye da dala 92 a kasuwar duniya. A wannan yanayi dai ko shakka babu, ƙasashe masu arzikin mai ne irinsu na Najeriya za su ci moriyar wannan rikici. Shiga alamar sauti, domin suararon cikakken shirin.

A yayin da yaƙi tsakanin Isra'ila da Amurka da Iran ke daɗa rincaɓewa, an fara gani tasirinsa a kasuwar ɗanyen mai da makamashi ta duniya. Ko a Najeriya, ƙasar da ta fi arziƙin ɗanyen mai a Afirka, farashin litar fetur ya tashi, kuma masana sun ce ana iya ganin cigaba da tashin farashin makamashi. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.

A Najeriya wata ƙungiyar ta'addanci da ba'a kai ga tantace wa ba, ta buƙaci a'ummar Utono ta ƙaramar hukumar Ngaski a jihar Kebbi da ta biya su zunzurutun ƙudi har Naira miliyan 100, kafin su bai wa malamai damar gudanar da Tafsiri ko wa'azi a wannan watan Azumi na Ramadana. Ƴan ta'addar sun bayyana bukatar ne a wata rubutacciyar wasika da suka aika garin na Utono. Wannan dai shine karon farko da wata ƙungiya da bukaci malamai biyan wani kudi domin gabatar da wa'azi, ko da ya ke al'umma a wasu yankunan sun saba biyan kudi don neman yancin walwa, ko ayyukan noma ko ma girɓi. Yaya kuke kallon wannan sabon bukata na ƴan ta‘adda? Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Dai dai lokacin da al'ummar musulmi suka faro azumin watan ramadana, can a jihar kano ta arewacin Najeriya da sauran jihohi maƙwabtanta, jama'a ne suka shiga cikin fargabar yiwuwar fuskantar hauhawar farashin kayakin masarufi sakamakon mummunar ɓarnar da gobara ta yi a kasuwar singa da ya haddasa ƙarancin kayakin na masarufi a kasuwannin jihar, kasancewar kasuwar ta singa babbar kasuwar da ke samar da kayakin Masarufi a kusan dukkanin arewacin Najeriyar dama wasu ƙasashen maƙwabta. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabiru Muhammad Ɗan Bauchi.

Ra'ayoyin masu saurare na wannan rana ya mayar da hankali ne kan yadda ake juyayin cika shekaru 36 da jami'an tsaro suka buɗe wuta kan ɗalibai da ke zanga-zangar neman kyautata ilimi, yin fatali da tsare-tsare Asusun Lamuni na Duniya da sauran matakai na tsuke bakin aljihun gwamnatia jamhuriyar Nijar, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla ɗalibai uku. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabiru Yusuf.

Ƙungiyar ƴan awaren IPOB, da ke fafutukar kafa ƙasar Biafra ta sanar da janye matakin tilastawa jama'a zaman gida a kowace litinin da aka shafe shekaru biyar ana yi a yankin kudu maso gabashin Najeriya. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabiru Yusuf don jin cikakken shirin.

Shekaru 29 bayan mutuwarsa, an bai wa shahararren mawaƙi kuma mai fafutuka Fela Kuti ya kasance ba'Afirke na farko da aka bai wa kyautar yabo ta Grammy wato Lifetime Achievement Award da ake bai wa wanda ya sadaukar da rayuwarsa yana rera waƙa. Fela ɗan Najeriya, ya yi fice ainun, ta hanyar rera waƙoƙin gwagwarmaya da kuma muradun talakawa. Shin ko me za ku iya tunawa a game Fela Kuti? Me za ku ce a game da wannan kyauta ta Grammy Awarda aka bayar bayan rasuwarsa? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Yau juma'a, rana ce da sashen Hausa na RFI ke bai wa masu sauraro damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwan da ke ci musu tuwo a ƙwarya, kama daga tattalin arziƙin, siyasa, zamantakewa da dai sauransu. Latsa alamar sauti don sauraren ra'ayoyi mabambanta...

Morocco da Senegal sun yi nasarar kaiwa wasan ƙarshe na gasar cin kofin Afrika ko kuma AFCON, nasarar da suka samu bayan ita mai masaukin baƙi ta doke Najeriya yayinda Senegal kuma ta doke Masar dukkaninsu a daren jiya Laraba, yayinda ake shirin haɗuwa don doka wasan ƙarshe na gasar tsakanin manyan ƙasashen 2 a ranar Lahadi. Anya kuwa ƙasashen na Masar da Najeriya sun taka rawar da ta dace gabanin fitar da su daga gasar? Wacce ƙasa kuke ganin za ta kai tsakanin labari wajen lashe kofin a wannan karon? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin....

Amurka ta sanar wa bai wa Najeriya wasu muhimman kayan aikin soji domin tunkarar ƙalubale na tsaro da ƙasar ke fama da shi. Rundunar Amurka mai kula da nahiyar Afirka wato Africom ce ta sanar da hakan, sama da makonni biyu da Amurka ta ƙaddamar da farmakin farko kan wasu wurare ta bayyana cewa maɓoyar yan ta'addace. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

A Najeriya, an koma makaranta bayan kammala hutun ƙarshen shekara, to sai dai yanzu haka akwai ɗimbin yara da ba sa zuwa makaranta saboda matsalar tsaro Mafi yawansu a jihohin Katsina, Neja, Sokoto, Zamfara da dai sauransu. Shin ko meye makomar yaran da ba sa samun damar zuwa makaranta sakamakon wannan matsala ta tsaro? Shin waɗannan matakai suku kamata a ɗauka don tunkarar wannan matsala da ke hana ɗimbin yara damar samun ilimi a wasu sassan Najeriya? Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Faruk Yabo.

Yau juma'a ce ranar da sashen Hausa na RFI ta cikin shirin Ra'ayoyinku masu sauraro ke baku damar bayyana abubuwan da ke ci muku tuwo a ƙwarya, kama daga sha'anin siyasa, tattalin arziƙi, zamantakewa da dai sauransu. Latsa alamar sauti don sauraren ra'ayoyi mabanbanta...

A gasar neman kofin Afirka da ke gudana a Morocco, a yanzu dai an tantance ƙasashe 8 da za su fafata da juna a matakin da ake kira Quarter Finals, inda Mali-Sénégal, Masar ta haɗu da Côte d'Ivoire, Kamaru ita da Morocco sai kuma Nigeria da za ta kece reni da Algéria. Waɗannan ƙasashe 8, tun farko su ne ake hasashen cewa za su iya taka gagarumar rawa a gasar. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Hukumar daidaita farashin wutar lantarki a Najeriya ta ce yanzu haka akwai sama da layuka milyan biyar da jama'a ke amfani da wuta ba tare da an ɗora su a kan mita ba. Wannan ya zo ne daidai lokacin da ake ci gaba da ɗiga ayar tambaya dangane da dalilan da suka sa aka gaza samar da mitocin a wadace. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

A Najeriya, gobe alhamis 1 ga watan Janairu, za a fara aiwatar da sabuwar dokar haraji ta ƙasa, a cikin yanayi da dokar ke shan suka saboda dalilai da dama. Yayin da jama'a ke cewa sabon tsarin karɓar haraji na matsayin ƙarin nauyi ne ga al'umma, hakazalika wasu ƴan majalisa sun yi zargin cewa abin da suka amince da shi ya sha bambam da abin da gwamnati ke shirin aiwatarwa. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Mahukuntan jamhuriyar Nijar sun shelanta kafa dokar-ta-ɓaci, wanda a ƙarƙashinta gwamnati za ta iya yin amfani da illahirin al'ummar ƙasar da kuma dukiyoyinsu duk lokacin da ta ga ya dace saboda tunkarar barazanar tsaro. Matakin ya zo ne kwanaki ɗaya bayan da Amurka ta ƙaddamar da farmaki kan maɓoyar ƴanbindiga a wani wuri da ke jihar Sokoton Najeriya daf da iyaka da Nijar. Shin ko me za ku ce a game da matakin? Anya hakan zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro da ƙasar ke fama da su? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Gwamnatin Najeriya ta ce da saninta Amurka ta ƙaddamar da hari jihar Sokoto da ke shiyar Arewa maso Yammacin ƙasar a makon daya gabata, inda ta ce an kai harin ne kan ƴan ta'addan da ta ce ke kwarara cikin ƙasar daga yankin Sahel. Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabir Muhammad Ɗan Bauchi.

Shirin ra'ayoyin ku masu saurare na wannan rana ya mayar da hankali ne kan yadda al'ummar Kirista suka gudanar da bikin Kirismeti na wannan shekara. Ku danna alamar saurare domin sauraren shirin tare da Abdullahi Isa.

Duk da cewa mafi yawan jama'a basu da cikakkiyar masaniya ko kuma fahimta a game da sabuwar dokar haraji da gwmanatin Tinubu za ta fara aiwatarwa daga ranar 1 ga watan janairu mai zuwa amma mafi yawan jama'a na nuna fargaba dangane da wannan doka. Wasu dai na kallon dokar a matsayin sabuwar hanya domin tatsar kuɗaɗe daga jama'a ba wai ba wai attajirai kawai ba harma daga talakawa, a daidai lokacin da wasu ke ganin gwamnati ta sauya dokar daga asalin wacce aka amince da ita. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...