POPULARITY
Categories
Shirin a wannan makon tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan nasarar da jihar Kano ke iƙirarin samu bayan fitar wani rahoto da ke cewa an samu raguwar mace-macen mata a lokacin haihuwa a sassan jihar wadda a baya ke sahun gaba wajen asarar rayukan ɗimbin mata a lokacin haihuwa ko goyon ciki Shiga alamar sauti don sauraron cikakken shirin..........
Shirin 'Mu Zagaya Duniya' na wannan makon tare da Oumar Sani ya yi bitar wasu daga cikin manyan labarai da suka fi ɗaukar hankali a makon da muka yi bankwana da shi ciki har da nasarar kuɓutar da dalibai tare da malamansu 40 a jihar Oyo da ke Najeriya bayan sun shafe kwanaki 50 a hannun wadanda su kayi garkuwa dasu.
Matsalar tsaro ta hare-haren da ‘yan ta'adda kan kai wa makarantu ko ɗalibai a sassan Najeriya, na ci gaba da ci wa al'ummar ƙasar tuwo a ƙwarya, la'akari da cewar ko a baya bayan nan, ‘yan bindiga sun kai hari tare da sace wasu ɗaliban wata Sakandare a ƙaramar hukumar Dekina da ke jihar Kogi. Wannan ya zo ne bayan hare-haren da a makwannin baya makarantun suka fuskanta a jihohin Oyo da kuma Borno. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da shugaban ƙungiyar Malaman Makarantu ta Najeriya, Comrade Audu Titus Amba. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Majalisar Wakilan Najeriya ta yi kira ga rundunar sojin saman ƙasar da ta buɗe ɓangaren hanyar Maiduguri zuwa Kano da ta toshe a anguwar Ngomari-Pompomari da ke wajen birnin Maiduguri kusan shekaru 10 wanda ke haddasa asarar ɗumbin rayuka. Ɗan Majalisa mai wakiltar Jere a jihar Borno, Hon. Satomi da ya gabatar da ƙudirin gaban Majalisar a makon jiya, ya yi wa Ahmed Abba ƙarin bayani dangane da girman matsalar da toshe hanyar ya haifar da kuma ƙoƙarin da gwamnati ke yi wajen ceto ɗalibai da malamai da Boko Haram ta yi garkuwa da su a Askira-Uba na jihar Borno. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana.
Shin ko addini na da tasiri ga rayuwar Musulmi, wajen hana su yin kabilanci? Shirin Taba Ka Lashe na wannan lokaci, ya yi nazari a kan wannan batu.
Yayin da ake ci gaba da jinjina wa rundunar sojin Najeriya saboda nasarar ceto ɗalibai da malamai 44 da ƴanbindiga suka yi garkuwa da su a jihar Oyo, wasu na gani cewa ya kamata mahukunta su ƙara azama don ceto ɗaruruwan mutanen da ake ci gaba da yin garkuwa da su a sasan ƙasar. Ko a jiya lahadi ɗimbin mutane ne suka gudanar da zanga-zangar neman gaggauta ceto ɗalibai da dama da ake yin garkuwa da su a jihar Borno ciki har da waɗanda aka sace rana ɗaya da na jihar Oyo. Abdoulkarim Ibrahinm Shikal ya zanta da Ibrahim Garba Wala da ke bin diddigin wannan batu na taɓarɓarewar tsaro a Najeriya, ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....
Shirin a wannan makon zai leka Gabas ta Tsakiya inda rikici ya sake barkewa tsakanin Amurka da Iran abin da ya kawo karshen yarjejeniyar fahimtar juna ta watanni uku da suka cimma a tsakaninsu. Bayan nan, shirin zai taɓo wasu mahimman lammuran da suka wakana a sassan yammacin nahiyar Afirka, musamman Najeriya, Nijar da Kamaru.
Cikin makon nan, kasuwar hada-hadar hannayen jarin Najeriya, ta kafa tarihin zama mafi ƙarfi gami da bunƙasa a faɗin Duniya, bayan zarta mai riƙe da kambun a baya bayan nan, wato takwararta ta Korea ta Kudu. Rahoton kamfanin Bloomberg ya nuna cewa, zuwa yanzu Kasuwar ta Najeriya ta samu tagomashi ne da kaso 67 cikin 100, yayin da ta Korea ta Kudu ke da kaso 66. Domin jin ƙarin bayanin kan dalilan samun wannan nasara, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Ƙasim Garba Kurfi, ɗaya daga cikin masu ruwa da tsaki a kasuwar hada-hadar hannayen jarin ta Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawar...
Majalisar dattijan Najeriya ta bukaci gwamnatin kasar da ta dakatar da shirin yin afuwa ko kuma sauya ɗabi'un tubabbun ƴan ta'adda a wani yunƙuri na dawo da su cikin al'umma, wanda ta ce ba ya taimakawa ƙoƙarin da ƙasar ke yi wajen yaƙi da ta'addancin da ya yi mata katutu. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Najeriya na tattaunawa da China wajen ganin ta samu goyon bayan da ya dace a fasahar zamani da kuma makamai domin shawo kan matsalolin tsaro da suka addibi ƙasar. Sabon jakadan Najeriya a ƙasar China Janar Abdurrahman Bello Dambazau mai ritaya ya bayyana haka a tattaunawar da suka kayi da Bashir Ibrahim Idris. Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirar.
Mai Alfarma Sarkin Musulmin Najeriya Muhammadu Sa'ad Abubakar na uku, ya ce mutunta addinan juna, daina furta kalaman ƙiyayya ko tsatsauran ra'ayi, abubuwa ne da za su iya taimakawa ta fannin kyautata zamantakewa a tsakanin al'umma. Wannan dai gargaɗi ne da ke ƙunshe a sanarwar da aka fitar bayan ganawar da aka yi a babban masallacin birnin Abuja tsakanin mai alfarma Sarkin Musulmin da kuma tawagar manyan jami'an Fadar Vatican ƙarƙashin jagorancin Archibishop Paul Richard Gallaghera. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Shirin kasuwa akai miki dole dake bibiyar harkokin kasuwanci da tattalin arziki na wannan makon tare da Ahmed Abba ya mayar da hankali ne kan yadda ci gabar fasahar zamani da aka samu a fannonin haɗar-haɗur ƙudi a Najeriya, ke shafar al'ummomi a yankunan ƙarƙara.
A wannan makon, shirin ya nufi yankunan karkara, inda inda gine-ginen makarantu ke ci gaba da kasancewa a matsayin kango, kasancewar babu dalibai. A wasu wuraren kuma, azuzuwan sun zama fanko, yayin da matasa da yara suka ƙaurace wa shiga, ‘yan mata na fita birni yin tallace-tallace, su kuma samari na dambatawa da aikin ƙwadagon fasa duwatsu da ɗiban yashi. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da sabon rahoton hukumar UNICEF ya nuna cewa, jihohin Kano, Katsina, da Jigawa ne ke kan gaba a faɗin Najeriya wajen yawan yaran da ba sa zuwa makaranta, inda a faɗin kasar kuwa, akwai yara sama da miliyan goma sha takwas da dubu ɗari uku da makoma ta iliminsu ke cikin haɗari. Sau da yawa, wannan zargi na komawa ga gwamnati, sai dai abin tambayar shine, shin ko laifin na iyaye ne da al'umma, ko kuwa suma hukumomi akwai nasu kason? Mun ziyarci garin Meshumi da ke karamar hukumar Ungoggo a jihar Kano, inda shirin ya tarar makarantar firamare na nan a gine, amma dakin karatu ya zama kufai. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin, tare da Shamsiyya Haruna
Shirin na Lafiya Jari ce zai a wannan makon tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan zazzaɓin Typhoid, cuta mai haɗari wadda ƙwayar cutar Salmonella Typhi ke haddasawa, inda ta kan yaɗu ta hanyar abinci ko ruwan da ya gurɓata. Danna alamar sauti don sauraron cikakken shirin.......
A Najeriya, daidai lokacin da ake neman sanin matsayin shugaba Bola Tinubu dangane da zargin kafawa da kuma tafiyar da wata ma'aikatar jabu a ƙarƙshin gwamnatin tarayya, sai kuma ga wasu bayanai daga Asusun Lamuni na Duniya IMF da ke cewa gwamnatin ta kashe sama da Naira triliyan 8 waɗanda sam kasafin kuɗin ƙasar bai san da su ba. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hira da Abdoulklarim Ibrahim Shikal ya yi da Kwamrad Nasiru Kura mai fafutukar yaƙi da rashawa a ƙasar..........
Ƙungiyar kare hakin bil Adam Amnesty International ta zargi gwamnatin shugaba Bola Ahmad Tinubu da gaza kare ƴan Najeriya daga matsalolin ta'addanci da na tattalin arziki da ake fama da shi a Najeriya.........
Ƙungiyar Amnesty International a Najeriya ta zargi gwamnatin shugaba Bola Ahmad Tinubu da gaza kare ƴan Najeriya daga matsaloli na ta'addanci da na tattalin arziki da ake fama da shi. Ruƙayya Abba Kabara ta tattauna da daraktan Amnesty a Najeriya, Malam Isa Sanusi kan rahoton nasu. Latsa alamar sauti don sauraren sa....
Babban Bankin Najeriya na CBN ya sanar da soke lasisin wasu ƙananan bankuna 46 saboda saɓawa ƙa'idar aiki. Waɗannan bankuna sun haɗa da guda 12 a Kano da wasu takwas a Lagos, baya ga wasu ɗaiɗaikun jihohi. Domin sanin tasirin wannan mataki, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Isa Abdullahi, masanin tattalin arziki, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.
Shirin "Kasuwa Akai Miki Dole" na wannan makon tare da Ahmed Abba ya mayar da hankali ne kan yadda ƴan Najeriya suka rungumi ɗaukar bashin kiran waya, wanda wani rahoto ya ce, a bara kaɗai anci bashin kiran waya da ƙudinsu ya kai Naira Tiriliyan 4 da biliyan 61. Wasu bayanai da cibiyar fintech firms Optasia mai tattara alƙaluman shige da ficen kuɗaɗen layukan sadarwa ta fitar a baya-bayan nan, ya nuna yadda ƴan Najeriya waɗanda ke amfani da wayar hannu, a kullum ke tururuwar ciwo bashin katin kira wanda ke ɗauke da kuɗin ruwa. Rahoton cibiyar ya ce a shekarar 2025 kawai ƴan Najeriya sun ci bashin katin kiran waya da ya kai Dala biliyan 3 da miliyan 18 kwatankwacin Naira tiriliyan 4 da biliyan 61, abinda ke haskawa ƙarara cewa adadin ya ƙaru da kaso 12.3 cikin 100 idan an kwatanta da shekarar 2024, wadda ya kasance Naira tiriliyan 4 da biliyan 38. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin na wannan mako ya mayar da hankali ne kan taron ƙaddamar da sabon littafin tarihin nan mai suna 'Mu San Magabata', wanda fitaccen matashin marubuci Kabiru Ahmad Kwalli ya rubuta da aka gudanar a jihar Kanon Najeriya. Taron ya haɗa masana, sarakuna, da ɗandazon al'umma domin duba yadda za a ceto tarihin ƙasar Hausa da ke shirin bacewa. Wannan littafi, kamar yadda masana da dama suka bayyana, ya zo ne a daidai lokacin da matasan yanzu ke ƙara nisanta da asalin tarihinsu. To ko me ya sa mawallafin, Kabiru Ahmad Kwalli, ya ɗauki tsawon lokaci yana wannan bincike? Ga abinda ya shaida mana lokacin da muke zantawa da shi.
An shiga wani yanayi na fargaba da tsananin tashin hankali a Afirka ta Kudu, yayin da yau wa'adin ranar 30 ga watan nan na Yuni ke cika, game da zanga-zangar da wasu ƙungiyoyin ƙyamar baki suka shirya don tilasta wa baƙin da ba su da takardu barin ƙasar. Ko da yake hukumar 'yansandan ƙasar ta ce ta tura ɗimbin jami'an tsaro zuwa yankunan da ake sa ran za su fuskanci tashin hankali, kamar su Pretoria, Johannesburg, da KwaZulu-Natal. Shamsiyya Haruna ta tattauna da Hajiya Rakiya Sa'idu, wata yar Najeriya da ke aiki a jami'ar Cape Town a Afirka ta Kudun, dangane da halin da suke ciki.
Duk da cewa an samu faɗuwar farashin ɗanyan man fetur a kasuwar duniya sakamakon sulhun tsakanin Amurka da Iran, amma har yanzu ana ci gaba da fama da tsadar wannan makamashi a mafi yawan ƙasashen duniya. A Najeriya tuni Hukumar kare masu amfani da kayan masarufi ta ƙasar ta yi gargaɗin cewa ko dai dillalan mai su karya farashi ko kuma ta ɗauki matakan ladaftarwa a kansu. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Mai marataba sarkin Sukur ke nan Luka Gizik, yake bayyana irin jimawar da masarautarsa da ke tsaunukan na Mandara a jihar Adamawan Najeriya ta yi.
A Najeriya ra'ayoyi sun sha bambam a tsakanin al'umma dangane da shirin bai wa jihohi damar kafa rundunar ƴansanda don inganta sha'anin tsaro a ƙasar. Tuni dai Majalisun Tarayyar Ƙasar biyu suka amince da daftarin dokar da ke bayar da damar ɗaukar wannan mataki, kamar dai yadda gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta buƙata. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon Kwamishinan Ƴansanda CP Muhammed Indabawa mai ritaya, domin jin yadda masana aikin ɗansanda ke kallon matakin. Latsa alamar sauti don sauraren zantawarsu...
Yayin da damina ta fara kankama a Tarayyar Najeriya, wani abu da ake fargaba shi ne yadda matsalar tsaro ke iya haddasa tarnaki ga aikin gona hatta ma a wannan shekara. Kusan a kowace rana za a samu labarin cewa an kai hare-hare kan manoma da kan yi sanadiyyar kisa, yin garkuwa domin neman kuɗin fansa, yayin da a wasu lokuta ake tilasta wa manoman biyan haraji kafin ba su damar shiga gonakinsu. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Fulani makiyaya a Najeriya sun koka dangane da irin tsangwama da kuma barazanar da suke fuskanta a kudancin ƙasar, sakamakon matsalar tsaro da kuma garkuwa da mutane da ake fama da shi. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da shugaban ƙungiyar Miyetti Allah, Baba Usman Ngelzerma. Ku danna alamar sauraro domin jin cikakkiyar tattaunawar.
A wannan makon, shirin ya mayar da hankali ne kan babban taron ƙungiyar Lagos Studies Association karo na goma da aka kammala a ƙarshen mako, wanda ya saba haɗa masana, malaman jami'o'i, da masu bincike daga sassa daban-daban na Najeriya da ƙasashen waje domin tattauna halin da ilimi yake ciki a nahiyar Afirka cikin wannan ƙarni. Wannan taro, wanda aka kafa shi shekaru goma da suka gabata a birnin New York, an dawo da shi gida Afirka domin tattauna ainihin matsaloli da ci gaban nahiyar ke fuskanta, kuma a bana, fiye da rukunonin tattaunawa 340 ne aka shirya, inda aka haɗa masana daga sassan duniya. Shekarar 2026 ta yi daidai da cikar kungiyar LSA shekaru 10 da kafuwa, inda aka gudanar da taron ƙarƙashin taken makomar ilimin nahiyar Afirka a wannan ƙarni. Wani sashe mai muhimmanci a taron shi ne tattaunawa kan littafi na musamman mai suna 'Our Digital Lives and Indigenous Pathways', wanda masana suka duba yadda za a haɗa fasahar zamani da dabarun gargajiya na Afirka don samun ci gaba mai dorewa. Baya ga tattaunawar kimiyya, taron ya haɗa da baje kolin fasaha na musamman mai taken 'Histories on Scissors: The Black Essence on the Map of Being' wanda Dominic James Aboi daga Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria ya gabatar. An kuma tattauna makaloli kan addini da rashin addini a Arewacin Najeriya. An dai gudanar da wannan taro ne domin nazarin al'adun zamani da na gargajiya, inda masana suka gabatar da maƙaloli kan tarihin Afirka, al'adu, da kafafen yaɗa labarai haɗi da baje kolin dabarun bincike na zamani. A taron na bana, masana sun gano muhimman abubuwa da suka shafi makomar nahiyar Afirka ta fuskar ilimi, zamantakewa, da fasaha, kuma babban jigon da aka mayar da hankali akai shi ne yadda za a fassara binciken ilimi ya zama abin da zai amfani rayuwar al'umma kai-tsaye. Haka zalika an gano cewa ko da yake yawan binciken da masana da ke zaune a cikin Afirka ke fitarwa ya ƙaru sosai, amma ingancinsa da kuma bayyanarsa a manyan jaridun ilimi na duniya ya ragu sosai.
Tawagar da Majalisar Ɗinkin Duniya ta tura zuwa Najeriya don gudanar da bincike a game da zargin kisa, yin garkuwa da mutane da kuma tilasta wa wasu barin muhallansu saboda dalilai na addini, ta ce wannan ba gaskiya ba ne. Jagorar tawagar Farfesa Nazila Ghanea, a ƙarshen ziyarar gani da ido ta kai a ƙasar, ta ce mutane na yin waɗannan zarge-zarge ne saboda gazawar gwamnati wajen ba su kariya da kuma gaza hukunta waɗanda ke aikata laifukan. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Kamar kowace shekara, a bana ma ana hasashen samun ambaliyar ruwa a wasu ƙasashen yammacin Afrika, inda akan samu rasa rayuka da dukiya mai tarin yawa. A Najeriya, an sha samun hasarar rayuka a sanadin matsalar ambaliyar ruwan, da kan rutsa da wasu yankunan ƙasar.
Shirin na wannan mako ya mayar da hankali kan bitar muhimman labaran da suka faru a sassan duniya cikin makon da muke bankwana da shi. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Oumarou Sanni.
Gobe ne hukumar zaɓe a Najeriya ke gudanar da zaɓen gwamnan Ekiti da ke yankin kudanci, inda ƴan takara 13 za su fafata. Ana kallon wannan zaɓen a matsayin zakaran gwajin dafi ga sabon shugaban hukumar zaɓen Farfesa Joash Amiputan. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai magana da yawun hukumar Hajiya Zainab Abubakar. Latsa alamar sauti don sauraren yadda zantawarsu ta gudana...
Yayin da ake shirin gudanar da zaɓuka cikin watan Fabarairun shekaru mai zuwa a Najeriya, wani abu da ke faruwa shi ne taƙaddamar ƴan siyasa a gaban kotunan ƙasar. Kusan a kowane mako, za a ji cewa kotu ta yanke hukunci kan jam'iyyun siyasa, lamarin da ke iya nisantar da su daga tsayawa takara a waɗannan zaɓuka. Wannan ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Ƙungiyar Kare Hakkin Bil'adama ta Amnesty International ta bukaci gwamnatin Najeriya da ta dauki matakai na gaggawa don kare dalibai da kuma ceto wadanda har yanzu suke hannun masu garkuwa da mutane. Ƙungiyar ta jaddada cewa gazawar hukumomi wajen kawo ƙarshen hare-hare da sace-sacen dalibai na nuna cewa rayuwar yara na cikin matsananciyar barazana. Ƙungiyar ta bukaci Shugaba Tinubu da ya dauki matakin gaggawa na kawo karshen satar yara da kai hari makarantu, tana mai cewa iyaye sun gaji da romon bakar da ake musu. Amnesty ta zargi gwamnatin da kasa kare kananan hukumomi, musamman a jihar Zamfara da sauran yankunan Arewa daga hare-haren yan bindiga. Kungiyar ta nuna damuwa kan yadda tsadar rayuwa da matsalar tsaro ke raba iyalai da muhallansu, lamarin da ke jefa yara da dama cikin yunwa da rashin ilimi. Kan wannan ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Daraktan Ƙungiyar a Najeriya Isah Sunusi. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Gwamnatin Jihar Filato da ke Najeriya ta bayyana matuƙar damuwar ta dangane da yadda ta ce wasu na amfani da hukuncin wata kotu dangane da baiwa wasu Hausawa takardar zama ƴan ƙasa domin haifar da tashin hankali a tsakanin al'ummar da suka kwashe shekaru da dama su na zaman lafiya da juna. Gwamnatin ta ja kunnen al'umma inda ta ce waɗanda ba su gamsu da hukuncin ba na da hurumin ɗaukaka ƙara kamar yadda dokokin ƙasa da suka tanada. Bashir Ibrahim Idris ya tuntuɓi kwamishiniyar yaɗa labaran jihar da ta gabatar da sanawar, Joyce Ramnap kuma ga yadda zantawarsu ta gudanar a kai.
Shirin ya duba zamantakewa da cudanyar Kiristoci da Musulmi a jihar Filato da ta bambanta da ta sauran wurare a Najeriya,
Shirinmu na yau ya leƙa sassan arewacin Najeriya da Jamhuriyar Nijar, tare da duba yadda wani fitaccen kiɗan gargajiya, wato kiɗan Gurmi, ke fuskantar barazanar bacewa a fadin ƙasar Hausa. Shin me ke janyo haka, kuma wane canji fasahar zamani ta kawo? Gurmi, kayan kiɗa ne da aka sani tun kaka da kakanni, wanda ƙera ta hanyar amfani da ƙoƙon ƙwarya da aka rufe shi da fatar dabba, musamman fatar guza, sannan a ɗaura masa tsirkiya guda biyu ko uku. A cikin shekarun da suka gabata, manyan mawaƙa irinsu Rabi'u mai Gurmi Gumel da Rabe mai Gurmi Jibia sun zagaya duniya suna baje kolin wannan fasaha. Amma a yau, idan ka zagaya biranen ƙasar Hausa, da kyar kake jin sautin wannan kiɗa, maimakon haka, sautin kiɗan na'urorin zamani na matasa sune suka mamaye ko'ina. Duk da wannan ƙalubale, wasu mawaƙan zamanin na ƙoƙarin haɗa sautin gurmi da kiɗan zamani don janyo hankalin matasa da kuma kaucewa ɓacewar wannan muhimmin kiɗa na al'ada.
Wata babbar kotu a Najeriya, ta bai wa hukumar zaɓe ta INEC umarnin soke wasu jam'iyyun adawa har guda biyar, saboda saɓawa dokokin zaɓen shekarar 2023 na ƙasa samun kashi 25 na ƙuri'un da aka kaɗa. Jam'iyyun sun haɗa da ADC da AA da APP da ZLP da Acoord Party. Tuni wannan hukunci ya haifar da mahawara da kuma zargin yunƙrin haa 'yan adawa shiga zaɓe mai zuwa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Abubakar Sadiq Gombe, shugaban Jam'iyyar adawa ta SDP. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
A Najeriya, mutuwar tsohon kakakin rundunar sojin ƙasar Janar Abubakar Rabe mai ritaya a hannun ƴan bindiga, lamari ne da ya yi matuƙar ɗaga hankulan jama'a, tare da ƙara haifar da shakkun game da yiyuwar cewa anya kuwa za a iya magance matsalar tsaro a ƙasar? An dai gaza ceto janar Rabe daga hannun ƴanbindigar, duk da cewa ya share kusan makonni biyu a hannunsu. Shiga alamar sauti don sauraron hirar da Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya yi da Air Commodore Ahmed Tijjani Baba Gama mai ritaya......
Ranar Alhamis 11 ga wannan watan aka yi bikin buɗe gasar cin kofin duniya karo na 23, gasar da itace karo na farko da ƙasashe 3, Amurka da Canada da kuma Mexico su ka karbi baƙunci, sai dai kuma an gudanar da zanga-zanga a wasu sassa na birnin ƙasar. Ƙasashe 48 ne ke fafata domin samun zakaran bana kuma yan wasa 1,248 da alkalan wasa 52 za su jagoranci wasanni 104 da za'a kwashe kwanaki 39 ana yi. A cikin shirin akwai labarin, shugaban Amurka Donald Trump, da ya ce ya soke shirinsa na kai munanan hare-haren da ya shirya yi a Iran, sakamakon wata tattaunawar da yace ya yi da wasu ƙusosshin gwamnatin ƙasar, Ikrarin da ya zuwa yanzu hukumomin ƙasar basu ce komai akai ba. Haka zalika, Majalisar Dokokin Najeriya ta amince da dokar kafa ƴansandan jihohi da gagarumar rinjaye, matakin da zai bai wa gwamnatocin jihohi damar kafa rundunar da za ta taimaka wajen magance matsalolin tsaron da suka addabi ƙasar. A Jamhuriyar Nijar gwamnati ce ta rattaɓa hannu a kan dokar haramta auran jinsi ko kuma mu'amalar jinsi guda wanda ta tanadi hukuncin ɗaurin da ka iya kai wa shekaru 20 a kan duk wanda aka samu da laifin yin haka. A wani abu da ba'a saba gani ba, Kungiyar mayaƙan JNIM mai alaƙa da Al Qaeda reshen Mali ta yi tayin bayar da tukwicin miliyoyin Yuro ga duk wanda ya ba ta bayanai kan inda shugaban kasar Assimi Goita da manyan jami'an sojinsa suke, a yayin da ta bayyana gwamnatin a matsayin haramtacciyar. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin, tare da Oumarou Sani.
Wasu fitattun mutane a Najeriya, da suka haɗa da tsohon shugaban hukumar zaɓe Farfesa Attahiru Jega, da tsohon jakadan ƙasar a Majalisar Dinkin Duniya Farfesa Ibrahim Gambari, sun yi gargaɗi a game da irin barazanar da ƙasar ke fuskanta sakamakon rashin tsaro, da yadda ake yi wa tsarin gudanar da zaɓuka na ƙasar karen-tsaye. Kan wannan na gana da guda daga cikin masu ruwa da tsakin da suka yi wannan jan hankali, wato Hussaini Abdu na ƙungiyar Action Aid. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Asusun bada lamuni na duniya IMF ya ce sauye-sauyen da gwamnatin Najeriya ke yi na ƙarfafa tattalin arzikin ƙasar, sai dai kuma sun haifar da ƙarin ƴan Najeriya sama da miliyan 60 da suka faɗa cikin talauci. Ku danna alamar saurare domin jin tattaunawar Bashir Ibrahim Idris, da masanin tattalin arziki a Najeriya Samaila Abdullahi Muhammad kan wannan batu.
Yankin arewacin Najeriya na ci gaba da ɗanɗana kuɗar sa a hannun ƴan bindiga, waɗanda ke kai hari suna sace mutane da kuma hallaka su ba tare da ƙauƙautawa ba. ko a jiya sai da ƴan bindigar suka yi garkuwa da wata tawagar masu neman sulhu da su a jihar Zamfara, baya ga wasu ɗaruruwa da ke hannun su a jihohi da dama, a daidai lokacin da gwamnoni da ƴan majalisun yankin suka mayar da hankali a kan siyasa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Bello Bada na Jami'ar Usman Dan Fodio da ke Sokoto. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana...........
Shirin lafiya Jari ce a wannan makon ya mayar da hankali kan yadda mata suka rungumi tsarin gyaran jiki ta fannoni daban-daban kama daga magungunan sha ko mayukan shafawa ko kuma salon amfani da na'ura da nufin ƙawata sura. Wasu daga cikin batutuwa mafi jan hankali a wannan babi na gyaran jiki shi ne tayar da komaɗar fata da sauran sassan jiki don killacewa ko kuma kange kai daga bayyanar tsufa, kuma guda cikin tsarin da ake amfani da shi shi ne na'urorin zamani wanda ƙwararru a wannan fanni na fata gashi da kuma ƙumba ke cewa kafin yanzu abin bai samu karɓuwa a Najeriya ba.
Gwamnatin jihar Lagos a Najeriya ta ƙaddamar da wani gagarumin samame kan mabarata da suka cika titunan birnin, inda aka cafke ɗimbin mabarata ciki har da masu fama da naƙasa da kuma waɗanda ke yi musu jagora, kazalika da ma waɗanda ke cikin ƙoshin lafiya. Kwamishin Ma'aikatar matasa da jin ɗadin jama'a na jihar Mobolaji Ogunlende, ya ce daga ƙarshen watan Mayun da ya gabata zuwa yau, sun cafke sama da mutane dubu 1 da 300 tare da hukunta aƙalla 450 daga cikinsu. Lura da cewa mafi yawan waɗanda suka riƙi bara a matsayin sana'a a birnin Lagos ƴan asalin Arewacin Najeriya ne, wannan ya sa Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da ɗaya daga cikin shugabannin al'ummar yankin da ke zaune a jihar, Alhaji Sa'adu Yusuf Ɗandare Gulma, ga kuma ƙarin bayanin da ya yi masa a game da wannan samame. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu.............
A yau wannan shiri zai ba da hankali ne akan yadda har yanzu, kananan manoma a Nigeria na nan kan tsarin noma na Kaka da Kakanni, lamarin da ake gani yana hana ruwa gudu wajen tabbatar da cimma burin kasar na kasancewa mai dogaro da-kai a fannin samun wadatar abinci.
Shirin na wannan mako ya waiwaya halin da duniya ke ciki a fannin tsaro, rikice-rikice da kuma Diflomasiyya
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.