POPULARITY
Categories
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Shirin "Duniya Akai Miki Dole" tare da Faruk Muhammad Yabo a wannan mako ya yi duba ne kan sabbin harajin da gwamnatin Najeriya ke shirin karɓa a hannun jama'ar ƙasar, a wani yanayi da ƙasar ke fatan tattara wani ɓangare na kuɗaɗen tafiyar da harkokinta. Shirin a wannan mako ci gaba ne na makon da ya gabata dangane da wannan dokar haraji wadda al'ummar Najeriya ke ci gaba da suka akanta. A cikin shirin akwai tattaunawa da ƙwararru a fagen na tattalin arziƙi waɗanda da dama suka yi suka ga sabon tsarin harajin na shugaba Tinubu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Mu kan komo da karfe 8 na safe agogon Najeriya da Nijar domin sake gabatar muku da labarai da hirarraki, da sharhin jaridu kama daga Najeriya zuwa Nijar har Ghana, da kuma ra'ayoyinku.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Duk da cewa mafi yawan jama'a basu da cikakkiyar masaniya ko kuma fahimta a game da sabuwar dokar haraji da gwmanatin Tinubu za ta fara aiwatarwa daga ranar 1 ga watan janairu mai zuwa amma mafi yawan jama'a na nuna fargaba dangane da wannan doka. Wasu dai na kallon dokar a matsayin sabuwar hanya domin tatsar kuÉ—aÉ—e daga jama'a ba wai ba wai attajirai kawai ba harma daga talakawa, a daidai lokacin da wasu ke ganin gwamnati ta sauya dokar daga asalin wacce aka amince da ita. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...
Mu kan komo da karfe 8 na safe agogon Najeriya da Nijar domin sake gabatar muku da labarai da hirarraki, da sharhin jaridu kama daga Najeriya zuwa Nijar har Ghana, da kuma ra'ayoyinku.
Mutane da suka tsinci kansu a cikin masu buƙata ta musamman sakamakon nau'ikan nakasar da suka fama da ita sun share shekaru suna fuskantar giɓi babba a muhimman fannonin rayuwa daban daban, ciki kuwa har da samun guraben ayyukan yi ko da kuwa a ce sun yi katarin tsallake shingen samun ilimi, matsalar da ta fi ƙamari a ƙasashe masu tasowa ciki har da na Nahiyar Afrika. Mutane da suka tsinci kansu a cikin masu buƙata ta musamman sakamakon nau'ikan nakasar da suka fama da ita sun share shekaru suna fuskantar giɓi babba a muhimman fannonin rayuwa daban daban, ciki kuwa har da samun guraben ayyukan yi ko da kuwa a ce sun yi katarin tsallake shingen samun ilimi, matsalar da ta fi ƙamari a ƙasashe masu tasowa ciki har da na Nahiyar Afrika. Kan wannan batu shirin Ilimi Hasken rayuwa na wannan lokaci zai tattauna, bayan da ya yi tattaki zuwa Jihar Jigawa da ke tarayyar Najeriya, akan ƙorafin da wasu fama da nakasar suka yi a bisa ganin cewar suna neman rasa damar samun guraben ayyukan yi da suka cancanci dafewa.  A latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Mu kan komo da karfe 8 na safe agogon Najeriya da Nijar domin sake gabatar muku da labarai da hirarraki, da sharhin jaridu kama daga Najeriya zuwa Nijar har Ghana, da kuma ra'ayoyinku.
Shugaban Najeriya Bola Ahmad Tinibu ya ƙaddamar da ababen hawa na sufuri masu amfani da lantarki guda dubu 3 da 620 da gwamnatin jihar Borno ta tanadar domin sauƙaƙa sufuri a tsakanin al'ummarta. Motocin sun haɗa ne da Kekuna dubu 3 da babura masu ƙafa 3 ko kuma adaidaita sahu guda 500 sai kuma ƙanana da manyan Motocin safa ko kuma bas bas masu ɗaukar mutum 20 da 42 guda 100, kari ga wasu motoci 650 masu amfani da lantarki da gwamnati ta samar don sufuri. Dangane da wanna ne Faruk Muhammad Yabo ya tattauna da Dauda Iliya mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Borno a fannin watsa labarai inda ya fara da tambayarsa yadda ababen hawan suke da kuma yawansu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar...
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Mu kan komo da karfe 8 na safe agogon Najeriya da Nijar domin sake gabatar muku da labarai da hirarraki, da sharhin jaridu kama daga Najeriya zuwa Nijar har Ghana, da kuma ra'ayoyinku.
Ibrahim Sherif bakano ne dan Najeriya da ya bar gida tun yana dan saurayi zuwa Birtaniya domin aikin sa kai. Inda daga baya ya nausa Afirka ta Kudu inda ya cika burinsa na zama matukin jirgin sama, har ma ya buge da tsere keke a can.
Adamu Garba II matashi ne mai kwarin gwiwa sannan wanda ya ke dan kasuwar da yayi iliminsa a tsakanin Najeriya har zuwa Amurka. Yana daga cikin 'yan takarar Shugaban Kasar Najeriya a shekarar 2023 mafi karancin shekaru a tsakanin masu neman wannan kujera a kasar da ta fi kowa ce kasar Afirka yawan al'umma da kuma karfin arzikin man fetur. Shine kuma wanda 'yan uwa da abokan arziki suka tara wa sama da naira miliyan 80 don yin takara a jam'iyyar APC amma kwatsam sai ya canja sheka zuwa YPP.
Aisha Hassan matashiya ce 'yar asalin jihar Neja a Najeriya da ta girma a Ingila, sannan ta yi karatu mai zurfi a fannin hada-hadar kasuwanci. Bugu da kari ba a barta a baya ba wajen shiga fagen kafafen sadarwar zamani inda take koyar da salon sa sutura da daurin dan-kwali a shafukanta na yanar gizo.
Mun sami tattaunawa Aminu Waziri Tambuwal gwamnan jihar Sokoto, kuma shugaban tawagar yakin neman zaben Alhaji Atiku Abubakar a matsayin shugaban Najeriya a 2023 da ke tafe. Inda ya bamu labarin kuruciyarsa har zuwa girma da shiga fagen siyasa. Ba mu bar shi ba sai da ya fada mana dalilinsa na janye wa daga takarar shugabancin Najeriya don mara wa Atikun a karkashin jam'iyyar PDP.
Kamaluddeen Kabir, dan asalin jigar Katsina ne mai digirin digirgir wanda yayi karatunsa a tsakanin Najeriya da Birtaniya sannan kuma Malami ne yanzu haka a jami'ar Umaru Musa 'YarAdua da ke jihar ta Katsina.
Na yi hira da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa ta Najeriya, Mai Girma Sanata Barau I. Jibrin (Maliya) game da rayuwarsa da kuma gudunmawarsa a siyasance, musamman ga 'yan Arewacin Najeriya.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Mu kan komo da karfe 8 na safe agogon Najeriya da Nijar domin sake gabatar muku da labarai da hirarraki, da sharhin jaridu kama daga Najeriya zuwa Nijar har Ghana, da kuma ra'ayoyinku.
Tarihin kafuwar kungiyar SASSAKAWA foundation dake taimakawa a harkar manoma a Najeriya, wai shin da gaske ne kungiyar daga Japan aka kafata kuma wanene ya kafata? Akan wannan tambaya ce muka zanta da Dr Abdulhamid Gambo mataimakin shugaban SASSAKAWA Foundation a Najeriya.
Karatu ne ya kai iyayen Iman Yusuf Al-Hassan zuwa Amurka, wanda su 'yan asalin jihohin Kano da Jigawa ne a Arewacin Najeriya, amma kuma kaddarar zama ta kama su har suka hayayyafa. Iman ta fada min yadda take da burin zaman Najeriya duk kuwa da cewa a Amurka aka haifeta ta girma.
Muhammad Marzuq Abubakar Ungogo wani hazikin matashin likitan dabbobi ne da yake digirin-digirgir a birtaniya, tare da yin binciken a fanni kwayoyin cututtukan dabbobin da kuma gano dalilan da ke hana wasu magungunan dabbobin aiki da ya kamata su yi. Ya bayyana mana tarihin rayuwarsa da ma yadda aka yi yayi digiri na biyu a Turai da ma ci gaba da digirinsa na uku. Ya tabo batun yadda yake ganin noma da kiwo a kasashe kamar Najeriya.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Majalisar wakilan Najeriya ta gudanar da wasu sauye-sauye ga dokar zaɓen ƙasar yayin zaman da ta yi a jiya Alhamis. Kuma daga cikin batutuwan da suka fi ɗaukar hankali akwai ƙara yawan kuɗaɗen da doka ta ƙayyade ɗan takara zai iya kashewa a yaƙin neman zaɓe, da kuma tilasta amfani da na'urorin tantance masu kaɗa ƙuri'a, gami da watsa sakamakon zaɓe kai tsaye. Sauyin dai na nufin daga yanzu masu neman shugabancin ƙasa na iya kashe Naira biliyan 10, saɓanin Naira biliyan 5, yayin da aka ƙara kasafin ‘yan takarar gwamna daga Naira Biliyan 1 zuwa biliyan 3. Domin jin yadda masana doka ke kallon wannan mataki, Nura Ado Suleiman ya tuntuɓi Barista Al-Zubair Abubakar da ke Najeriya. Latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana...
Mu kan komo da karfe 8 na safe agogon Najeriya da Nijar domin sake gabatar muku da labarai da hirarraki, da sharhin jaridu kama daga Najeriya zuwa Nijar har Ghana, da kuma ra'ayoyinku.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Mu kan komo da karfe 8 na safe agogon Najeriya da Nijar domin sake gabatar muku da labarai da hirarraki, da sharhin jaridu kama daga Najeriya zuwa Nijar har Ghana, da kuma ra'ayoyinku.
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya maye gurbin Engr Faruk Ahmed da Aliko Dangote ya zarga da hana ruwa gudu wajen harkokin kula da kasuwancin mai da kuma bada lasisi ta NMDPRA, tare da shugaban hukumar NUPRC. Fadar shugaban Najeriya ta ce jami'an biyu sun sauka daga mukaman su ne bisa dalilai na ƙashin kan su. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ibrahim Garba Wala kan lamarin. Ku latsa alamar sauti don jin yadda tattaunawarsu ta gudana...
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Mu kan komo da karfe 8 na safe agogon Najeriya da Nijar domin sake gabatar muku da labarai da hirarraki, da sharhin jaridu kama daga Najeriya zuwa Nijar har Ghana, da kuma ra'ayoyinku.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Hadiza Aliyu da aka fi sani da Gabon, na daya daga cikin fitattun taurarin fina-finan Hausa mafi shahara. Ta shiga Najeriya a lokacin da bata jin Hausa, amma kuma tana son zama tauraruwar fina-finan Hausa na Kannywood. Yanzu kuma sai gashi mun da cewa tana yawan tafiye-tafiye zuwa kasashen duniya, ciki har da Amurka inda muka yi wannan hirar da ita.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Maimuna Sulaiman Bichi da aka fi sani da ‘yar Bichi ko Lolo's Kitchen ‘yar asalin Najeriya ce ta suka dawo Amurka da zama tun tana shekaru 15 da haihuwa. Ta kuduri aniyar bude gidan abincin da zai kware a girke-girke musamman ma irin na gargajiyar Hausawa.
Bello haifaffen birnin Maiduguri ne amma girman Kano a tarayyar Najeriya, wanda ya ci karo da kalubalen rayuwa a dalilin basirarsa ta waka wanda har korarsa daga gidansu aka yi. Amma maimakon ya saduda, sai ma ya tsalleke kasar zuwa Jamus a tarayyar Turai inda a yanzu haka yake zaune a matsayin mawaki kuma mai koyar da rawai.
Binta Aliyu Zurmi da aka fi sani da Elbynt, ‘yar jarida ce daga Najeriya mazauniyar kasar Jamus kuma ma'aikaciya a daya daga fitattun gidajen radiyon Hausa da ke kasashen waje. Ku biyo mu don kallo ko sauraron tattaunawar da muka yi da ita game da tarihin rayuwarta a gida da kasahen waje.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Aliyu Mustapha Lawal, ya fito daga jihar Kano ne a Najeriya, wanda ya shiga gasar duniyar kasida ko waken-baka da larabci mai taken 'Gasar Yariman Sha'iran Larabawa' da aka yi a Birnin Abu Dhabi da ke hadaddiyar daular larabawa. Ya tattauna damu game da rayuwarsa tsakanin Najeriya da Misira da kuma yadda aka yi ya sami shiga gasar larabawa a matsayinsa na bahaushe.
Farfesa Yusuf Al-Hassan dan asalin cikin birnin Kano ne a Najeriya da ya kwashe shekaru yana koyo da koyarwa a tsakanin Najeriya da Amurka game da ilimin fasahar sana'o'in hannu inda har ya taba zama zakaran gasar malaman koyar da sana'o'i ta Amurka. Malamin ya kuduri aniyarsa ta yadda zai taimaki Najeriya ta hanyar kai Kanawa 100 zuwa Amurka don koyon ilimin sana'a.Yusuf Al-Hassan | MUK Na16
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Farfesa Abba Zubair Chedi na asibitin Mayo Clinic da ke Amurka, dan asalin jihar Kano ne a Najeriya da ya yi kaurin suna a Amurka, musamman a lokacin da ya shiga binciken yadda za a yi amfani da kimiyyar kwayar halitta ta 'stem cell' wajen kirkirar sassan jikin bil'adama, kamar zuciya da huhu don dasa wa mutanen da sassan jikin ya lalace ba tare da jiran sai wani ya mutum a cire a saka wa wani ba.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.
Kullum da karfe 6 na safe agogon Najeriya da Nijar muna gabatar da labarai da rahotanni da dumi-duminsu, sannan mu na gabatar da wasu shirye-shirye kamar Noma da Lafiya Uwar Jiki.