Shirye-shiryen DW Hausa a kan rayuwar matasa.
Abaya-bayan nan matasa daga sassan kasashen nahiyar Afirka sun dukufa harkar noma shin ko mene ne dalili? Saurarin shirin don jin karin bayani
Shirin ya duba yadda wasu daliban Jamus ke zuwa Kamaru da Côte D' Ivoire don yin musayar al'adu da takwarorinsu da ke amfana da koyon Jamusanci.
Shirin ya duba halin da wasu matasan Sokoto suka fada bayan da suka kammala karatu a manyan makarantu tare da samu aiki, amma daga karshe aikin ke kokarin sukurkucewa.
Shirin ya duba al'adar "Ramadan Basket" da ke sa masoyi gaggwanje masoyiyarsa da kayan shan ruwa idan Azumin watan Ramadana ya karato ko ya kama. Amma matsin rayuwa ya hana wasu matasa kai kyautar a bana.
Nadama wani yanayi da 'dan adam kan shiga ciki da zarar ya aikata wani abu cikin fushi
Irin ci-gaban da matasa za su iya samarwa kansu, ta hanyar fasahar sadarwa ta zamani da ta mamaye bangarori dabam-dabam na rayuwarsu.
Shirin ya yi nazari kan rawar matasa a siyasar kasar Senegal da a yanzu haka ta dauki dumi.
A Kamaru wani matashi da ya yi fice a fanni tace wakoki ya bude cibiyar koya wa matasa wakoki da kade-kaden da nufin inganta al'adun kasar don samar da mawaka sabbin jini.
Matasa da yanayin halin matsin tattalin arziki a Afirka
Shirin ya duba tasirin matakin raba da gari da ECOWAS da kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso suka dauka kan matasan yankin yammayin Afirka, musamman a fannin kasuwanci da ilimi da cudanyar kasa da kasa
Shirin ya duba kokarin matasa na samun matsayi a cikin gwamnati a kasashensu
Yawan kasancewar matasan Afirka a kafofin sada zumunta na haifar da kiyayya da rashin fahimta da cin zarafi tare da tunzurawa ga tashin hankali a wasu lokutan. Amma ta ya ya za a magance wadannan halayen da ke addabar dandamalin digital da biliyoyin mutane ke amfani da su yau da kullum?
Shirin ya mayar da hankali kan yadda matasa da yawa suka rungumi sana'ar waka musamman wakokin soyayya da ke cin zamani domin baje baiwar da Allah ya yi musu da samun kudin shiga.
Shiri ne da ya kunshi kokarin tashar DW na fadakar da jama'a kan matsalolin sauyin yanayi a kasashen Afirka musamman yadda suke haddasa rikici a tsakanin manoma da makiyaya musamman a arewacin Najeriya.
Shirin na wannan lokaci y agarzaya kasar Kamaru ne, inda ya tattauna da wata fitacciyar masaniyar kimiyyar harhada magunguna.
Matasa da dama sun samu mukamai a wasu jihohin Najeriya musamman na Arewa, sai dai yawancin gwamnatocin jihohin na fuskantar shari'a a kotunan sauraron kararrakin zabe. Ina makomar wadannan matasa idan shari'ar ta sauke gwamnonin da suka nada su? Shirin Dandalin Matasa ya tattauna wadannan batutuwa.
Shirin na wannan lokaci, ya yi nazari kan yadda matasa da dalibai ke shiga harkar hakar ma#adinai a jihar Plateau da ke Najeriya.
Shirin ya duba yadda matasan Ghana ke fadi tashi wajen mallamar wayar hannu ta iPhone, amma ba don binciken kimiyya da fasaha ba. Ko mene ne dalili?
'Yan Najeriya akalla miliyan 71 na fama da matsanancin talauci a cewar bayanan World Poverty Clock ma'aunin talauci a duniya. Wai ma waye talaka? Mene ne kuma talauci?
Shirin ya yi nazari kan batun yaki da talauci a tsakanin matasa, ta hanyar amfani da kafar Internet.
Shirin ya ya da zango a Jamhuriyar Nijar don duba halin da matasa suka samu kansu a ciki a fannoni daban daban bayan da sojoji suka kawo karshen mulkin Mohamed Bazoum na farar hula
Ko matasan Najeriya ka iya kawo sauyi a fagen siyassar kasar, bayan da aka ji su tsit tun da aka kafa sabuwar gwamnati? Ko kuma dai suna awani yunkuri? Shirin Dandalin Matasa na wannan lokaci ya yi nazari a kai.
Yadda mata bakar fata ke rayuwa ne a kasashen Larabawa musamman ma kasar Saudiyya.
Ko yaya rayuwar 'yan gudun hijira ke gudana musamman ta fannin ilimi? Shirin Dandalin Matasa na wannan lokaci ya yi nazari kan batun ilimi ga 'yan gudun hijirar a Kamaru.
Shin kun taba tsintar kanku cikin bukata da 'yan uwa suka gaza taimaka muku, ko kuwa ku ne kuka gaza bayar da tallafi? Shirin Darasin Rayuwa ya yi nazari kan wannan batu.
Shirin ya yi nazari kan yadda wani matashi ke taimakon 'yan uwansa matasa samun damarmaki da suka hadar da ayyuka ta kafar Internet.
Shirin na wannan lokaci, ya yi nazari ne kan gajiyar da matasan Najeriya suka ci ko akasin haka a kwanaki 100 na sabuwar gwamnatin kasar karkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na jam'iyyar APC.
Mawaka masu tasowa na auna mizanin fikirarsu da kuma isar da sako harma da samun bayanai daga dandazon masoya ta tkafar You Tube. Ko 'yan nanaye na cin moriyar damarmalin dake tattare da wannan fasaha?
Auratayyan da ake yi a wannan zamanin wanda dai aka fi sani da an yi Wuff
Ko kun san sabon taken kasa da aka yi a Jamhuriyar Nijar da ma yadda matasan kasar ke kallonsa? Shirin Dandalin Matasa yaa mayar da hankali a kai.
Wanne darasi wadanda suka saba yin layya suka koya a bana, sakamakon tsadar raguna da kkarancin kudi? Shirin Darasin Rayuwa.
Shirin Dandalin Matasa ya duba matakin jihar Borno da ke Arewa maso gabashin Najeriya na fara wani yunkuri na gayara dabi'un matasa.
Shirin ya yi nazari kan muhimmancin ranar 12 ga watan Yuni, ga matasan Najeriya da ma kasar baki daya.
Shin Wani rin darasi za a iya koya daga irin zamantakewa da cudanya da ake yi da miliyoyin mutane da ake haduwa da su a yayin gudanar da aikin Hajji?
A Najeriya, matasan da suka shiga harkokin zabe sun karu idan aka kwatanta da shekarun baya. Amma wasu me ya hana su taka rawar gani a fada a bana?
Shirin ya yi nazari kan matakin gyara ga dabi'un dalibai da jami'ar Abubakar Tafawa Balewa da ke jihar Bauchin Najeriya ta dauka.
a birnin Damagaram na Jamhuriyar Nijar, matasan da suka goge wajen taka leda na kwadayin rungumar buga kwallon kafa a matsayin sana'a a kasashen waje.
Jinkiri a zirga-zirgar sufurin jiragen sama a Najeriya ya gawurtar da har ta kai fasinjoji na kwashe tsowon lokaci suna jiran jirgin ba tare da kwakwarar hujja ba.
Yadda wani matashi mai bukata ta musanman ya raja'a a koyar da guragu fasahar kere-keren ababen hawa domin rage musu wahalhalun sufuri.
Shirin Dandalin Matasa ya yi nazari kan yadda matasa a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, ke fadakar da junansu batutuwan da suka shafi ilimin zamantakewar kasa da kishin kasa da kuma da'a, domin magance zama doya da manja da ake fuskanta tsakanin mabanbanta kabilu ko mabiya addinai.