Podcasts about jamhuriyar nijar

  • 16PODCASTS
  • 312EPISODES
  • 11mAVG DURATION
  • 1WEEKLY EPISODE
  • Jun 22, 2026LATEST

POPULARITY

20192020202120222023202420252026


Best podcasts about jamhuriyar nijar

Latest podcast episodes about jamhuriyar nijar

Bakonmu a Yau
Alhassane Intchinicar kan sharuɗɗan da Nijar ta kafa kafin buɗe iyaka da Benin

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 22, 2026 3:32


An fara tattaunawa tsakanin Benin da kuma Jamhuriyar Nijar da nufin sake buɗe iyakar ƙasashen biyu, sai dai mahukuntan birnin Yamai sun gindaya sharuɗɗa biyu kafin sake buɗe iyakar. Ministan cikin gida kuma jagoran tawagar Nijar a tattaunawar, ya ce na farko dole ne a ƙulla yarjejeniyar tsaro wadda a ƙarƙashinta ba ɗaya daga cikin ƙasashen biyu da za ta bari a yi amfani da ita domin kai wa ɗaya hari, sai kuma a kafa wata cibiyar musayar bayanan sirri ta haɗi-gwiwa da za ta bai wa Nijar damar sa-ido a game da kai-da-kawon sojojin ƙetare a kusa da iyakarta da Benin. Dangane da wannan Oumarou Sani ya tattaunawa da Alhassane Intchinicar guda daga cikin waɗanda suka jima suna fafutukar ganin a sake buɗe iyakar ga kuma yadda zantawarsu ta gudana.

benin kafa nijar jamhuriyar nijar
Al'adun Gargajiya
Yadda kiɗan Gurmi ke neman ɓacewa a ƙasar Hausa

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Jun 16, 2026 9:42


Shirinmu na yau ya leƙa sassan arewacin Najeriya da Jamhuriyar Nijar, tare da duba yadda wani fitaccen kiɗan gargajiya, wato kiɗan Gurmi, ke fuskantar barazanar bacewa a fadin ƙasar Hausa. Shin me ke janyo haka, kuma wane canji fasahar zamani ta kawo? Gurmi, kayan kiɗa ne da aka sani tun kaka da kakanni, wanda ƙera ta hanyar amfani da ƙoƙon ƙwarya da aka rufe shi da fatar dabba, musamman fatar guza, sannan a ɗaura masa tsirkiya guda biyu ko uku. A cikin shekarun da suka gabata, manyan mawaƙa irinsu Rabi'u mai Gurmi Gumel da Rabe mai Gurmi Jibia sun zagaya duniya suna baje kolin wannan fasaha. Amma a yau, idan ka zagaya biranen ƙasar Hausa, da kyar kake jin sautin wannan kiɗa, maimakon haka, sautin kiɗan na'urorin zamani na matasa sune suka mamaye ko'ina. Duk da wannan ƙalubale, wasu mawaƙan zamanin na ƙoƙarin haɗa sautin gurmi da kiɗan zamani don janyo hankalin matasa da kuma kaucewa ɓacewar wannan muhimmin kiɗa na al'ada.

shin rabe amma rabi asar hausa duk yadda nijar najeriya jamhuriyar nijar
Mu Zagaya Duniya
Shirin ya fara da yadda aka buɗe bikin gasar cin kofin duniya a ƙasar Mexico

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Jun 13, 2026 20:13


Ranar Alhamis 11 ga wannan watan  aka yi  bikin buɗe gasar cin kofin duniya karo na 23, gasar da itace karo na farko da ƙasashe 3, Amurka da Canada da kuma Mexico su ka karbi baƙunci, sai dai kuma an gudanar da zanga-zanga a wasu sassa na birnin ƙasar. Ƙasashe 48 ne ke fafata domin samun zakaran bana kuma yan wasa 1,248 da alkalan wasa 52 za su jagoranci wasanni 104 da za'a kwashe kwanaki 39 ana yi. A cikin shirin akwai labarin, shugaban Amurka Donald Trump, da ya ce ya soke shirinsa na kai munanan hare-haren da ya shirya yi a Iran, sakamakon wata tattaunawar da yace ya yi da wasu ƙusosshin gwamnatin ƙasar, Ikrarin da ya zuwa yanzu hukumomin ƙasar basu ce komai akai ba. Haka zalika, Majalisar Dokokin Najeriya ta amince da dokar kafa ƴansandan jihohi da gagarumar rinjaye, matakin da zai bai wa gwamnatocin jihohi damar kafa rundunar da za ta taimaka wajen magance matsalolin tsaron da suka addabi ƙasar. A Jamhuriyar Nijar gwamnati ce ta rattaɓa hannu a kan dokar haramta auran jinsi ko kuma mu'amalar jinsi guda wanda ta tanadi hukuncin ɗaurin da ka iya kai wa shekaru 20 a kan duk wanda aka samu da laifin yin haka. A wani abu da ba'a saba gani ba, Kungiyar mayaƙan JNIM mai alaƙa da Al Qaeda reshen Mali ta yi tayin bayar da tukwicin miliyoyin Yuro ga duk wanda ya ba ta bayanai kan inda shugaban kasar Assimi Goita  da manyan jami'an sojinsa suke, a yayin da ta bayyana gwamnatin a matsayin haramtacciyar. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin, tare da Oumarou Sani.

canada mexico iran fifa mali al qaeda bikin haka shirin duniya asar yadda shiga nijar yuro najeriya assimi goita jamhuriyar nijar amurka
Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle
Taba Ka Lashe 02.06.2026

Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle

Play Episode Listen Later Jun 2, 2026 9:41


A Nijar, watanda, al'adar hada kudi don sayen dabba (Saniya) lokacin bukukuwan salla ta kama hanyar bacewa a kasar Hausa.

hausa taba nijar jamhuriyar nijar
Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle
Taba Ka Lashe: 13.05.2025

Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle

Play Episode Listen Later May 19, 2026 10:30


Maazou Dan Alalo yana ɗaya daga cikin shahararrun mawakan Jamhuriyar Nijar.

taba maradi jamhuriyar nijar
Muhallinka Rayuwarka
Karfafa gwiwa ga jama'a su koma noma a jamhuriyar Nijar

Muhallinka Rayuwarka

Play Episode Listen Later Apr 25, 2026 20:00


Shirin muhallinka rayuwarka na wannan mako zai maida hankali ne kan yanda ake karfafa gwiwa ga jama'a su koma noma don ita ce babbar hanyar dogaro da kai ta fuskar abinci. Tun bayan halin matsin da jama'ar Jamhuriyar Nijar suka shiga biyo bayan juyin milkin soja da ta haddasa karamcin da tsadar abinci a cikin kasar aka rika zaburar da mutane su kama aikin noma musamman abincin da aka shigo da shi daga ketare Wanda ba a nomawa a cikin kasar irinsu shinkafa. Aka dai ce da rashin tayin ake barin arha, ganin yanda gwamnati ta kyautata wuraren da za a iya aikin noma a sassan kasar daban daban, mutane da yawa sun fada noman kuma hakika kwalliya ta fara biyan kudin sabulu. 

aka tun jama noma koma shirin nijar jamhuriyar nijar
Al'adun Gargajiya
Tasirin mayaƙa a masarautun gargajiyar ƙasar Hausa

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Apr 21, 2026 10:28


Shirin Al'adun mu na Gado a wannan makon ya leka Jamhuriyar Nijar ne, inda ya duba batun da ya shafi mazajen dauri, musaman mayaƙan gargajiya a wannan zamani, jaruman da ke ƙarƙashin inuwar sarakunan gargajiya. Duk inda akwai masarautun gargajiya an san su da tarin mayaƙa da ke yin tsarin daka a cikin kowane irin hali don kare su. Wannan tsarin ne da ya samo sali tun zamani da ake yaƙe-yaƙe tsakanin masarautu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa...........

ku gado asar hausa duk wannan jamhuriyar nijar abdoulaye issa
Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle
Taba Ka Lashe: 08.04.2026

Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle

Play Episode Listen Later Apr 14, 2026 9:53


Wai shin kun san cewa a yankin Agadez na Jamhuriyar Nijar, akwai wata sarauta da ake kira ANASTAFIDAT da ke da karfin fada a ji baya ga saurautar sarkin Abzun?

wai taba agadez jamhuriyar nijar
Muhallinka Rayuwarka
Dalilan da suka sanya Manoma Albasa a Nijar fuskantar ƙalubale a bana

Muhallinka Rayuwarka

Play Episode Listen Later Apr 14, 2026 20:00


Shirin 'Muhallinka Rayuwarka' na wannan makon, ya yi tattaki zuwa Jamhuriyar Nijar, inda aka fuskanci ƙalubale kan noman Albasa a shekarar bana. Bayanai daga ƙasar ta Nijar na cewa a halin da ake ciki, Manoma da dama sun shiga halin ƙaƙa-ni-kayi saboda rashin samun kuɗaɗen shiga, la'akari da irin rawar da noman na Albasa ke taka wa wajen sama musu abin kashewa.

noma suka bana sanya manoma nijar jamhuriyar nijar
Al'adun Gargajiya
Yadda kiɗan shantu ke ƙoƙarin ɓacewa duk da shaharar da ya yi a shekarun baya

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Apr 7, 2026 10:05


Shirin Al'adun mu na gado na wnnann mako ya waiwayi kiɗan Shantu ne da ya shahara tsakanin Mata a shekarun baya, wanda bayan tasirin da ya yi a waccan lokaci a fagen nishaɗantarwa, kiɗan na Shantu ke neman ɓacewa a yanzu. A shekarun baya dai wannan kiɗa na Shantu ya shahara ne tsakanin mata a yankunan arewacin Najeriya musamman a makarantu ko ɗalibai da kuma wasu sassan Jamhuriyar Nijar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Nura Ado Suleiman...........

mata ku arin baya yadda najeriya jamhuriyar nijar
Muhallinka Rayuwarka
Yadda sare itace a Nijar ke haifar da koma baya wajen samun amfanin gona

Muhallinka Rayuwarka

Play Episode Listen Later Apr 4, 2026 20:05


Shirin, ‘Muhallinka Rayuwarka a wannan makon ya yi duba ne kan yadda ake samu canjin yanayi ta hanyar saran icen "Gawo" barkatai daga Makiyaya da su kansu Manoman, wanda ake ganin ke haifar da koma baya wajen samun yalawar abinci kamar, bakamar yadda aka saba ba a shekarun baya a cikin gonaki na Jamhuriyar Nijar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Michael Kuduson..........

ku koma shirin sare baya yadda nijar jamhuriyar nijar
Bakonmu a Yau
Intinikar Alhassan kan ƙarewar wa'adin gwamnatin Bazoum da aka hamɓarar

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Apr 2, 2026 3:35


A wannan rana, ta biyu ga watan Afrilun shekarar 2026 da muke, wa'adin shugabancin hamɓararen shugaban ƙasar Jamhuriyar Nijar Muhammad Bazoum ke ƙarƙarewa da a ce yana kan karagar mulki. A irin wannan ranar ce dai ta watan Afrilun shekarar 2021, aka rantsar da Mohammed Bazoum a matsayin shugaban Jamhuriyar Nijar, bayan da ya lashe sama da kashi 55 na ƙuri'un zaɓen da aka yi a watan Fabrairun wannan shekara. Akan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Intinikar Alhassan, ɗaya daga cikin makusantan hamɓararren shugaban na Nijar. Ku latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu............

ku akan arar bazoum alhassan nijar jamhuriyar nijar
Kasuwanci
Yadda matasa ke fatan cin gajiyar yarjejeniyar tattalin arziki tsakanin Nijar da Algeria

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Apr 1, 2026 9:56


Matasa a Agadez da ke arewacin Jamhuriyar Nijar na cike da fatan cin moriyar sabuwar dangatakar da aka kyautata tsakanin kasar da makwabciyarsu Aljeriya. Ku danna alamar sauraro domin jin cikakken shirin tare da Ahmad Abba.

ku algeria yadda agadez nijar matasa fatan jamhuriyar nijar
Bakonmu a Yau
Mammane Wada kan shirin Nijar na kafa ƙungiyoyin samar da tsaro da basu makamai

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Apr 1, 2026 3:31


A Jamhuriyar Nijar, ra'ayoyi sun banbanta a kan shawarar da gwamnatin ƙasar ta yanke na kafa ƙungiyoyi waɗanda za ta bai wa horo tare da riƙe makamai don kare garuruwa daga hare-haren Ƴanbindiga. A cewar gwamnati, jami'an ƙungiyoyin kare kan, za su kasance sojoji, da ƴansanda da sauran jami'an tsaron da suka yi ritaya, waɗanda za a riƙa biyansu kuɗin alawus. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Mammane Wada na ƙungiyar Transparency International da ke bibiyar lamurra a ƙasar ta Nijar. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu............

Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle
Taba Ka Lashe: 25.03.2026

Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle

Play Episode Listen Later Mar 31, 2026 10:24


Nishadi ga samari da 'yan mata a shekarun baya a yankuna irin na Katsina, Maradi, Madawa har zuwa Tahoua da wasu sauran sassa.

taba katsina maradi jamhuriyar nijar
Ilimi Hasken Rayuwa
Tasirin faɗowar wasu sinadarai daga sama a fagen kimiyya da fasaha

Ilimi Hasken Rayuwa

Play Episode Listen Later Mar 3, 2026 9:57


Shirin "Ilimi Hasken Rayuwa" na wannan mako tare da Shamsiyya Haruna ya yada zango ne a Jamhuriyar Nijar inda abaya-bayan nan aka rika samun fadowar wasu abubuwa daga sararin samaniya, lamarin da ke ci gaba da faruwa a sassan a kasar. A baya bayan ne dai wasu abubuwa suka fado daga sararin samaniya a kauyuka 5 daban daban a yankin Kornaka, da Dakwaro da suka hada da Dan Madi, Baushi, da sauransu, haka abin ya taba kasancewa a 2021 inda aka samu wani babban dutse da ya fado daga sama a garin Aikawa na yankin Gazawa sannan, an samu wasu duwatsun a yankin Tanut, Agades da sauran yankunan Nijar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin...

sama ku daga fagen wasu nijar jamhuriyar nijar
Wasanni
FIFA za ta jagoranci koyar da ƙwallon ƙafa a makarantun Nijar

Wasanni

Play Episode Listen Later Mar 2, 2026 9:57


Shirin “Duniyar Wasanni” tare da Khamis Saleh a wannan lokaci zai yi duba ne kan yadda aka sanya tsarin koyar da wasan kwallon ƙafa a makarantun Boko na Jamhuriyar Nijar. A wannan makon mun yi dubi ne kan shirin koyar da wasan kwallon ƙafa da za a sirka a tsarin koyarwa a makarantun Boko a Jamhuriyar Nijar, a ƙoƙarin da ake yi na haɓɓaka harkar, ganin  yanda take a baya sosai a jadawalin ƙasashe da hukumar kwallon ƙafa ta duniya FIFA ta fitar inda Nijar ɗin ta ke a mataki na 111. Shi dai wannan tsarin, ya kasance wani shiri ne na haɗin gwiwa da aka yi tsakanin hukumar FIFA da kuma gwamnatin Nijar wanda hukumar kwallon kafa ta ƙasar fenifoot ke kula da shi. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

fifa ku shi boko wallon nijar jamhuriyar nijar
Wasanni
Yadda ta wakana a gasar tseren dawaki da ta gudana a garin Daura na jihar Katsina

Wasanni

Play Episode Listen Later Feb 23, 2026 9:59


Shirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan mako ya mayar da hankali ne kan gasar tseren dawaki da aka gudanar a garin Daura da ke jihar Katsina da ke a arewacin Najeriya. A farkon watan Faburairun wannan shekarar ne aka kammala babbar gasar tseren dawaki ta ƙasa da ƙasa da ƙungiyar sukuwar dawaki ta Najeriya ke shiryawa. Wannan ne dai karo na uku da ake gudanar da irin wannan sukuwa a cikin wannan shekarar, bayan da aka yi ta farko a birnin Katsina sai garin Hadeja na jihar Jigawa ya karbi bakunci sannan aka kamma sukuwan zangon farko na wannan shekarar a Daura. Mahaya daga Jihohin Kano da Sokoto da Neja da Bauchi da Kebbi da Katsina, waɗansu daga Jamhuriyar Nijar da Kamaru da Mali da Chadi da kuma Burkina Faso, suka halarci gasar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

mali ku burkina faso garin yadda kamaru chadi sokoto katsina neja daura bauchi kebbi jigawa wannan najeriya jamhuriyar nijar
Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle
Taba Ka Lashe: 11.02.2026

Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle

Play Episode Listen Later Feb 17, 2026 9:41


Suna dai linzami ne, kuma 'dan adam ya fara amfani da suna tun fil azal domin fayyace asali ko al'ada ko kuma jinsin da mutum ya fito.

suna hausa taba najeriya afirka jamhuriyar nijar hausawa
Kasuwanci
Yadda buɗe iyakokin Najeriya da Nijar zai taimaka wajen haɓaka kasuwanci

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Feb 11, 2026 10:00


Shirin Kasuwa Akai Miki Dole tare da Ahmed Abba a wannan mako ya yi dubi ne kan wani sabon yunkuri na kara inganta alakar kasuwanci tsakanin Najeriya da Nijar inda hukumar kwastom a jamhuriyar Nijar tayi tattaki zuwa Najeriya don tattaunawa hanyoyin da za'a bi don saukaka hada-hadar kayayyaki tsakanin kasashen biyu. Babban Kwanturolan Hukumar Kwastam na Najeriya Adewale Adeniyi, ya sake jaddada aniyar Hukumar na sauƙaƙe cinikayya a yankin, ta hanyar saukaka jigilar kayayyaki da kuma haɓaka haɗin gwiwar tsaro tsakanin ƙasashen da ke makwabtaka da su, musamman Jamhuriyar Nijar. Adeniyi ya bayyana hakan ne a ranar Juma'ar da ta gabata,  yayin wani babban taron haɗin gwiwa tsakanin Hukumar Kwastam ta Najeriya da takwararta ta Jamhuriyar Nijar, ƙarƙashin jagorancin Darakta Janar, Muhammadu Yaqouba, da aka gudanar da hedikwatan  Kwastam da ke Maitama a Abuja. Tawagar Nijar ta kunshi shugabannin cibiyar inganta kasuwanci na Nijar wato Chamber des Commerce. Cikin mahimman abubuwan da aka duba a ganawar akwai saukaka zirga-zirga a kayan a iyakokin kasashen biyu ciki harda jigilar man metur na kamfanin Dangote, hakazalika za'a bada damar wucewar wasu kayayyaki da suka makale a bodar Kamba na jihar Kebbi, tireloli 1,600, da suka kwashe sama da watanni 2. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

commerce chamber ku abuja juma dangote yadda kebbi nijar najeriya cikin jamhuriyar nijar hukumar ahmed abba
Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Alhaji Sani Shekarau kan buɗe iyakokin Najeriya da Nijar da Benin

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Feb 11, 2026 3:20


A ranar Litinin da ta gabata, mahukuntan Najeriya suka buɗe iyakokinsu da Nijar da kuma Jamhuriyar Benin ta ɓangaren jihar Kebbi, matakin da ya maido da zirga-zirgar kasuwanci tsakanin ƙasashen uku. Gabanin buɗe iyakokin dai sai da aka gana tsakanin wakilan Najeriya da na Nijar,  matakin da ya kawo ƙarshen katse jigilar manyan motocin dakon kaya fiye da Dubu Ɗaya da Ɗari Biyar, da suka shafe aƙalla wata guda a tsaye. Domin jin ƙarin bayani kan lamarin Nura Ado Suleiman ya tattauna da Alhaji Sani Shekarau, shugaban ƙungiyar manyan ‘yan kasuwa da ke jigilar kayayyaki zuwa ciki da wajen Jamhuriyar Nijar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

ku benin domin sani dubu kebbi nijar najeriya jamhuriyar nijar
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu saurare kan zanga-zangar ɗalibai a jamhuriyar Nijar

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Feb 10, 2026 9:52


Ra'ayoyin masu saurare na wannan rana ya mayar da hankali ne kan yadda ake juyayin cika shekaru  36 da jami'an tsaro suka buɗe wuta kan ɗalibai da ke zanga-zangar neman kyautata ilimi, yin fatali da tsare-tsare Asusun Lamuni na Duniya da sauran matakai na tsuke bakin aljihun gwamnatia jamhuriyar Nijar, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla ɗalibai uku. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabiru Yusuf.

ra ku duniya masu nijar jamhuriyar nijar
Wasanni
An kammala gasar kokowa ta ƙasa mafi girma a Jamhuriyyar Nijar

Wasanni

Play Episode Listen Later Dec 29, 2025 10:00


Shirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan lokaci zayyi duba ne kan yadda aka kammala gasar kokuwar gargajiya ta ƙasa a Jamhuriyar Nijar. Jiya Lahadi ne aka kammala gasar kokowar gargajiya ta ƙasa a Jamhuriyar Nijar da aka gudanar a garin Tawa, wacce ita ce karo ta 46, inda mai masaukin baki ta lashe takobin bayan ƴan kokowarta biyu sun kai wasan ƙarshe a wannan gasa. Bayan karawa ta mintuna 11 da daƙiƙu 6, Nura Hassan ne ya yi nasara kan Zakiru Zakari. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

ku bayan mafi tawa girma nijar jamhuriyar nijar
Mu Zagaya Duniya
Trump ya ƙaƙaba sabbin takunkuman hana shiga Amurka

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 20:07


Mu Zagaya Duniya wanda ke bitar wasu daga cikin muhimman lamurran da suka wakana  a makon da muka yi wa bankwana,shirin zai fara ne da matakin da shugaba Donald Trump ya ɗauka na ƙaƙaba sabbin takunkuman hana shiga Amurka kan wasu ƙarin ƙasashe bakwai na Afrika, ciki har da Burkina Faso da Mali da kuma Jamhuriyar Nijar a bisa dalilan da ya  ce na tsaro ne.

Kasuwanci
Al'ummar Nijar sun rungumi tsarin hada hadar kuɗi ta manhajar waya

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Dec 10, 2025 10:04


Shirin 'Kasuwa A kai Miki Dole' na wannan mako ya leka Jamhuriyar Nijar ne, inda a shekarun baya bayan nan, hada hadar kuɗi ke neman yin ƙaura daga bankuna zuwa manhajojin wayar salula da ake kira da Mobile Money a Turance, da ake amfani da tsarin wajen aikewa da kuɗi ko karɓarsu a ciki da wajen ƙasar ta Nijar. Samun damar aika kuɗaɗe ta hanyar amfani da manhajojin wayar hannu ba tare da yankar kuɗin haraji masu dama ba, dai tuni ya kawo sauyi dangane da hada-hadar kuɗi a Jamhuriyar ta Nijar, lamarin da ya zo a daidai lokacin da aka takaita fitar da kuɗaɗe daga Bankuna bayan juyin Mulki, tsarin da ya sa mutane da dama masu asusun ajiya a bankuna rungumar mahajojin na zamani a matsayin sabbin wuraren adana kuɗaɗen nasu.  Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Nura Ado Suleiman.........

ku hadar mobile money waya nijar jamhuriyar nijar
Al'adun Gargajiya
Yadda aka gudanar da bikin naɗin sarautar sarkin Komadugu a Maraɗi

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Dec 2, 2025 9:55


Shirin na yau ya yada zango jihar Diffa dake Jamhuriyar Nijar,yankin da aka gudanar da bikin nadin sabon sarkin Komadugu, wanda ya samu halartar baƙi daga ciki da wajen ƙasar. Diffa dai kamar dai yadda masana tarihi suka tabbatar, ana na nufin Diwa a harshen Kanuri kenan. Kalmar ta samo asali ne daga kalmar "Di wa Nallé wa," wadda ke nuna tsabtar jiki da dai sauran abubuwan da suka shafi maza da mata na yankin. Di na nufin farin gashi, kuma Nallé na nufin lalle wanda ke da ma'ana biyu. Wannan jumla, Di wa Nallé wa, na nufin mata waɗanda, ko da a cikin tsufa, suna rina gashinsu da lalle. Tarihi ya nuna  cewa a ƙarni na 19, yankin Diffa a lokaci na karkashin masarautar Kanem-Bornu,inda a shekarar 1933 Turawan mulkin mallaka a lokacin  sun kafa yankin Komadougou, wanda aka bayyana yankin  da farko yake zaune a Bosso sannan daga baya ya koma Gueskérou. An gudanar da zaɓen sabon sarkin na komadugu a jahar Diffa a gaban hukumomin  bariki da na gargajiya da kuma sauran al'umma, wanda ya kai ga zaɓen Hassan Mamadou Abba Kyari a matsayin sabon sarkin na Komadugu. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Abdoullaye Issa.

bikin shirin kalmar tarihi nall yadda shiga bosso diwa nijar wannan diffa jamhuriyar nijar
Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle
Taba Ka Lashe 02.12.2025

Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle

Play Episode Listen Later Dec 2, 2025 9:45


Shirin ya duba komabaya da al'adar wasannin karkara a lokacin kaka yayin tattara amfanin gona ke fuskanta a Zinder na Jamhuriyar Nijar.

shirin taba nijar jamhuriyar nijar
Muhallinka Rayuwarka
Yadda manoman Jamhuriyar Nijar ke fama da ɓarnar makiyaya a ƙarshen damina

Muhallinka Rayuwarka

Play Episode Listen Later Nov 29, 2025 20:01


Shirin muhallinka rayuwarka na wannan karon zai mayar da hankali ne kan irin fama da ake sha a karshen damina tsakanin manoman da suke tattarar Kayan gona da makiyayan dake dawowa daga kiwo zuwa wuraren da ake aikin noman a  wasu sasaan Jamhuriyar Nijar. A duk karshen damana makiyayan da suka tafi mashekari wurin kiwon dabbobinsu inda ke da isassar ciyawa nesa da gonaki na sabkowa wuraren da ake aikin noma don ganawa da jama'a, sannan da samun sauran tarikicen da manoman suka bari a gonakansu. Sai dai a irin lokacin na komawar makiyayan ana samun rikicin dake faruwa ' tsakaninsu da manoman da ba su ida tattare Kayan da suka noma ba, kuma da yanda wasu makiyayan ke saurin komowa a lokacin da manoman ke tsaka da aiki, duk da an tanadi dokar da ta tsaida komi a kasar ta Nijar.

fama sai shirin arnar yadda kayan nijar jamhuriyar nijar
Ilimi Hasken Rayuwa
Har yanzu Malama tsangaya na amfani da Ajami wajen musayar sakonni

Ilimi Hasken Rayuwa

Play Episode Listen Later Nov 11, 2025 9:59


Shirin a wannan mako, kareshe ne kan maudu'in da muka tattaunawa a makonni biyun da suka gabata, wanda ya mayar da hankali kan yadda rubutun Ajami a kasar Hausa ya yi shura, da kuma yadda yake neman bacewa a wannan zamani. Yayin da ake ganin har yanzu a Jamhuriyar Nijar, akwai yankunan da suke amfani da ajami wajen isar da sakonni, Malaman tsangaya daga Najeriya ma suna amfani da wannan tsarin rubutu wajen musayar bayanai a tsakaninsu. Yaɗuwar addinin Islama a Ƙasar Hausa masana suka ce, ya taimaka sosai wajen shaharar wannan salo na rubutu, sannan kuma ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen inganta hanyoyin sadarwa na wancan lokaci. A tattaunawarmu da masanin tarihi daga Kanon Najeriya, farfesa Tijjani Naniya, ya bayyana cewa, zuwan turawan mulkin mallaka, shine musabbabin gushewar wannan rubutu a kasar Hausa, amma a wancan lokaci, rubutun na ajami ya ci kasuwa tsakanin masana, malamai, sarakuna da kuma ‘yan kasuwa.

shirin hausa malama yayin ajami islama najeriya jamhuriyar nijar yanzu
Muhallinka Rayuwarka
Yadda wani ruwa da ke ɓulɓulowa ta ƙasa ke zubar da gidaje da kashe bishiyu a Nijar

Muhallinka Rayuwarka

Play Episode Listen Later Nov 8, 2025 20:00


Shirin muhallinka rayuwarka na wannan yau zai maida hankalin ne kan wani ruwan dake bullowa daga kasa Wanda ya yi sanadiyar zubewar gidaje da kashe bishiyoyi da ga gurbata hanyoyi a unguwar Garin Malam ta Damagaram a Jamhuriyar Nijar. Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Micheal Kuduson.

shirin wani ruwa yadda nijar jamhuriyar nijar damagaram micheal kuduson
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu saurare kan sabon matakin zaftare kuɗaɗe don ceto ƙasa a Nijar

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Nov 4, 2025 10:28


Ra'ayoyi sun sha bambam a tsakanin al'umma dangane da matakin zaftare kuɗaɗe don tallafa wa Gidauniyar Ceton Ƙasa da gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta kafa. Ƙarƙashin wannan gidauniya, kusan kowane rukuni na jama'a, tun daga ƙusoshin gwamnati, zuwa ma'aikata da kamfanoni, na gwamnati da masu zaman kansu, kai har ma da masu zaman kashe wando, ala dole sai kowa ya bayar da nasa tallafin. Shin me za ku ce a game da wannan Gidauniya, da har ake cewa har yanzu ba wanda ke da hurumin gudanar da bincike dangane da kuɗaɗen da ake tarawa a cikinta? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

ra shin masu ceto nijar wannan jamhuriyar nijar
Muhallinka Rayuwarka
Barazanar wutar daji da ke lakume gonakai a Jamhuriyar Nijar

Muhallinka Rayuwarka

Play Episode Listen Later Nov 1, 2025 20:01


A cikin wannan shirin ,za mu leko Jamhuriyar Nijar inda a duk shekara ake fuskantar barazanar wutar daji da ke lakume gonakai da cimaka. Hukumomin Nijar sun dau matakai domin kawo karshen  wannan al'amari da manoma da kuma jama'a ke kuka  a kai.

noma nijar jamhuriyar nijar
Al'adun Gargajiya
Yadda aka gudanar da bikin makiyaya na Cure Salee a Jamhuriyar Nijar

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Oct 21, 2025 9:38


Shirin a wannan mako ya yi tattaki ne, zuwa ƙauyen Ingal da ke Yankin Agadez a jamhuriyyar Nijar, domin waiwayar gagarumin bikin makiyaya da ƙabilu daban-daban da ake yi wa laƙabi da 'Cure Salee' wanda aka saba yi duk shekara. Bikin makiyayan na Cure Salee ya gudana ne a tsakanin ranakun 4 zuwa 6 ga watan da muke ciki na Oktoba. Manufar bikin ita ce yadda za a ƙarfafa haɗin kai tsakanin makiyaya domin kafa ginshiƙin zaman lafiya mai ɗorewa a tsakanin ƙabilu. Bikin na bana ya samu halattar ƙabilun Fulani da na Abzinawa da Larabawa a Nijar ɗin da wasu daga Najeriya, da Mali da burkina Faso da kuma Aljeriya. Latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Nura Ado Sulaiman...............

cure mali bikin shirin fulani faso yadda nijar oktoba najeriya jamhuriyar nijar
Wasanni
An fara gasar Super Ligue ta Jamhuriyar Nijar

Wasanni

Play Episode Listen Later Oct 20, 2025 9:59


Shirin duniyar wasanni na wannan mako zai maida hankali a kan yanda aka fara gasar ligue ta ƙasar Niger da ake ma lakabi da SUPER LIGUE. A ƙarshen mako ne aka faro gasar Lik ta Jamhuriyar Nijar wacce ake wa laƙabi da Super Ligue.Ita dai wannan gasa ta Super League ta kasance kololuwar gasar kwallon ƙafa a ƙasar, inda ta ke ƙumshe da ƙungiyoyi 16,  kuma babban birnin ƙasar Niamey ka dai na da club 12. A tsarin wasan kowa zai kara da kowa a gida da waje kamar yanda ake yi a sauran ƙasashe ke nan kowace ƙungiya za ta yi wasa 30. Haka kuma kamar a sauran ƙasashe zakaran da ta lashe wannan gasar za ta wakilci ƙasar a gasar ligue a matakin nahiyar Afrika da hukumar Caf ke shirya, don haka ɗaukacin waɗannan club ɗin ke maida hankali don ganin sun taka rawar gani a gasar. Kafin mu tsunduma cikin shirin bari muyi ratse don yin ɗaurayar yadda gasar ta gudana a bara tare da Magaji Minista mai sharhi ne kan harakar wasannin kwallon kafa.

Lafiya Jari ce
An gudanar da gangamin wayar da kai akan cutar daji a Jamhuriyar Nijar

Lafiya Jari ce

Play Episode Listen Later Oct 20, 2025 10:05


Kowanne watan Oktoba, lokaci ne da ɓangarorin lafiya a Jamhuriyyar Nijar ke amfani da shi wajen gudanar da gangamin wayar da kai a ƙasa baki ɗaya game da cutar sankara ko kuma Cancer wadda ake ganin ƙaruwar masu kamuwa da ita a sassan wannan ƙasa ta yankin Sahel,,,, wannan shi ne maudu'in da shirin na Lafiya jari ce zai mayar da hankali akai sai ku biyomu. Jamhuriyyar Nijar na ganin sabbin kamuwa da cutar ta cancer dubu 9 da 787 duk shekara ciki kuwa har da mata masu kamuwa sankarar mama dubu 2, wanda ke matsayin wani ɓangare na jumullar mata miliyan 2 da dubu 300 da ke kamuwa da sanakarar maman duk shekara a sassan duniya bisa alƙaluman hukumar WHO.

cancer akan sahel oktoba jamhuriyar nijar
Kasuwanci
Yadda ɗimbin matasan Najeriya masu sana'o'in hannu ke ƙaura zuwa Nijar

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Oct 15, 2025 10:05


A wannan makon shirin na Kasuwa Akai Miki Dole tare Abdulƙadir Haladu Kiyawa zai tattauna ne a kan yawaitar matasan Najeriya masu muhimman sana'o'in hannu da ke yin ƙaura ko kuma tafiya ci rani zuwa wasu ƙasashen Afrika domin neman na rufin asiri, abin da ake alaƙantawa da dalilai da dama da ke sanya matasan ficewa daga ƙasar tasu ta haihuwa. A shekarun baya ba haka lamarin yake ba, inda Najeriyar ke matsayin wajen da ɗimbin ƴan ƙasashen ƙetare ke kwarara don neman kuɗi musamman ƴan kasashen Afrika kamar Jamhuriyar Nijar, da Ghana, da Jamhuriyar Benin, har ma da Kamaru. To Sai dai a yanzu, waɗannan ƙasashen ne ƴan Najeriyar ke tururuwar zuwa cikinsu duk da kasancewar ƙasashen ba su da ɗinmbin arziƙi kamar Najeriyar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin...

Al'adun Gargajiya
Sannu a hankali sana'ar ƙira na shuɗewa a jihar Agadez ta Jamhuriyar Nijar

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Sep 16, 2025 9:48


Shirin Al'adunmu na Gado na wannan mako ya mayar da hankali ne kan yadda sannu a hankali sana'ar kira ke shudwa musamman ta ƴan Kabilar Abzinawa da ke jihar Agadez a jamhuriyar Nijar. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Abdullahi Issa.

sana ku gado agadez nijar jamhuriyar nijar
Bakonmu a Yau
Mammane Wada kan yadda jamhuriyar Nijar ke ci gaba da shaƙe wuyan masu chachakarta

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Sep 10, 2025 3:33


Gwamnatin mulkin sojin  Jamhuriyyar Nijar na ci gaba da kamen waɗanda ke sukar lamirinta da suka hadar da ƴan jarida da masu fafutuka har ma da ƴan siyasa. A wani rahoto da ta fitar a baya bayan nan kungiyar kare hakkin bil Adam Human Right Watch ta soki yadda sojojin da suka kwace muki a ƙasar ke tsare jama'a babu gaira babu dalili. Akan wanan abokin aiki Oumarou Sani ya tattaunawa da Mamane Wada shugaban kungiyar yaki da cin hanci da rashawa ga kuma yadda zantawarsu ta gudana.

akan gaba wada yadda masu nijar jamhuriyar nijar
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu saurare kan ƴancin faɗar albarkacin baki a Nijar

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Sep 10, 2025 8:32


A Jamhuriyar Nijar, batun ƴancin faɗin albarkacin baki, aikin jarida ko kafa ƙungiyoyi da sunan yi fafutuka na ci gaba da fuskantar barazana. Bayan rusa ilahirin jam'iyyun siyasa, daga bisani an ci gaba da kama ƴan jarida da masu fafutukar kare hakkin bil adama, tare da jefa ƙungiyoyin kwadago a cikin fargaba ta hanyar farawa da rusa kungiyoyin alƙalai na ƙasar. Ku latsa alamar sauti don jin ra'ayoyin jama'a kan wannan batu.

ku baki bayan masu nijar jamhuriyar nijar
Lafiya Jari ce
Yadda Jamhuriyyar Nijar ke ganin yawaitar yaran da ke fama da Tamowa

Lafiya Jari ce

Play Episode Listen Later Sep 8, 2025 9:55


Shirin lafiya jari ce a wannan mako ya leƙa Jamhuriyar Nijar, inda a dai dai lokacin da ake ganin yawaitar ƙananan yaran da ke fama da cutar yunwa sanadiyyar ƙarancin abinci mai gina jiki da ake kira ƙwamuso a sassan jamhuriyar Nijar, wata matsala da ke tunƙaro shirin yaƙi ko kuma taimakon masu fama da lalurar shi ne yadda ake karkatar da abincin da aka tanadar dominsu.............

fama shirin yadda nijar jamhuriyar nijar
Bakonmu a Yau
Nijar a duk kullum za ta kare hakokin ƴan ƙasar mazauna ketare

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Sep 6, 2025 3:23


Jamhuriyar Nijar a duk kullum za ta kare hakokin ƴan ƙasar mazauna ketare, Wasu daga ciki tarin matsalolli da ƴan Nijar mazauna ƙasashen ketare ke fuskanta sun hada da rashin takardun zama wadanan kasashe. Jakadan Nijar a Jamhuriyar Benin, Kadade Chaibou ya bayyana haka yayin zantawa da Abdoulaye Issa a ofishinsa dake birnin Kwatanu.

asar wasu nijar jamhuriyar nijar abdoulaye issa
Ilimi Hasken Rayuwa
Tsarin cigaban manyan malaman jami'a a Jamhuriyar Nijar

Ilimi Hasken Rayuwa

Play Episode Listen Later Aug 19, 2025 9:55


Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan makon zai duba tsarin cigaban manyan malaman jami'a a Jamhuriyar Nijar, wanda ke kai su ƙololuwa a harkar ilimi. Domin samun ingataccen ilimi, dole ne a samu ƙwararrun malamai da za su koyar da ɗalibai da ke karatu a fannoni dabam-dabam. haka zalika malaman da ke koyarwar su ma su na neman hanyoyin ƙara ƙwarewa don kai wa ƙololuwa a aikin na su na koyarwa.

domin jamhuriyar nijar
Muhallinka Rayuwarka
Rashin fitar shuka ya zame wa wasu manoma ƙalubale a Jamhuriyar Nijar

Muhallinka Rayuwarka

Play Episode Listen Later Aug 16, 2025 20:40


Shirin 'Muhallinka Rayuwarka' na wannan makon tare da Michael Kuduson, ya tattauna a kan rashin fitar shuka a farkon daminar bana, lamarin da ya zame wa manoma ƙalubale babba a Jamhuriyar Nijar, matsalar da suka fara fuskanta tun daga farkon daminar bana.

noma zame manoma wasu shuka rashin nijar jamhuriyar nijar
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu saurare kan yajin aikin lauyoyi a Nijar

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Aug 14, 2025 9:17


Lauyoyi a Jamhuriyar Nijar sun tsunduma yajin aikin kwanaki biyu daga yau Alhamis, domin nuna rashin amincewa da rusa ƙungiyoyin alƙalai da sauran ma'aikatan shari'a da gwamnatin ƙasar ta yi. Kafin rusa waɗannan ƙungiyoyi, tuni aka rusa ƙungiyoyin jami'an kare gandun daji da na kwastam da kuma illahirin jam'iyyun siyasar ƙasar. Shin, ko me za ku ce a game da wannan mataki na gwamnatin Nijar ta ɗauka? A irin wannan yanayi, ko meye makomar ƴancin gudanar da ƙungiyoyi a ƙasar? Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi...

shin masu nijar jamhuriyar nijar alhamis
Wasanni
Yadda wasanni ke ɗaukar hankalin matasa a lokacin hutu a Nijar

Wasanni

Play Episode Listen Later Aug 11, 2025 9:59


Shirin a wannan makon zayyi duba ne kan yanda wasanni ke ɗaukan hankalin matasa a irin wannan lokaci na hutun ƴan makaranta a Nijar. A duk lokacin da aka yi dogon hutun ƴan makaranta a Jamhuriyar Nijar, wanda ke farawa daga watan Yuli zuwa Satumba. Irin wannan lokaci na zama wata babbar dama ga masu kula da ɓangaren wasanni iri daban daban, don suna samun ɗinbin matasa da ke nuna sha'awarsu a ɓangaren wasanni.

shirin hutu yuli irin yadda nijar matasa jamhuriyar nijar
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu saurare kan yadda ambaliya ke yin ɓarna a wasu biranen Afrika

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Jul 7, 2025 10:33


Ambaliyar ruwa na ci gaba da yin ɓarna a wasu biranen ƙasashen Afrika, inda ko a baya-bayan nan ta laƙume rayuka fiye da 600 a ƙaramar hukumar Mokwa ta jihar Nejan Najeriya yayin da tituna suka fara cika da ruwa a wasu ƙananan hukumomin jihar Kano, baya ga babban birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar da aka samu iftila'in ambaliyar a kwanakin baya.   Ya ya matsalar ta ke a yankunan ku, ko wani mataki kuke ɗauka don ganin kun kare kanku daga iftila'in ambaliyar ruwan yayin da daminar bana ta sauka? Shin ko akwai wasu matakai da gwamnatocinku ke ɗauka?

afrika shin kano arna yadda masu wasu jamhuriyar nijar
Bakonmu a Yau
Issof Emoud kan sabuwar Majalisar Tuntuɓa da gwamnatin sojin Nijar da kafa

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 30, 2025 3:34


Majalisar Tuntuɓa da gwamnatin sojin Jamhuriyar Nijar ta kafa ta conseil consultatif na fara aiki a ranar Asabar 28 ga watan Yunin wannan shekara ta 2025, Majalisar mai kunshe da mambobi 194 an ɗaura mata nauyin bayar da shawarwari kan harokin da su ka shafi cigaban ƙasa da  kuma gayyato majalisa zartaswa domin amsa tambayoyi idan hakan ta kama. A kan haka Oumar Sani ya  tattauna da Hon. Issouf Emoud ɗan majalisa mai wakilta jihar Agadas.

kafa nijar jamhuriyar nijar majalisar
Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle
Taba Ka Lashe 10.06.2025

Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle

Play Episode Listen Later Jun 10, 2025 9:57


Shirin ya duba rayuwar fitacciyar zabiya Mariama Rabiou mai waka da Hausa da Zabamanci da Allah ya yi wa cikawa a Gaya ta Nijar.

allah gaya shirin waka hausa taba nijar jamhuriyar nijar
Bakonmu a Yau
Malaman makarantu sun sake tsunduma yajin aiki a Nijar

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 9, 2025 3:26


Gamayyar ƙungiyoyin malaman makarantu da ke koyarwa a matakai daban daban a Jamhuriyar Nijar, sun sanar da shiga yajin aikin kwanki 5 a jere daga wannan litinin, tare da barazanar da baiwa kowane ɗalibi maki ɗari bisa ɗari na jarabawar da aka yi masa. Malaman suna wannan yajin aiki  ne don neman gwamnati ta biya musu buƙatunsu da suka haɗa da: ɗaukar malaman kwantaragi a matsayin ma'aikata na dindindin, tare da biyan wasu kuɗaɗensu na alawus da suka maƙale a hannun gwamnati. A game da wannan batu, Ibrahim Malam Tchillo, ya zanta da shugaban ƙungiyar ASO EPT, mai fafutar samar da ilimi mai nagarta ga al'ummar Nijar wato Ibrahim Babaye Sani.Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana..................

sake ku aiki nijar jamhuriyar nijar
Lafiya Jari ce
Ƙaruwa masu kamuwa da cutar tarin fuka a sassan Jamhuriyar Nijar

Lafiya Jari ce

Play Episode Listen Later May 19, 2025 9:59


Shirin namu na wannan makon zai mayar da hankali ne kan ƙaruwar mutanen da ke kamauwa da cutar  babban tari, ko kuma tarin fuka, ko kuma TB a sassan Jamhuriyar Nijar, lamarin da ke zuwa a lokacin da ake fuskantar ƙarancin agajin magangunan yaƙi da wannan cuta. Wanmnan cuta na sahun daɗaɗɗun cutuka masu yaɗuwa, waɗanda wani kan iya goga wa wani.Abin da ya  sa ya zama wajibi a rika wayar da kan al'umma akan hanyoyin kariya daga ita.

tb shirin abin tarin masu sassan nijar jamhuriyar nijar