POPULARITY
in August of 1991 the old guard from the Soviet Union attempted a Coupe to over thrown the burgeoning 'democracy' that was to be a westernized version of Russa. This failed due to lack of military support, general public interest , and the sheer energy of the Russian youth To reward these efforts, the country 'gifted' the largest heavy metal concert in recorded history where an audience of 1.6 MILLION (in Dr. Evil voice) fans watched Pantera, The Black Crows, METALLICA, and AC/DC perform. Not only were these career defining performances for Pantera and Metallica, but it also was the bookend to the last days of the Soviet Union. Yadda yadda yadda and happily ever after....or so you think....stay tuned to learn more As always follow us on the stuff Merch Store- http://tee.pub/lic/doEoXMI_oPI Patreon- https://www.patreon.com/Artandjacobdoamerica Website- https://artandjacobdoamerica.com/ Instagram- https://www.instagram.com/artandjacobdoamerica Facebook- https://www.facebook.com/artandjacobdoamerica/
Shirin "Duniyar Wasanni" tare da Khamis Saleh a wannan lokaci zay yi duba ne kan yadda aka faro gasar lashe kofin nahiyar Afrika da ƙasar Morocco ke karɓar baƙunci. A daren jiya lahadi ne dai aka buɗe gasar lashe ƙofin nahigar Afrika ta AFCON karo na 35 da ƙasar Morocco ke karɓar baƙunci. An dai buga wasanni tsakanin Morocco da Comoros, inda Moroccon ta samu nasasara da ci 2 da nema, wani abu da ke nuna cewa ta faro gasar da ƙafar dama, bayan da Yariya Moulay Hassan bin Mohammed ya buɗe ta tare da rakiyar shugaban hukumar kwallon ƙafa ta duniya FIFA Gianni Infantio da kuma shugaban hukumar kwallon ƙafar Afrika CAF Patrice Motsepe. Ɗan wasan gaba na tawagar Morocco Brahim Diaz da ke bugawa Real Madrid ne ya fara jefa kwallo a raga a minti na 55, kafin Ayoub El Kaabi na ƙungiyar Olympiacos da ya shigo daga baya ya ƙara a minti na 74. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin Duniyar Wasanni a wannan lokaci tare da Khamis Saleh ya yi duba ne kan tarihin gasar lashe kofin Afrika AFCON da hukumar CAF ke shiryawa. An faro buga gasar lashe kofin nahiyar Afirka, wacce ke zaman gasar kwallon ƙafa mafi girma da daraja a nahiyar a shekarar 1957, da hukumar kula da kwallon ƙafar Afrika CAF ce ta jagoranci. An fara gudanar da gasar ne a watan Fabrairun shekarar 1957 a birnin Khartoum na ƙasar Sudan da ƙasashe 3, kafin a shekarar 2019 aka faɗaɗata zuwa tawogogun ƙasashe 24, kuma Masar ce ta fara lasheta bayan lallasa Sudan da ta karbi baƙunci a wasan karshe, inda ta lashe kofin da aka sanya masa sunan Abdel Aziz Abdallah Salem, ɗan ƙasar Masar da ya fara shugabantar hukumar CAF. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin a wannan lokaci zayyi duba ne kan yadda rabon jadawalin gasar lashe kofin duniya da za a yi a baɗi ya gudana. A makon da ya gabata ne Hukumar Kula da Kwallon Ƙafa ta Duniya FIFA ta fidda jadawalin Gasar Kofin Duniya na shekarar 2026, wacce za ta gudana a tsakanin ƙasashen Amurka da Canada da kuma Mexico. Bikin dai ya gudana a cibiyar Kennedy da ke birnin Washington DC, ƙarƙashin jagorancin shugaban Amurka Donald Trump da shugaban FIFA Gianni Infantino.
Ƴan Najeriya na ci gaba da neman bayani a kan yadda wasu kuɗaɗen da aka tara, da yawan su ya kai dala miliyan 30 domin samar da tsaro a makarantu suka shiga, sakamakon sake dawowar satar ɗalibai a yankin arewacin ƙasar. A ƙarƙashin wannan shirin da ya fara a shekarar 2014, kasashe da dama suka tallafawa Najeriya, cikin su har da ƙasar Norway da ta bada dala miliyan guda, da wata dala miliyan guda daga Bankin Raya ƙasashen Afirka na AfDB, sai kuma Fam miliyan guda daga gwamnatin Birtaniya. Gwamnatin Switzerland ta bada taimakon dala miliyan takwas, yayin da Amurka ta bada dala miliyan biyu, sai kuma Qatar da ta bada dala miliyan biyu, yayin da ƴan kasuwan Najeriya su kuma suka bada taimakon dala miliyan 10. Ganin yadda aka kasa samar da tsaron a makarantu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Abubakar sadiq Umar Gombe. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Shirin na yau ya yada zango jihar Diffa dake Jamhuriyar Nijar,yankin da aka gudanar da bikin nadin sabon sarkin Komadugu, wanda ya samu halartar baƙi daga ciki da wajen ƙasar. Diffa dai kamar dai yadda masana tarihi suka tabbatar, ana na nufin Diwa a harshen Kanuri kenan. Kalmar ta samo asali ne daga kalmar "Di wa Nallé wa," wadda ke nuna tsabtar jiki da dai sauran abubuwan da suka shafi maza da mata na yankin. Di na nufin farin gashi, kuma Nallé na nufin lalle wanda ke da ma'ana biyu. Wannan jumla, Di wa Nallé wa, na nufin mata waɗanda, ko da a cikin tsufa, suna rina gashinsu da lalle. Tarihi ya nuna cewa a ƙarni na 19, yankin Diffa a lokaci na karkashin masarautar Kanem-Bornu,inda a shekarar 1933 Turawan mulkin mallaka a lokacin sun kafa yankin Komadougou, wanda aka bayyana yankin da farko yake zaune a Bosso sannan daga baya ya koma Gueskérou. An gudanar da zaɓen sabon sarkin na komadugu a jahar Diffa a gaban hukumomin bariki da na gargajiya da kuma sauran al'umma, wanda ya kai ga zaɓen Hassan Mamadou Abba Kyari a matsayin sabon sarkin na Komadugu. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Abdoullaye Issa.
Shirin muhallinka rayuwarka na wannan karon zai mayar da hankali ne kan irin fama da ake sha a karshen damina tsakanin manoman da suke tattarar Kayan gona da makiyayan dake dawowa daga kiwo zuwa wuraren da ake aikin noman a wasu sasaan Jamhuriyar Nijar. A duk karshen damana makiyayan da suka tafi mashekari wurin kiwon dabbobinsu inda ke da isassar ciyawa nesa da gonaki na sabkowa wuraren da ake aikin noma don ganawa da jama'a, sannan da samun sauran tarikicen da manoman suka bari a gonakansu. Sai dai a irin lokacin na komawar makiyayan ana samun rikicin dake faruwa ' tsakaninsu da manoman da ba su ida tattare Kayan da suka noma ba, kuma da yanda wasu makiyayan ke saurin komowa a lokacin da manoman ke tsaka da aiki, duk da an tanadi dokar da ta tsaida komi a kasar ta Nijar.
Shirin "Al'adun mu na Gado" na wannan makon ya yi duba ne akan sana'ar nan ta sassaƙar Turmin, wadda ke a matsayin sana'ar al'adun gargajiya, ko da yake a yanzu samar da na'urori da ke amfanin da Turmin keyi ya mayar da sana'ar baya matuka gaya. A baya duk macen da za'a kai gidan miji, akan hadata da Turmin babba da ƙarami kana da kuma na ƙarfe wanda za ta rika daka kayan ƙanshi wasu ma hatta Kwalli fari da ake sanyawa jarirai da shi suke dakawa, baya da kuma na da kan sakwara da kuma babba na surfe da daka. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa............
Shirin "Duniyar Wasanni" tare da Khamis Saleh a wannan lokaci zayyi duba ne kan ƙyautar gwarzon ɗan wasan ƙwallon ƙafan Afirka da Achraf Hakimi na Morocco ya lashe. A makon daya gabata ne Hukumar Kwallon Ƙafar Afrika CAF, ta bayar da kyautuka ga zaratan ƴan wasan nahiyar da suka nuna bajinta a wannan shekarar da muke bankwana da ita. A yayin bikin da ya gudana a birnin Rabat na ƙasar Morocco, hukumar ta CAF ta sanar da ɗan wasan baya na tawagar ƙasar ta Morocco wanda kuma ya ke yi wa ƙungiyar PSG wasa Achraf Hakimi, a matsayin wanda ya lashe ƙyautar gwarzon ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Afirka a wannan shekarar. Hakimi ya samu nasarar ce bayan doke shahararrun ƴan wasan nahiyar da suka taɓa lashe kyautar irinsu Mohamed Salah na Masar da ke taka leda a Liverpool, da kuma Victor Osimhen na Nigeria da ke wasa a Galatasaray. Wannan ne dai karo na farko da ɗan wasan ya taɓa lashe ƙyautar, bayan da a karo biyu a jere ya na ƙarewa a mataki na biyu, a shekarar 2023 da Victor Osimhen ya lashe da kuma 2024 da Ademola Lookman ya lashe. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin...
Da alama masu ɗauke da makamai a Najeriya sun koma gidan jiya na sace-sacen dalibai, garkuwa da mutane da ajalin waɗanda basu ji basu gani ba gadan-gadan, yayin da a cikin kwanaki huɗu kacal aka yi awon gaba da mutum 145. Wannan na zuwa ne a yayin da matsalolin tsaro ke sake ta'azzara a sassan arewacin ƙasar, ciki har da satar ɗaliban da aka yi a jihar Kebbi, sai kuma labarin da ake ta yamaɗiɗin cewa mayaƙan ISWAP sun yi garkuwa da wani janar din soji tare da kashe shi a arewa maso gabashin Najeriyar. Shin kun gamsu da yadda jami'an tsaro ke aiki a yankunan ku. Me kuke ganin ya kamata hukumomi su yi domin kawo ƙarshen zulumin da jama'a ke ciki? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Gwamnan Jihar Borno Babagana Umara Zulum ya buƙaci rundunonin sojin Najeriya na sama da na ƙasa da kuma na ruwa, da su ƙaddamar da gagarumin farmaki kan sansanonin ƴan ta'addan da ke zagayen Yankin Tafkin Chadi, domin murƙushe matsalar tsaron da ta addabi Yankin. Kiran da gwamnan na Borno ya yi a farkon makon nan, na zuwa ne a yayin da matsalolin tsaro ke sake ta'azzara a sassan arewacin ƙasar, ciki har da satar ɗaliban da aka yi jihar Kebbi. Domin jin yadda masana tsaro ke kallon wannan lamari Nura Ado Suleiman ya tattauna da Kanal Muhammad Sani Ibrahim Makiga mai ritaya, masanin tsaro a Najeriya.
Shirin al'adun mu na gado na wannan mako ya mayar da hankali ne kan yadda ƴan siyasa ke katsalandan a masarautun gargajiya a Najeriya. Danna alamar sauarre domin jin cikakken shirin tare da Abdullahi Isa
Fatan Najeriya na samun gurbi a gasar cin kofin duniyar da za'a yi a shekara mai zuwa ya gushe, sakamakon rashin nasarar da ƙungiyar Super Eagles ta yi a hannun ƙasar Congo. Wannan shi ne karo na biyu a jere da Najeriya ba zata je gasar ta dunitya ba, bayan gaza zuwa Qatar shekaru 4 da suka gabata, kafin wannan karo. Bashir Ibrahim Idris, ya tattauna da tsohon sakatare janar na Hukumar Kwallon Kafa Najeriya, Hon Sani Ahmad Toro game da wannan koma baya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana a kai.
Shirin Duniyar Wasanni a wannan lokaci ya yi duba ne kan yadda wasan ƙarshe na nemon gurbin wakiltar Afrika a matakin duniya, wajen samun tikin zuwa gasar lashe kofin duniya ya gudana tsakanin Najeriya da Jamhuriyar Dimukaraɗiyyar Congo. Karawar da suka yi a filin wasa na Moulay Abdellah da ke birnin Rabat, ta kai matakin dugun daga kai sai mai tsaron gida bayan da suka tashi 1-1. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh............
Shirin lafiya jari ce na wannan mao ya mayar da hankali ne kan wani rahoto da ke cewa mutane akalla miliyan 24 ne ke fama da cutar Suga a Nahiyar Afrika kawai. Wannan kuwa na faruwa ne a dai-dai lokacin da cutar ke sauya salo da tsanani ga masu fama da ita, baya ga bijirewa magani. Danna alamar sauraro domin jin cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu.
Shirin Duniyar Wasanni na wannan mako ya mayar da hankali ne kan gasar da tsofaffin ƴan wasan Najeriya da suka fito daga jihohin Arewacin ƙasar suka fafata. A makon daya gabata ne garin Maiduguri babban birnin jihar Borno, ya karɓi baƙuncin gasar kofin Sardauna karo na 13, wacce tsofaffin ƴan wasan da suka fito daga jihohi 19 na Arewacin Najeriya suka ƙirƙira da zummar sada zumunci da kuma haɗa kan jihohin arewacin ƙasar. Tawagar da ta wakilci jihar Kebbi a wannan gasa ce dai ta yi nasarar lashe wannan kofi, bayan da ta doke takwararta ta Kano a bugun daga kai sai mai tsaron gida da ci 4-3. Latsa alamar sauti don sauraren shirin tare da Khamis Saleh...
Shirin muhallinka rayuwarka na wannan yau zai maida hankalin ne kan wani ruwan dake bullowa daga kasa Wanda ya yi sanadiyar zubewar gidaje da kashe bishiyoyi da ga gurbata hanyoyi a unguwar Garin Malam ta Damagaram a Jamhuriyar Nijar. Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Micheal Kuduson.
Shirin Al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali kan yadda sananniyar al'adar nan ta zaman ɗaki ke ƙoƙarin shuɗewa tsakanin al'ummar Hausawa. Shekaru aru-aru, da zarar an yi auren budurwa a ƙasar Hausa akan haɗata da ƙaramar yarinya da za ta yi mata zaman ɗaki, wanda a wasu lokutan anje kenan domin galibi aure ke raba wannan ƙaramar yarinya da gidan, kodayake wasu kan shafe wani wa'adi ne gabanin komawa gaban iyayensu na ainahi. Sai dai a ƴan shekarun nan wannan al'ada da kan yi tasiri wajen ƙarfafa zumunci ta zama tarihi, walau ko saboda yanayi na rayuwa, ko kuma saboda yadda aka tsagaita da auren ƴammata masu ƙarancin shekaru da dai sauran dalilai. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin...
Shirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan mako ya nazarci yadda aka yi fafatawa mai cike da armashi tsakanin Barcelona da Real Madrid wato haɗuwar hamayya tsakanin manyan ƙungiyoyin na Spain guda 2 karawar da ake kira El-Classico. Yayin haɗuwar ta wannan karo dai, Real Madrid ce ta yi nasara da ƙwallaye 2 da 1 duk da ya ke wasan ya gudana ne a gidanta wato filinta na Santiago. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin wannan makon zai tare ne a jihar Kano dake Tarayyar Najeriya, inda aka samu manoma da dama a wasu yankuna da suka duƙufa wajen noman barkono a wannan shekarar. Ba shakka sun yi aiki tuƙuru, kuma haƙarsu ta cimma ruwa duba da ɗimbim barkono da suka girba. Wannan lamari dai ya tayar da hankalin waɗannan manoma, waɗanda sun sauya alƙibla ne saboda ganin yadda farashin amfanin gona dangin hatsi ya faɗi warwas a kasuwanni, kuma sun yi haka ne domin su more daga ribar da aka yi ta ci daga barkono, amma sai gashi lamarin ya yi musu ta leƙo ta koma. A kusan ilahirin kasuwannin kayan gwari, gani za ka yi ga barkono, wanda kafin yanzu yake tamkar gwal, sai ga shi yanzu masu saye su na mai tayin da suka ga dama. Masana sun yi ittifakin cewa, ba shakka rashin tsari da alƙibla wajen noma da kuma binciken halin da kasuwa ke ciki sun taka rawa ainun a wcikin wannan matsala da aka samu. Sai dai kuma, matsaloli na yanayi ma sun taka irin nasu rawar, domin akwai matsin lamba daga yadda tsarin ruwan sama ya sauya, da sauraan matsaloli da suka addabi ƙasar noma. Matsalar yanayi da muhalli na mummunan tasiri akan ko wane irin nau'i na noma. shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin, tare da Michael Kuduson.
Shirin a wannan mako ya yi tattaki ne, zuwa ƙauyen Ingal da ke Yankin Agadez a jamhuriyyar Nijar, domin waiwayar gagarumin bikin makiyaya da ƙabilu daban-daban da ake yi wa laƙabi da 'Cure Salee' wanda aka saba yi duk shekara. Bikin makiyayan na Cure Salee ya gudana ne a tsakanin ranakun 4 zuwa 6 ga watan da muke ciki na Oktoba. Manufar bikin ita ce yadda za a ƙarfafa haɗin kai tsakanin makiyaya domin kafa ginshiƙin zaman lafiya mai ɗorewa a tsakanin ƙabilu. Bikin na bana ya samu halattar ƙabilun Fulani da na Abzinawa da Larabawa a Nijar ɗin da wasu daga Najeriya, da Mali da burkina Faso da kuma Aljeriya. Latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Nura Ado Sulaiman...............
A wannan makon shirin na Kasuwa Akai Miki Dole tare Abdulƙadir Haladu Kiyawa zai tattauna ne a kan yawaitar matasan Najeriya masu muhimman sana'o'in hannu da ke yin ƙaura ko kuma tafiya ci rani zuwa wasu ƙasashen Afrika domin neman na rufin asiri, abin da ake alaƙantawa da dalilai da dama da ke sanya matasan ficewa daga ƙasar tasu ta haihuwa. A shekarun baya ba haka lamarin yake ba, inda Najeriyar ke matsayin wajen da ɗimbin ƴan ƙasashen ƙetare ke kwarara don neman kuɗi musamman ƴan kasashen Afrika kamar Jamhuriyar Nijar, da Ghana, da Jamhuriyar Benin, har ma da Kamaru. To Sai dai a yanzu, waɗannan ƙasashen ne ƴan Najeriyar ke tururuwar zuwa cikinsu duk da kasancewar ƙasashen ba su da ɗinmbin arziƙi kamar Najeriyar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin...
Shirin al'adunmu na gado tare da Nura Ado Suleiman a wannan makon ya mayar da hankali ne kan gushewar sana'ar kaɗi a ƙasar Hausa duk da kasancewarta guda cikin sana'o'in Hausawan suka gada kaka da kakanni. Galibi sana'o'in Hausawa na tafiya ne da tsarin rayuwa da zamantakewar jama'a, cikin wannan kuwa har da sana'ar kaɗi wadda galibi dattawa Mata suka fi ƙwarewa akai, kodayake wannan sana'a na gab da gushewa. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin Ilimi Hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako ya mayar da hankali ne kan dokar da ta tilastawa makarantu masu zaman kansu rage kudin makaranta da gwamnatin Nijar ta kafa, wanda ke zuwa bayan ƙarin hutun makarantu na makwanni biyu saboda mamakon ruwan a ƙasar ta yankin Sahel. Ƙarƙashin wata doka da shugaban gwamnatin Sojin Nijar Abdourraham Tchiani ya sanya hannu ce ta buƙaci dukkanin makarantun su rage kuɗin da suke karɓa da kashi 20, kodayake wannan doka bata shafi makarantun da ke karɓar kuɗin da bai kai CFA jaka hamsin ba. Tuni iyaye suka yi maraba da wannan mataki. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin a wannan mako tare da Azima Bashir Aminu ya yi duba kan yawaitar samun cutar Kwalara ko kuma amai da gudawa a sassan Najeriya, cutar da a baya-bayan nan ta kashe ɗimbin al'umma a ƙasar mafi yawan jama'a a Nahiyar Afrika. Wasu alƙaluma da hukumar yaƙi da cututtuka masu yaɗuwa ta ƙasar NCDC ta fitar sun nuna cewa mutane kimanin dubu biyar (5,000) cutar ta kwalara ta halaka a sassan Najeriyar daga shekarar 2020 zuwa 2025 da muke ciki. Latsa alamar sauti don sauraron shirin tare da Azima Bashir Aminu.............
Shirin ‘Kasuwa A Kai Miki Dole' na wannan mako zai tattauna ne kan wasu alƙaluma da suka nuna yadda Najeriya ta Kashe Dala Biliyan 2.86 a cikin watanni 8 na farkon shekarar da muke ciki ta 2025, wajen Biyan Kuɗin Ruwan Basukan da ta karɓo daga ƙasashen ƙetare tare da Nura Ado Suleiman..... Latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin...........
Shirin kasuwa a Kai miki dole na wannan mako ya yi duba ne kan yadda ake gudanar da hada-hadar kayayyakin amfanin gona da ake samu a damina,waɗanda ake shukawa da sauran tsirrai da ake samu a daji saboda saukar ruwan sama.Ɗaya daga cikin falalar ruwa ita ce Allah ya rayar da amfanin gona.Da zarar damina ta yi nisa kayan amfanin gona da sauran tsirrai da ba shukasu aka yi ba, suka fara yabaya, to daga nan za'a fara ganin hada-hadar waɗannan kayayyaki irinsu ɗanyar masara,wake, gujiya,da wasu ƴaƴan itatuwa da ake samu a wannan lokaci kadai, harma halitu irinsu Fara. Latsa alamar sauti don sauraron shirin tare da Ahmed Abba............
Shirin ilimi hasken rayuwa na wannan mako ya duba yadda wasu manoma a Najeriya, musamman arewacin kasar ke hana yaransu zuwa makaranta, har sai an yi girbin amfanin gona, saboda wasu dalilai Ku shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.....
Shirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh ya mayar da hankali kan yadda ɗan wasan gaba na PSG ɗan Faransa Ousmane Dembele ya lashe kyautar Ballon d'Or a bana, bayan nasarar shi ta lashe kofuna da dama cikin kakar da ta gabata da ƙungiyar tasa da ke birnin Paris. Duk da cewa anjima ana hasashen Dembele ya lashe wannan kyauta lura da namijin ƙoƙarinsa a kakar da ta gabata, amma wasu na da ra'ayin cewa sam ɗan wasan bai cancanci wannan kyauta ba. Game da wannan saɓanin ra'ayi, shirin na Duniyar Wasanni ya tattauna da masana a fagen na wasanni waɗanda suka bayyana ra'ayoyinsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin ‘Muhallinka Rayuwarka' a wannan makon ya mayar da hankali ne kan yadda manoma a Nijar suka koma noman Gyaɗa da riɗi gadan-gadan bayan sun yi watsi da shi tsawon shekaru, saboda matsaloli da noman ke fuskanta.Maraɗi ce kan gaba a noma Gyada ko Gujiya shekaru aru aru, sai Zinder da kuma Doso, waɗanda suka taimaka wajan hada-hadar kasuwancin Gyaɗa har a Kano inda ake tattara Dalar Gyadar.Yawan noman Gyadar ne ma ya sa turawan mulkin mallaka suka kafa masana'antar sarrafa man Gyada a 1943 a Maraɗi. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Michael Kuduson...........
Shirin Ilimi Hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako ya mayar da hankali ne kan yadda bikin yaye ɗalibai da ɗabi'ar rubutu a jikin rigunan juna dama sauran shagulgulan da akanyi a bikin na kammala makaranta ke taka muhimmiyar rawa wajen lalata tarbiyyar ɗalibai. Tsawon shekaru aka ɗauka wannan dabi'a na ciwa iyaye tuwo a ƙwarya dama sauran masu ruwa da tsaki a ɓangaren tarbiyyar al'umma. Sai dai bayan tsanantar ƙorafe-ƙorafe kan wannan ta'ada, kwatsam an wayi gari gwamnatin jihar Kaduna ta yi uwa da makarɓiya wajen haramta irin bukukuwan har ma da wasu ƙarin dokoki da suka shafi sashen na ilimi ciki har da haramtawa makarantu ƙarin kuɗin makaranta. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Shamsiyya Haruna.
Shirin Al'adunmu na Gargajiya tare da Nura Ado Suleiman a wannan makon ya sake waiwayar fagen Waƙa guda daga cikin fannoni masu tasiri a Adabin Harshen Hausa la'akari da gudunmawar waƙoƙin da kuma mawaƙan da ke rera su wajen bunƙasa harshen. Tun cikin makon jiya masana da sauran jama'ar gari ke tofa albarkacin bakunansu akan karramawar da wata Jami'a mai suna European-American University ta yi wa fitaccen mawaƙin siyasa a Najeriya Dauda Kahutu Rarara, wanda ta bai wa Digirin Girmamawa na Dakta. Reshen Jami'ar da bayanai a yanar gizo suka nuna cewar hedikwatarta na ƙasar Faransa ne ta yi bikin Karrama mawaƙi Raran ne a Abuja, ranar Asabar, 20 ga watan nan na Satumba, taron da ya samu halartar wasu fitattun mutane. Sai dai Kash! ‘yan sa'o'i bayan bikin da aka yi Jami'ar da ake alaƙanta da Turai da Amurka ta ce ba ta fa san zance ba, domin ba da yawunta aka miƙa wa fitaccen mawaƙin siyasar Digirin na Girmamawa ba, zalika dukkanin mutanen da suka yi iƙirarin alaƙanta kansu da ita ta barranta da su, domin sun yaudari mutane ne da sunanta domin samun damar karɓar na goro a huce. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin na Lafiya Jari ce a wannan makon tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan yadda ake ganin yawaitar jinyace-jinyace mabanbanta da kan kwantar da jama'a kama daga mashasshara ko mura ko kuma ƙurajen jiki dama wasu nau'in cutukan daban-daban, musamman ga ƙananan yara a lokacin damuna. Zubar ruwan sama da yawaitar ƙwari baya ga raɓa na daga cikin abubuwan da kan haddasa cutukan dama ƙamjiki, batun da Dokta Ila Aishatou jagorar gidan asibiti CSI stade a birnin Damagaram ke cewa akwai matakai na kare kai daga irin cutukan na damuna musamman ga ƙananan yara. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.
Shirin ‘Muhallinka Rayuwarka' a wannan makon ya mayar da hankali ne kan wata matsala da ta kunno kai tsakanin makiyaya da manoma a yankin ƙananan hukuomin Guri da Kiri Kasamma da kuma Kaugama na jihar Jigawa a Arewacin Najeriya, inda Fulani makiyaya suka koka kan yadda aka salwantar da wuraren kiwon dabbobinsu da wurin shayar da su. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Michael Kuduson...........
Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Nigeria wato ICPC, ta bayyana damuwa kan yadda matsalar rashawa ke ci gaba da haɓaka, duk kuwa da matakan da ta ke ɗauka. A cewar Shugaban hukumar ta ICPC, Dr Musa Adamu Aliyu, a yanzu sun karkata akalarsu ne zuwa ga ƙananan hukumomi, don daƙile matsalar cin hanci da ta yi katutu... Latsa alamar sauti don sauraron ƙarin bayanin da Dr Musa Adamu, ya yi wa wakilinmu Ibrahim Malam Goje........
Shirin a wannan makon tare da Ahmed Abba ya mayar da hankali ne kan yadda ake ƙara samun raguwar kayayyakin masrufi a Najeriya. Hukumar ƙididdiga ta Najeriya NBS, tace watanni biyar jere kenan, ana samun raguwar hauhawar farashin kayayyaki a ƙasar, inda tace an samu sauƙar farashin kayyaki a watan Agustan da ya wuce, da kaso 1 da ɗigo 76 cikin 100, wanda hakan ke nuna yadda aka samu sauƙi fiye da kaso 21.88 na watan Yuli, yayin da yanzu kuma ya koma kaso 20.12 cikin 100. Latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin........
Hukukumar Yaƙi da Rasha ta ICPC a Najeriya, ta ce yanzu haka tana ƙara sa-ido dangane da yadda ake kashe kuɗaɗe mallakin ƙananan hukumomi a ƙasar. Wannan na zuwa ne a dai-dai lokacin da gwamnatin tarayya ke shan matsin lamba domin ganin ta aiwatar da hukuncin Kotun Ƙoli wanda ya buƙaci a zuba wa ƙananan hukumomin kuɗadensu kai-tsaye a maimakon bi ta hannun gwamnonin jihohi. Ko me za ku ce a game da jan ƙafa wajen aiwatar da wannan umarni da kotu ta bayar tun watan Yulin shekara ta 2024 da ta gabata? Wace irin rawa ya dace ICPC ta taka don kare dukiyar ƙananan hukumomi a Najeriya? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakin ku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi mabanbanta...
Shirin na wannan rana zai ɗora kan wanda muka gabatar muku a makon jiya game da karancin malamai a makarantun jihar Jigawa ta arewacin Najeriya. Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Nura Ado Sulaiman.
Kamfanin Dangote ya fara aikin rarraba man fetur daga matatarsa zuwa sassan Najeriya domin saukakawa jama'a, a dai-dai lokacin da manyan dilallan man fetur ke adawa da matakin. Dashi Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki, Alahji Isa Tafida Mafindi a kan yadda talakawa zasu ci gajiyar wannan shirin. Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar.
Shirin Lafiya Jari ce na wannan mako tare da Azima Bashir Aminu, ya maida hankali ne kan yadda jama'a suka fi yadda da shagunan sayar da magunguna na bakin titi wato Chemist, maimakon zuwa asibiti domin ganin Likita..... Latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin..........
Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyyar Nijar na ci gaba da kamen waɗanda ke sukar lamirinta da suka haɗar da ƴan jarida da masu fafutuka har ma da ƴan siyasa. A wani rahoto da ta fitar a baya bayan nan kungiyar kare haƙƙin bil Adam Human Right Watch ta soki yadda sojojin da suka ƙwace muki a ƙasar ke tsare jama'a babu gaira babu dalili. Akan wanan abokin aiki Oumarou Sani ya tattaunawa da Mamane Wada shugaban ƙungiyar yaƙi da cin hanci da rashawa ga kuma yadda zantawarsu ta gudana. Latsa alaamar sauti don sauraron yadda tattaunawar ta su ta gudana...........
Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyyar Nijar na ci gaba da kamen waɗanda ke sukar lamirinta da suka hadar da ƴan jarida da masu fafutuka har ma da ƴan siyasa. A wani rahoto da ta fitar a baya bayan nan kungiyar kare hakkin bil Adam Human Right Watch ta soki yadda sojojin da suka kwace muki a ƙasar ke tsare jama'a babu gaira babu dalili. Akan wanan abokin aiki Oumarou Sani ya tattaunawa da Mamane Wada shugaban kungiyar yaki da cin hanci da rashawa ga kuma yadda zantawarsu ta gudana.
Shirin ilimi Hasken rayuwa na wannan rana ya mayar da hankali ne kan tsarin koyarwa da Nijar ke yi na baiwa dalibai karin horaswa akan darussa masu wahala a lokutan hutu. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Nura Ado Sulaiman.
Kawo yanzu dai wasanni sun ɗauki zafi ganin cewa wasu daga cikin tawagogin ƙasashen sun fara jin kanshin halartar gasar, amma kuma wasu har yanzu tana ƙasa tana dabo. Tawagar ƙasar Morocco tuni ta samu nata tikitin bayan da ta haɗa maki 18, tazarar maki 8 tsakaninta da Tanzania. Tawagogin ƙasashe irinsu Masar da Algeria da Tunisia da Ghana da Afrika ta Kudu, duk da cewa akwai tazarar maki masu ɗan dama tsakaninsu da waɗanda ke mataki na biyu a rukunansu, har yanzu akwai sauran rina a kaba.
Shirin lafiya jari ce a wannan mako ya leƙa Jamhuriyar Nijar, inda a dai dai lokacin da ake ganin yawaitar ƙananan yaran da ke fama da cutar yunwa sanadiyyar ƙarancin abinci mai gina jiki da ake kira ƙwamuso a sassan jamhuriyar Nijar, wata matsala da ke tunƙaro shirin yaƙi ko kuma taimakon masu fama da lalurar shi ne yadda ake karkatar da abincin da aka tanadar dominsu.............
The Yadda Yadda is back for episode 118, and with some big news in the music world. They discuss the possible fallout with Jess Hilarious & Loren Lorosa, Playboi Carti selling 300k and Kanye's sad fall from grace.
For episode 119, the Yadda Yadda crew takes on a heavy topic today, as the crew discusses the new single from YG, "2004". Playboi Carti also continues his dominance on the charts and we also discuss the new albums from MyNameIsntJMack and Saba & No I.D.
2024 sure was a year that happened, huh? It really, really happened. Such an important, vital year. *Sigh* But hey! Some good stuff happened that year, and we’re gonna focus on it this week. What’s the GOOD stuff that… Continue Reading → The post 459: Yadda Yadda Dumb Place appeared first on Zero Issues Comic Podcast.
Without geese, sadly. X4, Wandering Inn. Yadda etc
Josh grew up in Chester, Virginia, about 20 minutes south of Richmond off I-95. Sports and competition made a big impact in his early years. After being All-State in two sports, he accepted a football scholarship to play Linebacker at Shippensburg University. He still holds the career solo tackles record from starting all 4 years. Josh's first job in hospitality was as a server and barback at Bottoms Up Pizza in Richmond, Va. Prior to PourMyBeer, he worked in Business Development with Modis, a publically traded IT Staffing Firm. He was hired to develop the Baltimore Metro market for the company. Landing several blue-chip accounts took that market from non-existent to a top producer in a matter of 24 months. One day in 2009, he decided he wanted to take a 95% pay cut, quit his job where he played golf 3 days a week, and invest his entire life savings in building a self-pour company. Yadda, yadda, yadda, here we are today after 3 significant chapters in business and life. To get the full story go to TapTheBigIdea.com His wife, Janette (Pieczynski) Goodman, is in the Shippensburg University Women's Basketball Hall of Fame, holds the school record for career steals (not including Josh's heart), and is a Marketing Director for Astellas Pharmaceuticals. They have 2 children, Tyler and Brianna, and live in Harleysville, Pa (30 minutes north of Philadelphia) with their Goldendoodle, Belle, and their bearded dragon Coco. Outside of PourMyBeer, Josh enjoys biking, snowboarding, basketball, pickleball, cornhole, grilling, hazy IPAs, and singing 90's hip hop in his car by himself. Follow Travis on:– IG