Podcasts about afirka

  • 18PODCASTS
  • 285EPISODES
  • 11mAVG DURATION
  • 1WEEKLY EPISODE
  • May 26, 2025LATEST

POPULARITY

20172018201920202021202220232024


Best podcasts about afirka

Latest podcast episodes about afirka

Lafiya Jari ce
Sharhi kan ƙiba fiye da ƙima da ke baraza ga matasan Afirka

Lafiya Jari ce

Play Episode Listen Later May 26, 2025 10:12


Shirin 'Lafiya Jari Ce na wannan mako tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan hasashen da wata ƙungiya ta yi cewar nan da shekarar 2025 raɓin al'ummar Afirka masamman matasa za su fuskanci cutar ƙibar da ta wuce ƙima ko Obesity a turance.

obesity baraza najeriya afirka
Bakonmu a Yau
Janar Alwali Kazir kan matakin ECOWAS na samar da rundunar yaki da ta'addanci

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later May 23, 2025 3:38


Kungiyar kasashen Afirka ta Yamma ta ECOWAS ta bayyana shirin kafa sabuwar rundunar hadin kai wadda za ta dinga yaki da yan ta'addan da suka addabi yankin. Wannan na da cikin shirin shugabannin yankin na dakile ayyukan ta'addanci, da suka ƙi ci suka ƙi cinyewa.Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Janar Kape Alwali Kazir mai ritaya a dangane da wannan shiri.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

samar ecowas yaki shiga yamma wannan afirka bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Malam Bashir Ibrahim Idris kan cika shekaru 18 da kafuwar RFI Hausa

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later May 21, 2025 3:39


A yau 21 ga watan Mayun 2025, shekaru 18 kenan da Radio France International ya fara yaɗa shirye-shiryensa a cikin harshen Hausa, wanda kuma shi ne harshen na farko daga Afirka da RFI ta fara yaɗa shirye-shiryenta da shi. Malam Bashir Ibrahim Idris, shi ne Babban Editan RFI Hausa, ya yi muna ƙarin bayani a game da yadda rediyon ya fara da kuma irin ci gaba da ya samu a waɗannan shekaru. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawar da Ƙaribullah Abdulmajid Namadobi ya yi da shi...........

ku malam rfi hausa najeriya afirka bashir ibrahim idris
Tambaya da Amsa
Tasirin harajin da shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaƙabawa wasu ƙasashe

Tambaya da Amsa

Play Episode Listen Later May 10, 2025 20:53


A yau shirin tamabaya da amsa, tare da Nasiru Sani, zai kawo muku bayanai ne akan tasirin tsarin harajin da shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaƙabawa ƙasashen Canada da Mexico da kuma China akan ƙasashe Afirka. Shirin ya kuma zanta da kwararru a fannin lafiya, kan dalilan da ke sanya shan ruwa a kai.Akwai kuma cikakken bayani kan Sultan Makenga, wato jagoran ƙungiyar 'yan tawayen M23 wanda ya hana zaman lafiya a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo, musamman ma a gabashin ƙasar.Shiga alamar sauti, domin saurarin cikakken shirin.

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan bikin ranar ma'aikata a sassan duniya

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later May 1, 2025 8:55


Kamar dai kowace shekara, yau 1 ga watan Mayu, ita ce Ranar Ma'aikata ta Duniya, bikin da a bana ana iya cewa ana gudanar da shi ne a cikin wani yanayi na tsadar rayuwa a mafi yawan ƙasashen duniya. Abin tambayar shine, shin ko a cikin wanne yanayi ake gudanar da bukukuwan na bana, musamman a kasashen Afirka?Waɗanne irin manyan buƙatu ma'akata suke son cimma wa?Shiga alamar sauti, diomin sauraron ciakken shirin.

Al'adun Gargajiya
Tasirin suturar ƙabilar Dagomba da ke ci gaba da mamaye sassan Ghana

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Apr 29, 2025 10:07


Shirin al'adunmu na gado tare da Oumarou Sani a wannan mako ya mayar da hankali ne kan al'adun ƙabilar Dagomba a ƙasar Ghana, ƙabilar da ke ci gaba da mamaya a wannan ƙasa ta yammacin Afirka suk da kasancewarta wadda a baya tafi ƙarfi a yankin arewacin ƙasar. Yanayin suturun wannan ƙabila na daga cikin abin da ke jan hankalin jama'a, musamman yanayin hularsu wadda ke da nufin ko kuma ma'anar zaman lafiya.Suturun wannan ƙabila dai akan saƙa su da hannu ne.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

Kasuwanci
Ghana ta bai wa 'yan ƙasashen waje wa'adin ficewa daga kasuwancin zinare

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Apr 23, 2025 9:57


Yau shirin ya yada zango ne ƙasar Ghana, inda ya mayar da hankali kan matakin gwamnatin ƙasar na bai wa ƴan ƙasashen waje wa'adin ficewa daga kasuwancin zinare.Ƙasar Ghana ta bai wa ƴan ƙasashen waje da su fice daga harkokinta na kasuwancin zinare a ƙarshen wannan wata na Afirilu a wani mataki na bunƙasa kananan masu hakar zinare na cikin gida da kuma samun ƙudin shiga. Ƙasar ta yammacin Afirka dake kan gaba a samar da zinare a nahiyar na ƙokarin tsaftace harkokin harƙar zinare ta hanyar daidaita cinikin zinari daga kananan masu hakar ma'adinai.

Kasuwanci
Tasirin sabbin harajin Amurka ga ƙasashen Afirka masamman Najeriya

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Apr 16, 2025 10:04


Shirin 'Kasuwa A kai Miki Dole' na wannan makon ya mayar da hankali kan tasirin matakin shugaban Amurka Donald Trump kan shirin sa na sanya gagarumin ƙarin haraji ga kusan ɗaukacin ƙasashen duniya, wanda ya jawo durƙushewar kasuwannin  hannayen jari ta duniya da lalata alaƙa tsakanin ƙasar da ƙawayenta, duk da cewa ya yi amai ya lashe wajen dakatar da harajin da watanni uku masu zuwa. Shirin ya duba tasirinsa ga ƙasashen Afirka masamman Najeriya.

shirin najeriya afirka amurka
Bakonmu a Yau
Tasirin harajin da Trump ya ɗorawa ƙasashen duniya a kan Afirka

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Apr 8, 2025 3:09


A Laraba 9 ga watan Afrilu, sabon harajin da ya kama daga kashi 10 zuwa sama, da shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaƙaba wa ƙasashen Afirka zai fara aiki, bayan da harajin da ya shafi sauran ƙasashe ya soma aiki a ranar 5 ga watan na Afrilu.  Tun cikin makon jiya ne dai matakin na Trump ya soma tasiri a kasuwannin Turai da Asiya, a yayin da ƙasashen Afirka suka shiga zulumi dangane da makomarsu.Don jin tasirin da sabon harajin na Amurka zai yi a kan tattalin Arzikin arziƙin ƙasashen Afirka, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dr Ƙasim Garba Kurfi.A latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar zanatawar.

Wasanni
Tasirin masu horarwa na cikin gida wajen ɗaga likafar tawagogin ƙasashen Afirka

Wasanni

Play Episode Listen Later Mar 24, 2025 9:59


Shirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan makon ya mayar da hankali kan tasirin masu horarwa na cikin gida a ci gaban ƙwallon ƙafar nahiyar Afirka. A baya-bayan nan ƙasashen na nahiyar Afirka sun mayar da hankali wajen ɗaukar masu horarwa na cikin gida tun bayan rawar da Morocco ta taka a gasar cin kofin Duniya ta 2022 karon farko da aka ga irin hakan daga wata ƙasa a nahiyar ta Afrika.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

Wasanni
Yadda zaɓen shugabannin Hukumar Ƙwallon Ƙafar Afirka ya gudana

Wasanni

Play Episode Listen Later Mar 17, 2025 9:59


A makon da ya gabata ne dai Hukumar Ƙwallonn Kafar Afirka CAF ta gudanar da zaɓenta, inda aka sake zabar Patrick Motsepe a matsayin shugaba a  karo na biyu. Bayan haka ne aka gudanar da zaɓen wakilan nahiyar a Hukumar Ƙwalllon Ƙafa ta Duniya, FIFA, inda Afirka ke da wakilai 6, har da shugaban CAF mai kujerar kai-tsaye..

Mu Zagaya Duniya
Majalisar Ƙoli ta Musulinci ta gargaɗi malaman Najeriya akan tada husuma

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Mar 1, 2025 20:02


Daga cikin labarun da shirin Mu Zagaya Duniya na wannan makon ya ƙunsa akwai gargaɗin da Majalisar Ƙoli kan Shari'ar Musulunci ta Najeriya ta yi wa Malamai kan cewa su yi taka tsan-tsan yayin gabatar da wa'azi, musamman a cikin watan Azumin Ramadana mai alfarma. Sojojin Somaliya sun halaka mayaƙan Al Shebaab a ƙalla 70.Muna kuma ɗauke da bitar rahoton da ya gano yadda wata muguwar ƙwaya mai ta kashe dubban mutane (Tare da ci gaba da aika wasu dubban zuwa asibiti) a wasu ƙasashen yammacin Afirka.

akan tada muna tare daga najeriya afirka majalisar
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu saurare kan shirin samar da lantarki ga gidaje 300M a Afirka

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Jan 30, 2025 9:36


Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sake jaddada aniyarsa ta inganta samar da wutar lantarki a faɗin ƙasar. Tinubu ya bayyana haka ne wajen taron ƙasashen Afirka wanda ya mayar da hankali akan yadda za a samar wa aƙalla mutane miliyan 300 wutar lantarki a nahiyar baki ɗaya. Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin...

Bakonmu a Yau
Akalla mutane miliyan 300 wutar zasu mori wutar lantarki-Tinubu

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jan 30, 2025 3:25


Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sake jaddada aniyarsa na inganta samar da wutar lantarki a fadin kasar. Tinubu ya bayyana haka ne wajen taron kasashen Afirka wanda ya tattauna yadda za'a samarwa akalla mutane miliyan 300 wutar a nahiyar baki daya. Ganin irin matsalolin wutar da ake fuskanta a Najeriya, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon manajan hukumar samar da wuta a kasar, Comrade musa Ayiga, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.

mori comrade akalla najeriya afirka bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Dr. Yahuza Getso kan ta'azzarar matsalolin tsaro a ƙasashen Afirka

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jan 15, 2025 7:01


Matsalolin tsaro na kara ta'azzara a ƙasashen Afirka masamman a Sahel da tafkin Chadi, inda aka ga yadda Boko Haram ke zafafa kai hare-hare a sansanoni da cibiyoyin jami'an tsaro a jihar Barno, yayin da mahara masu ikirarin jihadi suka tsanata kai farmaki a ƙasashen Nijar da Mali da Burkina Fado, ko a ranar Alhamis ƴan ta'adda sun kashe sojojin Benin kusan 30 a wani hari da suka kai arewacin ƙasar, sai kuma wani hari da ƴan bindiga suka kai fadar shugaban ƙasar Chadi da gwamnati ta  daƙile. A tattaunawarsa da Ahmed Abba, Dr. Yahuza Ahmad Getso masanin tsaro a Najeriya, ya ce duk da yadda ƙasashen ke ikirarin yaƙi da matsalolin tsaro, ba su da cikakkun tsare-tsaren da suka dace a bangaren soji da tafiyar da gwamnati, halisama ba da gaske su ke yi ba.

Bakonmu a Yau
Janar Pascal Lanni kan ficewar dakarun Faransa daga Chadi

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jan 13, 2025 3:42


A ranar Asabar ce Faransa ta mika sansanin sojinta na biyu a kasar Chadi ga mahukuntan kasar a wani bangare na janye sojojinta a karshen watan Janairu.Kimanin sojoji Faransa 100 ne suka bar sansanin Abéché a ranar Asabar, kafin janye na Djamena su kusan 1000.A tattaunawarsa da Ibrahima Timbi Bah, Editan sashin Fulatanci na RFI, kwamandan dakarun Faransa a Afrika Janar  Pascal Lanni ya yi karin haske kan ficewarsu daga Afirka. 

Mu Zagaya Duniya
Gudunmawar da marigayi Jimmiy Carter ya bai wa Afirka da Gabas ta Tsakiya

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Jan 4, 2025 20:08


Daga cikin labarun da shirin wannan makon ya waiwaya akwai yadda ɗaruruwan mutane mazauna ƙauyuka aƙalla 50 suka tsere daga muhallansu saboda barazanar da ƙasurgumin ɗan ta'adda Bello Turji yayi na kai musu farmaki, a ranar 1 ga watan Janairun da ya gabata. Sai kuma waiwayar rawar da tsohon shugaban Amurka marigayi Jimmiy Carter ya taka wajen samar da zaman lafiya a Yankin Gabas ta Tsakiya. 

sai daga afirka amurka
Bakonmu a Yau
Prof Shehu Abdullahi Zuru kan binciken yadda ƴan Afrika basa jin daɗin mulkin dimukaradiya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Oct 9, 2024 3:31


Shugaban Gidauniyar Shehu Musa Yar Adua Akin Kekere-Ekun, ya bayyana cewar kashi 80 na jama'ar nahiyar Afirka ba sa jin daɗin yadda zaɓaɓɓun shugabanninsu ke tafiyar da mulkin dimukiraɗiya a ƙasashen su. Jami'in ya ce akwai wagegen giɓi tsakanin yadda shugabannin ke mulki da kuma buƙatun jama'a, musamman abinda ya shafi ayyukan da suke so. Dangane da binciken da Gidauniyar ta yi, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Shehu Abdullahi Zuru na Jami'ar Baze da ke Abuja. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana........

prof afrika ku basa abuja baze abdullahi yadda zuru najeriya afirka bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Hukumar GIABA ta shirya taron fadakar da 'yan kasuwa da masu masana'antu da kuma lauyoyi

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Sep 26, 2024 3:19


Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasashen Afirka ta Yamma, wato GIABA ta shirya wani taron fadakar da 'yan kasuwa da masu masana'antu da kuma lauyoyi a kan hakkin da ya rataya a kansu na kin bada dama ga masu halarta kudaden haramun ko kuma 'yan ta'adad su yi amfani da su wajen boye kudaden sata. Taron na kwanaki 2 na gudana ne a birnin Lagos. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai magana da yawun GIABA Mr Timothy Melaye, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.

lagos taron masu yamma masana afirka hukumar bashir ibrahim idris
Mu Zagaya Duniya
Bitar labaran mako: Yadda sabon farashin man fetir ya shafi ƴan Najeriya

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Sep 7, 2024 20:31


Shirin 'Mu zagaya Duniya' na wannan mako tare da Rukayya Abba Kabara ya taɓo halin da aka shiga a Najeriya bayan da mahukunta suka kara farashin man fetur, sai kuma taron Afirka da China da kuma sabon fraministan Faransa.

china mako bitar shafi duniya yadda najeriya afirka faransa
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu saurare kan tasirin taron China da Afrika

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Sep 5, 2024 9:39


An fara taron shekara-shekara don kyautata hulɗa tsakanin China da Afirka wanda ya samo asali kimanin shekaru 24 da suka gabata.  Alƙaluma sun tabbatar da cewa China ita ce ƙasar da nahiyar Afirka ta gudanar da hulɗar tattalin arziki da kasuwanci fiye da kowace nahiya, yayin da a ɗaya bangare bashin da China ke bin Afirka ke ci gaba da ninkawa ninkin-ba-ninkin.Meye ra'ayoyinku a game da kamun lodayin China a fagen tattalin arziki, siyasa da kuma zamantakewa a nahiyar Afirka?Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Alheri Haruna.

Bakonmu a Yau
Dakta Ahmad Tijjani Lawal kan alaƙar Morocco da sauran ƙasashen Afrika

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Aug 28, 2024 3:36


Kasar Morocco ta tashi tsaye wajen kulla alaka ta kusa da sauran takwarorinta na nahiyar Afirka musamman ma kasashen da suke cikin ECOWAS, kungiyar da shekarun baya bayan nan Moroccon ta nemi a bata damar shiga cikinta. Yunkurin na Morocco na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke samun cigaba a fannoni da dama da suka hada da noma, samar da makamashi da kuma tattalin arziki.Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Ahmad Tijjani Lawal fashin baki kan lamurran kasa da Kasa dake Najeriya.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle
Taba Ka Lashe: 13.08.2024

Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle

Play Episode Listen Later Aug 13, 2024 9:47


Shirin ya duba yadda 'yan Afirka ke gudanaar da addinansu da ibadansu a kasar Jamus inda suke da zama. Wai shin suna zuwa masallantai da majami'u?

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu saurare kan gudummawar marigayi Issa Hayatou ga kwallon ƙafa

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Aug 12, 2024 10:03


A makon jiya ne Allah ya yiwa tsohon shugaban hukumar kwallon kafar Afirka Issa Hayatou rasuwa, bayan gajeruwar rashin lafiya. Hayatou da ya kwashe kusan shekaru 30 yana jagorancin hukumar, ya taka rawa sosai wajen ci gaban kwallon kafa a nahiyar, musamman bangaren matasa da kuma ganin an kara wa kasashen Afirka gurbi a gasar cin kofin duniya daga gurabe 2 zuwa 5.Shin kun gamsu da gudumawar da ya bayar?Kamar da me za ku tuna wannan gwarzo?

Mu Zagaya Duniya
Najeriya za ta bayar da damar shigar da kayan abinci ba tare da haraji ba

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Jul 13, 2024 20:00


Shirin duniya kamar yadda aka saba na duba manyan labaran da suka faru a sassan duniya A cikin shirin zaku ji cewa..............Gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin janye biyan kudaden haraji kan wasu muhimman kayayyakin abinci da ta dage haramcin shigar da su kasar, don saƙaƙawa jama'a raɗaɗin tsadar raywar da suke ciki.Matakin sojojin da suka yi juyin mulkin a Nijar, Mali da kuma Burkina Faso na tabbatar da ballaewarsu daga ECOWAS ya tayar da  hankalin kungiyar kasashen ta yammacin Afirka, a yayin da kwararru ke cigaba da bajakolin ra'ayoyinsu kan matakin.A Kenya kuwa, shugaban ƙasar William Ruto ne ya kori rankatakaf din ministocinsa sai fa ƙwaya biyu rak da ya bari, ‘yan kwanaki bayan zanga-zanga kan tsadar rayuwa da dubban matsasan kasar suka gudanar.Danna alamar saurare don jin gundarin shirin tare da Nura Ado Sulaiman.

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyi kan samar wa da Afrika alluran rigakafin cututtuka

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Jun 18, 2024 10:22


Gabanin taron da za a gudanar ranar Alhamis a birnin Paris don taimaka wa Afirka dangane da yadda za ta samar wa kanta da alluran rigakafin kariya daga wasu cututuka a wadace, tuni aka samu alƙawurran sama da Euro biliyan ɗaya daga ƙasashe da da kuma ƙungiyoyi daban daban a cewar fadar gwamnatin Faransa. Wadannan kuɗade za a yi amfani da su ne don tabbatar da cewa kamfanonin sarrafa magunguna sun samar da alluran rigakafin cututuka kamar Korona, Cholera da kuma zazzaɓin cizon sauro a cikin nahiyar.Shin me za ku ce a game da wannan tallafi na ƙasashen duniya zuwa ga nahiryar Afirka?Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin

Bakonmu a Yau
Girman tankiyar da ke tsakanin Nijar da Benin

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 18, 2024 3:30


Rikicin da ke wakana a halin yanzu  tsakanin Jamhuriya Nijar da Benin, na ci gaba da kawo cikas a kokarin da shugabani da gwamnatoci ke yi wajan samar cudanya  tsakanin kasashen Afirka. Tuni dai rikicin wanda ya shiga  kusan  wata na goma da farawa, ya haifar da gagarumin koma baya ta fuskar tattalin arziki, zamantakewa da kuma tsaro ga kasashe da dama na wanan yankin da ke yammacin nahiya Afirka.Akan haka ne, Umar Sani, ya tattauna daDakta Sani Alhaji Gambo, malami a jami'ar Andre Salifu da ke Zinder a Jamhuriya Nijar.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar tattaunawar

Bakonmu a Yau
Farfesa Usman Muhammad kan nakasu da jam'iyar ANC ta samu a zaben Afrika ta Kudu

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 4, 2024 3:24


A karon farko a cikin shekaru 30 da suka gabata, Jam'iyyar ANC mai mulkin kasar Afirka ta kudu ta gaza samun galabar da za ta kafa gwamnati ba tare da kawance ba a zaben da aka yi a kasar, abinda ke nuna yadda jama'a suka fara juya mata baya. Ganin irin tagomashin da jam'iyyar ta samu karkashin shugabanninta na farko irin su Nelson Mandela da Thabo Mbeki, ko me ya sa ta gamu da wannan koma baya?  Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Usman Muhammad na Cibiyar horar da 'yan majalisu dake Abuja.Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar zantawar ta su.......

Shirye-shiryen matasa | Deutsche Welle
Dandalin Matasa: Matasa da noman rani

Shirye-shiryen matasa | Deutsche Welle

Play Episode Listen Later Apr 25, 2024 9:44


Abaya-bayan nan matasa daga sassan kasashen nahiyar Afirka sun dukufa harkar noma shin ko mene ne dalili? Saurarin shirin don jin karin bayani

no man abaya manoma matasa afirka
Kasuwanci
Gidauniyar Dangote ta kashe naira biliyan 15 na tallafin abinci a Najeriya

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Mar 27, 2024 10:16


Shirin Kasuwa A Kai Miki Dole a wannan makon ya maida hankali ne kan rabon tallafin abincin naira biliyan 15, da Gidauniyar Aliko Dangote ta kaddamar a Najeriya. Wannan dai na daga cikin matakan rage radadin talauci a tsakanin al'ummar Najeriya, da gidauniyyar hamshakin attajirin Afirka ta kaddamar a birnin Kano da ke arewacin kasar. Ku latsa alamar sauti don jin cikakken shirin tare da Ahmed Abba.......

ku kano naira dangote wannan najeriya afirka ahmed abba
Tambaya da Amsa
Sanadin katsewar kafofin sadarwa na Internet a nahiyar Afirka

Tambaya da Amsa

Play Episode Listen Later Mar 23, 2024 20:00


shirin a wannnan mako zai ba da hankali ne akan abinda ya kai ga katsewar hanyoyin sadarwa na internet a wasu sassa na Nahiyar Afirka.

internet kamaru nijar najeriya afirka
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Yadda katsewar layukan sadarwa na karkashin teku ya shafi Afirka

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Mar 19, 2024 10:05


Yau kusan kwanaki 6 kenan da kasashe da dama na Afirka ke fama da matsalar Internet, a wani abu da masana ke cewa ya samo asali ne daga katsewar layukan sadarwa na karkashin teku. Duk da cewa ba a bayyana wa duniya lokacin da za a dauka kafin shawo kan wannan matsala ba, amma bisa ga dukan alamu tangardar za ta iya daukar dogon lokaci kafin a shawo kansa.Abin tambayar ita ce, ko yaya wannan matsala ta internet ke shafar harkokinku jama'a na yau da kullum?

Bakonmu a Yau
Alhaji Sirajo Jankado Sarkin Hausawa Turai kan batun bakin haure

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 14, 2024 3:35


Daya daga cikin matsalolin da suka addabi nahiyar Turai a wannan lokaci, shine batun bakin haure, ganin yadda matasa daga nahiyar Afirka ke tafiya mai hadari cikin kwale kwale da zummar zuwa nahiyar, abinda ke kai ga rasa rayuka da dama. Dangane da wannan matsala da kuma matakan da magabata ke dauka wajen fadakar da al'umma illar irin wannan tafiya, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Sarkin Hausawa Turai Alhaji Sirajo Jankado a fadarsa da ke kasar Faransa, kuma ga yadda zantawar su ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tasu......

ku daya turai afirka faransa hausawa bashir ibrahim idris
Shirye-shiryen matasa | Deutsche Welle
Dandalin Matasa: 08.02.2024

Shirye-shiryen matasa | Deutsche Welle

Play Episode Listen Later Feb 8, 2024 9:44


Matasa da yanayin halin matsin tattalin arziki a Afirka

matasa afirka
Afropop Worldwide
Planet Afropop - Syli D'Or Winners And Artists For Aid

Afropop Worldwide

Play Episode Listen Later Feb 6, 2024 52:15


Every winter, starting in February, the organizers of the annual Nuits D'Afrique festival put on a battle of the Afropop bands. Bands face off, three a night at Club Balatou, and the audience votes a winner for the night. Eventually, the field comes down to nine finalists, and that's when we at Afropop are asked to pick the winner of the Afropop prize from those nine acts. So as the festival is about to kick off again this year,we thought it would be great to honor the 2023 winners. The big winner of the entire contest was an awesome Afro-Latin band called Team Salsa Quintet. We'll also feature a visit with a group of young Algerian immigrants in Montreal - the band is called Afirka. And we'll wrap up with a report from correspondent Harrison Malkin on the recent Artist for Aid event in Newark, New Jersey. It was a star-studded evening aimed at raising awareness and funds for the victims of violence in Gaza and Sudan.

Wasanni
Yadda wasannin zagayen Kwata final suka kaya a gasar AFCON

Wasanni

Play Episode Listen Later Feb 5, 2024 10:00


Shirin 'Duniyar  Wasanni' na wannan lokacin yayi nazari ne akan wasannin matakin dab da na kusa da na karshe wato na zagayen Kwata final da aka yi a gasar AFCON.  Yanzu haka dai kasashe hudu ne suka rage a gasar ta cin kofin kasashen nahiyar Afirka da kasar Ivory Coast ke karbar bakunci, bayan wasannin da aka fafata a ranakun Juma'a da Asabar.

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Kan wasannin kasashen da suka rage a gasar AFCON

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Feb 5, 2024 9:05


Yayin da aka doshi zagayen dab da na karshe a gasar cin kofin nahiyar Afirka ta AFCON da ke gudanar a kasar Ivory Coast, ko wacce kasa ce za ta lashe wannan gasa? Kasashen Najeriya da Afirka ta Kudu, sai kuma Ivory Coast mai masaukin baki za ta fafata da jamhuriyar dimokaradiyyar Congo.Ko wadanne kasashe ne za su fafata a zagayen karshe?Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin, tare da Nasiru Sani.

Shirye-shiryen matasa | Deutsche Welle
Dandalin Matasa 02.02.2024

Shirye-shiryen matasa | Deutsche Welle

Play Episode Listen Later Feb 2, 2024 9:55


Shirin ya duba tasirin matakin raba da gari da ECOWAS da kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso suka dauka kan matasan yankin yammayin Afirka, musamman a fannin kasuwanci da ilimi da cudanyar kasa da kasa

Bakonmu a Yau
Zantawa da shugaban Radio France Internationale, Jean Mac-Four

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jan 31, 2024 3:43


Sabon Babban Daraktan RFI, Mr Jean-Marc Four yanzu haka yana ziyarar aiki a Najeriya dokin ganin yadda RFI Hausa ke gudanar da ayyukansa tare da ganawa da ma'aikatan sashen. Yayin ziyarar Mr Four ya bayyana gamsuwa da kwararrun ma'aikatan dake aiki da RFI Hausa tare da gabatar da sabon albishir a kan shirin da yake da shi ga sashen da kuma sauran sassan da ake amfani da karsunan Afirka. Ga yadda zantawarsu ta gudana da Bashir Ibrahim Idris.

ga internationale radio france yayin najeriya afirka shugaban bashir ibrahim idris
Wasanni
Najeria da Kamaru za su fafata a zagaye na 2 na gasar AFCON

Wasanni

Play Episode Listen Later Jan 26, 2024 9:57


Najeriya karkashin  mai horar da kungiyar Jose Peseiro za ta nemi kare maratabar ta da kuma neman ganin ta tsallaka mataki na gaba a wanan gangami,yayida a daya wajen ,Kamaru  a cewar mai horar da ita ,Rigobert Song za su kasance a kan bakar su na ganin su doke Najeriya. A tarihi,haduwar wadanan kungiyoyi Najeriya da Kamaru a shekaru baya suka kasance gagara badau a fagen tamola, Najeriya da Kamru sun hadu sau 22.,Najeriya ta samu nasara a wasanni 11 da ta buga da Kamaru. Yayin da Kamaru ta samu galaba a kan Najeriya sau  hudu Kungiyoyin biyu sun yi canjaras sau bakwai. A tarihin lashe kofin gasar Afirka na kwallon kafa baya ga Masar,da ta lashe Kofin sau 7,Kamaru ta daga wannan kofi sau 5 sai Ghana sau 4.   A bangaren Najeriya,kungiyar Super Eagles ta lashe kofin sau uku, shekarar 1980,1994 sai 2013..Khamis Saley a cikin wannan shiri na Duniyar wasanni,ya mayar da hankali a gasar.

ghana afcon super eagles kamaru masar yayin najeriya afirka jose peseiro duniyar
Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Dakta AbdulHakeem Garba Funtua kan ziyarar Blinken a Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jan 24, 2024 3:35


Sakataren harkokin wajen Amurka, Antony Blinken na ci gaba da ziyarar wasu kasashen Afirka da suka hada da Cape Verde da Cote d'Ivoire da Najeriya da kuma Angola. Da yammacin ranar Talata Blinken ya gana da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu dangane da bukatar hadin kan kasashen biyu.Dangane da wannan ziyarar da kuma tasirinta, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abdulhakeem Garba Funtua na Babbar kwalejin Fasaha ta Kaduna.

angola antony blinken cote cape verde kaduna garba najeriya afirka amurka bashir ibrahim idris
Mu Zagaya Duniya
Rikici tsakanin 'yan ta'adda a arewacin Najeriya ya illata bangaren Dogo Gide

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Jan 20, 2024 19:49


Shirin wannan makon zai fara ne da waiwayar bata-kashin da aka yi tsakanin ‘yan bindiga a Najeriya, lamarin da ya kai ga illata bangaren daya daga cikin jagoran ‘yan ta'adddan da ya addabi jama'a.Fira Ministan Jamhuriyar Nijar ya yi tatttaki zuwa Iran, bayan ganawarsa da mahukuntan kasar Rasha inda suka karfafa yarjejeniyar tsaron da suka kullla. A gabashin Afirka kuwa cibi ne ya zama kari, domin kuwa gwamnatin sojin Sudan ce ta katse alaka da kungiyar kasashen yankin gabashin nahiyar ta Afirka, saboda gayyatar shugaba kuma Janar Abdel Fattah al-Burhan da suka yi.

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Tattaunawa kan yadda gasar cin kofin kasashen Afirka ke gudana a Ivory Coast

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Jan 17, 2024 16:16


Shirin 'Ra'yoyin Masu Sauraro' na wannan rana ya ba da damar tattaunawa ne a kan gasar cin kofin kwallon kafa ta nahiyar Afirka da ke gudana a kasar Cote d'Ivoire, inda ‘yan kasashen nahiyar 24 ke fafatawa domin daukar kofin gasar na shekarar bana. 

Wasanni
Gasar cin kofin kasashen Afirka ta kankama a Ivory Coast

Wasanni

Play Episode Listen Later Jan 15, 2024 9:59


A ranar asabar da ta gabata ne aka fara gasar lashe kofin nahiyar Afrika wato AFCON da kasar Ivory Coast ke karbar bakunci. Wannan ne karo na 34 da ake gudanar da wannan gasa, kuma kasashe 24 zasu fafata a matakin rukuni.

Shirye-shiryen matasa | Deutsche Welle
Dandalin Matasa 11.01.2024

Shirye-shiryen matasa | Deutsche Welle

Play Episode Listen Later Jan 11, 2024 9:44


Yawan kasancewar matasan Afirka a kafofin sada zumunta na haifar da kiyayya da rashin fahimta da cin zarafi tare da tunzurawa ga tashin hankali a wasu lokutan. Amma ta ya ya za a magance wadannan halayen da ke addabar dandamalin digital da biliyoyin mutane ke amfani da su yau da kullum?

amma matasa afirka
Shirye-shiryen matasa | Deutsche Welle
Dandalin Matasa 28.12.2023

Shirye-shiryen matasa | Deutsche Welle

Play Episode Listen Later Dec 28, 2023 9:46


Shiri ne da ya kunshi kokarin tashar DW na fadakar da jama'a kan matsalolin sauyin yanayi a kasashen Afirka musamman yadda suke haddasa rikici a tsakanin manoma da makiyaya musamman a arewacin Najeriya.

dw shiri najeriya matasa afirka dw akademie
Bakonmu a Yau
Fati Hassan kan yadda kasashe masu tasowa za su tunkari matsalar sauyin yanayi

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 1, 2023 3:26


Kungiyar agaji ta OXFAM ta bayyana farin cikin ta da nasarar da aka samu wajen kafa asusun da manyan kasashen duniya zasu zuba kudade, domin tallafawa kasashe masu tasowa dake fuskantar matsalar sauyin yanayi.  Wannan mataki ya biyo vayan amincewar da wakilan kasashe sama da 175 suka cimma a wajen taron sauyin yanayin Majalisar dinkin duniyar dake gudana a Dubai. Bashir Ibrahim Idris ya tatatuna da Daraktar kungiyar dake kula da nahiyar Afirka, Fati Nzi Hassan.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

dubai oxfam fati yadda shiga masu wannan afirka majalisar dinkin duniya majalisar bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Dr. Abdurrahman kan matakin sojin Nijar na soke yarjejeniyar bakin haure

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 29, 2023 3:42


Kungiyar Turai ta bayyana matukar damuwarta da matakin da gwamnatin sojin Nijar ta dauka na soke yarjejeniyar hana baki bi ta cikin kasarta suna tsallakawa Turan, matakin da ake ganin zai bude kofa ga daruruwan bakin da ke neman barin Afirka daga yankin kudu da sahara.  Ita wannan yarjejeniyar da tsohuwar gwamnatin Nijar ta kulla da kungiyar EU na dauke da makudan kudade. Kwamishiniyar Cikin Gida Ylva Johannsson ta ce tana fargabar hadarin da ke tattare da irin wannan tafiyar, wanda ke kai ga rasa dimbin rayuka. Dangane da wannan dambarwa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Dicko Abdurrahman na Jami'ar Zinder.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu.

Madubin Kabara
NA'IMA IDRIS: Ta shiga sahun manyan gobe a Afirka

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Aug 1, 2022 14:53


Na'ima Idris Usman, cikakkiyar Likita ce da ke jihar Kanon Najeriya, ta yi karatun a tsakanin Najeriys da China. Ta bamu labarin rayuwarta daga kuruciya zuwa girmanta, da ma yadda aka yi ta fara ilimantar da mata ta kafafen sada zumunta game da lafiyar jikinsu duk da cewa furta kalmomin da ke da alaka da al'aura abu ne mai cike da kalubalen a kasar Hausa. Da kuma yadda karshe ta buge da zuwa shirin horar da shugabanci ga matasan Afirka a Amurka da a turance ake kira da Mandela Washington Fellowship da aka fi sani da Young African Leaders Initiative (YALI) na shekarar 2022. --- This episode is sponsored by · Anchor: The easiest way to make a podcast. https://anchor.fm/app --- Send in a voice message: https://anchor.fm/usmankabarahausa/message Support this podcast: https://anchor.fm/usmankabarahausa/support

china hausa gobe shiga mandela washington fellowship afirka amurka young african leaders initiative yali
Madubin Kabara
I SHARIF: Dan Najeriya matukin jirgi a Afirka ta Kudu

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Mar 5, 2022 36:47


Kaftin Ibrahim Sharif bakano ne dan Najeriya da ya bar gida tun yana dan saurayi zuwa Birtaniya domin aikin sa kai. Inda daga baya ya nausa Afirka ta Kudu inda ya cika burinsa na zama matukin jirgin sama, har ma ya buge da tsere keke a can. --- Send in a voice message: https://anchor.fm/usmankabarashowhausa/message Support this podcast: https://anchor.fm/usmankabarashowhausa/support

sharif inda kudu najeriya afirka birtaniya