POPULARITY
Yanzu haka ƙasashe masu tasowa na ci gaba da ƙoƙarin cike giɓin da aka samu bayan da Donald Trump ya janyewa tallafin da Amurka ke bai wa Hukumar Lafiya don yaƙi da wasu curutuka a duniya. A jawabinsa gaban Taron Hukumar Lafiya WHO da ke a birnin Geneva, shugaban Ghana John Dramani Mahama ya ce ya kamata Afirka ta samar da tsarin kula da lafiyar al'ummarta a maimakon barin lamarin a hannun hukumar WHO. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
A zantawarsa da Radio France Internationale, da France 24 da kuma TV5 Monde a ƙarshen taron Afrika da Faransa da aka kammala birnin Nairobi na ƙasar Kenya, Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana matsayinsa a game da taɓarɓarewar sha'anin tsaro a Mali da kuma alaƙar Faransa da sauran ƙasashen Afirka ta fannin tsaro da aikin soji. To amma da farko shugaban ya fara amsa wata tambaya ce dangane da dalilan da suka sa Faransa ke ci gaba da taka rawa a wajen tafiyar da takardar kuɗin CFA. Ga dai tattaunawar. Latsa alamar sauti domin sauraren zanatawar.
A taron Afirka da Faransa da aka kammala jiya talata a ƙasar Kenya, Faransa ta sanar da shirin saka jarin Euro bilyan 23 don ƙarfafa kasuwanci tsakanin ɓangarorin biyu. Shugaba Emmanuel Macron ne ya sanar da haka, yana mai cewa daga yanzu ɓangarorin biyu za su gudanar da mu'amala ce irin ta ba ni gishiri in ba ka manda a maimakon bai Afirka tallafi kamar yadda ake yi a baya. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
A ranar Talata ne ake kammala taron shugabannin ƙasashen Afirka da Faransa da ya gudana a birnin Nairobi ta ƙasar Kenya, wanda ya mayar da hankali kan hanyoyin ci gaban tattalin arziki da noma da samar da abinci ga jama'ar nahiyar. Yaƙin Iran na ɗaya daga cikin abubuwan da ake ganin na maida hannun agogo baya wajen magance ƙarancin abinci, musamman rufe mahsigin Hormuz da ake amfani da ita wajen safarar takin zamani. Kan haka ne Nura Ado Suleiman ya zanta da ministan noman Najeriya Sanata Abubakar Kyari a wurin wannan taro, inda kuma ya ce su na ƙoƙarin magance matsalar. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Wannan shirin ya dubi yadda wakokin bege na addinin Islama ke kara samun karbuwa tsakanin matasa a kasashen nahiyar Afirka, duk kuwa da yawan sabanin fahimta da ake da su.
A jiya ne ake faro taron kwanaki biyu tsakanin Faransa da ƙasashen Afrika a birnin Nairobi, wanda shugaba Emmanuel Macron da takwaransa William Ruto ke jagoranta. Taron ya haɗa shugabannin ƙasashen Afrika, da Hamshaƙan ƴan Kasuwa, da sauran masu ruwa da tsaki domin tattaunawa kan nemawa nahiyar Afrika mafita wajen samun ci gaban Tattalin Arziƙi a fannonin da suka haɗa da, bunƙasa Masana'antu da Kimiyya da Fasaha da inganta Noma da Tsarin Kiwon Lafiya, da kuma samun wadatar makamashi. Danna alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar Nura Ado Suleiman da hadimin shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu Daniel Bwala.......
Wasu daga cikin Ƴan Majalisun Dattawan Najeriya sun buƙaci ɗaukar matakai maus tsauri a kan Afirka ta Kudu, ciki harda kwace lasisin kamfanonin su na MTN da DSTV saboda yadda ake kai wa ƴan ƙasar hari ake kuma kashe su. Majalisar ta yanke hukuncin tura tawaga Afirka ta Kudu domin tattaunawa da hukumomin ƙasar, yayin da shi ma bangaren gwamnati ya tura ministan harkokin waje. Ambasada Ibrahim Kazaure, tsohon Jakadan Najeriya a Saudi Arabia ya yi tsokaci a kai, a tattaunawar su da Bashir Ibrahim Idris.
Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa za ta fara kwashe ƴan ƙasarta da ke son komawa gida daga Afirka ta Kudu, matakin da ta ce ya zama dole saboda tsananin kyamar baƙi da kuma rahoton mutuwar wasu ƴan Najeriya biyu sakamakon hare-haren da ake kai wa ƴan cirani. Akalla 'yan Najeriya 130 ne suka riga suka yi rajista don neman a kwashe su zuwa gida, sakamakon fargabar makomarsu na rashin tabbas. Dakta Rakiya Sa'idu daga jami'ar Capetown, ta bayyana mana yadda ƴan siyasa ke amfani da lokacin zaɓe wajen rura wutar wannan matsala. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawar da Shamsiyya Haruna ta yi da ita............
Shirin Lafiya Jari ce a wannan makon tare da Azima Bashir Aminu ya yi duba ne kan cutar ɗan sanƙarau ko kuma meningitis, cutar da a yanzu haka wasu ƙasashe ke cikin haɗarin fuskantar ɓullarta musamman a yammacin Afrika, waɗanda dama ke a tubalin fuskantar wannan cuta lokaci zuwa lokaci.
Shirin a wannan lokaci tare da Khamis Saleh ya yi duba ne kan yadda aka kammala samun tawagogin ƙasashen da za su fafata a gasar lashe kofin duniya da ke tafe a watan Yuni mai zuwa. Danna alamar sauti don sauraron cikakken shirin......
Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana fataucin bayi da aka share ɗaruruwan shekaru ana yi daga Afirka zuwa Turai da Amurka a matsayin ‘'cin zarafin bil Adama mafi girma'' da aka taɓa gani a tarihi. Ƙasashen duniya 123 ne suka kaɗa ƙuri'ar goyon bayan wannan ƙuduri, wasu uku wato Amurka, Isra'ila da Argentina suka ƙi amincewa yayin da wasu ƙasashe 52 suka yi ƙememe ta hanyar rowar ƙuri'unsu. To domin tuni a game da lokacin da aka fara ɗibar bayi daga Afirka da kuma yadda hakan ya shafi ci gaban nahiryar, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tarihi Dr Maman Kassou, malami a jami'ar Andre Salifou da ke Damagaram, ga kuma zantarwarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Shirin ya duba kabilar Dogon na kasar Mali da ta yi fice a yankin yammacin Afirka musamman a Kudu maso gabashin kasar Mali.
A yayin da yaƙi tsakanin Isra'ila da Amurka da Iran ke daɗa rincaɓewa, an fara gani tasirinsa a kasuwar ɗanyen mai da makamashi ta duniya. Ko a Najeriya, ƙasar da ta fi arziƙin ɗanyen mai a Afirka, farashin litar fetur ya tashi, kuma masana sun ce ana iya ganin cigaba da tashin farashin makamashi. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.
Dauri rayuwa ta zamantakewar al'ummar Hausa Fulani da ma wasu kabilun ta kasance cike da alkunya da kuima kamun kai ta yadda matar aure ke kauracewa fadar sunan danta ko mujinta.
A Najeriya, Matatar Man Dangote mafi girma a Afirka ta cimma matsaya da wasu manyan kamfanonin dallancin Mai guda 12 domin rarraba man fetir kimanin lita miliyan 60 zuwa 65 a kowace rana. Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya bayyana haka cikin wata sanarwar, da ya ce gagarumin mataki ne na wadata kasar da mai da kuma dogaro da kai a bangaren makashi. Domin sanin tasirin matakin, Ahmad Abba ya tattauna da Dr. Kasum Garba Kurfi, masanin tattalin arziki a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
Shirin ya yi nazari kan suna a tsakanin kabilu da kuma radin suna ko kuma zanen suna a kasashe daban-daban na Afirka.
Suna dai linzami ne, kuma 'dan adam ya fara amfani da suna tun fil azal domin fayyace asali ko al'ada ko kuma jinsin da mutum ya fito.
Amurka ta sanar da tura wata tawagar sojinta zuwa Najeriya, abinda a karon farko ke tabbatar da isar dakarun nata ƙasar, tun bayan ƙarfafa yarjejeniyar tsaron da ƙasashen biyu suka yi, biyo bayan zargin da shugaba Donald Trump ya yi a shekarar bara, cewa ana kashe Kiristoci a Najeriyar. Kwamandan rundunar sojin Amurka da ke kula da Afirka, Janar Dagvin R.M. Anderson ya ce sun tura dakarun ne a bisa amincewar Najeriya. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Yahuza Ahmed Getso masanin tsaro a Najeriya. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.......
Shirin tambaya da amsa na wannan mako zai fara ne da bayani akan abinda ke haifar da sukar ciki ko kuma naɗewar hanji a cikin mutum. Sai kuma tambayar da ke neman ƙarin bayani a kan yaushe aka fara taron duba lamuran tattalin arziki na Duniya da ake kira Davos world economic forum kuma wane tasiri yake da shi ga duniya da kuma yankin mu na Afirka. Sai kuma tambayarmu ta gaba wadda ke buƙatar ƙarin haske kan irin gudunmawar da ake la'akari da su kafin a ba wa mutum kyautar lambar yabon zaman lafiya ta duniya wato Nobel peace price, kamar yadda aka baiwa ƴar ƙasar Venezuela Maria Corina Machado. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin
Amurka ta sanar wa bai wa Najeriya wasu muhimman kayan aikin soji domin tunkarar ƙalubale na tsaro da ƙasar ke fama da shi. Rundunar Amurka mai kula da nahiyar Afirka wato Africom ce ta sanar da hakan, sama da makonni biyu da Amurka ta ƙaddamar da farmakin farko kan wasu wurare ta bayyana cewa maɓoyar yan ta'addace. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Hedikwatar rundunar sojin Amurka mai kula da nahiyar Afirka, AFRICOM, ta sanar da miƙa wa gwamnatin Najeriya taimakon kayayyakin aikin soji, matakin da ke ƙarfafa yarjejeniyar tsaron da ke tsakaninsu don yaƙi da ta'addanci. Sai dai cikin sanarwar da ta wallafa a shafinta na X, rundunar sojin Amurkan ba ta yi ƙarin bayani kan nau'ika da kuma adadin makaman ba. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Kabiru Adamu shugaban kamfanin Beacon Consulting da ke bincike kan tsaro a nahiyar Afrika.
Shirin muhallinka rayuwarka na wannan makon ya tattauna ne kan yadda sauyin yanayi ko dai na zafi ko na sanyi ko kuma damina ke bayyana ƙarara, musamman a yankin yammacin Afirka. Ga misali a Najeriya, ɗaya daga cikin sauye-sauyen yanayin da aka shaida shi ne rashin hunturu a shekarar bana, musamman a Yankin arewacin ƙasar, inda aka saba ganin kankamar Yanayin na sanyin mai tsanani daga ƙarshen watan Nuwamba ko farkon Disamba zuwa ƙarshen watan Janairu ko farkon Fabarairu. Gabanin fuskantar wannan lamari dai hatta yanayin damina da lokacin zuwanta ya sauya daga abinda aka saba da shi, batun da hatta a wasu wuraren da ke yankin Kudu maso yammacin Najeriya ma an shaida hakan. Tuni dai wannan al'amari na sauyin lokutan yanayin zafi da damina ko kuma sanyi ya zama abin tattaunawa a tsakanin jama'a dangane da dalilan da suka janyo hakan, da dai wasu sauran tambayoyi da ake da ƙishirwar neman amsoshinsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare Nura Ado Suleiman............
A gasar neman kofin Afirka da ke gudana a Morocco, a yanzu dai an tantance ƙasashe 8 da za su fafata da juna a matakin da ake kira Quarter Finals, inda Mali-Sénégal, Masar ta haɗu da Côte d'Ivoire, Kamaru ita da Morocco sai kuma Nigeria da za ta kece reni da Algéria. Waɗannan ƙasashe 8, tun farko su ne ake hasashen cewa za su iya taka gagarumar rawa a gasar. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Ibrahim Sherif bakano ne dan Najeriya da ya bar gida tun yana dan saurayi zuwa Birtaniya domin aikin sa kai. Inda daga baya ya nausa Afirka ta Kudu inda ya cika burinsa na zama matukin jirgin sama, har ma ya buge da tsere keke a can.
Adamu Garba II matashi ne mai kwarin gwiwa sannan wanda ya ke dan kasuwar da yayi iliminsa a tsakanin Najeriya har zuwa Amurka. Yana daga cikin 'yan takarar Shugaban Kasar Najeriya a shekarar 2023 mafi karancin shekaru a tsakanin masu neman wannan kujera a kasar da ta fi kowa ce kasar Afirka yawan al'umma da kuma karfin arzikin man fetur. Shine kuma wanda 'yan uwa da abokan arziki suka tara wa sama da naira miliyan 80 don yin takara a jam'iyyar APC amma kwatsam sai ya canja sheka zuwa YPP.
Na'ima Idris Usman, cikakkiyar Likita ce da ke jihar Kanon Najeriya, ta yi karatun a tsakanin Najeriys da China. Ta bamu labarin rayuwarta daga kuruciya zuwa girmanta, da ma yadda aka yi ta fara ilimantar da mata ta kafafen sada zumunta game da lafiyar jikinsu duk da cewa furta kalmomin da ke da alaka da al'aura abu ne mai cike da kalubalen a kasar Hausa. Da kuma yadda karshe ta buge da zuwa shirin horar da shugabanci ga matasan Afirka a Amurka da a turance ake kira da Mandela Washington Fellowship da aka fi sani da Young African Leaders Initiative (YALI) na shekarar 2022.
Shirin Duniyar Wasanni a wannan lokaci tare da Khamis Saleh ya yi duba ne kan tarihin gasar lashe kofin Afrika AFCON da hukumar CAF ke shiryawa. An faro buga gasar lashe kofin nahiyar Afirka, wacce ke zaman gasar kwallon ƙafa mafi girma da daraja a nahiyar a shekarar 1957, da hukumar kula da kwallon ƙafar Afrika CAF ce ta jagoranci. An fara gudanar da gasar ne a watan Fabrairun shekarar 1957 a birnin Khartoum na ƙasar Sudan da ƙasashe 3, kafin a shekarar 2019 aka faɗaɗata zuwa tawogogun ƙasashe 24, kuma Masar ce ta fara lasheta bayan lallasa Sudan da ta karbi baƙunci a wasan karshe, inda ta lashe kofin da aka sanya masa sunan Abdel Aziz Abdallah Salem, ɗan ƙasar Masar da ya fara shugabantar hukumar CAF. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin 'Kasuwa A kai Miki Dole' na wannan mako tare da Ahmed Abba ya mayar da hankali ne kan gina katafaren kamfanin tono da kuma sarrafa ƙarafu da duwatsu masu daraja da wani matashi ya ƙaddamar a jihar Nasarawa da ke arewacin Najeriya, irinsa mafi girma a Afirka, wanda zai laƙume dalar Amurka miliyan 400.
Ƴan Najeriya na ci gaba da neman bayani a kan yadda wasu kuɗaɗen da aka tara, da yawan su ya kai dala miliyan 30 domin samar da tsaro a makarantu suka shiga, sakamakon sake dawowar satar ɗalibai a yankin arewacin ƙasar. A ƙarƙashin wannan shirin da ya fara a shekarar 2014, kasashe da dama suka tallafawa Najeriya, cikin su har da ƙasar Norway da ta bada dala miliyan guda, da wata dala miliyan guda daga Bankin Raya ƙasashen Afirka na AfDB, sai kuma Fam miliyan guda daga gwamnatin Birtaniya. Gwamnatin Switzerland ta bada taimakon dala miliyan takwas, yayin da Amurka ta bada dala miliyan biyu, sai kuma Qatar da ta bada dala miliyan biyu, yayin da ƴan kasuwan Najeriya su kuma suka bada taimakon dala miliyan 10. Ganin yadda aka kasa samar da tsaron a makarantu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Abubakar sadiq Umar Gombe. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
A jiya ne sojoji suka hambarar da gwamnatin shugaba Umaro Sissiko Embalo, sakamakon rikicin zaɓen shugaban ƙasar da aka yi a ƙarshen mako, a daidai lokacin da ake shirin gabatar da sakamako yau Alhamis. Shugaban da madugun yan adawa duk sun yi iƙrarin nasara, a kasar da ta yi ƙaurin suna wajen juyin mulki. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Tukur Abdulkadir dangane da juyin mulkin, wanda shi ne na biyar a kasashen Afirka ta Yamma, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.
Shirin "Duniyar Wasanni" tare da Khamis Saleh a wannan lokaci zayyi duba ne kan ƙyautar gwarzon ɗan wasan ƙwallon ƙafan Afirka da Achraf Hakimi na Morocco ya lashe. A makon daya gabata ne Hukumar Kwallon Ƙafar Afrika CAF, ta bayar da kyautuka ga zaratan ƴan wasan nahiyar da suka nuna bajinta a wannan shekarar da muke bankwana da ita. A yayin bikin da ya gudana a birnin Rabat na ƙasar Morocco, hukumar ta CAF ta sanar da ɗan wasan baya na tawagar ƙasar ta Morocco wanda kuma ya ke yi wa ƙungiyar PSG wasa Achraf Hakimi, a matsayin wanda ya lashe ƙyautar gwarzon ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Afirka a wannan shekarar. Hakimi ya samu nasarar ce bayan doke shahararrun ƴan wasan nahiyar da suka taɓa lashe kyautar irinsu Mohamed Salah na Masar da ke taka leda a Liverpool, da kuma Victor Osimhen na Nigeria da ke wasa a Galatasaray. Wannan ne dai karo na farko da ɗan wasan ya taɓa lashe ƙyautar, bayan da a karo biyu a jere ya na ƙarewa a mataki na biyu, a shekarar 2023 da Victor Osimhen ya lashe da kuma 2024 da Ademola Lookman ya lashe. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin...
Dr. Murtala likitan yara ne dan asalin jihar Adamawar Najeriya da ya rikide ya zama kwararren masanin lafiyar al'umma musamman mata da yara, wanda a yanzu haka ma'aikaci ne a wata kungiya mai zaman kanta da ta ke tallafawa harkokin lafiyar iyali a duniya ciki har da kasashen Afirka mai suna Pathfinder International da ke kasar Amurka.Murtala Mai | Madubin Usman Kabara #11
A shekarar 1984 a Najeriya an sami wani saurayi dan jihar Kano da ya fi kowane dalibi a Najeriya cin makin jarrabawar gama sakandaren kasashen Afirka ta WAEC a takaice. Yanzu haka dai wannan dalibin mai suna Farfesa Sarki Abba Abdulkadir farfesa ne a bangaren haddasuwar cututtuka a Jami'ar Northwestern University da ke Chicago a Amurka.
A jiya ne aka gudanar da bikin ranar malamai ta duniya cikin yanayin ƙuncin rayuwa da ƙarancin albashi, musamman a wasu ƙasashen Afirka da malaman ke ɗanɗana kuɗarsu. An ware wannan rana ne, domin nuna goyon baya ga irin gudunmawar da suke bayarwa ga ci gaban rayuwar al'umma a fannoni da dama. Wanne hali malamai ke ciki a yankunanku? Shin kun gamsu da irin gudunmawar da suke bayarwa a yankunanku. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Ku latsa alamar sauti domin sauraren shirin...
A karon farko gwamnatin Najeriya ta hannun hukumarta da ke kula da sufurin jiragen ruwa a koguna ko kuma cikin gida, ta shelanta haramta jigilar duk wani jirgi ko kwale-kwale da ba a yi wa rijista da gwamnati ba, Ghana ta karɓi baƙi ‘yan Afirka ta yamma, waɗanda gwamnatin Amurka ta taso ƙeyarsu a ƙarƙashin shirin shugaba Donald Trump na korar baƙin-haure, wasu kenan daga cikin manyan labarun makon jiya da Nura Ado Suleiman zai kawo muku a cikin shirin Mu zagaya Duniya.. Latsa alamar sauti don sauraron shirin..........
Hafsoshin tsaro na ƙasashen Afirka a taron da suka yi a birinin Abujan Najeriya, sun ƙuduri aniyar haɗa gwiwa don tunkarar ƙalubalen tsaro da nahiyar ke fuskanta. Wannan taro dai ya samu halartar wakilan ƙasashe sama da 50, waɗanda suka yi imani da cewa la'akari da girman matsalar, akwai buƙatar ƙasashen su yi aiki a tare don tunkarar ta. Shin ko meye ra'ayoyinku a game da wannan yunƙuri na ƙasashen Afirka? Waɗannan shawarwari za ku bayar domin samun nasarar wannan fata? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin....
Shan shayi al'ada ce mai tushe da ta yadu a tsakanin al'umomi mabanbanta a fadin duniya.
Shirin ya mayar da hankali ne kan yadda matakin Amurka na janye tallafin da take ba wa ɓangaren kula da masu fama da cuta mai karya garkuwa jiki ta HIV da ake fargabar zai iya haifar da koma baya ga shirin yaƙi da cutar. Tuni hukumomi a duniya suka fara tofa albarkacin bakinsu kan wannan mataki da shugaban Amurka, Donald Trump ya ɗauka, wanda ake ganin zai fi yin tasiri ne ga nahiyar Afirka. Tuni mujallar Lancet ta Biritaniya ta yi hasashen cewa matakin na Donald Trump na iya haifar da mutuwar mutane sama da miliyan 14 nan da shekarar 2030, ciki har da yara sama da miliyan 4.5 'yan kasa da shekaru biyar. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Azima Bashi Aminu.
Shirin Duniyar Wasanni a wannan makon tareda Khamis Saley yayi duba ne kan wasan ƙarshe na gasar lashe kofin mata ta Afrika WAFCON da aka yi a ƙarshen mako. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin......
Ko kun san tarin kalubalen da kwararrun ma'aikata ke sha kafin su samu takardar izinin shiga Jamus wato Visa, duk da cewa kasar na matukar bukatarsu? Shirin Taba Ka Lashe na wannan lokaci ya yi nazari a kai.
Shirin 'Lafiya Jari Ce na wannan mako tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan hasashen da wata ƙungiya ta yi cewar nan da shekarar 2025 raɓin al'ummar Afirka masamman matasa za su fuskanci cutar ƙibar da ta wuce ƙima ko Obesity a turance.
Kungiyar kasashen Afirka ta Yamma ta ECOWAS ta bayyana shirin kafa sabuwar rundunar hadin kai wadda za ta dinga yaki da yan ta'addan da suka addabi yankin. Wannan na da cikin shirin shugabannin yankin na dakile ayyukan ta'addanci, da suka ƙi ci suka ƙi cinyewa.Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Janar Kape Alwali Kazir mai ritaya a dangane da wannan shiri.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
A yau 21 ga watan Mayun 2025, shekaru 18 kenan da Radio France International ya fara yaɗa shirye-shiryensa a cikin harshen Hausa, wanda kuma shi ne harshen na farko daga Afirka da RFI ta fara yaɗa shirye-shiryenta da shi. Malam Bashir Ibrahim Idris, shi ne Babban Editan RFI Hausa, ya yi muna ƙarin bayani a game da yadda rediyon ya fara da kuma irin ci gaba da ya samu a waɗannan shekaru. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawar da Ƙaribullah Abdulmajid Namadobi ya yi da shi...........
A yau shirin tamabaya da amsa, tare da Nasiru Sani, zai kawo muku bayanai ne akan tasirin tsarin harajin da shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaƙabawa ƙasashen Canada da Mexico da kuma China akan ƙasashe Afirka. Shirin ya kuma zanta da kwararru a fannin lafiya, kan dalilan da ke sanya shan ruwa a kai.Akwai kuma cikakken bayani kan Sultan Makenga, wato jagoran ƙungiyar 'yan tawayen M23 wanda ya hana zaman lafiya a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo, musamman ma a gabashin ƙasar.Shiga alamar sauti, domin saurarin cikakken shirin.
Kamar dai kowace shekara, yau 1 ga watan Mayu, ita ce Ranar Ma'aikata ta Duniya, bikin da a bana ana iya cewa ana gudanar da shi ne a cikin wani yanayi na tsadar rayuwa a mafi yawan ƙasashen duniya. Abin tambayar shine, shin ko a cikin wanne yanayi ake gudanar da bukukuwan na bana, musamman a kasashen Afirka?Waɗanne irin manyan buƙatu ma'akata suke son cimma wa?Shiga alamar sauti, diomin sauraron ciakken shirin.
Shirin al'adunmu na gado tare da Oumarou Sani a wannan mako ya mayar da hankali ne kan al'adun ƙabilar Dagomba a ƙasar Ghana, ƙabilar da ke ci gaba da mamaya a wannan ƙasa ta yammacin Afirka suk da kasancewarta wadda a baya tafi ƙarfi a yankin arewacin ƙasar. Yanayin suturun wannan ƙabila na daga cikin abin da ke jan hankalin jama'a, musamman yanayin hularsu wadda ke da nufin ko kuma ma'anar zaman lafiya.Suturun wannan ƙabila dai akan saƙa su da hannu ne.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Yau shirin ya yada zango ne ƙasar Ghana, inda ya mayar da hankali kan matakin gwamnatin ƙasar na bai wa ƴan ƙasashen waje wa'adin ficewa daga kasuwancin zinare.Ƙasar Ghana ta bai wa ƴan ƙasashen waje da su fice daga harkokinta na kasuwancin zinare a ƙarshen wannan wata na Afirilu a wani mataki na bunƙasa kananan masu hakar zinare na cikin gida da kuma samun ƙudin shiga. Ƙasar ta yammacin Afirka dake kan gaba a samar da zinare a nahiyar na ƙokarin tsaftace harkokin harƙar zinare ta hanyar daidaita cinikin zinari daga kananan masu hakar ma'adinai.
Shirin 'Kasuwa A kai Miki Dole' na wannan makon ya mayar da hankali kan tasirin matakin shugaban Amurka Donald Trump kan shirin sa na sanya gagarumin ƙarin haraji ga kusan ɗaukacin ƙasashen duniya, wanda ya jawo durƙushewar kasuwannin hannayen jari ta duniya da lalata alaƙa tsakanin ƙasar da ƙawayenta, duk da cewa ya yi amai ya lashe wajen dakatar da harajin da watanni uku masu zuwa. Shirin ya duba tasirinsa ga ƙasashen Afirka masamman Najeriya.
A Laraba 9 ga watan Afrilu, sabon harajin da ya kama daga kashi 10 zuwa sama, da shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaƙaba wa ƙasashen Afirka zai fara aiki, bayan da harajin da ya shafi sauran ƙasashe ya soma aiki a ranar 5 ga watan na Afrilu. Tun cikin makon jiya ne dai matakin na Trump ya soma tasiri a kasuwannin Turai da Asiya, a yayin da ƙasashen Afirka suka shiga zulumi dangane da makomarsu.Don jin tasirin da sabon harajin na Amurka zai yi a kan tattalin Arzikin arziƙin ƙasashen Afirka, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dr Ƙasim Garba Kurfi.A latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar zanatawar.
Every winter, starting in February, the organizers of the annual Nuits D'Afrique festival put on a battle of the Afropop bands. Bands face off, three a night at Club Balatou, and the audience votes a winner for the night. Eventually, the field comes down to nine finalists, and that's when we at Afropop are asked to pick the winner of the Afropop prize from those nine acts. So as the festival is about to kick off again this year,we thought it would be great to honor the 2023 winners. The big winner of the entire contest was an awesome Afro-Latin band called Team Salsa Quintet. We'll also feature a visit with a group of young Algerian immigrants in Montreal - the band is called Afirka. And we'll wrap up with a report from correspondent Harrison Malkin on the recent Artist for Aid event in Newark, New Jersey. It was a star-studded evening aimed at raising awareness and funds for the victims of violence in Gaza and Sudan.