POPULARITY
Yayin da ake shirin gudanar da zaɓuka cikin watan Fabarairun shekaru mai zuwa a Najeriya, wani abu da ke faruwa shi ne taƙaddamar ƴan siyasa a gaban kotunan ƙasar. Kusan a kowane mako, za a ji cewa kotu ta yanke hukunci kan jam'iyyun siyasa, lamarin da ke iya nisantar da su daga tsayawa takara a waɗannan zaɓuka. Wannan ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
A Najeriya, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta ƙaddamar da bincike akan zargin fitar bayan sirri daga rumbun ajiyar bayananta na masu zaɓe, wanda ya jamnyo cece-kuce a ƴan kwanakin nan. Wannan ya biyo bayan wallafa bayan wani ɗan takara ne da ake zargin wani ma'aikacin INEC ya yi a dandalin sada zumunta a yayin zaɓwen fidda gwani na wata jam'iyyar siyasa a babban birnin tarayyar Najeriya Abuja. Akan haka Michael Kuduson ya tattauna da Dakta Umar Yakubu, shugaban wata ƙungiyar farar hula a Abuja babban birnin Najeriya.
A yau take Sallah Babba! Ranar da ɗaukacin Musulmi a faɗin duniya ke murnar zagayowar Sallar layya. Wannan biki na zuwa ne a daidai lokacin da lamura suka yi tsauri, musamman ta ɓangaren tattalin arziƙi. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.
Shirin Muhallinka Rayuwarka na wannan makon ya tattauna na a kan yadda samun saukar Ruwan Sama na farko a bana ya jefa manoma a jihohin Arewacin Najeriya cikin ruɗani dangane da lokacin da ya dace su fara shuka. Wannan na zuwa ne a yayin da hukumar hasashen Yanayi ta Najeriya wato NIMET, da uma wasu masana ke gargaɗi game da yiwuwar ɗaukewar ruwan saman da wuri, lamarin da zai yi janyo tafka hasarar akasarin amfanin gonar da aka shugka da wuri.
Shirin 'Mu Zagaya Duniya' yana bita ne na mahimman labaran al'amura da suka wakana a makon da ya gabata. a wannan makon shirin ya soma ne daga Najeriya inda a farkon makon da ya wuce wani harin da dakarun Najeriya suka kai ta sama a kasuwar Tumfa ta karamar hukumar Zurmi ta jihar Zamafara ya hallaka akalla mutum dari 100 tare da jikkata wasu da dama. Wannan harin da ke zaman mafi muni da dakarun kasar su kai kan fararen hula shi ne na uku a cikin kasa da wata guda .
Gwamnatin Nijar ta fitar da wani daftari da ke ƙara adadin jihohi zuwa 19 ta hanyar ƙirƙiro sabbin 11 a maimakon 8 da ake da su a kasar yau kusan shekaru 30 kenan. Gwamnatin ta ce za ta ƙirƙiri sabbin jihohi da kuma gundumomi ne domin samar da ci gaba da ta hanyar ƙara matso da jama'a zuwa kusa da hukuma. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Wannan shirin ya dubi yadda wakokin bege na addinin Islama ke kara samun karbuwa tsakanin matasa a kasashen nahiyar Afirka, duk kuwa da yawan sabanin fahimta da ake da su.
A ranar juma'ar data gabata ne dai aka kammala gasar gasar Super 4, wacce aka fafata tsakacin ƙungiyoyi 4 da suka haɗa da Sporting Lagos da Inter Lagos da Ranchers Bees ta Kaduna sai kuma Doma United, da suka zama zagaru a rukunoninsu na gasar NNL, gasa ta biyu mafi daraja a Najeriya. An gudanar da gasar ne a yanayin yadda ake gudanar da gasar lik-lik, inda kowa ya kara da kowa ganin cewa kowaccensu za ta haska a gasar Firimiyar Najeriya a kakar baɗi. A wasannin ƙarshe da aka aka yi, Sporting Lagos ta sha kashi da ci ɗaya mai banshi a hannun Inter Lagos, amma sai dai hakan bai hanata lashi gasar ba da ban-bancin ƙwallaye, domin kowaccensu ta ƙare ne da maki 6. Wannan ne karo na farko da Sporting Lagos ta taɓa lashe kofin tun bayan samar da ita a shekarar 2022.
Kamfanin mai na NNPC ya sanya hannu kan wata yarjejeniya da wasu kamfanonin ƙasar China guda biyu, Sanjiang Chemical Company Limited da kuma Fuzhou Industrial Park, domin farfaɗo da matatun mai na Warri da Port Harcourt. Wannan mataki ya zo ne bayan matatun man sun laƙume kimanin biliyan 3.2 na dala ba tare da an samu biyan buƙata ba. Injiniya Kailani Muhammad, tsohon babban jami'in kamfanin na NNPC ne, a tattaunawarsa da Shamsiyya Haruna, ya bayyana gamsuwa da wannan yarjejeniya da kasar China bisa wasu dalilai. Ku latsa alamaru sauti don sauraren cikakkiyar hirar.
A wannan makon shirin na Lafiya Jari Ce tare da Azima Bashir Aminu ya yi nazari kan wani bincike can a Ghana da ke ƙiyasta cewa kusan kashi 13.3 na yawan jama'ar ƙasar na rayuwa da cutukan ƙoda, galibi ba tare da masaniyar suna ɗauke da ita ba, lura da yadda cutar bata nuna alamu a farko har sai ta kai ga ta'azzara. Wannan na nuna yadda cutar ta ƙoda ke matsayin babban ƙalubale a Ghana. Binciken ma'aikatar lafiyar Ghana ya nuna cewa matasa ne kan gaba wajen kamuwa da cutar ta ƙoda lamarin da ƙwararru a fannin cimaka ke cewa hakan na da nasaba da rashin daidaita cimaka da kuma yanayin rayuwar da jama'ar ƙasar suka runguma a yanzu wanda kai tsaye ke ƙara yawan masu kamuwa da cutar ta ƙoda. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
A yau shirin tambaya da amsa zai fara ne da ci gaban bayanin da muka faro a makon da ya gabata akan cutar gyambon ciki. Ku danna alamar sauraro dimin jin cikakken shirin tare da Nasiru Sani.
Matsalar nan ta karancin tsaftataccen ruwa, na ci gaba da addabar miliyoyin iyalai a sassan Nigeria, kila ko saboda rashin samun damar jan ruwan famfo a gidajensu, ko kuma rashin samun ruwan daga hukumomin samar da ruwan famfo na jihohinsu, duk da makudan kudin da gwamnatocin jihohin ke warewa, da sunan samar da ruwa wa jama'arsu. Wannan matsala ba kawai ta tsaya kan iyalai da kan rasa ruwan amfanin yau da kullum a gidajensu ba, har ma tana shafar ingancin muhalli, kasancewar a kan muhallin a kan dawo, don neman ruwan a karshe.
Shirin mu zagaya duniya na wannan mako ya duba manyan labaran da suka faru cikin wannan mako, a sassan duniya. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Oumarou Sani.
A yau shirin tambaya da amsa zai fara ne da ci gaban bayanin da muka faro a makon da ya gabata akan cutar gyambon ciki. Ku danna alamar sauraro dimin jin cikakken shirin tare da Nasiru Sani.
Wasu alƙaluma daga Hukumar Kula da Albarkatun Man Fetur na kan tudu da na cikin ruwa (NMDPRA) sun nuna cewa, adadin Iskar Gas ɗin da aka fitar daga Najeriya zuwa kasuwannin ƙetare ya kai kaso 62 cikin 100, cikin watanni uku na farkon wannan shekara. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Gas ɗin ya yi ƙaranci a Najeriyar, lamarin da ke taka rawa wajen raguwar hasken lantarkin da ake samu, fannin da kasonsa aƙalla 80 cikin 100 ya dogara da arziƙin na Gas. Don jin yadda masana ke kallon lamarin da kuma mafita, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Aminu Idris Harbau, ƙwararren kan tattalin arziki a Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraron hirar:
Shirin Al'adun mu na Gado a wannan makon ya leka Jamhuriyar Nijar ne, inda ya duba batun da ya shafi mazajen dauri, musaman mayaƙan gargajiya a wannan zamani, jaruman da ke ƙarƙashin inuwar sarakunan gargajiya. Duk inda akwai masarautun gargajiya an san su da tarin mayaƙa da ke yin tsarin daka a cikin kowane irin hali don kare su. Wannan tsarin ne da ya samo sali tun zamani da ake yaƙe-yaƙe tsakanin masarautu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa...........
Shirin Lafi Jari ce a wannan makon tare da Azima Bashir Aminu ya yi duba ne kan wani rahoton sashen bincike da kula da lafiyar jama'a na NDHS da ke ƙarƙashin hukumar kula da yawan jama'a ta Najeriya NPC, wanda ke nuna cewa daga shekarar 2024 yawan haihuwa ya ragu matuƙa tsakan matan Najeriya daga kashi 5.3 zuwa kashi 4.8. Wannan sakamakon rahoto na NDHS a cewar masana manuniya ce kan yadda mata a yanzu suka rungumi tsarin tazarar iyali bisa dalilai mabanbanta. Kafin yanzu dai, tsarin na tazarar iyali bai samu cikakkiyar karɓuwa a yankin arewacin Najeriya ba, yankin da ke sahun gaba ta fannin yawan haihuwa, sai dai a yanzu alamu na nuna wasu magidantan da kansu ke miƙa iyalansu ga likita don karɓar allura ko magungunan tazarar haihuwar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin Mu zagaya duniya tare da Oumarou Sani, kamar yadda ya ke zuwar muku a kowannen mako, a wannan karon ma ya yi bita ne kan muhimman labaran da suka faru a makon da muke ban kwana da shi. Cikin jerin labaran da ke ƙunshe a wannan shiri, akwai yadda Iran ta amince da buɗe mashigin Hormuz bayan ƙulla yarjejeniyar tsagaita wutar kwanaki 10 tsakanin Isra'ila da Lebanon. Wannan da sauran manyan labarai daga sassa daban-daban na nan ƙunshe a cikin shirin. Ku latsa alamar sauti don saurare.
Shirin na wannan makon ya mayar da hankali ne kan irin fargabar da 'yan kasuwar arewacin Najeriya da ke fatauncin kayayyaki zuwa wasu sassan jihohi ke ciki, sakamakon ayyukan bata gari da ke tare hanya wanda a wasu lokuta kan kai ga rasa rayuka. Abune da aka saba gani, ‘yan kasuwar dake hada Hada tsakankin jihohi daga wannan kasuwa zuwa waccan ko tsakanin kasuwannin kauyuka. To sai dai Kuma irin wannan tsarin na fuskantar cikas ko koma baya, alal misali ga yan kasuwa a jihar filato dake arewacin Najeriya, sakamakon munanan halaye na wasu bata gari marasa tausayin rayuwar Dan Adam, dake tare Yan tireda ko Kuma matafiya inda suke Kai musu farmaki, tare da yi musu kisan gilla. A kwanakin baya wasu Bata gari sun tare wasu Yan kasuwa da ke fatauci daga garin Jos zuwa yankin kudancin Jihar, inda suka kashe biyar daga cikinsu, Wannan al'amari ya Sanya Yan Kasuwar da sauran matafiya shiga hali na fargaba a kowane yanki dake jihar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Hukumar kwallon ƙafar Afrika ta sanar da ƙwace Kambun da Senegal ta lashe a gasar neman kofin nahiyar da aka kammala cikin watan Janairun da gabata tare da miƙa shi ga ƙasar Moroko. Wannan dai mataki ne da ya yi matuƙar girgizar masu shawar harkar ƙwallon ƙafa a sassan duniya, inda tuni Senegal a buƙaci a gudanar da bincike bisa zargin cewa akwai yiyuwar an bayar da rashawa ne don ƙwace wannan galaba. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabiru Yusuf.
Hukumar kwallon ƙafar Afrika ta sanar da ƙwace Kambun da Senegal ta lashe a gasar neman kofin nahiyar da aka kammala cikin watan Janairun da gabata tare da miƙa shi A a hannun ƙasar Moroko. Wannan dai mataki ne da ya yi matuƙar girgizar masu shawar harkar ƙwallon ƙafa ba wai a nahiyar Afrika ba har da sauran sassan duniya. To sai tuni Senegal ta buƙaci a gudanar da bincike bisa zargin cewa akwai yiyuwar an bayar da rashawa ne don ƙwace wannan galaba. A game da wannan mataki ne Michael Kuduson ya zanta da Aliyu Awwal Ibrahim, Sakataren tawagar ƙwallon ƙafar Najeriya ƴan ƙasa da shekaru 20. Ga kuma zantawarsu. A latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar tattaunawar.
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya fara ziyarar aiki a Birtaniya inda ya samu kyakkyawar tarba daga hukumomin ƙasar. Wannan ziyara na zuwa ne a dai dai lokacin da Najeriyar ke fuskantar matsalolin tsaro iri-iri. Dangane da ziyarar ta Tinubu da kuma alfanunta ga ƙasar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai taimakawa shugaban kan harkokin tsaro Malam Abdulaziz Abdulaziz kuma ga yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
Ga dukkanin alamu akwai yiwuwar yaƙi tsakanin Iran da kuma haɗin gwiwar Amurka da Isra'ila ya ɗauki tsawon lokaci saɓanin zaton da ake yi na ya kasance gajere, wannan kuwa ya biyo bayan jawabin shugaban Amurka Donald Trump a daren jiya da ke cewa mai yiwuwa a shafe makwanni 4 zuwa 5 suna kai hare-hare kan Iran. Wannan na zuwa ne a yayin da yaƙin da ya rincaɓe, ke ci gaba da shafar ƙasashe da dama a Yankin Gabas ta Tsakiya. Domin jin yadda masana siyasar ƙasa da ƙasa ke kallon lamarin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Tukur AbdulƘadir na Jami'ar Jihar Kaduna a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar..
Gwamnatin Jihar Benue a Najeriya, na neman amincewar gwamnatin tarayyar ƙasar wajen gina cibiyar sauya tunanin ‘yan bindigar da suka tuba, da ma sauran mutanen da wani yanayi ya sanya su taimaka wa ayyukan ta'addanci, ciki kuwa har da mata waɗanda ke yi wa ‘yan ta'addan aiki a bisa tilas bayan garkuwar da aka yi da su. Wannan na zuwa ne a yayin ake ci gaba da samun banbancin ra'ayi tsakanin ‘yan Najeriya a kan irin wannan yunƙuri. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Kabiru Adamu, shugaban kamfanin Beacon Consulting da ke bincike kan tsaro a nahiyar Afrika. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar..
Shirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan mako ya mayar da hankali ne kan gasar tseren dawaki da aka gudanar a garin Daura da ke jihar Katsina da ke a arewacin Najeriya. A farkon watan Faburairun wannan shekarar ne aka kammala babbar gasar tseren dawaki ta ƙasa da ƙasa da ƙungiyar sukuwar dawaki ta Najeriya ke shiryawa. Wannan ne dai karo na uku da ake gudanar da irin wannan sukuwa a cikin wannan shekarar, bayan da aka yi ta farko a birnin Katsina sai garin Hadeja na jihar Jigawa ya karbi bakunci sannan aka kamma sukuwan zangon farko na wannan shekarar a Daura. Mahaya daga Jihohin Kano da Sokoto da Neja da Bauchi da Kebbi da Katsina, waɗansu daga Jamhuriyar Nijar da Kamaru da Mali da Chadi da kuma Burkina Faso, suka halarci gasar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
A Najeriya wata ƙungiyar ta'addanci da ba'a kai ga tantace wa ba, ta buƙaci a'ummar Utono ta ƙaramar hukumar Ngaski a jihar Kebbi da ta biya su zunzurutun ƙudi har Naira miliyan 100, kafin su bai wa malamai damar gudanar da Tafsiri ko wa'azi a wannan watan Azumi na Ramadana. Ƴan ta'addar sun bayyana bukatar ne a wata rubutacciyar wasika da suka aika garin na Utono. Wannan dai shine karon farko da wata ƙungiya da bukaci malamai biyan wani kudi domin gabatar da wa'azi, ko da ya ke al'umma a wasu yankunan sun saba biyan kudi don neman yancin walwa, ko ayyukan noma ko ma girɓi. Yaya kuke kallon wannan sabon bukata na ƴan ta‘adda? Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Majalisar Ɗinkin Duniya ta ware 4 ga watan kowane watan Fabarairu a matsayin ranar yaƙi da Cutar Daji ko kuma Cancer ta Duniya, wadda hukumar lafiya ta Duniya WHO ke jagorancin gangamin wayar da kai a kanta, gami da bayyana halin da ake dangane da kula da masu fama da ita. Wannan rana ta zo ne a daidai lokacin da wani sabon rahoton masana ya ce daga cikin kusan mutane miliyan 19 da suka kamu da cutar ta Daji a shekarar 2022, ana iya bayar da kariya ga aƙalla mutane miliyan 7 daga kamuwa da cutar in da an ɗauki matakan da suka dace. Domin jin ƙalubalen da ƙasashe masu tasowa kamar Najeriya ke fuskanta dangane da cutar, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Shehu Usman AbdulMumin Maƙarfi, ƙwararren Likita a Jihar Kaduna da ke Najeriya. Sai a latsa alamar sautin da ke sama domin sauraron bayanan Dakta Shehu Usmanu Maƙarfi....
Shekaru 29 bayan mutuwarsa, an bai wa shahararren mawaƙi kuma mai fafutuka Fela Kuti ya kasance ba'Afirke na farko da aka bai wa kyautar yabo ta Grammy wato Lifetime Achievement Award da ake bai wa wanda ya sadaukar da rayuwarsa yana rera waƙa. Fela ɗan Najeriya, ya yi fice ainun, ta hanyar rera waƙoƙin gwagwarmaya da kuma muradun talakawa. Shin ko me za ku iya tunawa a game Fela Kuti? Me za ku ce a game da wannan kyauta ta Grammy Awarda aka bayar bayan rasuwarsa? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Morocco da Senegal sun yi nasarar kaiwa wasan ƙarshe na gasar cin kofin Afrika ko kuma AFCON, nasarar da suka samu bayan ita mai masaukin baƙi ta doke Najeriya yayinda Senegal kuma ta doke Masar dukkaninsu a daren jiya Laraba, yayinda ake shirin haɗuwa don doka wasan ƙarshe na gasar tsakanin manyan ƙasashen 2 a ranar Lahadi. Anya kuwa ƙasashen na Masar da Najeriya sun taka rawar da ta dace gabanin fitar da su daga gasar? Wacce ƙasa kuke ganin za ta kai tsakanin labari wajen lashe kofin a wannan karon? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin....
Hukumar daidaita farashin wutar lantarki a Najeriya ta ce yanzu haka akwai sama da layuka milyan biyar da jama'a ke amfani da wuta ba tare da an ɗora su a kan mita ba. Wannan ya zo ne daidai lokacin da ake ci gaba da ɗiga ayar tambaya dangane da dalilan da suka sa aka gaza samar da mitocin a wadace. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Mahukuntan jamhuriyar Nijar sun shelanta kafa dokar-ta-ɓaci, wanda a ƙarƙashinta gwamnati za ta iya yin amfani da illahirin al'ummar ƙasar da kuma dukiyoyinsu duk lokacin da ta ga ya dace saboda tunkarar barazanar tsaro. Matakin ya zo ne kwanaki ɗaya bayan da Amurka ta ƙaddamar da farmaki kan maɓoyar ƴanbindiga a wani wuri da ke jihar Sokoton Najeriya daf da iyaka da Nijar. Shin ko me za ku ce a game da matakin? Anya hakan zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro da ƙasar ke fama da su? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Shirin na yau ya yada zango jihar Diffa dake Jamhuriyar Nijar,yankin da aka gudanar da bikin nadin sabon sarkin Komadugu, wanda ya samu halartar baƙi daga ciki da wajen ƙasar. Diffa dai kamar dai yadda masana tarihi suka tabbatar, ana na nufin Diwa a harshen Kanuri kenan. Kalmar ta samo asali ne daga kalmar "Di wa Nallé wa," wadda ke nuna tsabtar jiki da dai sauran abubuwan da suka shafi maza da mata na yankin. Di na nufin farin gashi, kuma Nallé na nufin lalle wanda ke da ma'ana biyu. Wannan jumla, Di wa Nallé wa, na nufin mata waɗanda, ko da a cikin tsufa, suna rina gashinsu da lalle. Tarihi ya nuna cewa a ƙarni na 19, yankin Diffa a lokaci na karkashin masarautar Kanem-Bornu,inda a shekarar 1933 Turawan mulkin mallaka a lokacin sun kafa yankin Komadougou, wanda aka bayyana yankin da farko yake zaune a Bosso sannan daga baya ya koma Gueskérou. An gudanar da zaɓen sabon sarkin na komadugu a jahar Diffa a gaban hukumomin bariki da na gargajiya da kuma sauran al'umma, wanda ya kai ga zaɓen Hassan Mamadou Abba Kyari a matsayin sabon sarkin na Komadugu. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Abdoullaye Issa.
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umurnin janye dubban ƴansanda da ke kare manyan mutane a sassan ƙasar, tare da ta sanar da shirin ɗibar wasu sabbin ƴansanda kusan dubu 30 don tunkarar matsalar tsaro da ta addabin ƙasar. Shin ko wace irin gudunmuwa hakan zai bayar a ƙoƙarin tunkarar ƙalubalen tsaro da ƙasar ke fama da shi yanzu haka? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Shirin "Duniyar Wasanni" tare da Khamis Saleh a wannan lokaci zayyi duba ne kan ƙyautar gwarzon ɗan wasan ƙwallon ƙafan Afirka da Achraf Hakimi na Morocco ya lashe. A makon daya gabata ne Hukumar Kwallon Ƙafar Afrika CAF, ta bayar da kyautuka ga zaratan ƴan wasan nahiyar da suka nuna bajinta a wannan shekarar da muke bankwana da ita. A yayin bikin da ya gudana a birnin Rabat na ƙasar Morocco, hukumar ta CAF ta sanar da ɗan wasan baya na tawagar ƙasar ta Morocco wanda kuma ya ke yi wa ƙungiyar PSG wasa Achraf Hakimi, a matsayin wanda ya lashe ƙyautar gwarzon ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Afirka a wannan shekarar. Hakimi ya samu nasarar ce bayan doke shahararrun ƴan wasan nahiyar da suka taɓa lashe kyautar irinsu Mohamed Salah na Masar da ke taka leda a Liverpool, da kuma Victor Osimhen na Nigeria da ke wasa a Galatasaray. Wannan ne dai karo na farko da ɗan wasan ya taɓa lashe ƙyautar, bayan da a karo biyu a jere ya na ƙarewa a mataki na biyu, a shekarar 2023 da Victor Osimhen ya lashe da kuma 2024 da Ademola Lookman ya lashe. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin...
A Najeriya, ƴan bindiga masu gurkuwa da mutane domin ƙarbar ƙudin fansa, sun tsananta kai hare-hare makarantu tare da sace ɗaibai a baya-bayan nan, lamarin da ya sa gwamnatoci a wasu jihohin ƙasar suka ɗauki matakin rufe makarantu a matakai daban-daban. Hakan ya biyo bayan sace dalibai a jihohin Kebbi da Neja a makon da ya gabata, lamarin da ya sake haifar da fargaba kan tsaron dalibai da makarantu da kuma makomar ilimi a yankin arewacin Najeriya. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Ku latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Matsalolin tsaro na ci gaba da ɗaukar sabon salo a Tarayyar Najeriya, bayan da a baya-bayan nan aka ga yadda ƴan bindiga a yankin arewa maso yammacin ƙasar suka sace ɗalibai aƙalla 25 a jihar Kebbi, yayinda ana tsaka da jimamin wannan kuma aka sake ganin yadda suka kai hari wata majami'ar jihar Kwara tare da kashe mutane 2 da kuma sace wasu da dama. Wannan na zuwa ne kwanaki bayan dakarun Sojin Najeriyar sun sanar da samun gagarumar nasara a kan ƴan ta'adda musamman bayan barazanar Trump ta ɗaukar matakin Soji kan ƙasar ta yammacin Afrika. Dangane da wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da masanin tsaro a Najeriyar Dr Yahuza Getso........
Da alama masu ɗauke da makamai a Najeriya sun koma gidan jiya na sace-sacen dalibai, garkuwa da mutane da ajalin waɗanda basu ji basu gani ba gadan-gadan, yayin da a cikin kwanaki huɗu kacal aka yi awon gaba da mutum 145. Wannan na zuwa ne a yayin da matsalolin tsaro ke sake ta'azzara a sassan arewacin ƙasar, ciki har da satar ɗaliban da aka yi a jihar Kebbi, sai kuma labarin da ake ta yamaɗiɗin cewa mayaƙan ISWAP sun yi garkuwa da wani janar din soji tare da kashe shi a arewa maso gabashin Najeriyar. Shin kun gamsu da yadda jami'an tsaro ke aiki a yankunan ku. Me kuke ganin ya kamata hukumomi su yi domin kawo ƙarshen zulumin da jama'a ke ciki? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
A ranar Lahadin da ta gabata Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo ta kawo ƙarshen fatan Najeriya na samun tikitin halartar gasar cin kofin duniyar da za ayi a shekara mai zuwa. Karo na biyu kenan a jere da Najeriya ke rasa damar haska wa a gasar ta Tamula mafi daraja a Duniya. Waɗanne dalilai ne ke janyo wa Najeriya wannan koma baya a sha'anin ƙwalllon ƙafa? Wanene ya gaza sauke nauyin da rataya a wuyansa a tsakanin masu alhaki a wannan fage? Ta yaya kuma za a magance matsalar? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakin ku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Fatan Najeriya na samun gurbi a gasar cin kofin duniyar da za'a yi a shekara mai zuwa ya gushe, sakamakon rashin nasarar da ƙungiyar Super Eagles ta yi a hannun ƙasar Congo. Wannan shi ne karo na biyu a jere da Najeriya ba zata je gasar ta dunitya ba, bayan gaza zuwa Qatar shekaru 4 da suka gabata, kafin wannan karo. Bashir Ibrahim Idris, ya tattauna da tsohon sakatare janar na Hukumar Kwallon Kafa Najeriya, Hon Sani Ahmad Toro game da wannan koma baya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana a kai.
Shirin lafiya jari ce na wannan mao ya mayar da hankali ne kan wani rahoto da ke cewa mutane akalla miliyan 24 ne ke fama da cutar Suga a Nahiyar Afrika kawai. Wannan kuwa na faruwa ne a dai-dai lokacin da cutar ke sauya salo da tsanani ga masu fama da ita, baya ga bijirewa magani. Danna alamar sauraro domin jin cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu.
Yawaitar yajin aikin likitoci na neman kassara ɓangaren kiwon lafiya a Najeriya, domin kuwa yanzu haka likitocin da suka kammala karatu sannan suke cikin asibitoci don sanin makamar aiki, sun tsunduma yajin aiki saboda neman a biya su haƙƙoƙinsu kamar dai yadda yake ƙunshe a yarjejeniyar da ke tsakaninsu da hukuma. Shin ko yaya wannan yajin aiki ke shafar sha'anin kiwon lafiya a yankunan da ku ke rayuwa? Wace shawara za ku bai wa ɓangarorin don warware saɓanin da ke tsakaninsu? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...
Ra'ayoyi sun sha bambam a tsakanin al'umma dangane da matakin zaftare kuɗaɗe don tallafa wa Gidauniyar Ceton Ƙasa da gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta kafa. Ƙarƙashin wannan gidauniya, kusan kowane rukuni na jama'a, tun daga ƙusoshin gwamnati, zuwa ma'aikata da kamfanoni, na gwamnati da masu zaman kansu, kai har ma da masu zaman kashe wando, ala dole sai kowa ya bayar da nasa tallafin. Shin me za ku ce a game da wannan Gidauniya, da har ake cewa har yanzu ba wanda ke da hurumin gudanar da bincike dangane da kuɗaɗen da ake tarawa a cikinta? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...
Wataƙila sakamakon matsin lamba daga al'umma, shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake bitar afuwar da ya yi wa mutane sama da 170 da ke ɗaure a gidajen yari saboda laifukan aikata kisan kai, fataucin miyagun ƙwayoyi da dai sauransu. Shin me za ku ce dangane da wannan sabon mataki na shugaba Tinubu da ke tabbatar da cewa mafi yawan waɗanda aka yi wa afuwar a farko wannan wata, a yanzu za su ci gaba da kasancewa a gidan yari? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai cikin shirin Ra'ayoyin ku masu sauraro na wannan rana. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin....
Ga alama yajejeniyar tsagaita wutar da Isra'ila ta ƙulla tsakaninta da Hamas, wadda Amurka ta tsara ta kama hanyar rugujewa, sakamakon umarnin da Firaminista Benjamin netanyahu ya bayar na ƙaddamar da sabbin hare-hare a Gaza. Wannan ya biyo bayan abinda ya kira ƙin bada gawarwakin sauran Yahudawan da Hamas ta yi garkuwa da su. Domin tattauna wannan dambarwa, Bashir Ibrahim Idris, ya tuntuɓi Dakta Abdulhakin Garba Funtua, mai sharhi a kan harkokin Gabas ta Tsakiya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.........................
Shirin a wannan makon ya yi dubi ne kan zare sunan Najeriya da cibiyar da ke sanya idanu kan almundahanar kuɗaɗe da ɗaukar nauyin ta'addanci a duniya ta yi cikin baƙin kundinta. A makon da ya gabata ne, Cibiyar nan ta Yaƙi da Masu Safarar Kuɗi da Ɗaukar Nauyin Ta'addanci ta duniya (FATF), ta sanar da cire sunan Najeriya daga jerin ƙasashen da take ɗaukarsu a matsayin masu wanan ɗabi'a. Wannan mataki ba iya Najeriya ta shafa ba, harma da ƙasashen Burkina Faso da Afrika ta Kudu da ma Mozambique duk a nahiyar Afrika. Cibiyar wadda ke da hedikwata a birnin Paris na ƙasar Faransa, wadda ke gudanar da binciken kwakwaf kan yadda ake hada-hadar kuɗaɗe tsakananin ma'aikatun gwamnati da hukumomi ko kuma cibiyoyin gwamnati ta ce duk da cire waɗannan ƙasahe cikin baƙin littafinta, har yanzu za'a ci gaba da sanya idanu akan waɗannan ƙasashe. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin tare da Ahmed Abba................
Shirin wannan makon zai tare ne a jihar Kano dake Tarayyar Najeriya, inda aka samu manoma da dama a wasu yankuna da suka duƙufa wajen noman barkono a wannan shekarar. Ba shakka sun yi aiki tuƙuru, kuma haƙarsu ta cimma ruwa duba da ɗimbim barkono da suka girba. Wannan lamari dai ya tayar da hankalin waɗannan manoma, waɗanda sun sauya alƙibla ne saboda ganin yadda farashin amfanin gona dangin hatsi ya faɗi warwas a kasuwanni, kuma sun yi haka ne domin su more daga ribar da aka yi ta ci daga barkono, amma sai gashi lamarin ya yi musu ta leƙo ta koma. A kusan ilahirin kasuwannin kayan gwari, gani za ka yi ga barkono, wanda kafin yanzu yake tamkar gwal, sai ga shi yanzu masu saye su na mai tayin da suka ga dama. Masana sun yi ittifakin cewa, ba shakka rashin tsari da alƙibla wajen noma da kuma binciken halin da kasuwa ke ciki sun taka rawa ainun a wcikin wannan matsala da aka samu. Sai dai kuma, matsaloli na yanayi ma sun taka irin nasu rawar, domin akwai matsin lamba daga yadda tsarin ruwan sama ya sauya, da sauraan matsaloli da suka addabi ƙasar noma. Matsalar yanayi da muhalli na mummunan tasiri akan ko wane irin nau'i na noma. shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin, tare da Michael Kuduson.
Gwmanatin Jamhuriyar Nijar ta kafa kwamitin ƙwararru wanda ta ɗora wa alhakin sake rubuta tarihin ƙasar, lura da cewa yawancin abubuwan da ake faɗa game da ƙasar a halin yanzu Turanwan mulkin mallaka ne suka rubuta su. Shin ko meye muhimmanci rubuta sabon tarihin wanda aka ɗanka wa masana ƴan ƙasar a maimakon wanda aka gada daga ƴan mulkin mallaka? Anya abu ne mai yiyuwa a iya sauya bayanan da ke rubuce a game da ƙasar waɗanda tuni suka karaɗe duniya? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...
Mahukunta a Najeriya sun tasa ƙeyar ƴan asalin ƙasashen waje su 192 da aka tabbatar da sun shahara wajen aikata damfara ta yanar gizo a cikin ƙasar. Mutanen waɗanda aka kama a birnin Lagos, sun haɗa da China, Philippines, Malaysia, Pakistan, Tunisia da dai sauransu, waɗanda tuni kotu ta tabbatar da laifukansu. Shin me za ku ce a game da yadda ƴan damfara a yanar gizo ke neman mayar da Najeriya a matsayin tunga domin baje kolinsu? Shin ko kun gamsu da irin matakan da mahukunta ke ɗauka domin daƙile wannan matsala? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi...
A Najeriya yajin aikin malaman jami'o'i ya shiga rana ta biyu, lamarin da tuni ya fara haifar da cikas musamman ga ɗalibai da mafi yawansu na tsakiyar zana jarrabawa. Yayin da ƙungiyar Malaman ASUU ta ce ta shiga yajin aikin ne domin neman gwamnati ta cika aiwatar da yarjejeniyar da ɓangarorin biyu suka rattaba wa hnnu tun 20009, yayin da a gwamnati ke cewa tuni aka aiwatar da abubuwan da kunshe a yarjejeniyar. Shin ko yaya ku kallon wannan yajin aiki? Wace shawarar za ku bai wa bangarorin biyu domin gaggauta wannan saɓani da ke tsakaninsu. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...
Malaman Jami'o'in Najeriya sun kare matakin ƙungiyarsu na tsunduma yajin aikin gargaɗi na makwanni 2, inda suka zargi gwamnati da yaradara. Wannan kuwa na zuwa ne duk da gargaɗin da gwamnatin ƙasar ta yi na amfani da dokar nan ta babu aiki babu biya duk malamin da ya shiga yajin aiki na ASUU. Shugaban ƙungiyar Malaman reshen Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria, Farfesa Haruna Jibril ya yiwa Bashir Ibrahim Idris ƙarin bayani a tattaunawar da suka yi kamar haka... Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....