POPULARITY
Yayin da a yau aka ƙaddamar da makon rigakafi a duniya, Hukumomi a Najeriya da kuma Unicef, sun yi gargaɗin cewa yanzu haka nau'ukan cutar shan'inna har guda 17 da suka yaɗu a cikin jihohi 8 na ƙasar. Wannan dai babban ƙalubale ne ga sha'anin kiwon lafiya, bayan da aka shelanta kawo ƙarshen cutar tun 2020.Shin ko meye dalilan sake ɓullar wannan cuta a Najeriya?Waɗanne matakai ya kamata a ɗauka domin shawo kanta?Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin masu saurare.
Shirin Lafiya Jari ce tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan ƙaruwar masu kamuwa da cuta mai karya garkuwar jiki ko kuma HIV AIDS ko sida tsakanin matasan Ghana a shekarun baya-bayan nan, wadda masana ke ɗora alhakin yawaitarta kan rashin ɗaukar matakai. Wannan ƙaruwar alƙaluma na zuwa a dai dai lokacin da duniya ke ganin ƙarancin magunguna rage kaifin cutar sakamakon matakin Amurka na zaftare tallafin da ta ke bayarwa ƙarƙashin ƙungiyar USAID.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shiri.
Alƙaluma na nuni da cewa amfani da kuɗaɗen Crypto na daɗa samun karɓuwa a ƙasashen Yankin Kudu Da Saharar Afrika musamman ma Najeriya, inda a bara wani rahoto ya ce a tsakanin 2023 zuwa 2024, yawan kuɗaɗen Crypton da aka yi hada-hadarsu ya kai na Dalar Amurka biliyan 59. Wannan ya sa wasu ƙwararru bai wa mahukuntan Najeriyar shawarar, kamata yayi su rungumi sauyin domin amfana da shi a maimakon ƙoƙarin daƙile kasuwar Crypton, saboda illolin da suka ce na tattare da ita. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Nura Ado Suleiman da Dakta Ƙasim Garba Kurfi, masanin tattalin arziƙi a Najeriya..............
Shirin “Ilimi Hasken Rayuwa” namu na wannan mako, ya yada zango ne a tarayyar Najeriya, inda shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya rattaba hannu kan ƙudurin samar da sabuwar jami'a kimiyyan lafiya da fasaha ta tarayya wato Federal University of Health Science and Technology a garin Tsafe na Jihar Zamfara, bayan tsallake dukkan matakan majalisa dokokin ƙasar. Wannan saka nannu na shugaban ƙasar ya yi zai bada damar ƙara inganta harkan kiwon lafiya ta hanyar samar da kwararru.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Nura Ado Suleiman.........
Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali kan al'adar nan ta naɗin sarauta da wasu masarautun gargajiya ke yi ga ƙabilun da ba su ke da masarautar ba, wanda hakan ya biyo bayan sabbin naɗe-naɗe da ɗaya daga cikin manyan masarautun ƙabilar gwari a arewacin Najeriya ta yi wa wasu manyan shuwagabannin al'ummar fulani a jihar Neja. Wannan dai ba shi ne karon farko ba da ake samun masarautun Hausa da Fulani da ma wasu masarautun a yankin kudanci da kuma arewacin Najeriya ke baiwa ƙabilun da ke zaune a masarautar sarauta ba, abin da shirin Al'adu na wannan mako ya yi nazari akai tare da jin inda hakan ya samo asali da kuma alaƙar da ke tsakanin al'adun ƙabilar gwari da fulani daga masana al'adu da masarautu.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.
EXCLUSIVE INTERVIEW- Asher Fearn-Wannan AFLW draft prospect #aflw #footy
A Najeriya rahotanni sun bayyana cewar yanzu haka shugaba Bola Ahmed Tinubu ya umarci dukkanin ministocinsa da suka fito daga yankin arewacin ƙasar su koma jihohin da suka fito domin kare manufofinsa da kuma bayyana irin ayyukan da yake yi. Wannan na zuwa ne a dai dai lokacin da shugaban ke ganin matsananciyar suka daga ɓangaren adawa da kuma ganin tarin barazana musamman kan salon kamun ludayin gwamnatinsa.Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Harsanu Yunusa Guyaba.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.
Ƙasashen duniya sun bayyana matukar rashin amincewarsu da buƙatar shugaban Amurka Donald Trump, na ƙwace Gaza da kuma mayar da Falasdinawa wasu ƙasashe domin gina wurin shaƙatawa a ƙasarsu. Wannan matsayi ya gamu da suka daga ƙasashen duniya da dama ciki harda Majalisar Ɗinkin Duniya. Bashir Ibrahim Idris ya tatatuna shirin da Ambasada Abubakar Cika, tsohon Jakadan Najeriya a kasar Iran. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana.........
Ƙasashen duniya na ci gaba da bayyana damuwa dangane da shirin shugaban Amurka Donald Trump na dakatar da ayyukan hukumar USAID wadda ke taimakawa ƙasashen duniya . Wannan hukuma dai na taka gagarumar rawa a bangarori da dama a ƙasashe masu tasowa irin su Najeriya.Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Abba Gambo, mai bai wa gwamnonin Najeriya shawara a kan harkokin noma dangane da tasirin matakin a kan noman ƙasar.Latsa alamar sauti domin sauraren yadda tattaunawar ta kasance....
Hukumomin sojin Jamhuriyar Nijar sun gabatar da wata sabuwar dokar da zata hukunta baƙin da ke shiga cikin kasar ba tare da halartattun takardu ba. Wannan ya biyo bayan zarge zargen da ake na samun wasu baki da ke yiwa kasar zagon kasa. Domin tattauna wannan batu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai sharhi a kan Nijar, Abdoul Naseer, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
A wani yanayi da ba safai aka saba gani ba, mahukuntan Nijar sun sallami tuɓaɓɓun mayaƙan Boko Haram aƙalla 124 ciki har da ƙananan yara 44, waɗanda aka basu horan sauya ɗabi'u don komawa rayuwar fararen hula. Wannan shi ne karon farko da ake ganin irin hakan, tun bayan makamancin yunƙurin da hamɓararren shugaban ƙasar Bazoum Muhammad ya yi watanni ƙalilan gabanin hamɓarar da shi.Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi a cikin shirin...
Kamar yadda labari ya karaɗe kafafen yada labarai, ƙaasa da mako guda bayan da hukumar kwastan a Najeriya ta sanar da buɗe shafin yanar gizo don aikewa da takardun neman ɗaukar jami'ai kimanin dubu 4, sama da masu neman wannan aiki dubu dari 5 ne suka gabatar da buƙatunsu. Wannan al'amari ne da ke faruwa a kowace ma'aikata a duk lokacin da aka sanar da buƙatar ɗaukar ma'aikata.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Abida Shu'aibu Baraza.
A ranar Laraba ne shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatar da kasafin kudin ƙasar na shekarar 2025 na naira Tiriliyan 47.9. Sai dai wani batu da ya haifar da muhawara a tsakanin ‘yan Najeriya dangane da kasafin kuɗin na baɗi, shi ne yadda aƙalla kaso 30 zuwa 32 na yawan kuɗaɗen za su tafi a biyan basuka ko kuma kudin ruwan basukan, kwatankwacin naira tiriliyan 15 da biliyan 800, adadin da ya zarce yawan kudaden da aka warewa tsaro, ilimi, lafiya da manyan ayyuka.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin tare da Kabiru Mohammed Dan Bauchi...
Tsohon mataimakain shugaban Najeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a zaben 2023 da ya gabata Atiku Abubakar da kuma ɗan takarar LP a 2023 Peter Obi na shirin haɗewa domin kawar da gwamnatin APC wadda a cewarsu ta gaza, lamarin da ke zuwa tun kafin kakar zaɓen na shekarar 2027. Sai dai a martaninta, jam'iyyar APC ta ce babu wata haɗaka da za ta iya taka wa shugaba mai ci birki.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin...
Kamar yadda aka saba, RFI Hausa na bai wa masu saurare damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwa da dama da ke ci musu tuwo a ƙwarya. Majalisar dattawar Najeriya ta amince da wani kuɗirin doka da ya haramta fitar da duk wata masara mai yawa da ba'a sarrafa ta ba daga ƙasar zuwa ƙasashen waje, kuma ta tanadi hukuncin ɗaurin shekara guda ga duk wanda ya yi kunnen ƙashi.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau.Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyin mabanbanta..
Mataimakin shugaban ƙasa kuma ɗan takarar jam'iyya mai mulki a Ghana, Mahamudu Bawumia ya amince da shan kaye a zaɓen ƙasar, inda ya taya tsohon shugaban ƙasa John Mahama murnar lashe zaɓen. Wannan ya biyo bayan zaɓen shugaban ƙasar da aka yi a Asabar ɗin ƙarshen mako 7 ga watan Disamba, wanda rahotanni suka tabbatar da cewa ya gudana cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya.Shin ya ku ka kalli yadda zaɓen na Ghana ya gudana?Me za ku ce kan yadda Bawumia ya amince da shan kaye tun kafin a fitar da sakamakon zaɓen?Wane darasi ku ke ganin ƴan siyasa a yankunanku za su koya daga zaɓen Ghana?Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin
Mazauna yankunnan jihar Zamfara da ke arewacin Najeriya na ci gaba bayyana irin halin kuncin rayuwa da suka samu kansu sakamakon yadda suke biyan ƙudi ga ƴan bindiga kafin su yi noma a daminar da suka gabata, yanzu kuma lokacin girbi ƴan bindigar sun hana su zuwa girbi da kwaso amfanin gonar sai sun biya.Wannan matsala ta yi sanadiyar talauta akasarin mutanen da ke wannan yankin. Dangane da wannan batu ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da wani mazaunin yankin da ya bukaci a sakaya sunansa saboda dalilai na tsaro, kuma ga abinda ya shaida masa.
Kamar yadda aka saba, RFI Hausa na bai wa masu saurare damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwa da dama da ke ci musu tuwo a kwarya. Majalisar Ɗinkin Duniya ta ware ranar 3 ga watan Disambar kowacce shekara a matsayin ranar masu buƙata ta musamman, wato mutane da ke rayuwa da wata naƙasa a fadin duniya.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau.Ku latsa alamar sauti domin sauraren shirin tare da Hauwa Halliru Gwangwazo:
A Najeriya, kwanan nan ne kotu ta karbe wani rukuni mai ƙunshe da gidaje 753 mallakin wani tsohon gwamnan babban bankin ƙasar, nasara mafi girma da hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa ta'annati ta taɓa samu a cikin sama da shekaru 21 da kafuwarta. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin tare da Oumaru Sani:
Shirin Duniyar Wasanni na wannan mako yayi duba ne kan yadda aka kammala wasanni sojoji na nahiyar Afrika. Wannan ne dai karo na biyu da tawogogin ƙasashe 20 suka fafata a babban birnin tarayyar Najeriya Abuja, inda kuma tawagar ƴan wasan sojoji ta Najeriya ta zamo zakara, bayan da ta samu nasarar lashe lambar zinari 114 da azurfa 65 sai kuma tagulla 55 a jumlace ke nan ta samu lambobin yabo 234. Ƙasar Aljeriya ke bi mata a matsayin na 2 da lambar zinari 53 da azurfa 22 sai kuma agulla 21, a jumlace ita kuma ta samu lambobin yabo 96, Kenya ce tazo ta 3 bayan da ta lashe lambobin yabo 50.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin tare da Khamis Saleh.......
Hukumar Kasuwanci ta duniya WTO ta bai wa tsohuwar ministan kudin Najeriya Ngozi Okonjo Iweala wa'adi na 2 na shekaru 4, yayin da ta kawo karshen wa'adinta na farko. Wannan ya biyo bayan kasancewarta 'yar takara daya tilo da ta sake neman mukamin.Domin tasirin wannan nadi da kuma kalubalen dake gabanta, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Isa Abdullahi, masanin tattalin arziki a Najeriya.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Kusan shekara guda da rabi da juyin mulkin da sojoji suka yi a Jamhuriyar Nijar, har ya zuwa yanzu babu wani shiri daga sojojin na mayar da mulki ga fararen hula. Wannan ya sa wasu daga cikin jama'ar ƙasar gabatar da buƙata ga sojoji da su sake tunani akai domin bai wa jama'a damar zaɓin shugabannin da suke so. Domin tattauna wannan batu, Bashir Ibrahim Idris ya tintibi Alhaji Adamu Muhammad Madawa, daya daga cikin shugabannin ƴan Nijar mazauna Najeriya. Ku latsa alamar sauti dominjin yadda zantawarsu ta gudana........
Shirin Duniyar Wasanni a wannan makon ya yi duba ne kan irin gudummawar da cibiyoyin horar da matasa wasan kwallon ƙafa ke bayarwa wajen zakulo matasan ƴan wasa da horar da su a Nigeria. Wannan dai wani bangare ne na gudummawarsu ga ci gaban wasan kwallon ƙafa a Nigeria, tsofin ƴan wasan tawagar Super Eagles na ƙasar, sun fara kafa cibiyoyi masu zaman kan su, da su ke zakulowa tare da horar da matasa don yin fice a harkar ta kwallon kafa. Irin wadannan cibiyoyin horar da matasa wasan na kwallon kafa da a turance ake kira Football Academy, kan shiga birane da karkara don tuntubar ƙanana da matsakaitan club-club, domin samun ƴan wasan daga wajen su da za a yi rijistarsu a wannan cibiya.Pascal Patrick, tsohon ɗan wasan Super Eagles kuma shugaban Hukumar kwallon kafa ta NFA a jihar Bauchi kana co-odinetan tawagar Super Eagles na Nigeria, na daya daga cikin tsofaffin ƴan wasan ƙasar da suka kafa irin wannan cibiya a jihar Bauchi.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh.......
Babbar mai shari'a a Najeriya tare da Hukumar Kula da Ayyukan Shari'a ta NJC sun kaddamar da bincike a kan yadda wasu alkalai a jihar Rivers suka dinga bada hukunce hukunce da ke karo da juna dangane da zaben kananan hukumomin da aka yi a jihar. Wannan umarni na zuwa ne bayan an samu irin wannan matsala a jihar Kano. Saboda haka Bashir Ibrahim Idris ya tintibe masanin ɓangaren shari'a Farfesa Shehu Abdullahi Zuru na jami'ar Baze dake Abuja. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana.........
Mazauna yankin Arewacin Najeriya sun kwashe kwanaki 7 ba tare da hasken wutar lantarki ba, abinda ya yi sanadiyar durkushewar jama'a musamman masu sana'oin da suka dogara ga wutar. Wannan matsala na barazana ga rayuwa da kuma tattalin arzikin yankin. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da daya daga cikin dattawan yankin, Alhaji Sule Ammani Yarin Katsina. Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar zantawarsu ta su........
Shirin Duniyar Wasanni a wannan lokaci yayi duba ne kan danbarwar da aka samu tsakanin Najeriya da Libya. A makon daya gaba ne dai aka fara kai ruwa rana tsakanin bayan da tawagar Super Eagles ta Najeriya ta yi tattaki zuwa Libya don karawa da takwaransu ta ƙasar a wasa na biyu na neman gurbin zuwa gasar lashe kofin Afrika da za ayi a Morocco a shekara mai zuwa. Wannan al'amari dai ya haifar da cece-kuce a duniyar kwallon ƙafar, ganin yadda Super Eagles ta zargi hukumomin kwallon ƙafar Libya da yin watsi da su a filin jirgin sama ba tare da ance kuci kanku ba.Ku latsa alamar sauti don jin cikakken shirin tare da Khamis Saleh.....
Bankin duniya ya yaba da sauye sauyen tattalin arzikin da gwamnatin Najeriya ke aiwatarwa, tare da bai wa hukumomin ƙasar shawarar kar su kuskura su koma da baya. Wannan na zuwa ne a dai dai lokacin da talakawan ƙasar ke kokawa saboda ƙuncin rayuwa. Dangane da wannan matsayi Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki Dr Kasum Garba Kurfi. Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar zantawarsu..............
Bankin Duniya, ya ce Najeriya da wasu ƙasashe da dama masu tasowa, za su iya shafe tsawon shekara ɗari a nan gaba kafin su yi nasarar rage kaifin talauci da ke addabar al'ummominsu. Wannan gargaɗi na Bankin Duniya na zuwa ne a daidai lokacin da bayanai ke cewa kusan a kowace rana ta Allah ana samun karuwar mutanen da suka dogara da malauna ne domin samun abin da za su ci da kuma iyalansu.Shin, ko yaya za ku bayyana matsayin talauci ko fara a inda ku ke rayuwa?Ko kun gamsu da irin matakan da hukumomin ƙasashen ke ɗauka domin rage kaifin talauci a tsakanin al'umma?Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin
A karo na 4 tun bayan hawa karagar mulkin shugabancin Najeriya da Bola Ahmed Tinubu yayi, kamfanin man NNPCL ke sanar da ƙara farashin man fetur, inda yanzu farashin ya koma naira 998 a Lagos, ya yin da Abuja kuma ya koma naira dubu 1 da naira 30. Wannan ya sa talakawan ƙasar sake gabatar da korafinsu saboda yadda farashin zai sake shafar kayan masarufi. Dangane da wannan sake karin, Bashir Ibrahim Idris ya tatauna da Comrade Umar Danjani Hadejiya. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tasu......
A Najeriya, yayin a ke fama da matsalar tattalin arziki da tsanantar harkokin rayuwa, alkaluma na tabbatar da cewa bankunan ƙasar na ci gaba samun gagarumar riba a kowace rana ta Allah. Shin ko meye dalilin wannan gibi tsakanin bankuna da kuma al'umma? Wane gyara ya kamata ayi domin tabbatar da cewa arzikin kasa na zagayawa a cikin al'umma? Wannan shine maudu'in da masu sauraro suka tattauna akai.
A Najeriya, yanzu haka wasu sun fara nuna fargaba a game da yadda tsarin dimokuradiyya ke gudana a kasar, musamman lura da yadda da zarar aka gudanar da zaben kananan hukumomi, to ko shakka babu jam'iyyar da ke rike da kujerar gwamna ce za ta lashe zaben babu tantama. Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da aka bai wa kananan hukumomin damar cin gashin kansu.Abin tambaya anan shi ne, me ya sa a kullum jam'iyya mai rike da mukamin gwamna ce ke lashe zaben kananan hukomomi a Najeriya?Meye tasirin hakan game da fatan da ake da shi na ganin cewa al'umma ta morewa tsarin dimokuradiyya daga tushe?Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a
Yau 7 ga watan oktoban shekarar daya kenan da mayakan Hamas suka kaddamar da hare-hare a Isra'ila, inda suka kashe mutane 1 da 200 tare da yin garkuwa da wasu akalla 150. Wannan ya fusata Isra'ila inda ta mayar da martani ta hanyar kashe sama da mutane kusan dubu 43 a yankin Gaza, tare da yaduwar wannan rikici zuwa kasashen Lebanan da Iran.Shin me za ku ce a game da wannan lamari da ke kara jefa cikin zaman zullumi?Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin
Kamar dai kowane mako, a yau juma'a ma jaridar Aminiya da ake wallafa ta a Najeriya ta sake fitowa ɗauke da dimbin labarai da suka shafi fannoni daban nan na rayuwa. Kuma Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Muƙaddashin Editan jaridar Muhammad Amin Ahmed domin jin karin bayani dangane da labaran da suke ɗauke da su a wannan karo. domin sauraron cikakken shirin, a latsa alamar sauti.
Yamai babban birnin Jamhuriyar, ya fara karɓar baƙuncin taron ƙwararru da saurann masu ruwa da tsaki kan matsalar sauyin yanayi da ta shafe yankin yammacin Afrika. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da sassan yankin na Yammacin Afirka da Sahel ke fuskantar Iftila'in Ambaliyar mafi muni da aka taɓa gani cikin aƙalla shekaru 20, kamar yadda aka gani a garin Maiduguri, inda a baya bayan nan saukar ruwan sama ya janyo tumbatsar dam ɗin da ya fashe, lamarin ya haddasa mummunar ambaliyar da ta mamaye sassan birnin da dama.Wane hali ake ciki a garin na Maiduguri bayan iftila'in da ya auku?Wadanne dabaru ya dace a bi wajen daƙile sake aukuwar haka, ko kuma rage girman barazanar da aka gani, ta hanyar karkatar da tarin ruwan da ke ambaliya zuwa ga amfanin jama'a?Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin
A wannan makon shirin zai mayar da hankali kan cutar borin gishiri ko kuma kumburin da mata ke fama da ita yayin da suke da dauke da juna biyu, wacce kuma a lokuta da dama kan haddasa asarar rayuka. Wannan cuta a Jamhuriyar Nijar na daga cikin wacce ke ciwa hukumomi tuwo a kwarya ganin yadda mata sama da dari biyar da 30 cikin kowace mace dubu daya ne kamuwa da wannan cuta, kuma sama da 50 ke rasa ransu a sanadiyarta. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu.....
Shirin 'Kasuwa A kai Miki Dole' na wannan mako tare da Ahmed Abba ya duba yadda kasuwancin kifi a Najeriya ya ke neman ya gagari masu sana'ar saboda tsadar abincin da ake kiwon kifi da shi da farashin sa ya ƙaru, lamarin da ke barazana musamman ga ƙanana da matsakaitan ƴan kasuwa a fannin. Farashin buhun abincin kifi ya tashi daga N18,000 a shekarar 2023 zuwa N36,000 a wannan shekarar, wanda ya nuna karuwar kashi 100 cikin 100 a fadin Najeriya.Wannan al'amari ya yi kamari a yankin Neja Delta da suka yi kaurin suna a noman kifi.
Shirin Muhallinka Rayuwarka na wannan mako ya yi duba ne kan wata hadaka da aka samu tsakanin gwamnatin jihar Kogi da kuma katafaren kamfanin nan na sarrafa amfanin gona a Najeriya Wato OLAM, domin farfado da tsarin aikin Malaman Gona ta hanyar horar da wadanda jihar ke da su tare da kara yawansu a kokarin da bangarorin biyu ke yi na shirya samun ninkin amfanin gonar da za a rinka nomawa a jihar ta Kwara.
Shirin Tambaya da Amsa tare da Nasiru Sani a wannan mako ya amsa wasu daga cikin tambayoyin da aka aika mana, Shirin ya amsa tambaya kan yadda neman ƙarin bayani da wani mai sauraro ya yi kan zubu ko kuma yanayin siyasar Birtaniya dama banbancinta da siyasar da ake gani a ƙasashen da ta mulka.Wannan da sauran tambayoyi na tafe a cikin shirin na wannan mako.
Shirin mu zagaya duniya na wannan mako ya duba manyan labaran da suka faru a wannan mako ciki kuwa har da addin mutanen da hare-haren ta'addanci suna kashe a cikin shekaru biyar a Najeriya Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Nura Ado Sulaiman
Dubban ‘Yan Najeriya musamman matasa sun yi tsayuwar gwamen Jaki kan aniyarsu ta gudanar da zanga-zangar lumana daga yau zuwa wasu kwanaki, akan tsadar rayuwar da suke zargin gwamnati da gazawa wajen kawo ƙarshenta. Wannan na zuwa ne duk da jerin matakan sassauta tsananin da ake ciki da gwamnatin Najeriyar da ɗauka domin rarrashin ‘yan ƙasar ciki har da shirin fara sayar da buhun shinkafa mai kilo 50 akan naira dubu 40 a maimakon kusan naira dubu 80.Kan halin da ake ciki ne, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Kwamarade Bello Basi Fagge, mai fashin baƙi kan lamurran yau da kullum kuma ɗan gwagwarmaya a Najeriya.A latsa alamar sautin dake sama domin sauraron hirar...
Shirin ra'ayoyin ku masu saurare na wannan rana ya duba yadda rashin tsrao da kuma garkuwa da mutane ke kara yawaita a arewacin Najeriya, inda a baya-bayan nan kwamishin yan sandan jihar Zamfara da ke arewacin Najeriya ya sanar da cafke 'dan majalisar dokoki da hakimi tare da tsohon shugaban karamar hukumar Kaurar Namoda bisa zarginsu da hannu dumu dumu cikin ayyukan garkuwa da mutane domin karbar kuɗin fansa. Wannan al'amari ya sake tabbatar da zargin da ake yi wa wasu daga cikin shugabanni a Najeriya dangane da taka muhimmiyar rawa a matsalolin tsaron da suka addabi al'ummar ƙasar.Me za ku ce kan wannan lamari?Wane darasi ya kamata al'umma su koya?Wace mafita ce mafi dacewa a bi wajen magance matsalolin tsaron dake tagayyara jama'a?Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin, tare da Nasiruddeen Muhammad
Kwamishinan 'yan sandan jihar Zamfara dake Najeriya ya bayyana kama 'dan majalisar dokoki da hakimi tare da tsohon shugaban karamar hukumar Kaurar Namoda saboda zargin da ake musu da hannu dumu dumu cikin ayyukan garkuwa da mutane domin karbar diyya. Wannan ya dada fito da zargin da ake yiwa wasu shugabannin da taka rawa wajen ayyukan ta'addancin da ya addabi yankin arewa maso yamma. Dangane da wannan kamun, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Yahuza Getso, masanin harkar tsaro. Kuna iya latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar tattaunawar......
Shirin ra'ayoyin masu saurare na wannan rana ya mayar da hankali ne kan yadda kungiyoyin mayaka masu ikirarin jihadi ke kara zafafa hare-hare a kasashen yankin Sahel. Hare-haren mayakan ya fara tsallakawa zuwa kasashen Jamhuriyar Benin da Togo wadanda basu saba ganin irin haka a kasashen su ba.Ina ne kuke ganin ya kamata mahukunta su kara azama don samun zaman lafiya mai dorewa?Wace gudunmowa zaku bayar a matsayinku na al'umma don tabbatuwar tsaro a kasashen ku?Wannan shine maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau.
Hukumar tara kudaden haraji a Najeriya tace masu masana'antu a kasar sun yi asarar kudin da ya kai kusan naira triliyan 2 bara sakamakon faduwar darajar naira. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Hukumar kididdiga ta kasar ke cewa ma'aikata dubu 30 ne suka rasa ayyukansu saboda durkushewar ma'aikatun da suke aiki. Dangane da wanan labarai mai tada hankali, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ahaji Ali Madugu, mataimakin shugaban kungiyar masu masana'antu a Najeriya. Kuna iya latsa alamar sauti domin jin yadda zantawar ta su ta gudana...
Shirin ‘Muhallinka Rayuwarka' na wannan mako zai yi dubi ne kan shirin gwamnatin Najeriya na ɓullo da tsarin biyan haraji kan masu gurbata muhalli ta wajen ayyukan da suke gudanarwa, wanda a turance ake kira carbon tax. Kuma ana sa ran wannan harajin zai tursasa wa masana'antu da ke gurbata muhalli yin takatsantsan. Wannan sabon haraji dai har yanzu ba'a gama tantance jadawalin yadda za'a aiwatar da shi ba, amma kwararru a fannin na ta kira ga jama'a da su yi shirin rungumar sa, bayan da suka ce gwamnati na yin tsare-tsare ne don fito da kowa zai biya haraji daidai da yawan hayaƙi mai gurɓata muhalli da yake fitarwa.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Machael Kuduson.......
A wannan mako, shirin ya mayar da hankali ne kan yadda tsadar kuɗin wutar lantarki ke gurgunta harkokin karatu a manyan makarantun Najeriya.Kamar yadda aka sani, harkokin gudanarwar yau da kullum na manyan makarantu ba za su taɓa yiwu wa yadda ya kamata ba, muddin babu ingantacciyar wutar lantarki. To sai dai, baya ga rashin tsayayyiyar wutar a kusan manyan makarantun Najeriya, wata matsalar kuma ita ce ta tsadar wutar a sakamakon ƙarin farashin kuɗin wutar lantarki da gwamnatin ƙasar ta yi.Wannan dalili ne ya sanya ƙungiyar shugabannin jami'o'in Najeriya, ta yi kashedin cewa jami'o'in tarayyar ƙasar aƙalla 52 ka iya durƙushewa nan ba da jimawa ba, a sakamakon tsadar kuɗin wutar.Shugabannin Jami'o'in na Najeriya, sun yi wannan gargaɗi ne bayan wani sabon ƙari na kashi 300 da aka yi musu a kwanakin baya.Kuna iya latsa alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin...
In this episode of Talk Property To Me, real estate expert Aaron Downie joins Brad East to unpack the nuances of investing in houses versus apartments. As an experienced investor with a keen eye for market dynamics, Aaron offers practical insights on the hotly debated topic of real estate investing. Discover the key factors to consider when choosing between houses and apartments, such as location, market trends, rental yields, and long-term appreciation potential. Learn from real-world examples and expert analysis to find the investment strategy that works best for you. Whether you're a seasoned investor or just starting, this video will provide valuable tips and strategies to enhance your portfolio. Don't miss out on the opportunity to gain a deeper understanding of the real estate market and maximize your returns. Join our exclusive Facebook group for ongoing support and expert advice on Australian finance and real estate. → https://www.facebook.com/groups/talkpropertytome Follow our podcast instagram here → https://www.instagram.com/talkpropertytomepodcast/ Subscribe to our channel for more expert advice on real estate investing, market trends, and financial growth strategies. Hit the notification bell so you never miss an update! Timestamped summary of this episode: 00:00:13 Debunking the Myth: Houses vs. Apartments as Investments Exploring the misconception of only buying houses as an investment strategy, highlighting the importance of market analysis and investment strategy in property investment. 00:01:55 Pros and Cons of Apartments vs. Houses Discussing the affordability and lower entry price of apartments, maintenance considerations, rental yield, amenities, and capital growth in comparison to houses. 00:04:23 Considerations for Apartment Investment Exploring factors like body corporate fees, maintenance costs, and historical capital growth rates in apartments, while considering future trends and market dynamics. 00:06:21 Size and Investment Potential of Apartments Examining the size differences between apartments and houses, and showcasing a successful investment case of a large apartment with significant returns. 00:07:38 Advantages of Houses as Investments Highlighting the capital growth, land ownership, space, privacy, and maintenance costs associated with investing in houses over apartments. 00:09:39 Luxury Amenities in Property Buildings Discussion on the cost and benefits of properties with luxury amenities like teppanyaki bars and cinemas for renters and owners. 00:11:14 Best Performing Suburbs in Australia Analysis of the highest performing suburbs in Australia over the past twelve months, with significant growth rates in Gumdale, Ellen Grove, Keilor East, and Rosebud. 00:13:45 Top Growth in Apartment Suburbs Highlighting the substantial growth in apartment suburbs like Tennyson, Grange in Brisbane, and Doncaster East in Melbourne, with impressive annual growth rates. 00:15:43 Worst Performing Suburbs Exploring the decline in suburbs like O'Connor and Wannan in Canberra for houses, and Forrest in Canberra, East Lakes in Sydney, and Macquarie Park for apartments over the last twelve months. 00:17:00 Decade of Growth in Suburbs Insights into the top performing suburbs over the past ten years, showcasing significant increases in areas like Byron Bay, Bright in Victoria, Suffolk Park, and Kingscliffe. 00:19:46 Top Performing Suburbs for Apartments Discussion on top-performing suburbs for apartments, including Jindabyne and Kings Cliff, with notable growth percentages over the years. 00:21:24 Factors Influencing Property Prices Exploration of factors like infrastructure, population growth, and market demand affecting property prices in different suburbs. 00:22:27 Apartments as Valuable Assets Highlighting the long-term value of apartments, emphasizing diversification and low maintenance costs as key advantages. 00:23:24 Trend of Downsizing to Apartments Observations on the trend of downsizing to apartments, particularly by the aging population, driving demand and growth in certain Sydney suburbs. 00:24:47 Diversification in Property Investment Encouragement for diversifying investment portfolios, considering apartments as a viable option for first-time investors. ABOUT THE HOST BRAD EAST Brad East is the Managing Director of Wisebuy Home Loans. Brad is an award-winning mortgage broker and has helped thousands of clients gain finance to purchase properties. Wisebuy Home Loans is the go-to mortgage brokerage for clients wanting out-of-the-box applications approved. Website → https://wisebuygroup.com.au LinkedIn → https://www.linkedin.com/in/newcastlemortgagebroker/ Instagram → https://www.instagram.com/bradeast_mortgagebroker/ Facebook → https://www.facebook.com/bradeastofficial #realestate #propertyinvestment #podcast #finance #propertypodcast
A WANNAN SHIRIN ZAKU KASANCE TARE BABBAN BAKO MALAM AMINU IBRAHIM DAURAWA, BABBAN MALAMIN ADDINI, KUMA SHUGABAN HUKUMAR HISBAH TA JIHAR KANO, NAJERIYA. MUN TATTAUNA BATUTUWA MASU MAHIMMMACI DA SUKA SHAFI RAYUWARSA, KARATUNSA, TSARIN AIKIN DA'AWARSA DA KOYARWARSA, AIKINSA NA HUKUMAR HISBAH, DA KUMA WASU BABUTUWA DA SUKA SHAFI AL'UMMA NA YAU DA KULLUM. #nigeria #hausa #podcast #niger #ghana #hisba #daurawa