POPULARITY
Shirin 'Duniyar Wasanni' a wannan makon ya yi duba ne kan wasan ƙarshe na gasar zakarun Turai da aka yi a ƙarshen mako tsakanin PSG ta Faransa da kuma Inter Milan, inda PSG ta samu nasarar lashe gasar bayan da ta zazzaga wa Inter Milan ƙwallaye biyar. Wannan ne dai karon farko da PSG ta lashe wannan kofi, kuma karo na farko da wata ƙungiya daga Faransa ta lashe shi tun bayan Marseille a shekarar 1993.Ku latsa alamar sauti don sauraron shirin tare da Khamis Saleh............
Shirin Lafiya Jari Ce a wannan makon shirin ya mayar da hankali kan yadda wani bincike ke gano cewa yawan shan suger ko kuma sikari a lokutan ƙuriciya na taka muhimmiyar rawa wajen haddasawa mutum ciwon suga a lokacin girma. Wannan cuta ta suga ko kuma Diebetes na cikin jerin cutukan da ke barazana ga rayukan ɗimbin mutane musamman a sassan Najeriya da tuni cutar ta fara zama ruwan dare mai gama duniya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu............
Wannan shiri zai mayar da hankali ne kan yadda zamani ke tasiri akan salon magana ko gagara gwari a tsakanin al'umar hausawa, musamman ma matasa masana da dattawa da suka jiya suka ga yau sun bayyana dalilai da suka sanya irin wannan salo na zance, wanda ke nuna ƙwarewar harshe ke neman ɓacewa a tsakanin al'uma da gudummawar da kowanne ɓangare ke bayarwa wajen disashewar wannan fiƙira ta harshe.
Kungiyar kasashen Afirka ta Yamma ta ECOWAS ta bayyana shirin kafa sabuwar rundunar hadin kai wadda za ta dinga yaki da yan ta'addan da suka addabi yankin. Wannan na da cikin shirin shugabannin yankin na dakile ayyukan ta'addanci, da suka ƙi ci suka ƙi cinyewa.Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Janar Kape Alwali Kazir mai ritaya a dangane da wannan shiri.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Babban Hafsan tsaron Najeriya, Laftanar Janar Christopher Musa ya ce baya ga amfani da makamai wajen tinkarar mayakan Boko Haram, farfado da Tafkin Chadi zai taimaka wajen samarwa jama'ar yankin sana'oi. Wannan ya biyo bayan ziyarar aikin da ya kai Maiduguri bayan kazaman hare haren da boko haram ta kai cibiyoyin soji.Dangane da wannan bukatar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da wani mutumin yankin, Farfesa Sheriff Muhammad Almuhajir.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Shin ko kun san muhimmancin kula da lafiyar ƙwaƙwalwa kuwa? Wannan tambaya ce mai matuƙar muhimmanci, lura da cewa yanzu haka akwai ɗimɓin mutane da ke fama da wannan matsala a sassan duniya. Yayin da wasu ke kira wannan lalura a matsayin hauka, masana kuwa na cewa hatta shiga yanayi na damuwa ko da ƙuncin rayuwa na iya haddasa wannan matsalar.Shin ko wace irin kulawa ku ke bai wa lafiyar ƙwaƙwalwa?Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a.
Gwamnatin sojin Jamhuriyar Nijar ta bai wa hafsan sojojin ƙasar umarnin cewar babu wanda zai tafi ritaya a cikin wannan shekarar, sakamakon wasu matsalolin tsaron da kasar ke fuskanta. Dangane da wannan umarni, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Sani Yahya Janjuna, mai sharhi akan lamuran yau da kullum, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana akai.
Shirin a wannan makon zai tattauna ne a kan Camfi, da kuma yadda ya kasance a zamanin kaka da kakanni, da rawar da ya taka a waccan lokaci da kuma yadda yake shafar rayuwar jama'a a lokacin da muke.Duk da ƙarancin lokaci, shirin Al'adunmu na gado zai yi ƙoƙarin zayyana rabe-raben al'adar ta Camfi ko kuma wasu daga ciki.
Yayin da a yau aka ƙaddamar da makon rigakafi a duniya, Hukumomi a Najeriya da kuma Unicef, sun yi gargaɗin cewa yanzu haka nau'ukan cutar shan'inna har guda 17 da suka yaɗu a cikin jihohi 8 na ƙasar. Wannan dai babban ƙalubale ne ga sha'anin kiwon lafiya, bayan da aka shelanta kawo ƙarshen cutar tun 2020.Shin ko meye dalilan sake ɓullar wannan cuta a Najeriya?Waɗanne matakai ya kamata a ɗauka domin shawo kanta?Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin masu saurare.
Shirin Lafiya Jari ce tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan ƙaruwar masu kamuwa da cuta mai karya garkuwar jiki ko kuma HIV AIDS ko sida tsakanin matasan Ghana a shekarun baya-bayan nan, wadda masana ke ɗora alhakin yawaitarta kan rashin ɗaukar matakai. Wannan ƙaruwar alƙaluma na zuwa a dai dai lokacin da duniya ke ganin ƙarancin magunguna rage kaifin cutar sakamakon matakin Amurka na zaftare tallafin da ta ke bayarwa ƙarƙashin ƙungiyar USAID.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shiri.
Alƙaluma na nuni da cewa amfani da kuɗaɗen Crypto na daɗa samun karɓuwa a ƙasashen Yankin Kudu Da Saharar Afrika musamman ma Najeriya, inda a bara wani rahoto ya ce a tsakanin 2023 zuwa 2024, yawan kuɗaɗen Crypton da aka yi hada-hadarsu ya kai na Dalar Amurka biliyan 59. Wannan ya sa wasu ƙwararru bai wa mahukuntan Najeriyar shawarar, kamata yayi su rungumi sauyin domin amfana da shi a maimakon ƙoƙarin daƙile kasuwar Crypton, saboda illolin da suka ce na tattare da ita. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Nura Ado Suleiman da Dakta Ƙasim Garba Kurfi, masanin tattalin arziƙi a Najeriya..............
Shirin “Ilimi Hasken Rayuwa” namu na wannan mako, ya yada zango ne a tarayyar Najeriya, inda shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya rattaba hannu kan ƙudurin samar da sabuwar jami'a kimiyyan lafiya da fasaha ta tarayya wato Federal University of Health Science and Technology a garin Tsafe na Jihar Zamfara, bayan tsallake dukkan matakan majalisa dokokin ƙasar. Wannan saka nannu na shugaban ƙasar ya yi zai bada damar ƙara inganta harkan kiwon lafiya ta hanyar samar da kwararru.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Nura Ado Suleiman.........
Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali kan al'adar nan ta naɗin sarauta da wasu masarautun gargajiya ke yi ga ƙabilun da ba su ke da masarautar ba, wanda hakan ya biyo bayan sabbin naɗe-naɗe da ɗaya daga cikin manyan masarautun ƙabilar gwari a arewacin Najeriya ta yi wa wasu manyan shuwagabannin al'ummar fulani a jihar Neja. Wannan dai ba shi ne karon farko ba da ake samun masarautun Hausa da Fulani da ma wasu masarautun a yankin kudanci da kuma arewacin Najeriya ke baiwa ƙabilun da ke zaune a masarautar sarauta ba, abin da shirin Al'adu na wannan mako ya yi nazari akai tare da jin inda hakan ya samo asali da kuma alaƙar da ke tsakanin al'adun ƙabilar gwari da fulani daga masana al'adu da masarautu.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.
EXCLUSIVE INTERVIEW- Asher Fearn-Wannan AFLW draft prospect #aflw #footy
A Najeriya rahotanni sun bayyana cewar yanzu haka shugaba Bola Ahmed Tinubu ya umarci dukkanin ministocinsa da suka fito daga yankin arewacin ƙasar su koma jihohin da suka fito domin kare manufofinsa da kuma bayyana irin ayyukan da yake yi. Wannan na zuwa ne a dai dai lokacin da shugaban ke ganin matsananciyar suka daga ɓangaren adawa da kuma ganin tarin barazana musamman kan salon kamun ludayin gwamnatinsa.Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Harsanu Yunusa Guyaba.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.
Ƙasashen duniya sun bayyana matukar rashin amincewarsu da buƙatar shugaban Amurka Donald Trump, na ƙwace Gaza da kuma mayar da Falasdinawa wasu ƙasashe domin gina wurin shaƙatawa a ƙasarsu. Wannan matsayi ya gamu da suka daga ƙasashen duniya da dama ciki harda Majalisar Ɗinkin Duniya. Bashir Ibrahim Idris ya tatatuna shirin da Ambasada Abubakar Cika, tsohon Jakadan Najeriya a kasar Iran. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana.........
Ƙasashen duniya na ci gaba da bayyana damuwa dangane da shirin shugaban Amurka Donald Trump na dakatar da ayyukan hukumar USAID wadda ke taimakawa ƙasashen duniya . Wannan hukuma dai na taka gagarumar rawa a bangarori da dama a ƙasashe masu tasowa irin su Najeriya.Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Abba Gambo, mai bai wa gwamnonin Najeriya shawara a kan harkokin noma dangane da tasirin matakin a kan noman ƙasar.Latsa alamar sauti domin sauraren yadda tattaunawar ta kasance....
Hukumomin sojin Jamhuriyar Nijar sun gabatar da wata sabuwar dokar da zata hukunta baƙin da ke shiga cikin kasar ba tare da halartattun takardu ba. Wannan ya biyo bayan zarge zargen da ake na samun wasu baki da ke yiwa kasar zagon kasa. Domin tattauna wannan batu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai sharhi a kan Nijar, Abdoul Naseer, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
A wani yanayi da ba safai aka saba gani ba, mahukuntan Nijar sun sallami tuɓaɓɓun mayaƙan Boko Haram aƙalla 124 ciki har da ƙananan yara 44, waɗanda aka basu horan sauya ɗabi'u don komawa rayuwar fararen hula. Wannan shi ne karon farko da ake ganin irin hakan, tun bayan makamancin yunƙurin da hamɓararren shugaban ƙasar Bazoum Muhammad ya yi watanni ƙalilan gabanin hamɓarar da shi.Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi a cikin shirin...
Kamar yadda labari ya karaɗe kafafen yada labarai, ƙaasa da mako guda bayan da hukumar kwastan a Najeriya ta sanar da buɗe shafin yanar gizo don aikewa da takardun neman ɗaukar jami'ai kimanin dubu 4, sama da masu neman wannan aiki dubu dari 5 ne suka gabatar da buƙatunsu. Wannan al'amari ne da ke faruwa a kowace ma'aikata a duk lokacin da aka sanar da buƙatar ɗaukar ma'aikata.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Abida Shu'aibu Baraza.
A ranar Laraba ne shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatar da kasafin kudin ƙasar na shekarar 2025 na naira Tiriliyan 47.9. Sai dai wani batu da ya haifar da muhawara a tsakanin ‘yan Najeriya dangane da kasafin kuɗin na baɗi, shi ne yadda aƙalla kaso 30 zuwa 32 na yawan kuɗaɗen za su tafi a biyan basuka ko kuma kudin ruwan basukan, kwatankwacin naira tiriliyan 15 da biliyan 800, adadin da ya zarce yawan kudaden da aka warewa tsaro, ilimi, lafiya da manyan ayyuka.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin tare da Kabiru Mohammed Dan Bauchi...
Tsohon mataimakain shugaban Najeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a zaben 2023 da ya gabata Atiku Abubakar da kuma ɗan takarar LP a 2023 Peter Obi na shirin haɗewa domin kawar da gwamnatin APC wadda a cewarsu ta gaza, lamarin da ke zuwa tun kafin kakar zaɓen na shekarar 2027. Sai dai a martaninta, jam'iyyar APC ta ce babu wata haɗaka da za ta iya taka wa shugaba mai ci birki.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin...
Kamar yadda aka saba, RFI Hausa na bai wa masu saurare damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwa da dama da ke ci musu tuwo a ƙwarya. Majalisar dattawar Najeriya ta amince da wani kuɗirin doka da ya haramta fitar da duk wata masara mai yawa da ba'a sarrafa ta ba daga ƙasar zuwa ƙasashen waje, kuma ta tanadi hukuncin ɗaurin shekara guda ga duk wanda ya yi kunnen ƙashi.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau.Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyin mabanbanta..
Mataimakin shugaban ƙasa kuma ɗan takarar jam'iyya mai mulki a Ghana, Mahamudu Bawumia ya amince da shan kaye a zaɓen ƙasar, inda ya taya tsohon shugaban ƙasa John Mahama murnar lashe zaɓen. Wannan ya biyo bayan zaɓen shugaban ƙasar da aka yi a Asabar ɗin ƙarshen mako 7 ga watan Disamba, wanda rahotanni suka tabbatar da cewa ya gudana cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya.Shin ya ku ka kalli yadda zaɓen na Ghana ya gudana?Me za ku ce kan yadda Bawumia ya amince da shan kaye tun kafin a fitar da sakamakon zaɓen?Wane darasi ku ke ganin ƴan siyasa a yankunanku za su koya daga zaɓen Ghana?Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin
Mazauna yankunnan jihar Zamfara da ke arewacin Najeriya na ci gaba bayyana irin halin kuncin rayuwa da suka samu kansu sakamakon yadda suke biyan ƙudi ga ƴan bindiga kafin su yi noma a daminar da suka gabata, yanzu kuma lokacin girbi ƴan bindigar sun hana su zuwa girbi da kwaso amfanin gonar sai sun biya.Wannan matsala ta yi sanadiyar talauta akasarin mutanen da ke wannan yankin. Dangane da wannan batu ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da wani mazaunin yankin da ya bukaci a sakaya sunansa saboda dalilai na tsaro, kuma ga abinda ya shaida masa.
A Najeriya, kwanan nan ne kotu ta karbe wani rukuni mai ƙunshe da gidaje 753 mallakin wani tsohon gwamnan babban bankin ƙasar, nasara mafi girma da hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa ta'annati ta taɓa samu a cikin sama da shekaru 21 da kafuwarta. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin tare da Oumaru Sani:
Kamar yadda aka saba, RFI Hausa na bai wa masu saurare damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwa da dama da ke ci musu tuwo a kwarya. Majalisar Ɗinkin Duniya ta ware ranar 3 ga watan Disambar kowacce shekara a matsayin ranar masu buƙata ta musamman, wato mutane da ke rayuwa da wata naƙasa a fadin duniya.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau.Ku latsa alamar sauti domin sauraren shirin tare da Hauwa Halliru Gwangwazo:
Shirin Duniyar Wasanni na wannan mako yayi duba ne kan yadda aka kammala wasanni sojoji na nahiyar Afrika. Wannan ne dai karo na biyu da tawogogin ƙasashe 20 suka fafata a babban birnin tarayyar Najeriya Abuja, inda kuma tawagar ƴan wasan sojoji ta Najeriya ta zamo zakara, bayan da ta samu nasarar lashe lambar zinari 114 da azurfa 65 sai kuma tagulla 55 a jumlace ke nan ta samu lambobin yabo 234. Ƙasar Aljeriya ke bi mata a matsayin na 2 da lambar zinari 53 da azurfa 22 sai kuma agulla 21, a jumlace ita kuma ta samu lambobin yabo 96, Kenya ce tazo ta 3 bayan da ta lashe lambobin yabo 50.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin tare da Khamis Saleh.......
Hukumar Kasuwanci ta duniya WTO ta bai wa tsohuwar ministan kudin Najeriya Ngozi Okonjo Iweala wa'adi na 2 na shekaru 4, yayin da ta kawo karshen wa'adinta na farko. Wannan ya biyo bayan kasancewarta 'yar takara daya tilo da ta sake neman mukamin.Domin tasirin wannan nadi da kuma kalubalen dake gabanta, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Isa Abdullahi, masanin tattalin arziki a Najeriya.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Kusan shekara guda da rabi da juyin mulkin da sojoji suka yi a Jamhuriyar Nijar, har ya zuwa yanzu babu wani shiri daga sojojin na mayar da mulki ga fararen hula. Wannan ya sa wasu daga cikin jama'ar ƙasar gabatar da buƙata ga sojoji da su sake tunani akai domin bai wa jama'a damar zaɓin shugabannin da suke so. Domin tattauna wannan batu, Bashir Ibrahim Idris ya tintibi Alhaji Adamu Muhammad Madawa, daya daga cikin shugabannin ƴan Nijar mazauna Najeriya. Ku latsa alamar sauti dominjin yadda zantawarsu ta gudana........
Shirin Duniyar Wasanni a wannan makon ya yi duba ne kan irin gudummawar da cibiyoyin horar da matasa wasan kwallon ƙafa ke bayarwa wajen zakulo matasan ƴan wasa da horar da su a Nigeria. Wannan dai wani bangare ne na gudummawarsu ga ci gaban wasan kwallon ƙafa a Nigeria, tsofin ƴan wasan tawagar Super Eagles na ƙasar, sun fara kafa cibiyoyi masu zaman kan su, da su ke zakulowa tare da horar da matasa don yin fice a harkar ta kwallon kafa. Irin wadannan cibiyoyin horar da matasa wasan na kwallon kafa da a turance ake kira Football Academy, kan shiga birane da karkara don tuntubar ƙanana da matsakaitan club-club, domin samun ƴan wasan daga wajen su da za a yi rijistarsu a wannan cibiya.Pascal Patrick, tsohon ɗan wasan Super Eagles kuma shugaban Hukumar kwallon kafa ta NFA a jihar Bauchi kana co-odinetan tawagar Super Eagles na Nigeria, na daya daga cikin tsofaffin ƴan wasan ƙasar da suka kafa irin wannan cibiya a jihar Bauchi.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh.......
Babbar mai shari'a a Najeriya tare da Hukumar Kula da Ayyukan Shari'a ta NJC sun kaddamar da bincike a kan yadda wasu alkalai a jihar Rivers suka dinga bada hukunce hukunce da ke karo da juna dangane da zaben kananan hukumomin da aka yi a jihar. Wannan umarni na zuwa ne bayan an samu irin wannan matsala a jihar Kano. Saboda haka Bashir Ibrahim Idris ya tintibe masanin ɓangaren shari'a Farfesa Shehu Abdullahi Zuru na jami'ar Baze dake Abuja. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana.........
Mazauna yankin Arewacin Najeriya sun kwashe kwanaki 7 ba tare da hasken wutar lantarki ba, abinda ya yi sanadiyar durkushewar jama'a musamman masu sana'oin da suka dogara ga wutar. Wannan matsala na barazana ga rayuwa da kuma tattalin arzikin yankin. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da daya daga cikin dattawan yankin, Alhaji Sule Ammani Yarin Katsina. Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar zantawarsu ta su........
Bankin duniya ya yaba da sauye sauyen tattalin arzikin da gwamnatin Najeriya ke aiwatarwa, tare da bai wa hukumomin ƙasar shawarar kar su kuskura su koma da baya. Wannan na zuwa ne a dai dai lokacin da talakawan ƙasar ke kokawa saboda ƙuncin rayuwa. Dangane da wannan matsayi Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki Dr Kasum Garba Kurfi. Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar zantawarsu..............
Shirin Duniyar Wasanni a wannan lokaci yayi duba ne kan danbarwar da aka samu tsakanin Najeriya da Libya. A makon daya gaba ne dai aka fara kai ruwa rana tsakanin bayan da tawagar Super Eagles ta Najeriya ta yi tattaki zuwa Libya don karawa da takwaransu ta ƙasar a wasa na biyu na neman gurbin zuwa gasar lashe kofin Afrika da za ayi a Morocco a shekara mai zuwa. Wannan al'amari dai ya haifar da cece-kuce a duniyar kwallon ƙafar, ganin yadda Super Eagles ta zargi hukumomin kwallon ƙafar Libya da yin watsi da su a filin jirgin sama ba tare da ance kuci kanku ba.Ku latsa alamar sauti don jin cikakken shirin tare da Khamis Saleh.....
Bankin Duniya, ya ce Najeriya da wasu ƙasashe da dama masu tasowa, za su iya shafe tsawon shekara ɗari a nan gaba kafin su yi nasarar rage kaifin talauci da ke addabar al'ummominsu. Wannan gargaɗi na Bankin Duniya na zuwa ne a daidai lokacin da bayanai ke cewa kusan a kowace rana ta Allah ana samun karuwar mutanen da suka dogara da malauna ne domin samun abin da za su ci da kuma iyalansu.Shin, ko yaya za ku bayyana matsayin talauci ko fara a inda ku ke rayuwa?Ko kun gamsu da irin matakan da hukumomin ƙasashen ke ɗauka domin rage kaifin talauci a tsakanin al'umma?Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin
A karo na 4 tun bayan hawa karagar mulkin shugabancin Najeriya da Bola Ahmed Tinubu yayi, kamfanin man NNPCL ke sanar da ƙara farashin man fetur, inda yanzu farashin ya koma naira 998 a Lagos, ya yin da Abuja kuma ya koma naira dubu 1 da naira 30. Wannan ya sa talakawan ƙasar sake gabatar da korafinsu saboda yadda farashin zai sake shafar kayan masarufi. Dangane da wannan sake karin, Bashir Ibrahim Idris ya tatauna da Comrade Umar Danjani Hadejiya. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tasu......
A Najeriya, yayin a ke fama da matsalar tattalin arziki da tsanantar harkokin rayuwa, alkaluma na tabbatar da cewa bankunan ƙasar na ci gaba samun gagarumar riba a kowace rana ta Allah. Shin ko meye dalilin wannan gibi tsakanin bankuna da kuma al'umma? Wane gyara ya kamata ayi domin tabbatar da cewa arzikin kasa na zagayawa a cikin al'umma? Wannan shine maudu'in da masu sauraro suka tattauna akai.
A Najeriya, yanzu haka wasu sun fara nuna fargaba a game da yadda tsarin dimokuradiyya ke gudana a kasar, musamman lura da yadda da zarar aka gudanar da zaben kananan hukumomi, to ko shakka babu jam'iyyar da ke rike da kujerar gwamna ce za ta lashe zaben babu tantama. Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da aka bai wa kananan hukumomin damar cin gashin kansu.Abin tambaya anan shi ne, me ya sa a kullum jam'iyya mai rike da mukamin gwamna ce ke lashe zaben kananan hukomomi a Najeriya?Meye tasirin hakan game da fatan da ake da shi na ganin cewa al'umma ta morewa tsarin dimokuradiyya daga tushe?Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a
Yau 7 ga watan oktoban shekarar daya kenan da mayakan Hamas suka kaddamar da hare-hare a Isra'ila, inda suka kashe mutane 1 da 200 tare da yin garkuwa da wasu akalla 150. Wannan ya fusata Isra'ila inda ta mayar da martani ta hanyar kashe sama da mutane kusan dubu 43 a yankin Gaza, tare da yaduwar wannan rikici zuwa kasashen Lebanan da Iran.Shin me za ku ce a game da wannan lamari da ke kara jefa cikin zaman zullumi?Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin
Kamar dai kowane mako, a yau juma'a ma jaridar Aminiya da ake wallafa ta a Najeriya ta sake fitowa ɗauke da dimbin labarai da suka shafi fannoni daban nan na rayuwa. Kuma Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Muƙaddashin Editan jaridar Muhammad Amin Ahmed domin jin karin bayani dangane da labaran da suke ɗauke da su a wannan karo. domin sauraron cikakken shirin, a latsa alamar sauti.
Yamai babban birnin Jamhuriyar, ya fara karɓar baƙuncin taron ƙwararru da saurann masu ruwa da tsaki kan matsalar sauyin yanayi da ta shafe yankin yammacin Afrika. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da sassan yankin na Yammacin Afirka da Sahel ke fuskantar Iftila'in Ambaliyar mafi muni da aka taɓa gani cikin aƙalla shekaru 20, kamar yadda aka gani a garin Maiduguri, inda a baya bayan nan saukar ruwan sama ya janyo tumbatsar dam ɗin da ya fashe, lamarin ya haddasa mummunar ambaliyar da ta mamaye sassan birnin da dama.Wane hali ake ciki a garin na Maiduguri bayan iftila'in da ya auku?Wadanne dabaru ya dace a bi wajen daƙile sake aukuwar haka, ko kuma rage girman barazanar da aka gani, ta hanyar karkatar da tarin ruwan da ke ambaliya zuwa ga amfanin jama'a?Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin
A wannan makon shirin zai mayar da hankali kan cutar borin gishiri ko kuma kumburin da mata ke fama da ita yayin da suke da dauke da juna biyu, wacce kuma a lokuta da dama kan haddasa asarar rayuka. Wannan cuta a Jamhuriyar Nijar na daga cikin wacce ke ciwa hukumomi tuwo a kwarya ganin yadda mata sama da dari biyar da 30 cikin kowace mace dubu daya ne kamuwa da wannan cuta, kuma sama da 50 ke rasa ransu a sanadiyarta. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu.....
Shirin 'Kasuwa A kai Miki Dole' na wannan mako tare da Ahmed Abba ya duba yadda kasuwancin kifi a Najeriya ya ke neman ya gagari masu sana'ar saboda tsadar abincin da ake kiwon kifi da shi da farashin sa ya ƙaru, lamarin da ke barazana musamman ga ƙanana da matsakaitan ƴan kasuwa a fannin. Farashin buhun abincin kifi ya tashi daga N18,000 a shekarar 2023 zuwa N36,000 a wannan shekarar, wanda ya nuna karuwar kashi 100 cikin 100 a fadin Najeriya.Wannan al'amari ya yi kamari a yankin Neja Delta da suka yi kaurin suna a noman kifi.
Shirin Tambaya da Amsa tare da Nasiru Sani a wannan mako ya amsa wasu daga cikin tambayoyin da aka aika mana, Shirin ya amsa tambaya kan yadda neman ƙarin bayani da wani mai sauraro ya yi kan zubu ko kuma yanayin siyasar Birtaniya dama banbancinta da siyasar da ake gani a ƙasashen da ta mulka.Wannan da sauran tambayoyi na tafe a cikin shirin na wannan mako.
Shirin Muhallinka Rayuwarka na wannan mako ya yi duba ne kan wata hadaka da aka samu tsakanin gwamnatin jihar Kogi da kuma katafaren kamfanin nan na sarrafa amfanin gona a Najeriya Wato OLAM, domin farfado da tsarin aikin Malaman Gona ta hanyar horar da wadanda jihar ke da su tare da kara yawansu a kokarin da bangarorin biyu ke yi na shirya samun ninkin amfanin gonar da za a rinka nomawa a jihar ta Kwara.
Shirin mu zagaya duniya na wannan mako ya duba manyan labaran da suka faru a wannan mako ciki kuwa har da addin mutanen da hare-haren ta'addanci suna kashe a cikin shekaru biyar a Najeriya Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Nura Ado Sulaiman
A WANNAN SHIRIN ZAKU KASANCE TARE BABBAN BAKO MALAM AMINU IBRAHIM DAURAWA, BABBAN MALAMIN ADDINI, KUMA SHUGABAN HUKUMAR HISBAH TA JIHAR KANO, NAJERIYA. MUN TATTAUNA BATUTUWA MASU MAHIMMMACI DA SUKA SHAFI RAYUWARSA, KARATUNSA, TSARIN AIKIN DA'AWARSA DA KOYARWARSA, AIKINSA NA HUKUMAR HISBAH, DA KUMA WASU BABUTUWA DA SUKA SHAFI AL'UMMA NA YAU DA KULLUM. #nigeria #hausa #podcast #niger #ghana #hisba #daurawa