Podcasts about wannan

  • 29PODCASTS
  • 368EPISODES
  • 11mAVG DURATION
  • 5WEEKLY NEW EPISODES
  • Jul 16, 2026LATEST

POPULARITY

20192020202120222023202420252026


Best podcasts about wannan

Latest podcast episodes about wannan

Bakonmu a Yau
Tattaunawa kan matsalar hare-haren ƴanbindiga a makarantun Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jul 16, 2026 3:35


Matsalar tsaro ta hare-haren da ‘yan ta'adda kan kai wa makarantu ko ɗalibai a sassan Najeriya, na ci gaba da ci wa  al'ummar ƙasar tuwo a ƙwarya, la'akari da cewar ko a baya bayan nan, ‘yan bindiga sun kai hari tare da sace wasu ɗaliban wata Sakandare a ƙaramar hukumar Dekina da ke jihar Kogi. Wannan ya zo ne bayan hare-haren da a makwannin baya makarantun suka fuskanta a jihohin Oyo da kuma Borno. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da shugaban ƙungiyar Malaman Makarantu ta Najeriya, Comrade Audu Titus Amba. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

oyo haren kogi borno wannan najeriya
Dandalin Fasahar Fina-finai
Manyan labaran da suka wakana a wannan mako a duniyar fina-finai

Dandalin Fasahar Fina-finai

Play Episode Listen Later Jul 11, 2026 20:01


A cikin shirin na wannan rana zamu zagaya da ku masana'antun shirya fina-finai don tsamo muku manyan labaran da suka wakana a wannan mako. Akwai mu da yadda aka fitar da jerin fina-finan da suka fi jan hankalin ƴan kallo a watanni 6 na wannan shekara daga ƙasar India. Muna tafe da yadda muhawara ta barke a shafukan sada zumunta, kan yadda jarumai daga jihar Plateau suka mamaye Kanywood, yayin da ake da karancin jarumai daga jihar Katsina.

plateau suka mako muna katsina wannan akwai duniyar
Bakonmu a Yau
Dakta Sani Gambo kan taron ƙasashen ƙungiyar AES da Rasha

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jul 8, 2026 3:30


A wannan Laraba ake fara taron tuntuɓa tsakanin ƙasashen ƙungiyar AES wato Mali, Nijar da Burkina Faso da kuma  ƙasar Rasha a gefe guda a Yamai fadar gwamnatin  Nijar, inda ake sa ran za su tattauna batutuwan da suka shafi tsaro, tattalin arziki da kuma makamashi. Wannan ne karo na biyu da ake gudanar taron bayan makamancinsa da aka yi a birnin Moscow na Rasha a watan Afrilun 2025, kuma ya na zuwa a daidai lokacin da mayaƙa masu ikirarin jihadi suka zafafa kai hare-hare a waɗannan ƙasashen na Sahel. A kan wannan Oumarou Sani ya tattauna da Dakta Sani Gambo malami a jami'ar Andre Salifou da ke Zinder a Jamhuriyar Nijar, game da ci gaban da hakan zai kawo ga ƙasashen biyu. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyi kan ziyarar da wakilan Vatican suka kai wa Sarkin Musulmin Najeriya

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Jul 8, 2026 10:52


Mai Alfarma Sarkin Musulmin Najeriya Muhammadu Sa'ad Abubakar na uku, ya ce mutunta addinan juna, daina furta kalaman ƙiyayya ko tsatsauran ra'ayi, abubuwa ne da za su iya taimakawa ta fannin kyautata zamantakewa a tsakanin al'umma. Wannan dai gargaɗi ne da ke ƙunshe a sanarwar da aka fitar bayan ganawar da aka yi a babban masallacin birnin Abuja tsakanin mai alfarma Sarkin Musulmin da kuma tawagar manyan jami'an Fadar Vatican ƙarƙashin jagorancin Archibishop Paul Richard Gallaghera. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Ilimi Hasken Rayuwa
Yadda makomar ilimin yaran karkara a Najeriya ke cikin rashin tabbas

Ilimi Hasken Rayuwa

Play Episode Listen Later Jul 8, 2026 10:00


A wannan makon, shirin ya nufi yankunan karkara, inda inda gine-ginen makarantu ke ci gaba da kasancewa a matsayin kango, kasancewar babu dalibai. A wasu wuraren kuma, azuzuwan sun zama fanko, yayin da matasa da yara suka ƙaurace wa shiga, ‘yan mata na fita birni yin tallace-tallace, su kuma samari na dambatawa da aikin ƙwadagon fasa duwatsu da ɗiban yashi. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da sabon rahoton hukumar UNICEF ya nuna cewa, jihohin Kano, Katsina, da Jigawa ne ke kan gaba a faɗin Najeriya wajen yawan yaran da ba sa zuwa makaranta, inda a faɗin kasar kuwa, akwai yara sama da miliyan goma sha takwas da dubu ɗari uku da makoma ta iliminsu ke cikin haɗari. Sau da yawa, wannan zargi na komawa ga gwamnati, sai dai abin tambayar shine, shin ko laifin na iyaye ne da al'umma, ko kuwa suma hukumomi akwai nasu kason? Mun ziyarci garin Meshumi da ke karamar hukumar Ungoggo a jihar Kano, inda shirin ya tarar makarantar firamare na nan a gine, amma dakin karatu ya zama kufai. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin, tare da Shamsiyya Haruna

unicef sau kano mun yadda shiga katsina rashin jigawa wannan najeriya cikin
Ilimi Hasken Rayuwa
Taron ƙaddamar da littafin tarihi na wani fitaccen matashi a Kanon Najeriya

Ilimi Hasken Rayuwa

Play Episode Listen Later Jun 30, 2026 10:02


Shirin na wannan mako ya mayar da hankali ne kan taron ƙaddamar da sabon littafin tarihin nan mai suna 'Mu San Magabata', wanda fitaccen matashin marubuci Kabiru Ahmad Kwalli ya rubuta da aka gudanar a jihar Kanon Najeriya. Taron ya haɗa masana, sarakuna, da ɗandazon al'umma domin duba yadda za a ceto tarihin ƙasar Hausa da ke shirin bacewa. Wannan littafi, kamar yadda masana da dama suka bayyana, ya zo ne a daidai lokacin da matasan yanzu ke ƙara nisanta da asalin tarihinsu. To ko me ya sa mawallafin, Kabiru Ahmad Kwalli,  ya ɗauki tsawon lokaci yana wannan bincike? Ga abinda ya shaida mana lokacin da muke zantawa da shi.

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan rawar ƙasashen Afrika a Gasar Kofin Duniya

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Jun 29, 2026 9:36


Ƙasashen Afrika 9 daga cikin 10 da ke halartar gasar cin kofin duniya ne suka samu nasarar tsallakawa zuwa zagayen ƙasashen 32 na wannan gasa da ke gudana a ƙasashen Amurka da Canada da kuma Mexico. Wannan dai shi ke matsayin babban tagomashi da nahiyar ta Afrika ta taɓa samu a irin wannan gasa ta cin kofin duniya. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Lafiya Jari ce
Ƙaruwar masu fama da cutar sikila a Jamhuriyar Kamaru

Lafiya Jari ce

Play Episode Listen Later Jun 29, 2026 10:08


A wannan makon shirin ya yi duba ne kan ƙaruwar masu fama da cutar sikila a jamhuriyyar Kamaru bayan fitar wani rahoto da ke cewa cikin shekara 1 kaɗai an tattara alƙaluman sabbin mutum dubu 6 da aka gano suna ɗauke da cutar. Wannan cuta mai alaƙa da nau'in jini, na daga cikin matakan yaƙi da ita shi ne tabbatar da gwaje-gwajen jini tun kafin aure don kaucewa haifar yara masu ɗauke da ita, ganin cewa hanya ɗaya tal ta samun masu cutar shi ne ta hanyar gado wato daga iyaye.

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan ƙaryata zargin kisan Kiristoci da MDD ta yi

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Jun 23, 2026 10:06


Tawagar da Majalisar Ɗinkin Duniya ta tura zuwa Najeriya don gudanar da bincike a game da zargin kisa, yin garkuwa da mutane da kuma tilasta wa wasu barin muhallansu saboda dalilai na addini, ta ce wannan ba gaskiya ba ne. Jagorar tawagar Farfesa Nazila Ghanea, a ƙarshen ziyarar gani da ido ta kai a ƙasar, ta ce mutane na yin waɗannan zarge-zarge ne saboda gazawar gwamnati wajen ba su kariya da kuma gaza hukunta waɗanda ke aikata laifukan. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

duniya kisan masu wannan najeriya majalisar
Bakonmu a Yau
Dakta Abdulhakeem Garba kan cikar Birtaniya shekaru 10 da ficewa daga EU

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 23, 2026 3:29


Yau ake cika shekaru 10 da ficewar Birtaniya daga cikin kungiyar ƙasashen Turai domin cin gashin kan ta wajen gudanar da harkokin mulki da kuma kasuwancin ta ba tare da sanya hannun ƙungiyar EU ba. Bayan share shekaru ana tattaunawa, Birtaniya ta fita a hukumance a ranar 31 ga Janairun 2020. Wannan mataki na Birtaniya ya canza taswirar siyasa, tattalin arziki, da dangantakar kasuwanci ta duniya baki ɗaya Domin duba tasirin wannan mataki da kuma nasarar da za'a ce ƙasar ta samu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Abdulhakeem Garba Funtua, mai sharhi kan harkokin siyasar duniya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

european union domin bayan daga garba shiga yau turai wannan birtaniya bashir ibrahim idris
Ilimi Hasken Rayuwa
Yadda aka gudanar da taron manyan masana na duniya a birnin Lagos

Ilimi Hasken Rayuwa

Play Episode Listen Later Jun 23, 2026 10:00


A wannan makon, shirin ya mayar da hankali ne kan babban taron ƙungiyar Lagos Studies Association karo na goma da aka kammala a ƙarshen mako, wanda ya saba haɗa masana, malaman jami'o'i, da masu bincike daga sassa daban-daban na Najeriya da ƙasashen waje domin tattauna halin da ilimi yake ciki a nahiyar Afirka cikin wannan ƙarni. Wannan taro, wanda aka kafa shi shekaru goma da suka gabata a birnin New York, an dawo da shi gida Afirka domin tattauna ainihin matsaloli da ci gaban nahiyar ke fuskanta, kuma a bana, fiye da rukunonin tattaunawa 340 ne aka shirya, inda aka haɗa masana daga sassan duniya. Shekarar 2026 ta yi daidai da cikar kungiyar LSA shekaru 10 da kafuwa, inda aka gudanar da taron ƙarƙashin taken makomar ilimin nahiyar Afirka a wannan ƙarni. Wani sashe mai muhimmanci a taron shi ne tattaunawa kan littafi na musamman mai suna 'Our Digital Lives and Indigenous Pathways', wanda masana suka duba yadda za a haɗa fasahar zamani da dabarun gargajiya na Afirka don samun ci gaba mai dorewa. Baya ga tattaunawar kimiyya, taron ya haɗa da baje kolin fasaha na musamman mai taken 'Histories on Scissors: The Black Essence on the Map of Being' wanda Dominic James Aboi daga Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria ya gabatar. An kuma tattauna makaloli kan addini da rashin addini a Arewacin Najeriya. An dai gudanar da wannan taro ne domin nazarin al'adun zamani da na gargajiya, inda masana suka gabatar da maƙaloli kan tarihin Afirka, al'adu, da kafafen yaɗa labarai haɗi da baje kolin dabarun bincike na zamani. A taron na bana, masana sun gano muhimman abubuwa da suka shafi makomar nahiyar Afirka ta fuskar ilimi, zamantakewa, da fasaha, kuma babban jigon da aka mayar da hankali akai shi ne yadda za a fassara binciken ilimi ya zama abin da zai amfani rayuwar al'umma kai-tsaye. Haka zalika an gano cewa ko da yake yawan binciken da masana da ke zaune a cikin Afirka ke fitarwa ya ƙaru sosai, amma ingancinsa da kuma bayyanarsa a manyan jaridun ilimi na duniya ya ragu sosai.

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan taƙaddamar ƴan siyasa a kotunan Najeriya

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Jun 18, 2026 10:10


Yayin da ake shirin gudanar da zaɓuka cikin watan Fabarairun shekaru mai zuwa a Najeriya, wani abu da ke faruwa shi ne taƙaddamar ƴan siyasa a gaban kotunan ƙasar. Kusan a kowane mako, za a ji cewa kotu ta yanke hukunci kan jam'iyyun siyasa, lamarin da ke iya nisantar da su daga tsayawa takara a waɗannan zaɓuka. Wannan ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

masu yayin wannan najeriya
Bakonmu a Yau
Dr Umar Yakubu kan fitar bayanan sirri daga rumbun ajiyar bayanan INEC

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 5, 2026 3:35


A Najeriya, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta ƙaddamar da bincike akan zargin fitar bayan sirri daga rumbun ajiyar bayananta na masu zaɓe, wanda ya jamnyo cece-kuce  a ƴan kwanakin nan.   Wannan ya biyo bayan wallafa bayan wani ɗan takara ne da ake zargin wani ma'aikacin INEC ya yi a dandalin sada zumunta a yayin zaɓwen fidda gwani na wata jam'iyyar siyasa a babban birnin tarayyar Najeriya Abuja. Akan haka Michael Kuduson ya tattauna da Dakta Umar Yakubu, shugaban wata  ƙungiyar farar hula a Abuja babban birnin Najeriya.

umar akan abuja daga wannan najeriya
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Saƙon gaisuwar sallah daga masu bibiyar shafin RFI

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later May 27, 2026 10:33


A yau take Sallah Babba! Ranar da ɗaukacin Musulmi a faɗin duniya ke murnar zagayowar Sallar layya. Wannan biki na zuwa ne a daidai lokacin da lamura suka yi tsauri, musamman ta ɓangaren tattalin arziƙi. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.

daga sallah kamaru shiga masu chadi nijar wannan najeriya musulmi shafin
Muhallinka Rayuwarka
Sauyin Yanayi ya jefa Manoma cikin ruɗani kan lokacin da ya dace su fara shuka

Muhallinka Rayuwarka

Play Episode Listen Later May 16, 2026 18:43


Shirin Muhallinka Rayuwarka na wannan makon ya tattauna na a kan yadda samun saukar Ruwan Sama na farko a bana ya jefa manoma a jihohin Arewacin Najeriya cikin ruɗani dangane da lokacin da ya dace su fara shuka. Wannan na zuwa ne a yayin da hukumar hasashen Yanayi ta Najeriya wato NIMET, da uma wasu masana ke gargaɗi game da yiwuwar ɗaukewar ruwan saman da wuri, lamarin da zai yi janyo tafka hasarar akasarin amfanin gonar da aka shugka da wuri.

noma jefa dace nimet manoma shuka wannan najeriya cikin
Mu Zagaya Duniya
Yadda harin dakarun Najeriya ya kashe ɗimbin mutane a kasuwar Zurmi

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later May 16, 2026 21:04


Shirin 'Mu Zagaya Duniya' yana bita ne na mahimman labaran al'amura  da suka wakana a makon da ya gabata. a wannan makon shirin ya soma ne daga Najeriya inda a farkon makon da ya wuce wani harin da dakarun Najeriya suka kai ta sama a kasuwar Tumfa ta karamar hukumar Zurmi ta jihar Zamafara ya hallaka akalla mutum dari 100 tare da jikkata wasu da dama. Wannan harin da ke zaman mafi muni da dakarun kasar su kai kan fararen hula shi ne na uku a cikin kasa da wata guda .

yadda wannan najeriya
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan ƙara yawan jihohi a Nijar

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later May 14, 2026 10:24


Gwamnatin Nijar ta fitar da wani daftari da ke ƙara adadin jihohi zuwa 19 ta hanyar ƙirƙiro sabbin 11 a maimakon 8 da ake da su a kasar yau kusan shekaru 30 kenan. Gwamnatin ta ce za ta ƙirƙiri sabbin jihohi da kuma gundumomi ne domin samar da ci gaba da ta hanyar ƙara matso da jama'a zuwa kusa da hukuma. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

masu nijar wannan
Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle
Taba Ka Lashe 12.05.2026

Taɓa Ka Lashe | Deutsche Welle

Play Episode Listen Later May 12, 2026 10:12


Wannan shirin ya dubi yadda wakokin bege na addinin Islama ke kara samun karbuwa tsakanin matasa a kasashen nahiyar Afirka, duk kuwa da yawan sabanin fahimta da ake da su.

taba wannan islama afirka
Wasanni
Yadda aka gudanar da gasar Super 4 ta a Najeriya

Wasanni

Play Episode Listen Later May 11, 2026 9:59


A ranar juma'ar data gabata ne dai aka kammala gasar gasar Super 4, wacce aka fafata tsakacin ƙungiyoyi 4 da suka haɗa da Sporting Lagos da Inter Lagos da Ranchers Bees ta Kaduna sai kuma Doma United, da suka zama zagaru a rukunoninsu na gasar NNL, gasa ta biyu mafi daraja a Najeriya. An gudanar da gasar ne a yanayin yadda ake gudanar da gasar lik-lik, inda kowa ya kara da kowa ganin cewa kowaccensu za ta haska a gasar Firimiyar Najeriya a kakar baɗi. A wasannin ƙarshe da aka aka yi, Sporting Lagos ta sha kashi da ci ɗaya mai banshi a hannun Inter Lagos, amma sai dai hakan bai hanata lashi gasar ba da ban-bancin ƙwallaye, domin kowaccensu ta ƙare ne da maki 6. Wannan ne karo na farko da Sporting Lagos ta taɓa lashe kofin tun bayan samar da ita a shekarar 2022.

kaduna yadda nnl wannan najeriya
Bakonmu a Yau
Hira da Kailani Muhammad kan baiwa China ragamar farfaɗo da matatun man Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later May 6, 2026 3:48


Kamfanin mai na NNPC ya sanya hannu kan wata yarjejeniya da wasu kamfanonin ƙasar China guda biyu, Sanjiang Chemical Company Limited da kuma Fuzhou Industrial Park, domin farfaɗo da matatun mai na Warri da Port Harcourt. Wannan mataki ya zo ne bayan matatun man sun laƙume kimanin biliyan 3.2 na dala ba tare da an samu biyan buƙata ba. Injiniya Kailani Muhammad, tsohon babban jami'in kamfanin na NNPC ne, a tattaunawarsa da Shamsiyya Haruna, ya bayyana gamsuwa da wannan yarjejeniya da kasar China bisa wasu dalilai. Ku latsa alamaru sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

Lafiya Jari ce
Wani bincike ya gano yadda kashi 13 na al'ummar Ghana ke rayuwa cutar ƙoda

Lafiya Jari ce

Play Episode Listen Later May 4, 2026 9:51


A wannan makon shirin na Lafiya Jari Ce tare da Azima Bashir Aminu ya yi nazari kan wani bincike can a Ghana da ke ƙiyasta cewa kusan kashi 13.3 na yawan jama'ar ƙasar na rayuwa da cutukan ƙoda, galibi ba tare da masaniyar suna ɗauke da ita ba, lura da yadda cutar bata nuna alamu a farko har sai ta kai ga ta'azzara. Wannan na nuna yadda cutar ta ƙoda ke matsayin babban ƙalubale a Ghana. Binciken ma'aikatar lafiyar Ghana ya nuna cewa matasa ne kan gaba wajen kamuwa da cutar ta ƙoda lamarin da ƙwararru a fannin cimaka ke cewa hakan na da nasaba da rashin daidaita cimaka da kuma yanayin rayuwar da jama'ar ƙasar suka runguma a yanzu wanda kai tsaye ke ƙara yawan masu kamuwa da cutar ta ƙoda. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

Tambaya da Amsa
Shirin tambaya da amsa na wannan mako ci gaba ne kan illar cutar olsa

Tambaya da Amsa

Play Episode Listen Later May 2, 2026 18:56


A yau shirin tambaya da amsa zai fara ne da ci gaban bayanin da muka faro a makon da ya gabata akan cutar gyambon ciki. Ku danna alamar sauraro dimin jin cikakken shirin tare da Nasiru Sani.

Muhallinka Rayuwarka
Matsalar karancin tsaftataccen ruwa, na ci gaba da addabar iyalai a sassan Nigeria

Muhallinka Rayuwarka

Play Episode Listen Later May 2, 2026 20:00


Matsalar nan ta karancin tsaftataccen ruwa, na ci gaba da addabar miliyoyin iyalai a sassan Nigeria, kila ko saboda rashin samun damar jan ruwan famfo a gidajensu, ko kuma rashin samun ruwan daga hukumomin samar da ruwan famfo na jihohinsu, duk da makudan kudin da gwamnatocin jihohin ke warewa, da sunan samar da ruwa wa jama'arsu. Wannan matsala ba kawai ta tsaya kan iyalai da kan rasa ruwan amfanin yau da kullum a gidajensu ba, har ma tana shafar ingancin muhalli, kasancewar a kan muhallin a kan dawo, don neman ruwan a karshe.

nigeria gaba ruwa sassan wannan
Mu Zagaya Duniya
Shirin mu zagaya duniya ya tattaro manyan labaran da suka faru a wannan mako

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Apr 25, 2026 20:32


Shirin mu zagaya duniya na wannan mako ya duba manyan labaran da suka faru cikin wannan mako, a sassan duniya. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Oumarou Sani.

Tambaya da Amsa
Shirin tambaya da amsa na wannan mako ya ɗora ne kan illar cutar gyambon ciki

Tambaya da Amsa

Play Episode Listen Later Apr 25, 2026 18:56


A yau shirin tambaya da amsa zai fara ne da ci gaban bayanin da muka faro a makon da ya gabata akan cutar gyambon ciki. Ku danna alamar sauraro dimin jin cikakken shirin tare da Nasiru Sani.

Bakonmu a Yau
Dakta Harbau akan yawan iskar gas da Najeriya ta fitar

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Apr 23, 2026 3:20


Wasu alƙaluma daga Hukumar Kula da Albarkatun Man Fetur na kan tudu da na cikin ruwa (NMDPRA) sun nuna cewa, adadin Iskar Gas ɗin da aka fitar daga Najeriya zuwa kasuwannin ƙetare ya kai kaso 62 cikin 100, cikin watanni uku na farkon wannan shekara. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Gas ɗin ya yi ƙaranci a Najeriyar, lamarin da ke taka rawa wajen raguwar hasken lantarkin da ake samu, fannin da kasonsa aƙalla 80 cikin 100 ya dogara da arziƙin na Gas. Don jin yadda masana ke kallon lamarin da kuma mafita, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Aminu Idris Harbau, ƙwararren kan tattalin arziki a Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraron hirar:

gas akan wasu wannan najeriya
Al'adun Gargajiya
Tasirin mayaƙa a masarautun gargajiyar ƙasar Hausa

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Apr 21, 2026 10:28


Shirin Al'adun mu na Gado a wannan makon ya leka Jamhuriyar Nijar ne, inda ya duba batun da ya shafi mazajen dauri, musaman mayaƙan gargajiya a wannan zamani, jaruman da ke ƙarƙashin inuwar sarakunan gargajiya. Duk inda akwai masarautun gargajiya an san su da tarin mayaƙa da ke yin tsarin daka a cikin kowane irin hali don kare su. Wannan tsarin ne da ya samo sali tun zamani da ake yaƙe-yaƙe tsakanin masarautu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa...........

ku gado asar hausa duk wannan jamhuriyar nijar abdoulaye issa
Lafiya Jari ce
An samu raguwar haihuwa a Najeriya sakamakon rungumar tsarin tazarar Iyali

Lafiya Jari ce

Play Episode Listen Later Apr 20, 2026 10:05


Shirin Lafi Jari ce a wannan makon tare da Azima Bashir Aminu ya yi duba ne kan wani rahoton sashen bincike da kula da lafiyar jama'a na NDHS da ke ƙarƙashin hukumar kula da yawan jama'a ta Najeriya NPC, wanda ke nuna cewa daga shekarar 2024 yawan haihuwa ya ragu matuƙa tsakan matan Najeriya daga kashi 5.3 zuwa kashi 4.8. Wannan sakamakon rahoto na NDHS a cewar masana manuniya ce kan yadda mata a yanzu suka rungumi tsarin tazarar iyali bisa dalilai mabanbanta. Kafin yanzu dai, tsarin na tazarar iyali bai samu cikakkiyar karɓuwa a yankin arewacin Najeriya ba, yankin da ke sahun gaba ta fannin yawan haihuwa, sai dai a yanzu alamu na nuna wasu magidantan da kansu ke miƙa iyalansu ga likita don karɓar allura ko magungunan tazarar haihuwar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

ku samu wannan najeriya
Mu Zagaya Duniya
Bitar Labaran mako: Iran ta amince da buɗe mashigin Hormuz ga jiragen kasuwanci

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Apr 18, 2026 19:50


Shirin Mu zagaya duniya tare da Oumarou Sani, kamar yadda ya ke zuwar muku a kowannen mako, a wannan karon ma ya yi bita ne kan muhimman labaran da suka faru a makon da muke ban kwana da shi. Cikin jerin labaran da ke ƙunshe a wannan shiri, akwai yadda Iran ta amince da buɗe mashigin Hormuz bayan ƙulla yarjejeniyar tsagaita wutar kwanaki 10 tsakanin Isra'ila da Lebanon. Wannan da sauran manyan labarai daga sassa daban-daban na nan ƙunshe a cikin shirin. Ku latsa alamar sauti don saurare.

Kasuwanci
Yadda matsalolin tsaro ke kassara kasuwanci a arewacin Najeriya

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Apr 8, 2026 10:00


Shirin na wannan makon ya mayar da hankali ne kan irin fargabar da 'yan kasuwar arewacin Najeriya da ke fatauncin kayayyaki zuwa wasu sassan jihohi ke ciki, sakamakon ayyukan bata gari da ke tare hanya wanda a wasu lokuta kan kai ga rasa rayuka. Abune da aka saba gani, ‘yan kasuwar dake hada Hada tsakankin jihohi daga wannan kasuwa zuwa waccan ko tsakanin kasuwannin kauyuka. To sai dai Kuma irin wannan tsarin na fuskantar cikas ko koma baya, alal misali ga yan kasuwa a jihar filato dake arewacin Najeriya, sakamakon munanan halaye na wasu bata gari marasa tausayin rayuwar Dan Adam, dake tare Yan tireda ko Kuma matafiya inda suke Kai musu farmaki, tare da yi musu kisan gilla. A kwanakin baya wasu Bata gari sun tare wasu Yan kasuwa da ke fatauci daga garin Jos zuwa yankin kudancin Jihar, inda suka kashe biyar daga cikinsu, Wannan  al'amari ya Sanya Yan Kasuwar da sauran matafiya shiga hali na fargaba a kowane yanki dake jihar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu saurare kan matakin CAF na kwace nasarar AFCON daga Senegal

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Mar 19, 2026 10:04


Hukumar kwallon ƙafar Afrika ta sanar da ƙwace Kambun da Senegal ta lashe a gasar neman kofin nahiyar da aka kammala cikin watan Janairun da gabata tare da miƙa shi ga ƙasar Moroko. Wannan dai mataki ne da ya yi matuƙar girgizar masu shawar harkar ƙwallon ƙafa a sassan duniya, inda tuni Senegal a buƙaci a gudanar da bincike bisa zargin cewa akwai yiyuwar an bayar da rashawa ne don ƙwace wannan galaba. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabiru Yusuf.

Bakonmu a Yau
Hukumar ƙwallon ƙafar AFCON ta ƙwace nasarar da Senegal ta miƙawa Morocco

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 19, 2026 3:28


Hukumar kwallon ƙafar Afrika ta sanar da ƙwace Kambun da Senegal ta lashe a gasar neman kofin nahiyar da aka kammala cikin watan Janairun da gabata tare da miƙa shi A a hannun ƙasar Moroko. Wannan dai mataki ne da ya yi matuƙar girgizar masu shawar harkar ƙwallon ƙafa ba wai a nahiyar Afrika ba har da sauran sassan duniya. To sai tuni Senegal ta buƙaci a gudanar da bincike bisa zargin cewa akwai yiyuwar an bayar da rashawa ne don ƙwace wannan galaba.   A game da wannan mataki ne Michael Kuduson ya zanta da Aliyu Awwal Ibrahim, Sakataren tawagar ƙwallon ƙafar Najeriya ƴan ƙasa da shekaru 20. Ga kuma zantawarsu. A latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar tattaunawar.

Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Abdulaziz Abdulaziz game da ziyarar Tinubu a Birtaniya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 18, 2026 3:36


Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya fara ziyarar aiki a Birtaniya inda ya samu kyakkyawar tarba daga hukumomin ƙasar. Wannan ziyara na zuwa ne a dai dai lokacin da Najeriyar ke fuskantar matsalolin tsaro iri-iri. Dangane da ziyarar ta Tinubu da kuma alfanunta ga ƙasar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai taimakawa shugaban kan harkokin tsaro Malam Abdulaziz Abdulaziz kuma ga yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

game ku abdul aziz bola ahmed tinubu wannan najeriya birtaniya bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Farfesa Tukur AbdulƘadir kan fargabar tsanantar yaƙin Iran

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 3, 2026 3:38


Ga dukkanin alamu akwai yiwuwar yaƙi tsakanin Iran da kuma haɗin gwiwar Amurka da Isra'ila ya ɗauki tsawon lokaci saɓanin zaton da ake yi na ya kasance gajere, wannan kuwa ya biyo bayan jawabin shugaban Amurka Donald Trump a daren jiya da ke cewa mai yiwuwa a shafe makwanni 4 zuwa 5 suna kai hare-hare kan Iran. Wannan na zuwa ne a yayin da yaƙin da ya rincaɓe, ke ci gaba da shafar ƙasashe da dama a Yankin Gabas ta Tsakiya. Domin jin yadda masana siyasar ƙasa da ƙasa ke kallon lamarin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Tukur AbdulƘadir na Jami'ar Jihar Kaduna a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar..

iran ga ku isra abdul domin adir wannan najeriya amurka
Bakonmu a Yau
Dakta Kabiru Adamu kan fatan samar da cibiyar sauya tunanin tubabbun ƴan bindiga

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Feb 24, 2026 3:39


Gwamnatin Jihar Benue a Najeriya, na neman amincewar gwamnatin tarayyar ƙasar wajen gina cibiyar sauya tunanin ‘yan bindigar da suka tuba, da ma sauran mutanen da wani yanayi ya sanya su taimaka wa ayyukan ta'addanci, ciki kuwa har da mata waɗanda ke yi wa ‘yan ta'addan aiki a bisa tilas bayan garkuwar da aka yi da su. Wannan na zuwa ne a yayin ake ci gaba da samun banbancin ra'ayi tsakanin ‘yan Najeriya a kan irin wannan yunƙuri. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Kabiru Adamu, shugaban kamfanin Beacon Consulting da ke bincike kan tsaro a nahiyar Afrika. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar..

afrika ku samar adamu wannan najeriya fatan
Wasanni
Yadda ta wakana a gasar tseren dawaki da ta gudana a garin Daura na jihar Katsina

Wasanni

Play Episode Listen Later Feb 23, 2026 9:59


Shirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan mako ya mayar da hankali ne kan gasar tseren dawaki da aka gudanar a garin Daura da ke jihar Katsina da ke a arewacin Najeriya. A farkon watan Faburairun wannan shekarar ne aka kammala babbar gasar tseren dawaki ta ƙasa da ƙasa da ƙungiyar sukuwar dawaki ta Najeriya ke shiryawa. Wannan ne dai karo na uku da ake gudanar da irin wannan sukuwa a cikin wannan shekarar, bayan da aka yi ta farko a birnin Katsina sai garin Hadeja na jihar Jigawa ya karbi bakunci sannan aka kamma sukuwan zangon farko na wannan shekarar a Daura. Mahaya daga Jihohin Kano da Sokoto da Neja da Bauchi da Kebbi da Katsina, waɗansu daga Jamhuriyar Nijar da Kamaru da Mali da Chadi da kuma Burkina Faso, suka halarci gasar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

mali ku burkina faso garin yadda kamaru chadi sokoto katsina neja daura bauchi kebbi jigawa wannan najeriya jamhuriyar nijar
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan harajin yin wa'azi da ƴan bindiga suka sanya a Kebbi

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Feb 23, 2026 10:00


A Najeriya wata ƙungiyar ta'addanci da ba'a kai ga tantace wa ba, ta buƙaci a'ummar Utono ta ƙaramar hukumar Ngaski a jihar Kebbi da ta biya su zunzurutun ƙudi har Naira miliyan 100, kafin su bai wa malamai damar gudanar da Tafsiri ko wa'azi a wannan watan Azumi na Ramadana. Ƴan ta'addar sun bayyana bukatar ne a wata rubutacciyar wasika da suka aika garin na Utono. Wannan dai shine karon farko da wata ƙungiya da bukaci malamai biyan wani kudi domin gabatar da wa'azi, ko da ya ke al'umma a wasu yankunan sun saba biyan kudi don neman yancin walwa, ko ayyukan noma ko ma girɓi. Yaya kuke kallon wannan sabon bukata na ƴan ta‘adda? Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

suka yaya sanya naira masu kebbi azumi wannan najeriya
Bakonmu a Yau
Halin da masu fama da Cutar Daji ke ciki a Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Feb 6, 2026 3:39


Majalisar Ɗinkin Duniya ta ware 4 ga watan kowane watan Fabarairu a matsayin ranar yaƙi da Cutar Daji ko kuma Cancer ta Duniya, wadda hukumar lafiya ta Duniya WHO ke jagorancin gangamin wayar da kai a kanta, gami da bayyana halin da ake dangane da kula da masu fama da ita.   Wannan rana ta zo ne a daidai lokacin da wani sabon rahoton masana ya ce daga cikin kusan mutane miliyan 19 da suka kamu da cutar ta Daji a shekarar 2022, ana iya bayar da kariya ga aƙalla mutane miliyan 7 daga kamuwa da cutar in da an ɗauki matakan da suka dace. Domin jin ƙalubalen da ƙasashe masu tasowa kamar Najeriya ke fuskanta dangane da cutar, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Shehu Usman AbdulMumin Maƙarfi, ƙwararren Likita a Jihar Kaduna da ke Najeriya. Sai a latsa alamar sautin da ke sama domin sauraron bayanan Dakta Shehu Usmanu Maƙarfi....

cancer fama sai domin duniya masu ciki wannan najeriya majalisar
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan kyautar Grammy da Fela Kuti ya samu bayan rasuwarsa

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Feb 3, 2026 10:05


Shekaru 29 bayan mutuwarsa, an bai wa shahararren mawaƙi kuma mai fafutuka Fela Kuti ya kasance ba'Afirke na farko da aka bai wa kyautar yabo ta Grammy wato Lifetime Achievement Award da ake bai wa wanda ya sadaukar da rayuwarsa yana rera waƙa. Fela ɗan Najeriya, ya yi fice ainun, ta hanyar rera waƙoƙin gwagwarmaya da kuma muradun talakawa. Shin ko me za ku iya tunawa a game Fela Kuti? Me za ku ce a game da wannan kyauta ta Grammy Awarda aka bayar bayan rasuwarsa? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan yadda wasan kusa da na ƙarshe ya gudana a AFCON

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Jan 15, 2026 9:57


Morocco da Senegal sun yi nasarar kaiwa wasan ƙarshe na gasar cin kofin Afrika ko kuma AFCON, nasarar da suka samu bayan ita mai masaukin baƙi ta doke Najeriya yayinda Senegal kuma ta doke Masar dukkaninsu a daren jiya Laraba, yayinda ake shirin haɗuwa don doka wasan ƙarshe na gasar tsakanin manyan ƙasashen 2 a ranar Lahadi.   Anya kuwa ƙasashen na Masar da Najeriya sun taka rawar da ta dace gabanin fitar da su daga gasar? Wacce ƙasa kuke ganin za ta kai tsakanin labari wajen lashe kofin a wannan karon? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin....

morocco afrika senegal afcon yadda masu kusa masar wannan najeriya
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan miliyoyin ƴan Najeriya da basa amfani da wutar mita

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Jan 7, 2026 10:36


Hukumar daidaita farashin wutar lantarki a Najeriya ta ce yanzu haka akwai sama da layuka milyan biyar da jama'a ke amfani da wuta ba tare da an ɗora su a kan mita ba. Wannan ya zo ne daidai lokacin da ake ci gaba da ɗiga ayar tambaya dangane da dalilan da suka sa aka gaza samar da mitocin a wadace. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

basa mita masu wannan najeriya hukumar
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan dokar-ta-baci da gwamnati ta kafa a Nijar

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Dec 30, 2025 9:12


Mahukuntan jamhuriyar Nijar sun shelanta kafa dokar-ta-ɓaci, wanda a ƙarƙashinta gwamnati za ta iya yin amfani da illahirin al'ummar ƙasar da kuma dukiyoyinsu duk lokacin da ta ga ya dace saboda tunkarar barazanar tsaro. Matakin ya zo ne kwanaki ɗaya bayan da Amurka ta ƙaddamar da farmaki kan maɓoyar ƴanbindiga a wani wuri da ke jihar Sokoton Najeriya daf da iyaka da Nijar. Shin ko me za ku ce a game da matakin? Anya hakan zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro da ƙasar ke fama da su? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

shin baci kafa masu nijar wannan amurka
Al'adun Gargajiya
Yadda aka gudanar da bikin naɗin sarautar sarkin Komadugu a Maraɗi

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Dec 2, 2025 9:55


Shirin na yau ya yada zango jihar Diffa dake Jamhuriyar Nijar,yankin da aka gudanar da bikin nadin sabon sarkin Komadugu, wanda ya samu halartar baƙi daga ciki da wajen ƙasar. Diffa dai kamar dai yadda masana tarihi suka tabbatar, ana na nufin Diwa a harshen Kanuri kenan. Kalmar ta samo asali ne daga kalmar "Di wa Nallé wa," wadda ke nuna tsabtar jiki da dai sauran abubuwan da suka shafi maza da mata na yankin. Di na nufin farin gashi, kuma Nallé na nufin lalle wanda ke da ma'ana biyu. Wannan jumla, Di wa Nallé wa, na nufin mata waɗanda, ko da a cikin tsufa, suna rina gashinsu da lalle. Tarihi ya nuna  cewa a ƙarni na 19, yankin Diffa a lokaci na karkashin masarautar Kanem-Bornu,inda a shekarar 1933 Turawan mulkin mallaka a lokacin  sun kafa yankin Komadougou, wanda aka bayyana yankin  da farko yake zaune a Bosso sannan daga baya ya koma Gueskérou. An gudanar da zaɓen sabon sarkin na komadugu a jahar Diffa a gaban hukumomin  bariki da na gargajiya da kuma sauran al'umma, wanda ya kai ga zaɓen Hassan Mamadou Abba Kyari a matsayin sabon sarkin na Komadugu. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Abdoullaye Issa.

bikin shirin kalmar tarihi nall yadda shiga bosso diwa nijar wannan diffa jamhuriyar nijar
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu saurare kan ɗaukar sabbin 'yansanda dubu 30 a Najeriya

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Nov 25, 2025 10:22


Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umurnin janye dubban ƴansanda da ke kare manyan mutane a sassan ƙasar, tare da ta sanar da shirin ɗibar wasu sabbin ƴansanda kusan dubu 30 don tunkarar matsalar tsaro da ta addabin ƙasar. Shin ko wace irin gudunmuwa hakan zai bayar a ƙoƙarin tunkarar ƙalubalen tsaro da ƙasar ke fama da shi yanzu haka? Wannan shi ne maudu'in da  muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

shin masu dubu bola ahmed tinubu wannan najeriya
Wasanni
Yadda Ashraf Hakimi ya lashe gwarzon shekara na Afrika karon farko

Wasanni

Play Episode Listen Later Nov 24, 2025 9:59


Shirin "Duniyar Wasanni" tare da Khamis Saleh a wannan lokaci zayyi duba ne kan ƙyautar gwarzon ɗan wasan ƙwallon ƙafan Afirka da Achraf Hakimi na Morocco ya lashe. A makon daya gabata ne Hukumar Kwallon Ƙafar Afrika CAF, ta bayar da kyautuka ga zaratan ƴan wasan nahiyar da suka nuna bajinta a wannan shekarar da muke bankwana da ita. A yayin bikin da ya gudana a birnin Rabat na ƙasar Morocco, hukumar ta CAF ta sanar da ɗan wasan baya na tawagar ƙasar ta Morocco wanda kuma ya ke yi wa ƙungiyar PSG wasa Achraf Hakimi,  a matsayin wanda ya lashe ƙyautar gwarzon ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Afirka a wannan shekarar. Hakimi ya samu nasarar ce bayan doke shahararrun ƴan wasan nahiyar da suka taɓa lashe kyautar irinsu Mohamed Salah na Masar da ke taka leda a Liverpool,  da kuma Victor Osimhen na Nigeria da ke wasa a Galatasaray. Wannan ne dai karo na farko da ɗan wasan ya taɓa lashe ƙyautar, bayan da a karo biyu a jere ya na ƙarewa a mataki na biyu, a shekarar 2023 da Victor Osimhen ya lashe da kuma 2024 da Ademola Lookman ya lashe. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin...

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu saurare kan ta'azzarar matsalolin tsaro a Najeriya

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Nov 24, 2025 9:55


A Najeriya, ƴan bindiga masu gurkuwa da mutane domin ƙarbar ƙudin fansa, sun tsananta kai hare-hare makarantu tare da sace ɗaibai a baya-bayan nan, lamarin da ya sa gwamnatoci a wasu jihohin ƙasar suka ɗauki matakin rufe makarantu a matakai daban-daban. Hakan ya biyo bayan sace dalibai a jihohin Kebbi da Neja a makon da ya gabata, lamarin da ya sake haifar da fargaba kan tsaron dalibai da makarantu da kuma makomar ilimi a yankin arewacin Najeriya. Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Ku latsa alamar sauti don sauraren shirin...

ku hakan masu neja kebbi wannan najeriya
Bakonmu a Yau
Dr Yahuza Getso kan sabbin hare-hare ƴan bindiga a Arewacin Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 20, 2025 3:30


Matsalolin tsaro na ci gaba da ɗaukar sabon salo a Tarayyar Najeriya, bayan da a baya-bayan nan aka ga yadda ƴan bindiga a yankin arewa maso yammacin ƙasar suka sace ɗalibai aƙalla 25 a jihar Kebbi, yayinda ana tsaka da jimamin wannan kuma aka sake ganin yadda suka kai hari wata majami'ar jihar Kwara tare da kashe mutane 2 da kuma sace wasu da dama. Wannan na zuwa ne kwanaki bayan dakarun Sojin Najeriyar sun sanar da samun gagarumar nasara a kan ƴan ta'adda musamman bayan barazanar Trump ta ɗaukar matakin Soji kan ƙasar ta yammacin Afrika. Dangane da wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da masanin tsaro a Najeriyar Dr Yahuza Getso........

donald trump afrika soji kebbi hare hare wannan najeriya tarayyar najeriya
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan yadda matsalar tsaro ke komawa ɗanya a Najeriya

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Nov 19, 2025 10:00


Da alama masu ɗauke da makamai a Najeriya sun koma gidan jiya na sace-sacen dalibai, garkuwa da mutane da ajalin waɗanda basu ji basu gani ba gadan-gadan, yayin da a cikin kwanaki huɗu kacal aka yi awon gaba da mutum 145. Wannan na zuwa ne a yayin da matsalolin tsaro ke sake ta'azzara a sassan arewacin ƙasar, ciki har da satar ɗaliban da aka yi a jihar Kebbi, sai kuma labarin da ake ta yamaɗiɗin cewa mayaƙan ISWAP sun yi garkuwa da wani janar din soji tare da kashe shi a arewa maso gabashin Najeriyar. Shin kun gamsu da yadda jami'an tsaro ke aiki a yankunan ku. Me kuke ganin ya kamata hukumomi su yi domin kawo ƙarshen zulumin da jama'a ke ciki? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

shin yadda masu kebbi wannan najeriya
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan rashin samun tikitin zuwa gasar kofin duniya da Najeriya ta yi

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Nov 18, 2025 10:44


A ranar Lahadin da ta gabata Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo ta kawo ƙarshen fatan Najeriya na samun tikitin halartar gasar cin kofin duniyar da za ayi a shekara mai zuwa. Karo na biyu kenan a jere da Najeriya ke rasa damar haska wa a gasar ta Tamula mafi daraja a Duniya. Waɗanne dalilai ne ke janyo wa Najeriya wannan koma baya a sha'anin ƙwalllon ƙafa? Wanene ya gaza sauke nauyin da rataya a wuyansa a tsakanin masu alhaki a wannan fage? Ta yaya kuma za a magance matsalar? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakin ku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

wa congo karo duniya masu rashin wannan najeriya
Bakonmu a Yau
Hon Sani Ahmad Toro kan yadda Najeriya ta gaza samun tikitin World Cup

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 18, 2025 3:37


Fatan Najeriya na samun gurbi a gasar cin kofin duniyar da za'a yi a shekara mai zuwa ya gushe, sakamakon rashin nasarar da ƙungiyar Super Eagles ta yi a hannun ƙasar Congo. Wannan shi ne karo na biyu a jere da Najeriya ba zata je gasar ta dunitya ba, bayan gaza zuwa Qatar shekaru 4 da suka gabata, kafin wannan karo. Bashir Ibrahim Idris, ya tattauna da tsohon sakatare janar na Hukumar Kwallon Kafa Najeriya, Hon Sani Ahmad Toro game da wannan koma baya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana a kai.