Podcasts about shugaban najeriya muhammadu buhari

  • 6PODCASTS
  • 15EPISODES
  • 6mAVG DURATION
  • ?INFREQUENT EPISODES
  • Nov 22, 2022LATEST

POPULARITY

20172018201920202021202220232024


Best podcasts about shugaban najeriya muhammadu buhari

Latest podcast episodes about shugaban najeriya muhammadu buhari

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Kan samar da rijojin mai a arewacin Najeriya

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Nov 22, 2022 15:37


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari yai kaddamar da aikin fara binciken man fetur da iskar gaz a yankin Kolmani da ke kan iyakar jihohin Bauchi da Gombe.   Alkaluma dai na nuni da cewa akwai kusan ganga bilyan daya nan danyan mai tare da samar wa Najeriya sama da dala bilyan 73 matukar aka fara aikin hako shi.   Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.

samar gombe shiga bauchi najeriya shugaban najeriya muhammadu buhari
Bakonmu a Yau
Shugaba Buhari ya ki sanya hannu a kan sabuwar dokar zaben kasar

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 20, 2021 3:08


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari yaki sanya hannu akan sabuwar dokar zaben da majalisa ta amince da ita wadda zata baiwa jama'a damar tsayawa zabe ba tare da neman Ubangida ba da kuma aikewa da sakamakon zaben kai tsaye daga tashoshin da aka gudanar da zabe. Sashen hausa na rfi  ya tattauna da Tsohon Dan Majalisar Dattawa kuma tsohon Sakataren Jam'iyyar PDP na kasa Sanata umar Ibrahim Tsauri, kuma ga tsokacin da yayi a kai. Daukar wannan mataki na biyo bayan cikar wa'adin sanya hannu akan daftarin da Majalisa ta mika masa a jiya lahadi.

pdp sanya buhari hannu sashen shugaban najeriya muhammadu buhari
Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - Yara miliyan 12 ba sa zuwa makaranta saboda tsoron 'yan bindiga - Buhari

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Oct 28, 2021 3:29


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa yara sama da miliyan 12 ne ke fargabar zuwa makaranta a kasar saboda tsanantar ayyukan ‘yan ta'adda da  ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane. Bayanai sun nuna cewa ‘yan ta'adda sun yi garkuwa da dalibai sama da dubu 1 a Najeriya cikin kasa da shekara, daya, abinda ke jefa yaran cikin halin ni ‘ya su.   Ga tattaunawar Dr.Idris Salisu Rogo na jami'ar Bayero da ke Kano,  da Rukayya Abba Kabara.

kano buhari najeriya shugaban najeriya muhammadu buhari
Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - Tattaunawa da Mustapha Jokolo kan neman taimakon Amurka ga tsaron Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Apr 29, 2021 3:43


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci taimakon Amurka wajen shawo kan matsalolin tsaron da suka addabi nahiyar Afirka baki daya, inda ya roke ta da ta dawo da Cibiyar rundunar ta da ke kula da Afirka daga Jamus zuwa nahiyar. A tattaunawar da suka yi da Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken Buhari ya ce dawo da Cibiyar rundunar Afirka zai taimaka wajen dakile matsalolin tsaron da suka mamaye nahiyar. Dangane da wannan bukata, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Mai Martaba Sarki Gwandu na 19 Manjo Almustapha Haruna Jokolo, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.

mustapha jamus najeriya afirka amurka bashir ibrahim idris shugaban najeriya muhammadu buhari
Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - Dr. Elharun kan taimakon da Najeriya ke nema daga Amurka

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Apr 28, 2021 3:44


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci taimakon Amurka wajen shawo kan matsalolin tsaron da suka addabi nahiyar Afirka baki daya, inda ya roke ta da ta dawo da Cibiyar rundunarta da ke kula da Afirka daga Jamus zuwa nahiyar. A tattaunawar da suka yi da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Anthony Blinken Buhari ya ce, dawo da Cibiyar Rundunar Afirka zai taimaka wajen dakile matsalolin tsaron da suka mamaye nahiyar. A game da wannan batu Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr. El Harun Muhammed, masanin siyasar duniya. Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirar

ku nema daga jamus najeriya afirka amurka shugaban najeriya muhammadu buhari
Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - Tattaunawa da Alhaji Tukur Mamu kan wa'adin da Buhari ya dibarwa 'yan bindiga

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 10, 2021 3:43


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya dibawa ‘yan bindiga da suka hana sukuni a jihohin arewa maso yammacin Nigeria musamman Jihar Zamfara, wa’adin watanni biyu da su bada kai ko kuma ya sanya kafar wando daya da su. Gwamnan Zamfara Bello Matawalle ya gabatar da sakon shugaban kasar a jawabi ga al’ummar jihar. Garba Aliyu Zaria ya tuntubi Alhaji Tukur Mamu, dan Jarida, kuma mai sharhi gameda harkokin yau da kullum ko yaya yake kallon matakin.  

nigeria buhari mamu shugaban najeriya muhammadu buhari garba aliyu zaria
Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - Tattaunawa da Air Commodore Tijjani Baba Gamawa kan nadin sabbin hafsoshin tsaro a Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jan 27, 2021 3:08


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nada sabbin manyan hafsoshin sojin kasar, domin maye gurbin wadanda ya nada shekaru 5 da suka gabata. Nadin sabbin hafsoshin na zuwa ne a wani lokaci da matsalolin tsaro suka addabi kasar daga kowane bangare. Dangane da sauyin da aka samu, mun tattauna da Air Commodore Tijjani Baba Gamawa mai ritaya, wanda yayi tookaci akai kamar haka.

baba commodore nadin najeriya shugaban najeriya muhammadu buhari
Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - Jami'an tsaro basu kashe kowa a Lekki ba - Buhari

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 19, 2020 3:08


A karon farko gwamnatin Najeriya ta ce babu ko da mutum guda da jami`an tsaro suka kashe a shingen karbar harajin ababen hawa a hanyar Lekki da ke Legas, a lokacin zanga-zangar EndSARS. Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya musanta zarginda ake yiwa sojan kasar cewa sun kashe masu zanga-zangan ENDSARS a kwanan baya. Shugaban yace, bayanan da aka yi ta yadawa ta kafafen sada zumunta jita-jita ne kawai, babu gaskiya a ciki. Masu zanga-zangar da wasu kungiyoyin kare hakkin bil'adama sun yi zargin cewa an kashe a kalla mutane 12 a harabar ta Lekki. Kan haka ne muka tattauna da Malam Garba Shehu, kakakin shugaban kasa Mohammadu Buhari, kuma ga abinda yake cewa.

basu buhari lekki kowa masu legas najeriya shugaban shugaban najeriya muhammadu buhari
Mu Zagaya Duniya
Mu Zagaya Duniya - Tarzoma a Najeriya da ta yi sanaddiyar mutuwar mutane a Lagas

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Oct 24, 2020 20:00


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewar mutane 69 suka mutu sakamakon tarzomar da aka samu lokacin zanga zangar adawa da cin zarafin yan Sanda, yayin da 37 suka samu raunuka, kuma adadin ya hada da fararen hula da jami’an Yan Sanda da kuma soji.Garba Aliyu Zaria ya mayar da hanakali a cikin shirin Mu zagaya Duniya.

mu sanda duniya najeriya shugaban najeriya muhammadu buhari garba aliyu zaria
Wasanni
Wasanni - Dan Najeriya ya lashe babbar gasar dambe a Amurka

Wasanni

Play Episode Listen Later Jul 20, 2020 10:02


Shirin Duniyar Wasanni na wannan makon tare da Abdurrahman Gambo Ahmad ya tattauna ne kan nasarar da dan Najeriyar nan, Kamaru Usman ya samu a babbar gasar damben zamani da aka gudanar a Amurka. Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya jinjina wa dan wasan saboda bajintar da ya nuna. Kazalika shirin ya yi nazari kan kalubalen da ke gaban Real Madrid bayan ta lashe kofin La Liga karo na 34 a Spain.

spain real madrid la liga kamaru usman najeriya amurka shugaban najeriya muhammadu buhari
Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - Mallam Abdullahi Umar kan dambarwar daukan ma'aikata dubu 774 tsakanin Festo Kiyamo da Majalisar wakilan Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jul 15, 2020 2:11


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bai wa karamin ministan ayyukan kasar Festus Keyamo umarnin cigaba da shirin dibar ma’aikata dubu 774 bayan takaddamar da ta kaure tsakanin sa da 'yan Majalisun kasar da suka nemi a dakatar da aikin. Ministan ya ce shugaba Buhari ya bashi umurnin cigaba da aikin kamar yadda doka ta tanada, yayin da kungiyoyi daban daban za su taka rawa wajen dibar ma’aikatan a matakan kananan hukumomi 774 da ke fadin Najeriya a shirin da ake saran ya lakume naira biliyan 52. Dangane da wannan cigaba mun tattauna da Mallam Abdullahi Umar, kuma ga tsokacin da ya yi akai.

umar buhari festo abdullahi dubu najeriya majalisar shugaban najeriya muhammadu buhari
Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - Tattaunawa da Alhaji Umaru Dembo kan ginin bututun gas daga Ajaokuta zuwa Kaduna da Kano

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jul 1, 2020 3:34


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sake jaddada matsayin gwamnatin sa na aiwatar da gina bututun iskar gas wanda zai tashi daga Ajaokuta zuwa Kaduna da Kano domin saukakawa jama’a samun sinadarin cikin lokaci kuma kamar yadda aka tsara. Yayin da yake kaddamar da fara aikin ta kafar bidiyo a Ajaokuta dake Jihar Kogi da kuma Rigachikum dake Jihar Kaduna, jiya Talata, Buhari yace aikin na da matukar muhimmanci ga ‘Yan Najeriya saboda haka ya zama dole a samu nasarar sa. Dangane da wannan shiri, Umaru Dembo, tsohon ministan albarkatun manfetur a Najeriya ya bayyanawa Ahmad Abba tasirin wannan shirin a tattaunawar da suka yi.

kano buhari daga kaduna umaru yayin dembo najeriya talata shugaban najeriya muhammadu buhari
Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - Sakataren yada labaran manoman Najeriya, Muhammad Magaji kan umarnin Buhari na wadata kasar da abinci

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later May 26, 2020 3:43


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya bukaci manoman kasar da su kara azama don wadatar da kasar da abinci, saboda a cewarsa, Najeriya ba ta da kudin da za ta yi amfani da su domin sayo abinci daga ketare. Sai dai sakataren yada labaran kungiyar manoman Najeriya, Alhaji Muhammad Magaji, ya ce akwai abubuwan da ya kamata gwamnati ta yi domin ganin cewa manoma sun wadatar da kasar da abinci.

sai yada buhari najeriya shugaban najeriya muhammadu buhari
HausaRadio.net
DW Hausa Shirin Safe na 2019-03-01

HausaRadio.net

Play Episode Listen Later Mar 1, 2019 1:20


DW Hausa Shirin Safe 01.03.2019 [1] Masana tattalin arziki da hada-hadar kudi a Najeriya, sun bada shawarar cewa ya kamata gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari, ta bada himma wajen raya tattalin arzikin kasar musamman a yankin arewacinta domin magance matsalolin da ke addabar yankin. Hosts: Muntaqa Ahiwa Nigeria: Cikin shirin za'a ji yadda masana suka soma baiwa Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, shawara kan buƙatar zaburar da harkokin tattalin arziƙi, musamman ma na arewacin ƙasar da ke fama da matsaloli. Cameroon: Yara ne da ke fama da cutar nan ta HIV mai karya garkuwar jiki da ke cikin mummunar yanayi na rashin maganin rage raɗaɗin wannan cuta. Senegal: Zaɓen da aka kammala. North Korea: Koriya ta Arewa ta yi alƙawarin sake zama da Amurka bayan tashi taron birnin Hanoi da aka yi ba tare da wata nasara ba. Amurka ta taya Najeriya murnar kammala zaɓe cikin kwanciyar hankali. Somalia: Wani harin ƙunar baƙin wake, ya salwantar da rayuka a ƙasar Somaliya.

safe hiv hanoi shirin hausa arewa najeriya masana amurka shugaban najeriya muhammadu buhari
Dandalin Siyasa
Dandalin Siyasa - Shiri kan dakatar da Babban mai shari'ar Najeriya

Dandalin Siyasa

Play Episode Listen Later Jan 30, 2019 10:40


Shirin Dandalin siyasa na wannan mako ya mayar da hankaline kan dakatar da babban mai shari'ar Najeriya Walter Onnonghen da Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari yayi.

shiri najeriya shugaban najeriya muhammadu buhari