Podcasts about amurka

  • 16PODCASTS
  • 274EPISODES
  • 14mAVG DURATION
  • 5WEEKLY NEW EPISODES
  • Jun 15, 2026LATEST

POPULARITY

20192020202120222023202420252026


Best podcasts about amurka

Latest podcast episodes about amurka

Wasanni
Dalilan da ya sa ƴan Afirka suka juyawa tawagar Afirka ta Kudu baya

Wasanni

Play Episode Listen Later Jun 15, 2026 9:59


Shirin Duniyar Wasanni na wannan mako tare da Khamis Saleh ya yi duba kan irin wainar da ake toyawa a gasar nema cin kofin duniya da ƙasashen Canada da Mexico da kuma Amurka ke karbar bakunci. Danna alamar sauti don sauraron cikakken shiri........

Mu Zagaya Duniya
Shirin ya fara da yadda aka buɗe bikin gasar cin kofin duniya a ƙasar Mexico

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Jun 13, 2026 20:13


Ranar Alhamis 11 ga wannan watan  aka yi  bikin buɗe gasar cin kofin duniya karo na 23, gasar da itace karo na farko da ƙasashe 3, Amurka da Canada da kuma Mexico su ka karbi baƙunci, sai dai kuma an gudanar da zanga-zanga a wasu sassa na birnin ƙasar. Ƙasashe 48 ne ke fafata domin samun zakaran bana kuma yan wasa 1,248 da alkalan wasa 52 za su jagoranci wasanni 104 da za'a kwashe kwanaki 39 ana yi. A cikin shirin akwai labarin, shugaban Amurka Donald Trump, da ya ce ya soke shirinsa na kai munanan hare-haren da ya shirya yi a Iran, sakamakon wata tattaunawar da yace ya yi da wasu ƙusosshin gwamnatin ƙasar, Ikrarin da ya zuwa yanzu hukumomin ƙasar basu ce komai akai ba. Haka zalika, Majalisar Dokokin Najeriya ta amince da dokar kafa ƴansandan jihohi da gagarumar rinjaye, matakin da zai bai wa gwamnatocin jihohi damar kafa rundunar da za ta taimaka wajen magance matsalolin tsaron da suka addabi ƙasar. A Jamhuriyar Nijar gwamnati ce ta rattaɓa hannu a kan dokar haramta auran jinsi ko kuma mu'amalar jinsi guda wanda ta tanadi hukuncin ɗaurin da ka iya kai wa shekaru 20 a kan duk wanda aka samu da laifin yin haka. A wani abu da ba'a saba gani ba, Kungiyar mayaƙan JNIM mai alaƙa da Al Qaeda reshen Mali ta yi tayin bayar da tukwicin miliyoyin Yuro ga duk wanda ya ba ta bayanai kan inda shugaban kasar Assimi Goita  da manyan jami'an sojinsa suke, a yayin da ta bayyana gwamnatin a matsayin haramtacciyar. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin, tare da Oumarou Sani.

canada mexico iran fifa mali al qaeda bikin haka shirin duniya asar yadda shiga nijar yuro najeriya assimi goita jamhuriyar nijar amurka
Bakonmu a Yau
Abubuwan da ya kamata ku sani a gameda gasar cin kofin duniya ta 2026

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 11, 2026 3:34


Yau ake fara gasar cin kofin duniya ta bana, inda ƙasashe 48 za su fafata domin samun zakarar bana. A karon farko ƙasashe uku ne ke daukar nauyin gasar, wato Amurka da Cnada da kuma Mexico kuma kalla yan wasa 1,248 da alkalan wasa 52 za su jagoranci wasanni 104 da za'a kwashe kwanaki 39 ana yi. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar da Bashir Ibrahim Idris ya yi da tsohon Sakataren hukumar kwallon kafar Najeriya Hon Sani Ahmed Toro.....

mexico sani duniya shiga yau amurka bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Hon Sani Ahmed Toro kan ƙalubalen samun takardar Visa zuwa gasar lashe kofin duniya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 2, 2026 3:37


A yayin da ya yage kwana 9 a fara gasar lashe kofin duniya da ƙasashen Amurka da Canada da kuma Mexico za su karɓi baƙunci, har yanzu wasu ƙasashe na ci gaba da fuskantar ƙalubale wajen samun takardar izinin shiga ƙasashen. Ko a baya-bayan nan, anga yadda ƴan wasan tawagar ƙasar Afrika ta Kudu suka samu jinkiri wajen tafiya gasar sabida dalilai na Visa, bayaga ƙalubalen da ƙasashen Jamhuriyar Dimukaraɗiyyar Congo da Iran suma suka fuskanta. Kan wannan batu Khamis Saleh ya tattauna da Hon Sani Ahmed Toro, tsohon sakataren Hukumar Kwallon Ƙafara ta Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu..........

Mu Zagaya Duniya
Mahajjata kusan miliyan biyu sun gudanar da aikin Hajjin bana

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later May 30, 2026 20:57


Shirin 'Mu Zagaya Duniya' na wannan makon tare da Oumarou Sani, kamaar yadda aka saba ya yi bitar wasu daga cikin muhimman lamurran da suka wakana a makon da muka yi wa bankwana. Daga cikin muhimman batutuwan kuma akwai, yadda Musulmi kusan miliyan biyu suka samu nasarar gudanar da aikin Hajjin bana. Shirin ya kuma leƙa Yankin Gabas ta Tsakiya domin jin halin da ake ciki, musamman kan ƙoƙarin kawo ƙarshen yaƙin Amurka da Iran.

iran bana shirin daga nijar najeriya amurka musulmi
Bakonmu a Yau
Mubarak Abdul-Aziz kan ci gaban da ake samu a tattaunawar Amurka da Iran

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later May 27, 2026 3:16


A daidai lokacin da ake kan tattaunawa tsakanin Iran da Amurka don samar da yarjejeniyar kawo ƙarshen yakin da ake yi tsakaninsu, kafafen yaɗa labaran Iran sun ce akwai gagarumin cigaba a tattaunawar. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Malam Mubarak Abdul-Aziz, ɗan Najeriya mazauni Tehran, wanda ya yi masa ƙarin bayani a game da halin da jama'a ke ciki daidai wannan lokaci da ake dakon cimma yarjejeniya don kawo ƙarshen wannan yaƙi. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

iran tehran samu mubarak abdul aziz shiga najeriya amurka abdoulkarim ibrahim shikal
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan giɓin kuɗaɗe da WHO ke fuskanta

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later May 19, 2026 10:15


Yanzu haka ƙasashe masu tasowa na ci gaba da ƙoƙarin cike giɓin da aka samu bayan da Donald Trump ya janyewa tallafin da Amurka ke bai wa Hukumar Lafiya don yaƙi da wasu curutuka a duniya. A jawabinsa gaban Taron Hukumar Lafiya WHO da ke a birnin Geneva, shugaban Ghana John Dramani Mahama ya ce ya kamata Afirka ta samar da tsarin kula da lafiyar al'ummarta a maimakon barin lamarin a hannun hukumar WHO. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

donald trump masu afirka amurka yanzu
Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Dakta Nasiru Sani Gwarzo kan giɓin kasafin da WHO ke fuskanta

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later May 19, 2026 3:40


Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta fara babban taronta karo na 79 jiya Litinin a birnin Geneva, wanda kuma za a ƙarƙare shi a ranar 23 ga watan Mayu da muke. Daga cikin muhimman batututwan da taron zai fi mayar da hankali a kai dai akwai giɓin kasafin kuɗin da ya kai Dala Biliyan 1 da Hukumar Lafiyar ta Duniya ke fuskanta, da kuma tasirin janyewa daga cikinta da Amurka ta yi. Kan wannan da kuma sauran batutuwa masu alaƙa, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Nasiru Sani Gwarzo, ƙwrarre kan sha'anin lafiya da ke Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

ku sani daga duniya mayu najeriya amurka majalisar dinkin duniya
Bakonmu a Yau
Dr Kabiru Adamu kan kisan jagoran ƙungiyar IS Abu Bilal Al-Minuki

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later May 18, 2026 3:35


Yanzu haka na ci gaba da bayyana ra'ayoyi dangane da sanarwar da Amurka ta fitar da ke cewa ta kashe Abu Bilal Al-Minuki da ke matsayin jagora a ƙungiyar IS a Najeriya, labarin daga bisani hukumomin tsaron Najeriya suka tabbatar. To domin jin ƙarin bayani a game da wannan ɗan taliki da ake cewa an kashe, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Kabiru Adamu na Cibiyar da ke nazari kan sha'anin tsaro ta Beacon da ke Abuja, ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar...............

beacon ku bilal abuja adamu kisan najeriya amurka yanzu abdoulkarim ibrahim shikal
Mu Zagaya Duniya
Yadda haɗakar ƙungiyoyi suka ƙaddamar da farmaki a sassan Mali

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later May 2, 2026 20:45


Shirin ya soma daga ƙasar Mali inda a ranar 25 ga watan Afrilun da mu kayi ban kwana haɗakar mayakan Abzinawa na FLA da na ƙungiya masu ikirarin jihadi ta  JNIM suka ƙaddamar da mugayen hare-hare a garuruwa huɗu na ƙasar da suka haɗa da Sevare, Kidal, Gao da kuma  Kati. A garin Kati da ke zaman babban sansanin sojin ƙasar ƴan bindigar sun yi amfani da motoci shake da bama-bamai da manyan bindigogi inda suka kai hari kan gidan ministan tsaron kasar Sadio Camara tare da hallaka shi. A kasar Chadi kuwa aƙalla mutum 42 ne suka mutu bayan ɓarkewar wani rikicin ƙabilanci da ya faro sanadiyyar taƙaddama tsakanin wasu mata biyu yayin da suke ɗiban ruwa a wata rijiyar bayan gari. A Najeriya kuwa, ranar Alhamis ne kotun ƙolin ƙasar ta yanke hukunci kan rikicin cikin gida na jam'iyyun ADC da PDP. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin, tare da Oumarou Sani.

Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Dr Yahuza Getso kan yarjejeniyar tsaro tsakanin Najeriya da Turkiya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Apr 20, 2026 3:27


Najeriya da kuma Turkiyya sun ƙulla yarjejeniyar tsaro a tsakaninsu, wadda a ƙarƙashinta matakin farko Najeriya za ta tura zatan sojoji 200 don samun horo na musamman a Turkiyya. Hakan dai na zuwa ne watanni kaɗan bayan da mahukuntan a birnin Abuja suka sanar da ƙulla irin wannan yarjejeniya da ke bai wa Amurka damar turo sojojinta zuwa Najeriya don yaƙi da ta'addanci? Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tsaro lamurran tsaro Dr Yahuza Getso, domin jin tasa fahintar a game da yadda alaƙar tsaron za ta kasance tsakanin Najeriya da kuma Turkiyya. Ga dai zantawarsu.

ga hakan abuja najeriya amurka abdoulkarim ibrahim shikal
Mu Zagaya Duniya
Makomar masu shiga tsakani,kan neman ƙulla yarjejeniya tsakanin Amurka da Iran

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Apr 18, 2026 20:01


Mecece makomar ƙoƙari da masu shiga tsakanin, musamman Pakistan ke yi a kan neman ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran duba da tsaurin wasu ko da dama daga cikin sharuɗɗan da ɓangarorin biyu suka gabatarwa juna? Nura Ado Suleiman ke  yi muku barka da sake haɗuwa cikin shirin Duniyarmu a Yau

Bakonmu a Yau
Abubuwan da suka haifar da saɓani a tattaunawar Amurka da Iran

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Apr 13, 2026 3:32


An tashi baram-baram tsakanin Amurka da Iran a tattaunawar da suka faro ranar Asabar a birnin Islamabad bisa shiga tsakanin Pakistan a ƙoƙarin kawo ƙarshen wannan yaƙi, tattaunawar da ke zuwa bayan cimma jituwar tsagaita wutar kwanaki 14 tsakanin ɓangarorin biyu. Tuni ƙasashe suka fara kiraye-kirayen ganin rashin cimma jituwar Amurkan da Iran bai taɓa yarjejeniyar da ke tsakaninsu ba Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hira da Dakta Dicko Abdourahmane malami a jami'ar Zinder Nijar....

Mu Zagaya Duniya
An cimma yarjejeniyar tsagaita wutar makwanni 2 tsakanin Amurka da Iran

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Apr 11, 2026 20:29


Shirin 'Mu Zagaya Duniya' tare da Oumaru Sani, ya yi bitar wasu daga cikin muhimman labaru kan lamurran da suka wakana a makon da muka yi wa bankwana, daga cikinsu kuma akwai yarjejeniyar tsagaita wutar kwanaki 14 da aka cimma tsakanin Amurka da Iran, bayan da ƙasar Pakistan ta shiga tsakani.

Bakonmu a Yau
Riya'uddeen Zubairu Maitama kan yarjejeniyar tsagaita wutar Amurka da Iran

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Apr 9, 2026 3:24


‘Yan Sa'o'i bayan amincewa da yarjejeniyar tsagaita wutar kwanaki 14, Amurka da Iran sun zargi juna da karya yarjejeniyar, lamarin da ya kai ga Iran ta sake datse mashigin ruwan Hormuz jim kaɗan bayan buɗe shi da ta yi. Domin jin yiwuwar ɗorewar wannan yarjejeniya ta tsagaita wuta da kuma makomar ƙoƙarin da masu shiga tsakani ke yi, Nura Ado Suleiman ya tattauna da masanin Siyasar ƙasa da ƙasa, Dakta Riya'uddeen Zubairu Maitama na Jami'ar Bayero da ke Kano a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar ta su.............

Mu Zagaya Duniya
Rikicin Gabas ta Tsakkiya: Dakarun Amurka sama da 2000 sun isa yankin

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Apr 4, 2026 20:55


Shirin mu na yau ya fara yadda zango a yankin Gabas ta Tsakiya inda rikicin Amurka da Isra'ila kan Iran ke cigaba da tsananta duk da tayin shiga tsakani da wasu kasashen Larabawa su ka faro karshen mako a Pakistan  da zummar kawo karshen rikicin da tuni ya kasara tattalin arzikin duniya. A cikin ranakun ƙarshen mako kamfanin dilancin labaran Reuters ya bayyana cewa sojojin Amurkan dubu 2 da 500 sun isa yankin na Gabas ta Tsakiya. 

Bakonmu a Yau
Darusan da aka koya a kwanaki 30 na yakin Gabas ta Tsakiya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 30, 2026 3:35


Yayinda ake cika wata guda curr da fara yaƙi tsakanin haɗin gwiwar Amurka da Isra'ila a gefe guda kuma da Iran, a yau ɓangarorin da ke rikici na ƙara zafafa hare-hare, a wani abu da duniya ke ci gaba da mamakinsa. Zuwa yanzu dai wannan yaƙi ya laƙume dubban rayuwa, inda kuma Iran ke zargin Amurka da shirya afka mata da sojoji ta ƙasa, yayinda wasu ƙasashe suka fara yunƙurin sulhunta tsakani. Shiga alamar sauti don sauraron karin bayani a hirar da Rukayya Abba Kabara ta yi da Bash M Bash....

Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Dr Maman Kassou na jami'ar Andre Salifou a Nijar kan cinikin bayi

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 26, 2026 3:34


Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana fataucin bayi da aka share ɗaruruwan shekaru ana yi daga Afirka zuwa Turai da Amurka a matsayin ‘'cin zarafin bil  Adama mafi girma'' da aka taɓa gani a tarihi. Ƙasashen duniya 123 ne suka kaɗa ƙuri'ar goyon bayan wannan ƙuduri, wasu uku wato Amurka, Isra'ila da Argentina suka ƙi amincewa yayin da wasu ƙasashe 52 suka yi ƙememe ta hanyar rowar ƙuri'unsu. To domin tuni a game da lokacin da aka fara ɗibar bayi daga Afirka da kuma yadda hakan ya shafi ci gaban nahiryar, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tarihi Dr Maman Kassou, malami a jami'ar Andre Salifou da ke Damagaram, ga kuma zantarwarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.

argentina ku isra maman adama bayi duniya nijar turai afirka amurka majalisar damagaram abdoulkarim ibrahim shikal
Bakonmu a Yau
Yadda rikicin Gabas ta Tsakiya ke tasiri akan farashin kayayyaki a duniya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 25, 2026 3:38


Farashin hajoji da sauran muhimman abubuwa na ci gaba da hauhawa a kasuwannin duniya sakamakon yadda yaƙin da ake yi a yankin Gabas ta Tsakiya ya hana fitar da mafi yawan man fetur da kamfanoni da masana'antu suka yi oda ya maƙale a Mashigin Ruwan Hormuz. To domin fahintar girman wannan matsala da kuma ɓangarorin da suka fi fama da ƙarancin makamashi a duniya saboda wannan rikici, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya tuntuɓi masani tattalin arziki Dr Isa Abdullahi, malami a jami'ar Tarayya da ke Kashere a jihar Gomben Najeriya, ga kuma zantawarsu. A latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawar

iran akan duniya yadda amurka abdoulkarim ibrahim shikal
Bakonmu a Yau
Yaƙin da ake a Iran ya ritsa da ɗimbin ƴan ƙasashen waje da ke karatu a ƙasar

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 24, 2026 0:59


Yanzu haka yaƙin da ake fama da shi a yanzu Gabas ta Tsakiya ya rutsa da ɗimbin ƴan kasashen waje musamman ɗalibai da ke karatu a ƙasar Iran. To sai dai yayin da wasu ƙasashe suka fara kwashe mutane zuwa gida ko kuma wasu ƙasashe, amma har yanzu Najeriya ba su samu irin wannan tallafi daga gwamnatinsu ba. A game da haka ne Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Muhammad Umar Nuruddeen, ɗaya daga cikin ɗaliban ƴan Najeriya wadanda adadinsu ya zarta 500, wanda ya fara da yin bayani a game da yadda rikicin ya tarar da su Ku latsa alamar sauti da ke sama domin jin wannan tattaunawa.................................

iran ku asar waje najeriya amurka yanzu abdoulkarim ibrahim shikal
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu saurare kan yadda yaƙin Gabas ta tsakiya ya haddasa tsadar kayan masarufi

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Mar 23, 2026 10:24


An shiga mako na huɗu da barkewar rikicin Yankin Gabas ta Tsakiya, inda ɓangarorin da ke hannu a rikicin ke ci gaba da kai wa juna hare-hare tare da kashe mutane da kuma lalata cibiyoyin makamashi. Tuni dai hakan ya haifar da tashin goron zabi ga farshin abubuwa da dama sanadiyar hauhawar farashin mai a kasuwar duniya. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabiru Yusuf

iran ku yadda masu kayan tuni amurka
Kasuwanci
Koma bayan da kasuwancin duniya ya fuskanta sakamakon rikicin Gabas Ta Tsakiya

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Mar 18, 2026 10:18


Shirin "Kasuwa Akai Miki Dole" tare da Ahmed Abba a wannan mako ya ɗora ne kan inda ya tsaya a makon jiya, game da gagarumin koma baya a fannin kasuwanci da tattalin arziki da duniya ke fuskanta masamman a bangaren makamashi, sakamakon yaƙin da kawancen Amurka da Isra'ila suka kaddamar kan Iran, da kuma martinin jamhuriyar musuluncin kan Isra'ila da muradun Amurka a kasashen labarawa suka janyo. A makon jiya, shirin ya tattauna wannan batu ne da malaman da muka gayyato, wato Dr. Aminu Idris Harbau masamanin tattalin arziki a tarayyar Najeriya, da Dr. Ibrahim Adamu na sashin nazarin yankin gabas ta Tsakiya a jami'ar Havard da ke Dubai na haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, sai Mohammad Qaddam Sidiq Isa, mai sharhi kan al'amuran Yau da Kullum shima a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, sai kuma Isma'il Albabawee ɗan jarida kuma ɗalibi a jami'ar Karbala a ƙasar Iraki. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

Bakonmu a Yau
Amurka na ci gaba da lallshn ƙawanta wajen samun buɗe mashigin Hormuz

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 16, 2026 3:39


Shugaban Amurka Donalad Trump, ya ce yanzu haka ya samu tabbaci daga wasu ƙasashen duniya cewa za su taimaka don tabbatar da cewa an ci gaba da zirga-zirgar jiragen ruwa a Mashigin Ruwan Hormuz. Domin jin irin sarƙaƙiyar da ke tattare da irin wannan aiki, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tsaro Air Commodore Tijjani Ahmed Baba Gamawa mai ritaya, ga kuma zantawarsu. A lasa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

hormuz gaba domin amurka abdoulkarim ibrahim shikal
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Yadda farashin makamashi ya yi tashin gwauro zabi a duniya

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Mar 12, 2026 9:41


Yanzu haka farashin ɗanyen man fetur na ci gaba da hauhawa sakamakon yaƙin da Amurka da Isra'il suka ƙaddamar kan Iran, inda yanzu haka ake sayar da gangar mai fiye da dala 92 a kasuwar duniya. A wannan yanayi dai ko shakka babu, ƙasashe masu arzikin mai ne irinsu na Najeriya za su ci moriyar wannan rikici. Shiga alamar sauti, domin suararon cikakken shirin.

Kasuwanci
Yadda yaƙin Iran ya haifar da koma baya ga tattalin arzikin Duniya

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Mar 11, 2026 9:56


A yau shirin Kasuwa A kai Miki Dole na wanan mako tare da Ahmad Abba ya mayar da hankali ne a kan yadda Yaƙin da kawancen Amurka da Isra'ila suka kaddamar kan Iran, da hare-haren mayar da martini na jamhuriyar musuluncin kan yahudun Isra'ila da muradun Amurka a kasashen labarawa suka janyo gagarumar koma baya a fannin kasuwanci da tattalin arzikin duniya masamman a bangaren makamashi.     Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin......

Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Dr Isa Abdullahi illar yaƙin Amurka a Iran ga tattalin arziƙin duniya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 10, 2026 3:13


Ƙasashen duniya sun fara jin raɗaɗin yaƙin Iran sakamakon tashin farashin man fetur a kasuwannin duniya, wanda ya shafi harkokin yau da kullum. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Isa Abdullahi, masanin tattalin arziki a kan lamarin, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

iran ku duniya abdullahi amurka bashir ibrahim idris
Wasanni
Amurka ta gargaɗi masu aniyar maƙalewa idan suka je kallon gasar cin kofin duniya

Wasanni

Play Episode Listen Later Mar 9, 2026 10:00


Shirin Duniyar Wassani a wannan lokaci yayi duba ne kan yadda Amurka ta fara gargaɗin ƴan Ghana da ke da aniyar maƙalewa idan suka je ƙasar don kallon gasar cin kofin duniya da ƙasashen Amurka da Canada da kuma Mexico za su karɓi baƙunci a watan Yuni mai zuwa. Ganin irin matakan da dama gwamnatin Amurka ke ɗauka kan shigar baki ƙasar tuni ofishin Jakadancin ƙasar da ke Ghana ya fara gargaɗin masu shirin halartar gasar da su guji wuce wa'adin da aka basu. Jakadan Amurka a Ghana Rolf Olson ya ce saɓawa dokokin shige da fice na ƙasar na iya haifar da mummunan sakamako, gami da rashin sake samun damar shiga ƙasar a nan gaba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh..............

Mu Zagaya Duniya
Yadda rikicin Iran ke faɗaɗa a yankin Gabas ta Tsakiya

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Mar 7, 2026 20:44


A Wanan makon shirin zai karkata alakarsa ne yankin Gabas ta Tsakiya inda sabon rikici ya barke tsakanin hadakar Amurka da Isra'ila da kuma Iran. A cikin shirin zamu yi duba dangane da yadda rikicin  ke cigaba da faɗaɗa zuwa sauran kasashen yankin da ma  tasirinsa kan bangarori daban-daban a  wanan duniyar sai a gyara zama domin sauraron cikakakken shirin.

Tambaya da Amsa
Shin akwai dokar da ta ba Amurka damar hukunta wani sshugaban ƙasa?

Tambaya da Amsa

Play Episode Listen Later Mar 7, 2026 21:31


  Shirin 'Tambaya da Amsa' shiri ne da ke zuwa muku da  amsoshin wasu tambayoyin da masu sauraronmu suka aiko mana, kuma a kowane mako yake zuwa muku a daidai wannan lokaci. A yau shirin tambaya da amsa zai fara ne da bayani akan ko akwai wata doka da ta baiwa shugaban Amurka Donald Trump ikon hukunta wani shugaban ƙasa a Duniya.

Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Dakta Bashir Nuhu Mabai kan sake ta'azzarar yaƙin Iran da Amurka

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 5, 2026 3:40


Masana siyasar Duniya gami da rikicin Yankin Gabas ta Tsakiya, na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu kan yaƙin da ya shiga rana ta shida tsakanin Iran da Amurka, wadda ke taimaka wa Isra'ila. Ya zuwa jiya Laraba dai Isra'ilar ta yi iƙirarin kai wa Iran hare-hare sama da dubu 5, yayin da ita ma Amurka ke ci gaba kai wa Iran ɗin farmaki ta sama, da zummar rusa duk wani ƙarfi da ya rage wa gwamnatin ƙasar. Kan wannan, da kuma yadda yaƙin ke daɗa rincaɓewa da shafar ƙasashen Yankin Gabas ta Tsakiya, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Bashir Nuhu Mabai, Malami a Jami'ar Dutsinma da ke Katsina a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

iran sake ku isra bashir duniya katsina najeriya masana malami amurka
Bakonmu a Yau
Ana zaman ɗar-ɗar a Iraqi da sauran ƙasashen yankin Gulf saboda hare-haren Iran

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 4, 2026 3:35


Iran ta ci gaba da kai munanan hare-hare kan Isra'ila da muradun Amurka a Gabas ta Tsakiya.To sai dai ƙasashen yankin Gulf na zarginta da faɗaɗa hare-haren kan fararen hula da ababen more rayuwa kamar Otel-otel da filayen jiragen sama da kuma cibiyoyin makamashi. Ko a jiya, dakarun juyin juya halin Iran sun yi ikirarin tarwatsa cibiyoyi da dama a yankin kurdawa, wadanda ta ce mayakanta na shirin yi mata kutse domin kai mata hare-hare. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....

Madubin Kabara
Nazir Hausawa (Ziriums) | MUK Na 37

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 22, 2025 59:34


Nazir Ahmed Hausawa (Ziriums), yana daya daga cikin ‘yan masana'antar finafinan Kannywood, Makadin Fiyano, Mawakin gambarar Hausa HipHop, Tsohon malamin koyar da kida, Tsohon ma'aikacin BBC World Service Trust da VOA Hausa, Masanin harkokin gidajen alfama na Amurka. A cikin hirarsa da Madubin Usman Kabara a Amurka, ya bayyana min darussan da ya koya a zamansa na shekaru a Amurka.

nazir amurka hausawa
Madubin Kabara
Nafisat Abdullahi | MUK Na 36

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 88:02


Na sami yin hira da shahararriyar Jarumar Fina-finan Hausa Nafisat Abdullahi a birnin Washington DC da ke Amurka, don sanin asalinta da kuma yadda take tafiyar da rayuwarta.

Madubin Kabara
Usman Umar SojaBoy | MUK Na 31

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 35:52


Usman Umar da aka fi sani da Soja Boy mawaki ne, dan wasan kwaikwayon zahirin rayuwa da ya fito a tauraron wani shirin wasan talbijin a Amurka mai suna 90DayFiance wanda ake bibiyar saurayi da budurwa don ganin yadda alakarsu ta soyayya ke tafiya.

Madubin Kabara
Na'ima Idris Usman | MUK Na 32

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 14:14


Na'ima Idris Usman, cikakkiyar Likita ce da ke jihar Kanon Najeriya, ta yi karatun a tsakanin Najeriys da China. Ta bamu labarin rayuwarta daga kuruciya zuwa girmanta, da ma yadda aka yi ta fara ilimantar da mata ta kafafen sada zumunta game da lafiyar jikinsu duk da cewa furta kalmomin da ke da alaka da al'aura abu ne mai cike da kalubalen a kasar Hausa. Da kuma yadda karshe ta buge da zuwa shirin horar da shugabanci ga matasan Afirka a Amurka da a turance ake kira da Mandela Washington Fellowship da aka fi sani da Young African Leaders Initiative (YALI) na shekarar 2022.

china usman hausa mandela washington fellowship afirka amurka young african leaders initiative yali
Madubin Kabara
Adamu Garba II | MUK Na 28

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 30:26


Adamu Garba II matashi ne mai kwarin gwiwa sannan wanda ya ke dan kasuwar da yayi iliminsa a tsakanin Najeriya har zuwa Amurka. Yana daga cikin 'yan takarar Shugaban Kasar Najeriya a shekarar 2023 mafi karancin shekaru a tsakanin masu neman wannan kujera a kasar da ta fi kowa ce kasar Afirka yawan al'umma da kuma karfin arzikin man fetur. Shine kuma wanda 'yan uwa da abokan arziki suka tara wa sama da naira miliyan 80 don yin takara a jam'iyyar APC amma kwatsam sai ya canja sheka zuwa YPP.

shine yana apc garba adamu ypp najeriya afirka amurka
Madubin Kabara
Nura Abubakar | MUK Na 25

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 29:43


Dalibi ne da ya ke digirin digirgir a fannin Turanci da fasahar hotunan finafinan majigi. Matashin ya bayyana yadda jin wani shiri a gidan radiyon Muryar Amurka na VOA ya ba shi kaimin neman zuwa karatu a Amurka, har ya buge da koyar da harshen Hausa tun a digirinsa na biyu a wata jami'a ta Amurka.

Madubin Kabara
Iman Al-Hassan | MUK Na 23

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 19, 2025 22:55


Karatu ne ya kai iyayen Iman Yusuf Al-Hassan zuwa Amurka, wanda su 'yan asalin jihohin Kano da Jigawa ne a Arewacin Najeriya, amma kuma kaddarar zama ta kama su har suka hayayyafa. Iman ta fada min yadda take da burin zaman Najeriya duk kuwa da cewa a Amurka aka haifeta ta girma.

iman kano jigawa najeriya amurka
Madubin Kabara
Hadiza Aliyu Gabon | MUK Na 21

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 11, 2025 16:01


Hadiza Aliyu da aka fi sani da Gabon, na daya daga cikin fitattun taurarin fina-finan Hausa mafi shahara. Ta shiga Najeriya a lokacin da bata jin Hausa, amma kuma tana son zama tauraruwar fina-finan Hausa na Kannywood. Yanzu kuma sai gashi mun da cewa tana yawan tafiye-tafiye zuwa kasashen duniya, ciki har da Amurka inda muka yi wannan hirar da ita.

gabon hausa najeriya amurka yanzu
Madubin Kabara
Mohammed Ladan | MUK Na 19

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 10, 2025 33:46


Dakta Mohammed Ladan dai an fi saninsa da suna Dakta Ladan, sakamakon wani fitaccen shirin lafiya na gidan radiyon sashen Hausa na Muryar Amurka. Amma a likitance shi masanin kimiyyar hada magunguna ne wato ‘phamacist'. Dan asalin jihar Neja ne da ke Arewacin Najeriya, sannan a yanzu mazaunin Amurka fiye da shekara 40 tun bayan zuwansa.

Madubin Kabara
Maimuna Sulaiman Bichi | MUK Na 21

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 10, 2025 40:51


Maimuna Sulaiman Bichi da aka fi sani da ‘yar Bichi ko Lolo's Kitchen ‘yar asalin Najeriya ce ta suka dawo Amurka da zama tun tana shekaru 15 da haihuwa. Ta kuduri aniyar bude gidan abincin da zai kware a girke-girke musamman ma irin na gargajiyar Hausawa.

kitchen lolo sulaiman najeriya amurka hausawa
Madubin Kabara
Yusuf Al-Hassan | MUK Na 16

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 9, 2025 61:57


Farfesa Yusuf Al-Hassan dan asalin cikin birnin Kano ne a Najeriya da ya kwashe shekaru yana koyo da koyarwa a tsakanin Najeriya da Amurka game da ilimin fasahar sana'o'in hannu inda har ya taba zama zakaran gasar malaman koyar da sana'o'i ta Amurka. Malamin ya kuduri aniyarsa ta yadda zai taimaki Najeriya ta hanyar kai Kanawa 100 zuwa Amurka don koyon ilimin sana'a.Yusuf Al-Hassan | MUK Na16

kano kanawa najeriya amurka
Madubin Kabara
Hauwa Mustapha Babura | MUK Na 13

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 8, 2025 30:54


Na yi hira da Hauwa Mustapha Babura, 'yar asalin garin Babura da ke jihar Jigawa ta Arewacin Najeriya. Ta bani labarin rayuwarta tun bayan shigarta Amurka da kuruciya, inda a yanzu haka 'yar kasa ce a can kamar yadda take a kasarta ta asali. Da kuma yadda aka yi ta zama kwararriyar malamar makaranta a bangaren ilimin kananan yara da kuma yadda ake renon kwakwalwarsu.

mustapha jigawa amurka
Madubin Kabara
Abba Zubair | MUK Na 14

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 8, 2025 41:16


Farfesa Abba Zubair Chedi na asibitin Mayo Clinic da ke Amurka, dan asalin jihar Kano ne a Najeriya da ya yi kaurin suna a Amurka, musamman a lokacin da ya shiga binciken yadda za a yi amfani da kimiyyar kwayar halitta ta 'stem cell' wajen kirkirar sassan jikin bil'adama, kamar zuciya da huhu don dasa wa mutanen da sassan jikin ya lalace ba tare da jiran sai wani ya mutum a cire a saka wa wani ba.

Madubin Kabara
Murtala Mai | Madubin Usman Kabara #11

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 20, 2025 56:11


Dr. Murtala likitan yara ne dan asalin jihar Adamawar Najeriya da ya rikide ya zama kwararren masanin lafiyar al'umma musamman mata da yara, wanda a yanzu haka ma'aikaci ne a wata kungiya mai zaman kanta da ta ke tallafawa harkokin lafiyar iyali a duniya ciki har da kasashen Afirka mai suna Pathfinder International da ke kasar Amurka.Murtala Mai | Madubin Usman Kabara #11

usman afirka amurka kabara
Madubin Kabara
Fadji Maina | Madubin Usman Kabara #10

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 19, 2025 45:45


‘Yar Nijar kuma masaniyar kimiyyar ruwa da doron kasa da ke aiki a hukumar sama-jannatin Amurka ta NASA. Dr. Fadji Maina tana cikin wacce mujallar tereren arziki ta Forbes ta wallafa sunanta a cikin matasan duniya guda 30 ‘yan kasa da shekara 30 da suka sami nasara a rayuwa. Yanzu haka ma'aikaciya ce a hukumar sama jannatin Amurka ta NASA da ke aiki bisa kwarewar ta a fannin ruwa da kimiyyar doron kasa.

forbes nasa usman maina amurka fadji yanzu kabara
Madubin Kabara
Sarki Abba Abdulkadir | Madubin Usman Kabara #9

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 18, 2025 61:07


A shekarar 1984 a Najeriya an sami wani saurayi dan jihar Kano da ya fi kowane dalibi a Najeriya cin makin jarrabawar gama sakandaren kasashen Afirka ta WAEC a takaice. Yanzu haka dai wannan dalibin mai suna Farfesa Sarki Abba Abdulkadir farfesa ne a bangaren haddasuwar cututtuka a Jami'ar Northwestern University da ke Chicago a Amurka.

chicago abba northwestern university usman kano sarki abdulkadir najeriya afirka amurka yanzu kabara
Madubin Kabara
Adamu Hamza Bamalli | Madubin Usman Kabara #7

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 16, 2025 120:07


Adamu Hamza Bamalli ya sha gwagwarmaya a Najeriya da Amurka kama daga zama direban babbar mota zuwa rikidewa ya zama kwararren Injiniya a jihar Maryland ta Amurka.

maryland usman adamu najeriya amurka kabara
Madubin Kabara
Sabo Tanimu | Madubin Usman Kabara #3

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 12, 2025 29:40


Na ziyarci Dr. Sabo Tanimu a jihar Wisconsin ta Amurka. Yana daya daga cikin kwararrun likitocin kayan cikin bil'adama a kasar inda yake shugabantar bangaren cutar dajin da ta shafi kayan ciki. Dan asalin Najeriya ne daga jihar Benue a tsakiyar Arewacin Najeriya. Shin yaya aka yi Likita Sabo ya fara daga Najeriya har ya tsinci kansa a Amurka inda ya shafe shekaru da dama yana aikin Likita a can.

wisconsin shin usman yana sabo benue najeriya amurka kabara
Madubin Kabara
Ali Nuhu | Madubin Usman Kabara #2

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 11, 2025 12:09


Na yi hira da Ali Nuhu Mohammed jarumin fina-finan Hausa da Turanci na Najeriya a lokacin da ya ziyarci birnin Washington DC da ke Amurka,, in da na tambaye shi darussan da ya koya a cikin shekaru 20 da ya kwashe yana harkar shirya finafinai.

washington dc usman hausa najeriya amurka kabara