POPULARITY
A ranar Alhamis, shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaddamar da fara aikin Kwamitin Zaman Lafiyar Duniya da ya kafa. Wakilai daga aƙalla ƙasashe 47 da kuma ƙungiyar Tarayyar Turai da Isra'ila ne suka halarci taron farkon na Kwamitin Zaman Lafiyar na Duniya a birnin Washington. Muhimman batutuwan da taron ya mayar da hankali kai sun haɗa da kafa Rundunar zaman lafiya a Gaza, da karɓe makamai daga hannun Hamas, da kuma sake gina Zirin na Gaza. Shiga alamar sauti, domin sauraron tattaunawar Nura Ado Suleiman da AbdulHakim Garba Funtua, masanin siyasar ƙasa da ƙasa.
Shirin 'Mu zagaya Duniya' na wannan mako tare da Oumar Sani kamar kullum ya mayar da hankali kan labarai da suka fi ɗaukar hankali a makon da muka bankwana da shi, masamman harin da ya kashe sama da mutane 170 a jihar Kwara dake arewacin Najeriya.
Amurka ta sanar da tura wata tawagar sojinta zuwa Najeriya, abinda a karon farko ke tabbatar da isar dakarun nata ƙasar, tun bayan ƙarfafa yarjejeniyar tsaron da ƙasashen biyu suka yi, biyo bayan zargin da shugaba Donald Trump ya yi a shekarar bara, cewa ana kashe Kiristoci a Najeriyar. Kwamandan rundunar sojin Amurka da ke kula da Afirka, Janar Dagvin R.M. Anderson ya ce sun tura dakarun ne a bisa amincewar Najeriya. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Yahuza Ahmed Getso masanin tsaro a Najeriya. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.......
Yau shirin ya mayar da hankali ne dangane gagarumar yarjejeniyar cinikayya mafi girma da ba'a taba ganin irinta ba, da aka cimma tsakanin ƙungiyar Tarayyar Turain ƙasar India. Yarjejeniyar da aka cimma yayin ziyarar da shugabannin Turai suka kai New Delhi na ƙasar India, za ta bada damar kasuwanci mara shinge tsakanin ƙasashe mambobin EU 27 da kuma ƙasar da ta fi yawan jama'a a duniya, waɗanda suka kaɗai suka mamaye kusan kashi 25% na jimillar hada-hadar kasuwancin cikin gida na duniya da kuma cinkayyar mutane biliyan biyu. Domin ko a shekarar 2024 kaɗai, an yi cinikin sama da Euro biliyan 120 a tsakanin ɓangarorin biyu. Masu sharhi na ganin cewa kalaman wannan yarjejeniya da ɓangarorin biyu suka cimma, alaƙa da manufofin Shugaban Amurka, Donald Trump, musamman duba da yadda Tarayyar Turai ke ƙoƙarin faɗaɗa abokan hulɗar kasuwancinta, ba tare da dogaro da Amurka kaɗai ba. Yarjejeniyar dai na nufin cewa daga yanzu, India za ta soke ko kuma zaftare haraji kan hajoji da dama da take shigarwa yankin Turai, da suka haɗa da motoci daga kaso 110% zuwa 10% kachal, matakin da zai shafi kayan abinci da barasa da tufafi da kayan ado da dai sauransu. An dai ƙulla yarjejeniyar ce a daidai lokacin da mafi yawan ƙasashen duniya ke takun-saka da Amurka sakamakon haraji babu ƙaƙƙautawa da Donald Trump ke amfani da shi don tursasawa abokan hulɗa. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.
A Najeriya babban abin da mafi yawan mutane ke neman ƙarin haske a kai su ne abubuwan da ke ƙunshe a yarjejeniyar tsaron da aka ƙulla tsakanin ƙasar da Amurka domin kawo ƙarshen ƴanbindigar da Amurkan ta ce suna yi wa Kiristoci kisan gilla. A game da wannan yarjejeniyar ce Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Yahuza Getso, masani tsaro da ke game da ayykan ƴanbingar da suka addabin jama'a, ga kuma yadda zantawarsu ta gudana. A latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar zantawar.
Amurka ta kawo ƙarshen tallafin da ta ke bayar wa a hukumar Lafiya ta Duniya WHO daga wannan Alhamis, 22 ga watan Janairun 2026, duk kuwa da kasancewarta jigo wajen samar da kuɗaɗen tafiyar da hukumar wadda ke samar da tallafin magunguna da sauran ɓangarorin lafiya ga ƙasashe da dama musamman masu tasowa. Donald Trump ya sanar da aniyar janyewar ƙasar daga hukumar koda yake tun a wancan lokaci ya ƙulla yarjejeniyar cewa sai bayan shekara guda ne ficewar za ta fara aiki a hukumance. Kan haka ne Faruk Muhammad Yabo ya tattauna da Dr Adam Mustapha na sashen nazarin ƙananan halittu a jami'ar Maiduguri ya yi mana tsokaci kan illar da matakin na Amurka ka iya haifarwa.
Yau Donald Trump ke cika shekara guda da komawa shugabancin Amurka, wa'adin da wasu ke ganin tamkar shugaban ya shafe shekara da shekaru bisa mulkin, la'akari da jerin matakan da ya riƙa aiwatarwa a matakin ƙasa da ƙasa da kuma cikin gida, ba tare da la'akari da caccakar da ake yi masa ba a gida da waje. Domin jin hasashen masana kan abinda ke tafe a ragowar shekaru uku da suka rage wa shugaban na Amurka Donald Trump, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta AbdulHakim Garba Funtua masanin siyasar ƙasa da ƙasa. Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawarsu...........
Shirin tambaya da amsa da ke zuwa muku da wasu amsoshin tambayoyin da masu sauraronmu su ka aiko mana, mu kan mika wadanan tambayoyi ga masana domin baku amsar da ta dace................
Mahukuntan Iran sun yi barzanar amfani da hukuncin kisa kan masu zanga-zangar wadda ta juye zuwa tarzoma inda ofishin babban mai shigar da ƙara na gwamnati ya ce akwai yiwuwar idan aka fara ɗaukar wannan mataki a samu sassaucin zanga-zangar. A nasa bangare shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar daukar mataki mai tsauri kan Iran muddun hukumomin ƙasar suka fara kashe masu zanga-zangar tsadar rayuwa.
Hedikwatar rundunar sojin Amurka mai kula da nahiyar Afirka, AFRICOM, ta sanar da miƙa wa gwamnatin Najeriya taimakon kayayyakin aikin soji, matakin da ke ƙarfafa yarjejeniyar tsaron da ke tsakaninsu don yaƙi da ta'addanci. Sai dai cikin sanarwar da ta wallafa a shafinta na X, rundunar sojin Amurkan ba ta yi ƙarin bayani kan nau'ika da kuma adadin makaman ba. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Kabiru Adamu shugaban kamfanin Beacon Consulting da ke bincike kan tsaro a nahiyar Afrika.
Amurka ta sanar wa bai wa Najeriya wasu muhimman kayan aikin soji domin tunkarar ƙalubale na tsaro da ƙasar ke fama da shi. Rundunar Amurka mai kula da nahiyar Afirka wato Africom ce ta sanar da hakan, sama da makonni biyu da Amurka ta ƙaddamar da farmakin farko kan wasu wurare ta bayyana cewa maɓoyar yan ta'addace. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Gwamnatin Iran ta ce tabbas an buɗe hanyoyin tuntubar juna tsakaninta da Amurka, bayan da shugaba Donald Trump ya yi barazanar yin amfani da ƙarfi kan ƙasar matuƙar ta ci gaba da kashe masu zanga-zanga. Mahukuntan Iran dai na ƙoƙarin shawo kan ɗaya daga cikin bore mafi muni da suka taɓa faruwa a ƙasar. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon jakadan Najeriya a Iran Amabasada Abubakar Cika, ga kuma zantawarsu dangane da wannan tarzoma ta Iran. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
A cikin shirin na wannan mako tare da Oumarou Sani, zakuji bitar muhimman labaran da suka wakana a makon da muke bakwana da shi, ciki har da yadda Amurka ta yi gaban kanta wajen kutsawa cikin Venezuela tare da kame shugaba Nicolas Maduro. Muna tafe da tattaunawar masana a ɓangarori daban-daban kan wannan katsalandan na Amurka. Hallau dai a cikin shirin zaku ji bitar ɓarkewar sabon rikici a Yemen da Syria. A Najeriya kuwa akwai mu da bitar hare-haren ƴan ta'adda a jihar Neja da kuma rikicin siyasar ƙasar. Ku latsa lamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin 'Kasuwa A kai Miki Dole' na wannan mako tare da Ahmed Abba ya tattauna da masana da sauran masu ruwa da tsaki kan harkokin man fetir dangane da tasirin kama shugaban ƙasar Venezuela Nicolas Maduro da Amurka ta yi zai yi ga tattalin arzikin duniya.
Mahukuntan jamhuriyar Nijar sun shelanta kafa dokar-ta-ɓaci, wanda a ƙarƙashinta gwamnati za ta iya yin amfani da illahirin al'ummar ƙasar da kuma dukiyoyinsu duk lokacin da ta ga ya dace saboda tunkarar barazanar tsaro. Matakin ya zo ne kwanaki ɗaya bayan da Amurka ta ƙaddamar da farmaki kan maɓoyar ƴanbindiga a wani wuri da ke jihar Sokoton Najeriya daf da iyaka da Nijar. Shin ko me za ku ce a game da matakin? Anya hakan zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro da ƙasar ke fama da su? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
Gwamnatin Najeriya ta ce da saninta Amurka ta ƙaddamar da hari jihar Sokoto da ke shiyar Arewa maso Yammacin ƙasar a makon daya gabata, inda ta ce an kai harin ne kan ƴan ta'addan da ta ce ke kwarara cikin ƙasar daga yankin Sahel. Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabir Muhammad Ɗan Bauchi.
A Najeriya, ko baya ga farbaga dangane yadda Amurka ta fara kai hare-hare ta sama a kan waɗanda ta kira a matsayin ƴanta'adda a yankin arewacin ƙasar, wani abin tambaya shi ne halascin ɗaukar mataki bai wa wata ƙasa ta ƙetare damar yin amfani da sojojinta ba tare da amincewar majalisun dokokin ƙasar ba. Abdoulkarim Ibrahinm Shikal ya zanta da masani doka Barrister Modibbo Bakari Danna alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hirar.......
A cikin daren ranar Alhamis da ta gabata Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da harin da Amurka ta kai a wasu yankuna biyu na jihar Sokoto wato Tangaza inda nan ne ‘yan Lakurawa ke da maɓoya da kuma Jabo da ke yankin ƙaramar hukumar Tambuwal. Sai dai mazauna yankin Jabo sun bayyana fargabar zama a ƙauyukansu saboda fargabar yin kuskuren kai musu farmaki a yayin wasu hare-haren da watakila Amurkar ka iya kai wa a nan gaba.
Da sanyin safiyar yau Juma'a aka wayi gari da sanarwar gwamnatin Najeriya da ke tabbatar da harin da Amurka ta kai a wasu yankunan ƙananan hukumomin Tambuwal da Tangaza, da ke jihar Sokoto a yankin arewa maso yammacin ƙasar. Ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Maitama Tuggar, ya ce Amurka ta kai hare-haren ne tare da haɗin gwiwar dakarun ƙasar, a wani ɓangare na ƙawancen da suka ƙulla da zummar murƙushe ta'addanci. Dangane da wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Yahuza Gesto masanin tsaro da ke tarayyar Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawar...
Nazir Ahmed Hausawa (Ziriums), yana daya daga cikin ‘yan masana'antar finafinan Kannywood, Makadin Fiyano, Mawakin gambarar Hausa HipHop, Tsohon malamin koyar da kida, Tsohon ma'aikacin BBC World Service Trust da VOA Hausa, Masanin harkokin gidajen alfama na Amurka. A cikin hirarsa da Madubin Usman Kabara a Amurka, ya bayyana min darussan da ya koya a zamansa na shekaru a Amurka.
Usman Umar da aka fi sani da Soja Boy mawaki ne, dan wasan kwaikwayon zahirin rayuwa da ya fito a tauraron wani shirin wasan talbijin a Amurka mai suna 90DayFiance wanda ake bibiyar saurayi da budurwa don ganin yadda alakarsu ta soyayya ke tafiya.
Dalibi ne da ya ke digirin digirgir a fannin Turanci da fasahar hotunan finafinan majigi. Matashin ya bayyana yadda jin wani shiri a gidan radiyon Muryar Amurka na VOA ya ba shi kaimin neman zuwa karatu a Amurka, har ya buge da koyar da harshen Hausa tun a digirinsa na biyu a wata jami'a ta Amurka.
Adamu Garba II matashi ne mai kwarin gwiwa sannan wanda ya ke dan kasuwar da yayi iliminsa a tsakanin Najeriya har zuwa Amurka. Yana daga cikin 'yan takarar Shugaban Kasar Najeriya a shekarar 2023 mafi karancin shekaru a tsakanin masu neman wannan kujera a kasar da ta fi kowa ce kasar Afirka yawan al'umma da kuma karfin arzikin man fetur. Shine kuma wanda 'yan uwa da abokan arziki suka tara wa sama da naira miliyan 80 don yin takara a jam'iyyar APC amma kwatsam sai ya canja sheka zuwa YPP.
Na'ima Idris Usman, cikakkiyar Likita ce da ke jihar Kanon Najeriya, ta yi karatun a tsakanin Najeriys da China. Ta bamu labarin rayuwarta daga kuruciya zuwa girmanta, da ma yadda aka yi ta fara ilimantar da mata ta kafafen sada zumunta game da lafiyar jikinsu duk da cewa furta kalmomin da ke da alaka da al'aura abu ne mai cike da kalubalen a kasar Hausa. Da kuma yadda karshe ta buge da zuwa shirin horar da shugabanci ga matasan Afirka a Amurka da a turance ake kira da Mandela Washington Fellowship da aka fi sani da Young African Leaders Initiative (YALI) na shekarar 2022.
Na sami yin hira da shahararriyar Jarumar Fina-finan Hausa Nafisat Abdullahi a birnin Washington DC da ke Amurka, don sanin asalinta da kuma yadda take tafiyar da rayuwarta.
Mu Zagaya Duniya wanda ke bitar wasu daga cikin muhimman lamurran da suka wakana a makon da muka yi wa bankwana,shirin zai fara ne da matakin da shugaba Donald Trump ya ɗauka na ƙaƙaba sabbin takunkuman hana shiga Amurka kan wasu ƙarin ƙasashe bakwai na Afrika, ciki har da Burkina Faso da Mali da kuma Jamhuriyar Nijar a bisa dalilan da ya ce na tsaro ne.
Karatu ne ya kai iyayen Iman Yusuf Al-Hassan zuwa Amurka, wanda su 'yan asalin jihohin Kano da Jigawa ne a Arewacin Najeriya, amma kuma kaddarar zama ta kama su har suka hayayyafa. Iman ta fada min yadda take da burin zaman Najeriya duk kuwa da cewa a Amurka aka haifeta ta girma.
Hadiza Aliyu da aka fi sani da Gabon, na daya daga cikin fitattun taurarin fina-finan Hausa mafi shahara. Ta shiga Najeriya a lokacin da bata jin Hausa, amma kuma tana son zama tauraruwar fina-finan Hausa na Kannywood. Yanzu kuma sai gashi mun da cewa tana yawan tafiye-tafiye zuwa kasashen duniya, ciki har da Amurka inda muka yi wannan hirar da ita.
Dakta Mohammed Ladan dai an fi saninsa da suna Dakta Ladan, sakamakon wani fitaccen shirin lafiya na gidan radiyon sashen Hausa na Muryar Amurka. Amma a likitance shi masanin kimiyyar hada magunguna ne wato ‘phamacist'. Dan asalin jihar Neja ne da ke Arewacin Najeriya, sannan a yanzu mazaunin Amurka fiye da shekara 40 tun bayan zuwansa.
Maimuna Sulaiman Bichi da aka fi sani da ‘yar Bichi ko Lolo's Kitchen ‘yar asalin Najeriya ce ta suka dawo Amurka da zama tun tana shekaru 15 da haihuwa. Ta kuduri aniyar bude gidan abincin da zai kware a girke-girke musamman ma irin na gargajiyar Hausawa.
Farfesa Yusuf Al-Hassan dan asalin cikin birnin Kano ne a Najeriya da ya kwashe shekaru yana koyo da koyarwa a tsakanin Najeriya da Amurka game da ilimin fasahar sana'o'in hannu inda har ya taba zama zakaran gasar malaman koyar da sana'o'i ta Amurka. Malamin ya kuduri aniyarsa ta yadda zai taimaki Najeriya ta hanyar kai Kanawa 100 zuwa Amurka don koyon ilimin sana'a.Yusuf Al-Hassan | MUK Na16
Na yi hira da Hauwa Mustapha Babura, 'yar asalin garin Babura da ke jihar Jigawa ta Arewacin Najeriya. Ta bani labarin rayuwarta tun bayan shigarta Amurka da kuruciya, inda a yanzu haka 'yar kasa ce a can kamar yadda take a kasarta ta asali. Da kuma yadda aka yi ta zama kwararriyar malamar makaranta a bangaren ilimin kananan yara da kuma yadda ake renon kwakwalwarsu.
Farfesa Abba Zubair Chedi na asibitin Mayo Clinic da ke Amurka, dan asalin jihar Kano ne a Najeriya da ya yi kaurin suna a Amurka, musamman a lokacin da ya shiga binciken yadda za a yi amfani da kimiyyar kwayar halitta ta 'stem cell' wajen kirkirar sassan jikin bil'adama, kamar zuciya da huhu don dasa wa mutanen da sassan jikin ya lalace ba tare da jiran sai wani ya mutum a cire a saka wa wani ba.
Shirin a wannan lokaci zayyi duba ne kan yadda rabon jadawalin gasar lashe kofin duniya da za a yi a baɗi ya gudana. A makon da ya gabata ne Hukumar Kula da Kwallon Ƙafa ta Duniya FIFA ta fidda jadawalin Gasar Kofin Duniya na shekarar 2026, wacce za ta gudana a tsakanin ƙasashen Amurka da Canada da kuma Mexico. Bikin dai ya gudana a cibiyar Kennedy da ke birnin Washington DC, ƙarƙashin jagorancin shugaban Amurka Donald Trump da shugaban FIFA Gianni Infantino.
Shirin Mu Zagaya Duniya tare da Azima Bashir a wannan mako ya yi bita tare da bibiyar manyan labarai mafiya jan hankali a makon da mukayi bankwana da shi daga sassa daban-daban na duniya. Labarai mafiya jan hankali a Najeriya cikin makon da muke bankwana da shi shi ne naɗin sabon ministan tsaro Janar Christopher Musa mai ritaya bayan murabus ɗin bazata da Alhaji Badaru Abubakar ya yi daga kan kujerar bisa dalilai na rashin lafiya dai dai lokacin da matsalolin tsrao ke ci gaba da ta'azzara a wannan ƙasa. Sai kuma batun tantance ƙarin Jakadun da shugaba Tinubu ya miƙawa Majalisar dattijai kana mutuwar ɗan adawa Anicet Ekane can a Kamaru, yayinda aka ga yadda tattaunawa ta yi nisa da fatan kawo ƙarshen yaƙin Ukraine tsakanin masu shiga tsakani, a gefe guda kuma aka ƙulla yarjejeniya mai cike da tarihi tsakanin Congo da Rwanda bisa jagorancin Amurka. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Ƴan Najeriya na ci gaba da neman bayani a kan yadda wasu kuɗaɗen da aka tara, da yawan su ya kai dala miliyan 30 domin samar da tsaro a makarantu suka shiga, sakamakon sake dawowar satar ɗalibai a yankin arewacin ƙasar. A ƙarƙashin wannan shirin da ya fara a shekarar 2014, kasashe da dama suka tallafawa Najeriya, cikin su har da ƙasar Norway da ta bada dala miliyan guda, da wata dala miliyan guda daga Bankin Raya ƙasashen Afirka na AfDB, sai kuma Fam miliyan guda daga gwamnatin Birtaniya. Gwamnatin Switzerland ta bada taimakon dala miliyan takwas, yayin da Amurka ta bada dala miliyan biyu, sai kuma Qatar da ta bada dala miliyan biyu, yayin da ƴan kasuwan Najeriya su kuma suka bada taimakon dala miliyan 10. Ganin yadda aka kasa samar da tsaron a makarantu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Abubakar sadiq Umar Gombe. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Shirin 'Kasuwa A kai Miki Dole' na wannan mako tare da Ahmed Abba ya mayar da hankali ne kan gina katafaren kamfanin tono da kuma sarrafa ƙarafu da duwatsu masu daraja da wani matashi ya ƙaddamar a jihar Nasarawa da ke arewacin Najeriya, irinsa mafi girma a Afirka, wanda zai laƙume dalar Amurka miliyan 400.
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatar da sunan Janar Christopher Musa mai ritaya ga majalisar Dattawa domin amincewar ta ya zama ministan tsaro. Christopher Musa ya yi aiki a matsayin babban hafsan tsaron Najeriya daga ranar 23 ga watan Yunin 2023 zuwa 30 ga watan Octoban 2025, lokacin da shugaban ƙasar Bola Ahmad Tinubu ya yi masa ritaya. Idan majalisa ta amince, Janar Musa zai maye gurbin Badaru Abubakar da ya yi murabus a ranar Litinin. Bayanai sun nuna cewa fannonin da Musa ya fi ƙwarewa a kai shine fatattarkar ƴan ta'adda, da dubarun yaƙi, kasancewar ya yi aiki a matsayin jagoran rundunar sojojin Najeriya da ke kula da tsaron iyakokin Najeriya ta arewa maso gabashi da kuma yankin tafkin Chadi, haka nan ya kuma yi aiki a matsayin guda daga cikin dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya a Sierra Leone, da kuma wasu ayyukan a Amurka da Majalisar Ɗinkin Duniya.. Domin sanin tasirin wannan nadin da kuma kalubalen dake gaban Janar Musa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon kakakin rundunar sojin kasa ta Najeria, Janar Sani Usman Kukasheka mai ritaya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Kamar dai kowace shekara, 1 ga watan Disamba ita ce ranar da Hukumar Lafiya ta Duniya ta keɓe don yaƙi da cuta mai karya garkuwar jikin ɗan Adam wato HIV ko kuma SIDA. Bikin na bana ya zo ne a cikin wani yanayi da shugaba Donald Trump ya katse tallafin da Amurka ke bai wa ƙasashe masu tasowa ciki har da na ɓangaren yaƙi da wannan cuta. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Nasir Sani Gwarzo ƙwararren likitan yaƙi da annoba a Najeriya, wanda ya fara da bayyana halin da ake ciki game da yaƙi da HIV a ƙasar. Ga zantawarsu.
Dr. Murtala likitan yara ne dan asalin jihar Adamawar Najeriya da ya rikide ya zama kwararren masanin lafiyar al'umma musamman mata da yara, wanda a yanzu haka ma'aikaci ne a wata kungiya mai zaman kanta da ta ke tallafawa harkokin lafiyar iyali a duniya ciki har da kasashen Afirka mai suna Pathfinder International da ke kasar Amurka.Murtala Mai | Madubin Usman Kabara #11
‘Yar Nijar kuma masaniyar kimiyyar ruwa da doron kasa da ke aiki a hukumar sama-jannatin Amurka ta NASA. Dr. Fadji Maina tana cikin wacce mujallar tereren arziki ta Forbes ta wallafa sunanta a cikin matasan duniya guda 30 ‘yan kasa da shekara 30 da suka sami nasara a rayuwa. Yanzu haka ma'aikaciya ce a hukumar sama jannatin Amurka ta NASA da ke aiki bisa kwarewar ta a fannin ruwa da kimiyyar doron kasa.
A shekarar 1984 a Najeriya an sami wani saurayi dan jihar Kano da ya fi kowane dalibi a Najeriya cin makin jarrabawar gama sakandaren kasashen Afirka ta WAEC a takaice. Yanzu haka dai wannan dalibin mai suna Farfesa Sarki Abba Abdulkadir farfesa ne a bangaren haddasuwar cututtuka a Jami'ar Northwestern University da ke Chicago a Amurka.
Adamu Hamza Bamalli ya sha gwagwarmaya a Najeriya da Amurka kama daga zama direban babbar mota zuwa rikidewa ya zama kwararren Injiniya a jihar Maryland ta Amurka.
Shirin Mu zagaya Duniya tare da Nura Ado Suleiman a wannan mako kamar yadda ya saba ya yi bitar muhimman labaran da suka faru a makon da muke bankwana da shi daga ɓangarori daban-daban na duniya. A Najeriya shirin ya faro da batun Siyasa inda a cikin makon da muka yi wa bankwana rikicin cikin gidan babbar Jam'iyyar adawar Najeriyar wato PDP ya zama ɗaya daga cikin batutuwan da suka ɗauki hankali. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Na ziyarci Dr. Sabo Tanimu a jihar Wisconsin ta Amurka. Yana daya daga cikin kwararrun likitocin kayan cikin bil'adama a kasar inda yake shugabantar bangaren cutar dajin da ta shafi kayan ciki. Dan asalin Najeriya ne daga jihar Benue a tsakiyar Arewacin Najeriya. Shin yaya aka yi Likita Sabo ya fara daga Najeriya har ya tsinci kansa a Amurka inda ya shafe shekaru da dama yana aikin Likita a can.
Na yi hira da Ali Nuhu Mohammed jarumin fina-finan Hausa da Turanci na Najeriya a lokacin da ya ziyarci birnin Washington DC da ke Amurka,, in da na tambaye shi darussan da ya koya a cikin shekaru 20 da ya kwashe yana harkar shirya finafinai.
Yayin da hukumomin Najeriya suka yi watsi da barazanar shugaban Amurka na kai wa ƙasar hari saboda zargin kashe Kiristoci, ƴan kasar da dama na ci gaba da bayyana ra'ayi a kan matsayin na shugaba Donald Trump. Daga cikin waɗanda suka bayyana ra'ayin su a kan wannan barazana har da tsohon Jakadan Najeriya a ƙasar Iran, Ambasada Abubakar Cika, kamar yadda za ku ji a tattaunawarsu da Bashir Ibrahim Idris.
Ga alama yajejeniyar tsagaita wutar da Isra'ila ta ƙulla tsakaninta da Hamas, wadda Amurka ta tsara ta kama hanyar rugujewa, sakamakon umarnin da Firaminista Benjamin netanyahu ya bayar na ƙaddamar da sabbin hare-hare a Gaza. Wannan ya biyo bayan abinda ya kira ƙin bada gawarwakin sauran Yahudawan da Hamas ta yi garkuwa da su. Domin tattauna wannan dambarwa, Bashir Ibrahim Idris, ya tuntuɓi Dakta Abdulhakin Garba Funtua, mai sharhi a kan harkokin Gabas ta Tsakiya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.........................
Daga cikin labarun da shirin 'Mu zagaya Duniya' na wannan makon ya kunsa akwai labarin matakin da shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ɗauka na yin tankaɗe da rairaya a manyan hukumomin tsaron ƙasar, inda ya sallami manyan hafsoshin tsaron ƙasar, dai dai lokacin da rundunar sojin Najeriya ta ce ta samu nasarar kashe ‘yan ta'adda fiye da 50 yayin wasu jerin hare-hare da mayaƙan Boko Haram suka ƙaddamar kusan lokaci guda a kan garuruwan daban daban a jihohin Borno da Yobe. Shirin ya waiwayi wasu daga cikin lamurran da suka wakana a Kamaru inda ake cigaba da dakoon Kotun Fasalta Kundin tsarin mulki ta tabbatar da sakamakon zaɓen shugabancin ƙasar. A yankin gabas ta tsakiya, Amurka ta hau kujerar naki kan yunƙurin wasu na ganin Isra'ila ta kwace iko ya yankin Falasɗinu na Gaɓar yamma da kogin Jordan.
Shirin a wannan mako ya mayar da hankali ne kan wasannin neman tikitin zuwa gasar cin kofin Duniya ta 2026 da ƙasashen Amurka, Mexico da Canada za su karɓi baƙunci. A Nahiyar Afrika tuni dai wasu ƙasashe suka sami tikitin zuwa gasar da suka haɗar da Morocco da Tunisia da Aljeriya da Ivory Cost, sai dai ƙasashen Najeriya da Afrika ta Kudu da kuma Senegal na cikin halin rashin tabbas, sai dai a wannan Talata ne za su san makomarsu. Latsa alamar sauti don sauraron shirin tare da Abubakar Isah Ɗandago..................