Podcasts about amurka

  • 16PODCASTS
  • 248EPISODES
  • 14mAVG DURATION
  • 5WEEKLY NEW EPISODES
  • Mar 9, 2026LATEST

POPULARITY

20192020202120222023202420252026


Best podcasts about amurka

Latest podcast episodes about amurka

Wasanni
Amurka ta gargaɗi masu aniyar maƙalewa idan suka je kallon gasar cin kofin duniya

Wasanni

Play Episode Listen Later Mar 9, 2026 10:00


Shirin Duniyar Wassani a wannan lokaci yayi duba ne kan yadda Amurka ta fara gargaɗin ƴan Ghana da ke da aniyar maƙalewa idan suka je ƙasar don kallon gasar cin kofin duniya da ƙasashen Amurka da Canada da kuma Mexico za su karɓi baƙunci a watan Yuni mai zuwa. Ganin irin matakan da dama gwamnatin Amurka ke ɗauka kan shigar baki ƙasar tuni ofishin Jakadancin ƙasar da ke Ghana ya fara gargaɗin masu shirin halartar gasar da su guji wuce wa'adin da aka basu. Jakadan Amurka a Ghana Rolf Olson ya ce saɓawa dokokin shige da fice na ƙasar na iya haifar da mummunan sakamako, gami da rashin sake samun damar shiga ƙasar a nan gaba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh..............

Tambaya da Amsa
Shin akwai dokar da ta ba Amurka damar hukunta wani sshugaban ƙasa?

Tambaya da Amsa

Play Episode Listen Later Mar 7, 2026 21:31


  Shirin 'Tambaya da Amsa' shiri ne da ke zuwa muku da  amsoshin wasu tambayoyin da masu sauraronmu suka aiko mana, kuma a kowane mako yake zuwa muku a daidai wannan lokaci. A yau shirin tambaya da amsa zai fara ne da bayani akan ko akwai wata doka da ta baiwa shugaban Amurka Donald Trump ikon hukunta wani shugaban ƙasa a Duniya.

Mu Zagaya Duniya
Yadda rikicin Iran ke faɗaɗa a yankin Gabas ta Tsakiya

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Mar 7, 2026 20:44


A Wanan makon shirin zai karkata alakarsa ne yankin Gabas ta Tsakiya inda sabon rikici ya barke tsakanin hadakar Amurka da Isra'ila da kuma Iran. A cikin shirin zamu yi duba dangane da yadda rikicin  ke cigaba da faɗaɗa zuwa sauran kasashen yankin da ma  tasirinsa kan bangarori daban-daban a  wanan duniyar sai a gyara zama domin sauraron cikakakken shirin.

Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Dakta Bashir Nuhu Mabai kan sake ta'azzarar yaƙin Iran da Amurka

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 5, 2026 3:40


Masana siyasar Duniya gami da rikicin Yankin Gabas ta Tsakiya, na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu kan yaƙin da ya shiga rana ta shida tsakanin Iran da Amurka, wadda ke taimaka wa Isra'ila. Ya zuwa jiya Laraba dai Isra'ilar ta yi iƙirarin kai wa Iran hare-hare sama da dubu 5, yayin da ita ma Amurka ke ci gaba kai wa Iran ɗin farmaki ta sama, da zummar rusa duk wani ƙarfi da ya rage wa gwamnatin ƙasar. Kan wannan, da kuma yadda yaƙin ke daɗa rincaɓewa da shafar ƙasashen Yankin Gabas ta Tsakiya, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Bashir Nuhu Mabai, Malami a Jami'ar Dutsinma da ke Katsina a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

iran sake ku isra bashir duniya katsina najeriya masana malami amurka
Bakonmu a Yau
Ana zaman ɗar-ɗar a Iraqi da sauran ƙasashen yankin Gulf saboda hare-haren Iran

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 4, 2026 3:35


Iran ta ci gaba da kai munanan hare-hare kan Isra'ila da muradun Amurka a Gabas ta Tsakiya.To sai dai ƙasashen yankin Gulf na zarginta da faɗaɗa hare-haren kan fararen hula da ababen more rayuwa kamar Otel-otel da filayen jiragen sama da kuma cibiyoyin makamashi. Ko a jiya, dakarun juyin juya halin Iran sun yi ikirarin tarwatsa cibiyoyi da dama a yankin kurdawa, wadanda ta ce mayakanta na shirin yi mata kutse domin kai mata hare-hare. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Yadda yaƙin Gabas ta Tsakiya ya haifar da tsadar makamashi a duniya

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Mar 4, 2026 9:55


A yayin da yaƙi tsakanin Isra'ila da Amurka da Iran ke daɗa rincaɓewa, an fara gani tasirinsa a kasuwar ɗanyen mai da makamashi ta duniya. Ko a Najeriya, ƙasar da ta fi arziƙin ɗanyen mai a Afirka, farashin litar fetur ya tashi, kuma masana sun ce ana iya ganin cigaba da tashin farashin makamashi. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.

iran ko isra duniya yadda shiga najeriya afirka amurka
Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Farfesa Tukur AbdulƘadir kan fargabar tsanantar yaƙin Iran

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 3, 2026 3:38


Ga dukkanin alamu akwai yiwuwar yaƙi tsakanin Iran da kuma haɗin gwiwar Amurka da Isra'ila ya ɗauki tsawon lokaci saɓanin zaton da ake yi na ya kasance gajere, wannan kuwa ya biyo bayan jawabin shugaban Amurka Donald Trump a daren jiya da ke cewa mai yiwuwa a shafe makwanni 4 zuwa 5 suna kai hare-hare kan Iran. Wannan na zuwa ne a yayin da yaƙin da ya rincaɓe, ke ci gaba da shafar ƙasashe da dama a Yankin Gabas ta Tsakiya. Domin jin yadda masana siyasar ƙasa da ƙasa ke kallon lamarin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Tukur AbdulƘadir na Jami'ar Jihar Kaduna a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar..

iran ga ku isra abdul domin adir wannan najeriya amurka
Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Dakta Ibrahim Adamu kan hare-haren Iran a ƙasashen Gulf

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 2, 2026 3:40


Iran ta kai jerin hare-hare kan sansanonin sojin Amurka da wasu muhimman wurare biranen Dubai da Abu Dhabi a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, sai kuma Doha a Qatar da kuma Manama a Baharain, domin ɗaukar fansa kan farmakin da haɗin gwiwar Amurka da Isra'ila suka ƙaddamar kanta tun daga ranar Asabar. Baya ga harba makamai masu linzami kan Isra'ila, Iran ta tsananta kai hare-haren kan sansanonin sojin Amurka ne bayan mutuwar jagoranta Ayatollah Khamenei. Domin jin halin da ake ciki da sauran batutuwa masu alaƙa da yaƙin da ya ɓarke, Nura Ado Suleiman ya tattauna Dakta Ibrahim Adamu, masanin Yankin Gabas ta Tsakiya da ke Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.

Mu Zagaya Duniya
Majalisar Ɗinkin Duniya ta buƙaci Pakistan da Afghanistan su kai zuciya nesa

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Feb 28, 2026 19:31


Shirin 'Mu zagaya Duniya' na wannan mako tare da Oumarou Sani ya mayar da hankali kan labarai da suka fi ɗaukar hankali a makon da muka bankwana da shi, masamman kan ƙazancewar rikici tsakanin Afghanistan da Pakistan, bayan da Pakistan ta ƙaddamar da harin Operation Ghazab lil-Haq a matsayin martani ga hare-haren da tace Taliban ta kai wa sojojinta, da kuma dambarwar Amurka da Iran kan yarjejeniyar ƙera makaman nukiliya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shiin tare Oumarou Sani...............

Tambaya da Amsa
Tarihin kafuwar Ƙungiyar Kare Hakkin Ɗan Adam ta Duniya

Tambaya da Amsa

Play Episode Listen Later Feb 28, 2026 19:59


A cikin shirin Tambaya da Amsa daga sashen hausa na RFI,a yau shirin ya mayar da hankali ne kan tarihin kafuwar Ƙungiyar Kare Hakkin Ɗan Adam ta Duniya ta Human Rights Watch, wanda ya samo asali daga ƙoƙarin sa-ido kan yarjejeniyoyin ƙasa da ƙasa, musamman a lokacin yaƙin cacar baka. Hedikwatar ƙungiyar tana birnin New York na Amurka. Babban burinta shi ne bincike, tattara bayanai, da wallafa rahotanni kan take haƙƙin ɗan adam a faɗin duniya don matsa wa gwamnatoci lamba su gyara. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Nasiru sani.

Bakonmu a Yau
AbdulHakim Garba Funtua kan Kwamitin Zaman Lafiya Gaza da Trump ya kafa

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Feb 20, 2026 3:31


A ranar Alhamis, shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaddamar da fara aikin  Kwamitin Zaman Lafiyar Duniya da ya kafa. Wakilai daga aƙalla ƙasashe 47 da kuma ƙungiyar Tarayyar Turai da Isra'ila ne suka halarci taron farkon na Kwamitin Zaman Lafiyar na Duniya a birnin Washington. Muhimman batutuwan da taron ya mayar da hankali kai sun haɗa da kafa Rundunar zaman lafiya a Gaza, da karɓe makamai daga hannun Hamas, da kuma sake gina Zirin na Gaza. Shiga alamar sauti, domin sauraron tattaunawar Nura Ado Suleiman da AbdulHakim Garba Funtua, masanin siyasar ƙasa da ƙasa.

Mu Zagaya Duniya
Harin Kwara da dambarwar Nukiliyar Iran na cikin manyan labaran makon da ya gabata

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Feb 7, 2026 20:23


Shirin 'Mu zagaya Duniya' na wannan mako tare da Oumar Sani kamar kullum ya mayar da hankali kan labarai da suka fi ɗaukar hankali a makon da muka bankwana da shi, masamman harin da ya kashe sama da mutane 170 a jihar Kwara dake arewacin Najeriya. 

iran duniya najeriya cikin amurka
Bakonmu a Yau
Tattaunawa kan matakin Amurka na tura sojojinta zuwa Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Feb 5, 2026 3:27


Amurka ta sanar da tura wata tawagar sojinta zuwa Najeriya, abinda a karon farko ke tabbatar da isar dakarun nata ƙasar, tun bayan ƙarfafa yarjejeniyar tsaron da ƙasashen biyu suka yi, biyo bayan zargin da shugaba Donald Trump ya yi a shekarar bara, cewa ana kashe Kiristoci a Najeriyar. Kwamandan rundunar sojin Amurka da ke kula da Afirka, Janar Dagvin R.M. Anderson ya ce sun tura dakarun ne a bisa amincewar Najeriya.  Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Yahuza Ahmed Getso masanin tsaro a Najeriya. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.......

donald trump tura shiga najeriya afirka amurka
Kasuwanci
Yadda aka ƙulla yarjejeniyar kasuwanci mafi girma a duniya tsakanin India da EU

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Jan 28, 2026 10:01


Yau shirin ya mayar da hankali ne dangane gagarumar yarjejeniyar cinikayya mafi girma da ba'a taba ganin irinta ba, da aka cimma tsakanin ƙungiyar Tarayyar Turain ƙasar India. Yarjejeniyar da aka cimma yayin ziyarar da shugabannin Turai suka kai New Delhi na ƙasar India, za ta bada damar kasuwanci mara shinge tsakanin ƙasashe mambobin EU 27 da kuma ƙasar da ta fi yawan jama'a a duniya, waɗanda suka kaɗai suka mamaye kusan kashi 25% na jimillar hada-hadar kasuwancin cikin gida na duniya da kuma cinkayyar mutane biliyan biyu. Domin ko a shekarar 2024 kaɗai, an yi cinikin sama da Euro biliyan 120 a tsakanin ɓangarorin biyu. Masu sharhi na ganin cewa kalaman wannan yarjejeniya da ɓangarorin biyu suka cimma, alaƙa da manufofin Shugaban Amurka, Donald Trump, musamman duba da yadda Tarayyar Turai ke ƙoƙarin faɗaɗa abokan hulɗar kasuwancinta, ba tare da dogaro da Amurka kaɗai ba. Yarjejeniyar dai na nufin cewa daga yanzu, India za ta soke ko kuma zaftare haraji kan hajoji da dama da take shigarwa yankin Turai, da suka haɗa da motoci daga kaso 110% zuwa 10% kachal, matakin da zai shafi kayan abinci da barasa da tufafi da kayan ado da dai sauransu. An dai ƙulla yarjejeniyar ce a daidai lokacin da mafi yawan ƙasashen duniya ke takun-saka da Amurka sakamakon haraji babu ƙaƙƙautawa da Donald Trump ke amfani da shi don tursasawa abokan hulɗa. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.

Bakonmu a Yau
Waɗanne abubuwa ne yarjejeniyar Najeriya da Amurka ta ƙunsa

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jan 26, 2026 3:14


A Najeriya babban abin da mafi yawan mutane ke neman ƙarin haske a kai su ne abubuwan da ke ƙunshe a yarjejeniyar tsaron da aka ƙulla tsakanin ƙasar da Amurka domin kawo ƙarshen ƴanbindigar da Amurkan ta ce suna yi wa Kiristoci kisan gilla. A game da wannan yarjejeniyar ce Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Yahuza Getso, masani tsaro da ke game da ayykan ƴanbingar da suka addabin jama'a, ga kuma yadda zantawarsu ta gudana. A latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar zantawar.

unsa najeriya amurka abdoulkarim ibrahim shikal
Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Dakta Adam Mustapha kan tasirin ficewar Amurka daga WHO

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jan 23, 2026 3:29


Amurka ta kawo ƙarshen tallafin da ta ke bayar wa a hukumar Lafiya ta Duniya WHO daga wannan Alhamis, 22 ga watan Janairun 2026, duk kuwa da kasancewarta jigo wajen samar da kuɗaɗen tafiyar da hukumar wadda ke samar da tallafin magunguna da sauran ɓangarorin lafiya ga ƙasashe da dama musamman masu tasowa. Donald Trump ya sanar da aniyar janyewar ƙasar daga hukumar koda yake tun a wancan lokaci ya ƙulla yarjejeniyar cewa sai bayan shekara guda ne ficewar za ta fara aiki a hukumance. Kan haka ne Faruk Muhammad Yabo ya tattauna da Dr Adam Mustapha na sashen nazarin ƙananan halittu a jami'ar Maiduguri ya yi mana tsokaci kan illar da matakin na Amurka ka iya haifarwa.

donald trump mustapha daga maiduguri amurka alhamis majalisar dinkin duniya
Bakonmu a Yau
Dr AbdulHakim Funtua kan cika shekara guda da Trump ya yi kan karagar mulki

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jan 20, 2026 3:37


Yau Donald Trump ke cika shekara guda da komawa shugabancin Amurka, wa'adin da wasu ke ganin tamkar shugaban ya shafe shekara da shekaru bisa mulkin, la'akari da jerin matakan da ya riƙa aiwatarwa a matakin ƙasa da ƙasa da kuma cikin gida, ba tare da la'akari da caccakar da ake yi masa ba a gida da  waje.  Domin jin hasashen masana kan abinda ke tafe a ragowar shekaru uku da suka rage wa shugaban na Amurka Donald Trump, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta AbdulHakim Garba Funtua masanin siyasar ƙasa da ƙasa. Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawarsu...........

Tambaya da Amsa
Me ya sa darajar kuɗaɗen wasu ƙasashen larabawa su ka fi na Amurka daraja?

Tambaya da Amsa

Play Episode Listen Later Jan 17, 2026 20:53


Shirin tambaya da amsa da ke zuwa muku da wasu amsoshin tambayoyin da masu sauraronmu su ka aiko mana, mu kan mika wadanan tambayoyi ga masana domin baku amsar da ta dace................

shirin wasu amurka
Mu Zagaya Duniya
Aƙalla mutane 5000 ake fargabar sun mutu a zanga-zangar Iran

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Jan 17, 2026 20:31


Mahukuntan Iran sun yi barzanar amfani da hukuncin kisa kan masu zanga-zangar wadda ta juye zuwa tarzoma inda ofishin babban mai shigar da ƙara na gwamnati ya ce akwai yiwuwar idan aka fara ɗaukar wannan mataki a samu sassaucin zanga-zangar. A nasa bangare shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar daukar mataki mai tsauri kan Iran muddun hukumomin ƙasar suka fara kashe masu  zanga-zangar tsadar rayuwa.

iran mutu amurka
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan kayan aikin soji da Amurka ta bai wa Najeriya

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Jan 14, 2026 10:32


Amurka ta sanar wa bai wa Najeriya wasu muhimman kayan aikin soji domin tunkarar ƙalubale na tsaro da ƙasar ke fama da shi. Rundunar Amurka mai kula da nahiyar Afirka wato Africom ce ta sanar da hakan, sama da makonni biyu da Amurka ta ƙaddamar da farmakin farko kan wasu wurare ta bayyana cewa maɓoyar yan ta'addace. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

soji africom masu kayan najeriya afirka amurka
Bakonmu a Yau
Dr Kabiru Adamu na Beacon Consulting kan tallafin kayan yaƙin Amurka ga Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jan 14, 2026 3:35


Hedikwatar rundunar sojin Amurka mai kula da nahiyar Afirka, AFRICOM, ta sanar da miƙa wa gwamnatin Najeriya taimakon kayayyakin aikin soji, matakin da ke ƙarfafa yarjejeniyar tsaron da ke tsakaninsu don yaƙi da ta'addanci. Sai dai cikin sanarwar da ta wallafa a shafinta na X, rundunar sojin Amurkan ba ta yi ƙarin bayani kan nau'ika da kuma adadin makaman ba. Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Kabiru Adamu  shugaban  kamfanin Beacon Consulting da ke bincike kan tsaro a nahiyar Afrika.

consulting afrika beacon sai africom adamu kayan najeriya afirka amurka
Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Amabasada Abubakar Cika game da tsanantar zanga-zanga a Iran

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jan 13, 2026 3:30


Gwamnatin Iran ta ce tabbas an buɗe hanyoyin tuntubar juna tsakaninta da Amurka, bayan da shugaba Donald Trump ya yi barazanar yin amfani da ƙarfi kan ƙasar matuƙar ta ci gaba da kashe masu zanga-zanga. Mahukuntan Iran dai na ƙoƙarin shawo kan ɗaya daga cikin bore mafi muni da suka taɓa faruwa a ƙasar. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon jakadan Najeriya a Iran Amabasada Abubakar Cika, ga kuma zantawarsu dangane da wannan tarzoma ta Iran. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

game donald trump iran ku abubakar najeriya amurka abdoulkarim ibrahim shikal
Mu Zagaya Duniya
Bitar muhimman labaran da suka gudana a makon da muke bankwana da shi

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Jan 10, 2026 19:38


A cikin shirin na wannan mako tare da Oumarou Sani, zakuji bitar muhimman labaran da suka wakana a makon da muke bakwana da shi, ciki har da yadda Amurka ta yi gaban kanta wajen kutsawa cikin Venezuela tare da kame shugaba Nicolas Maduro. Muna tafe da tattaunawar masana a ɓangarori daban-daban kan wannan katsalandan na Amurka. Hallau dai a cikin shirin zaku ji bitar ɓarkewar sabon rikici a Yemen da Syria. A Najeriya kuwa akwai mu da bitar hare-haren ƴan ta'adda a jihar Neja da kuma rikicin siyasar ƙasar. Ku latsa lamar sauti don sauraron cikakken shirin.

Kasuwanci
Tasirin kama shugaba Maduro na Venezuela ga tattalin arzikin duniya

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Jan 7, 2026 10:30


Shirin 'Kasuwa A kai Miki Dole' na wannan mako tare da Ahmed Abba ya tattauna da masana da sauran masu ruwa da tsaki kan harkokin man fetir dangane da tasirin kama shugaban ƙasar Venezuela Nicolas Maduro da Amurka ta yi zai yi ga tattalin arzikin duniya.

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu sauraro kan dokar-ta-baci da gwamnati ta kafa a Nijar

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Dec 30, 2025 9:12


Mahukuntan jamhuriyar Nijar sun shelanta kafa dokar-ta-ɓaci, wanda a ƙarƙashinta gwamnati za ta iya yin amfani da illahirin al'ummar ƙasar da kuma dukiyoyinsu duk lokacin da ta ga ya dace saboda tunkarar barazanar tsaro. Matakin ya zo ne kwanaki ɗaya bayan da Amurka ta ƙaddamar da farmaki kan maɓoyar ƴanbindiga a wani wuri da ke jihar Sokoton Najeriya daf da iyaka da Nijar. Shin ko me za ku ce a game da matakin? Anya hakan zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro da ƙasar ke fama da su? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...

shin baci kafa masu nijar wannan amurka
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyin masu saurare kan harin Amurka a Najeriya

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Dec 29, 2025 9:58


Gwamnatin Najeriya ta ce da saninta Amurka ta ƙaddamar da hari jihar Sokoto da ke shiyar Arewa maso Yammacin ƙasar a makon daya gabata, inda ta ce an kai harin ne kan ƴan ta'addan da ta ce ke kwarara cikin ƙasar daga yankin Sahel. Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabir Muhammad Ɗan Bauchi.

sahel masu sokoto bauchi arewa najeriya amurka
Bakonmu a Yau
Abin da masana doka ke cewa kan hare-haren Amurka a Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 29, 2025 3:41


A Najeriya, ko baya ga farbaga dangane yadda Amurka ta fara kai hare-hare ta sama a kan waɗanda ta kira a matsayin ƴanta'adda a yankin arewacin ƙasar, wani abin tambaya shi ne halascin ɗaukar mataki bai wa wata ƙasa ta ƙetare damar yin amfani da sojojinta ba tare da amincewar majalisun dokokin ƙasar ba. Abdoulkarim Ibrahinm Shikal ya zanta da masani doka Barrister Modibbo Bakari Danna alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hirar.......

haren abin doka najeriya masana amurka
Mu Zagaya Duniya
Najeriya ta tabbatar da harin da Amurka ta kai a wasu yankuna na jihar Sokoto

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Dec 27, 2025 19:15


A cikin daren  ranar Alhamis da ta gabata Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da harin da Amurka ta kai a wasu yankuna biyu na jihar Sokoto wato Tangaza inda nan ne ‘yan Lakurawa ke da maɓoya da kuma Jabo da ke yankin ƙaramar hukumar Tambuwal. Sai dai mazauna yankin Jabo sun bayyana fargabar zama a ƙauyukansu saboda fargabar yin kuskuren kai musu farmaki a yayin wasu hare-haren da watakila Amurkar ka iya kai wa a nan gaba.

sai sokoto jabo wasu najeriya amurka alhamis
Bakonmu a Yau
Dr Yahuza Getso kan harin da Amurka ta kai jihar Sokoto ta arewacin Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 26, 2025 3:32


Da sanyin safiyar yau Juma'a aka wayi gari da sanarwar gwamnatin Najeriya da ke tabbatar da harin da Amurka ta kai a wasu yankunan ƙananan hukumomin Tambuwal da Tangaza, da ke jihar Sokoto a yankin arewa maso yammacin ƙasar. Ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Maitama Tuggar, ya ce Amurka ta kai hare-haren ne tare da haɗin gwiwar dakarun ƙasar, a wani ɓangare na ƙawancen da suka ƙulla da zummar murƙushe ta'addanci. Dangane da wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Yahuza Gesto masanin tsaro da ke tarayyar Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawar...

juma sokoto najeriya amurka
Madubin Kabara
Nazir Hausawa (Ziriums) | MUK Na 37

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 22, 2025 59:34


Nazir Ahmed Hausawa (Ziriums), yana daya daga cikin ‘yan masana'antar finafinan Kannywood, Makadin Fiyano, Mawakin gambarar Hausa HipHop, Tsohon malamin koyar da kida, Tsohon ma'aikacin BBC World Service Trust da VOA Hausa, Masanin harkokin gidajen alfama na Amurka. A cikin hirarsa da Madubin Usman Kabara a Amurka, ya bayyana min darussan da ya koya a zamansa na shekaru a Amurka.

nazir amurka hausawa
Madubin Kabara
Usman Umar SojaBoy | MUK Na 31

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 35:52


Usman Umar da aka fi sani da Soja Boy mawaki ne, dan wasan kwaikwayon zahirin rayuwa da ya fito a tauraron wani shirin wasan talbijin a Amurka mai suna 90DayFiance wanda ake bibiyar saurayi da budurwa don ganin yadda alakarsu ta soyayya ke tafiya.

Madubin Kabara
Na'ima Idris Usman | MUK Na 32

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 14:14


Na'ima Idris Usman, cikakkiyar Likita ce da ke jihar Kanon Najeriya, ta yi karatun a tsakanin Najeriys da China. Ta bamu labarin rayuwarta daga kuruciya zuwa girmanta, da ma yadda aka yi ta fara ilimantar da mata ta kafafen sada zumunta game da lafiyar jikinsu duk da cewa furta kalmomin da ke da alaka da al'aura abu ne mai cike da kalubalen a kasar Hausa. Da kuma yadda karshe ta buge da zuwa shirin horar da shugabanci ga matasan Afirka a Amurka da a turance ake kira da Mandela Washington Fellowship da aka fi sani da Young African Leaders Initiative (YALI) na shekarar 2022.

china usman hausa mandela washington fellowship afirka amurka young african leaders initiative yali
Madubin Kabara
Nura Abubakar | MUK Na 25

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 29:43


Dalibi ne da ya ke digirin digirgir a fannin Turanci da fasahar hotunan finafinan majigi. Matashin ya bayyana yadda jin wani shiri a gidan radiyon Muryar Amurka na VOA ya ba shi kaimin neman zuwa karatu a Amurka, har ya buge da koyar da harshen Hausa tun a digirinsa na biyu a wata jami'a ta Amurka.

Madubin Kabara
Adamu Garba II | MUK Na 28

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 30:26


Adamu Garba II matashi ne mai kwarin gwiwa sannan wanda ya ke dan kasuwar da yayi iliminsa a tsakanin Najeriya har zuwa Amurka. Yana daga cikin 'yan takarar Shugaban Kasar Najeriya a shekarar 2023 mafi karancin shekaru a tsakanin masu neman wannan kujera a kasar da ta fi kowa ce kasar Afirka yawan al'umma da kuma karfin arzikin man fetur. Shine kuma wanda 'yan uwa da abokan arziki suka tara wa sama da naira miliyan 80 don yin takara a jam'iyyar APC amma kwatsam sai ya canja sheka zuwa YPP.

shine yana apc garba adamu ypp najeriya afirka amurka
Madubin Kabara
Nafisat Abdullahi | MUK Na 36

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 88:02


Na sami yin hira da shahararriyar Jarumar Fina-finan Hausa Nafisat Abdullahi a birnin Washington DC da ke Amurka, don sanin asalinta da kuma yadda take tafiyar da rayuwarta.

Mu Zagaya Duniya
Trump ya ƙaƙaba sabbin takunkuman hana shiga Amurka

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 20:07


Mu Zagaya Duniya wanda ke bitar wasu daga cikin muhimman lamurran da suka wakana  a makon da muka yi wa bankwana,shirin zai fara ne da matakin da shugaba Donald Trump ya ɗauka na ƙaƙaba sabbin takunkuman hana shiga Amurka kan wasu ƙarin ƙasashe bakwai na Afrika, ciki har da Burkina Faso da Mali da kuma Jamhuriyar Nijar a bisa dalilan da ya  ce na tsaro ne.

Madubin Kabara
Iman Al-Hassan | MUK Na 23

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 19, 2025 22:55


Karatu ne ya kai iyayen Iman Yusuf Al-Hassan zuwa Amurka, wanda su 'yan asalin jihohin Kano da Jigawa ne a Arewacin Najeriya, amma kuma kaddarar zama ta kama su har suka hayayyafa. Iman ta fada min yadda take da burin zaman Najeriya duk kuwa da cewa a Amurka aka haifeta ta girma.

iman kano jigawa najeriya amurka
Madubin Kabara
Hadiza Aliyu Gabon | MUK Na 21

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 11, 2025 16:01


Hadiza Aliyu da aka fi sani da Gabon, na daya daga cikin fitattun taurarin fina-finan Hausa mafi shahara. Ta shiga Najeriya a lokacin da bata jin Hausa, amma kuma tana son zama tauraruwar fina-finan Hausa na Kannywood. Yanzu kuma sai gashi mun da cewa tana yawan tafiye-tafiye zuwa kasashen duniya, ciki har da Amurka inda muka yi wannan hirar da ita.

gabon hausa najeriya amurka yanzu
Madubin Kabara
Maimuna Sulaiman Bichi | MUK Na 21

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 10, 2025 40:51


Maimuna Sulaiman Bichi da aka fi sani da ‘yar Bichi ko Lolo's Kitchen ‘yar asalin Najeriya ce ta suka dawo Amurka da zama tun tana shekaru 15 da haihuwa. Ta kuduri aniyar bude gidan abincin da zai kware a girke-girke musamman ma irin na gargajiyar Hausawa.

kitchen lolo sulaiman najeriya amurka hausawa
Madubin Kabara
Mohammed Ladan | MUK Na 19

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 10, 2025 33:46


Dakta Mohammed Ladan dai an fi saninsa da suna Dakta Ladan, sakamakon wani fitaccen shirin lafiya na gidan radiyon sashen Hausa na Muryar Amurka. Amma a likitance shi masanin kimiyyar hada magunguna ne wato ‘phamacist'. Dan asalin jihar Neja ne da ke Arewacin Najeriya, sannan a yanzu mazaunin Amurka fiye da shekara 40 tun bayan zuwansa.

amma hausa ladan neja amurka
Madubin Kabara
Yusuf Al-Hassan | MUK Na 16

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 9, 2025 61:57


Farfesa Yusuf Al-Hassan dan asalin cikin birnin Kano ne a Najeriya da ya kwashe shekaru yana koyo da koyarwa a tsakanin Najeriya da Amurka game da ilimin fasahar sana'o'in hannu inda har ya taba zama zakaran gasar malaman koyar da sana'o'i ta Amurka. Malamin ya kuduri aniyarsa ta yadda zai taimaki Najeriya ta hanyar kai Kanawa 100 zuwa Amurka don koyon ilimin sana'a.Yusuf Al-Hassan | MUK Na16

kano kanawa najeriya amurka
Madubin Kabara
Hauwa Mustapha Babura | MUK Na 13

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 8, 2025 30:54


Na yi hira da Hauwa Mustapha Babura, 'yar asalin garin Babura da ke jihar Jigawa ta Arewacin Najeriya. Ta bani labarin rayuwarta tun bayan shigarta Amurka da kuruciya, inda a yanzu haka 'yar kasa ce a can kamar yadda take a kasarta ta asali. Da kuma yadda aka yi ta zama kwararriyar malamar makaranta a bangaren ilimin kananan yara da kuma yadda ake renon kwakwalwarsu.

mustapha jigawa amurka
Madubin Kabara
Abba Zubair | MUK Na 14

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 8, 2025 41:16


Farfesa Abba Zubair Chedi na asibitin Mayo Clinic da ke Amurka, dan asalin jihar Kano ne a Najeriya da ya yi kaurin suna a Amurka, musamman a lokacin da ya shiga binciken yadda za a yi amfani da kimiyyar kwayar halitta ta 'stem cell' wajen kirkirar sassan jikin bil'adama, kamar zuciya da huhu don dasa wa mutanen da sassan jikin ya lalace ba tare da jiran sai wani ya mutum a cire a saka wa wani ba.

Wasanni
Yadda aka gudanar da jadawalin gasar cin kofin duniya ta 2026

Wasanni

Play Episode Listen Later Dec 8, 2025 10:04


Shirin a wannan lokaci zayyi duba ne kan yadda rabon jadawalin gasar lashe kofin duniya da za a yi a baɗi ya gudana. A makon da ya gabata ne Hukumar Kula da Kwallon Ƙafa ta Duniya FIFA ta fidda jadawalin Gasar Kofin Duniya na shekarar 2026, wacce za ta gudana a tsakanin ƙasashen Amurka da Canada da kuma Mexico. Bikin dai ya gudana a cibiyar Kennedy da ke birnin Washington DC, ƙarƙashin jagorancin shugaban Amurka Donald Trump da shugaban FIFA Gianni Infantino.

Madubin Kabara
Murtala Mai | Madubin Usman Kabara #11

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 20, 2025 56:11


Dr. Murtala likitan yara ne dan asalin jihar Adamawar Najeriya da ya rikide ya zama kwararren masanin lafiyar al'umma musamman mata da yara, wanda a yanzu haka ma'aikaci ne a wata kungiya mai zaman kanta da ta ke tallafawa harkokin lafiyar iyali a duniya ciki har da kasashen Afirka mai suna Pathfinder International da ke kasar Amurka.Murtala Mai | Madubin Usman Kabara #11

usman afirka amurka kabara
Madubin Kabara
Fadji Maina | Madubin Usman Kabara #10

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 19, 2025 45:45


‘Yar Nijar kuma masaniyar kimiyyar ruwa da doron kasa da ke aiki a hukumar sama-jannatin Amurka ta NASA. Dr. Fadji Maina tana cikin wacce mujallar tereren arziki ta Forbes ta wallafa sunanta a cikin matasan duniya guda 30 ‘yan kasa da shekara 30 da suka sami nasara a rayuwa. Yanzu haka ma'aikaciya ce a hukumar sama jannatin Amurka ta NASA da ke aiki bisa kwarewar ta a fannin ruwa da kimiyyar doron kasa.

forbes nasa usman maina amurka fadji yanzu kabara
Madubin Kabara
Sarki Abba Abdulkadir | Madubin Usman Kabara #9

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 18, 2025 61:07


A shekarar 1984 a Najeriya an sami wani saurayi dan jihar Kano da ya fi kowane dalibi a Najeriya cin makin jarrabawar gama sakandaren kasashen Afirka ta WAEC a takaice. Yanzu haka dai wannan dalibin mai suna Farfesa Sarki Abba Abdulkadir farfesa ne a bangaren haddasuwar cututtuka a Jami'ar Northwestern University da ke Chicago a Amurka.

chicago abba northwestern university usman kano sarki abdulkadir najeriya afirka amurka yanzu kabara
Madubin Kabara
Adamu Hamza Bamalli | Madubin Usman Kabara #7

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 16, 2025 120:07


Adamu Hamza Bamalli ya sha gwagwarmaya a Najeriya da Amurka kama daga zama direban babbar mota zuwa rikidewa ya zama kwararren Injiniya a jihar Maryland ta Amurka.

maryland usman adamu najeriya amurka kabara
Madubin Kabara
Sabo Tanimu | Madubin Usman Kabara #3

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 12, 2025 29:40


Na ziyarci Dr. Sabo Tanimu a jihar Wisconsin ta Amurka. Yana daya daga cikin kwararrun likitocin kayan cikin bil'adama a kasar inda yake shugabantar bangaren cutar dajin da ta shafi kayan ciki. Dan asalin Najeriya ne daga jihar Benue a tsakiyar Arewacin Najeriya. Shin yaya aka yi Likita Sabo ya fara daga Najeriya har ya tsinci kansa a Amurka inda ya shafe shekaru da dama yana aikin Likita a can.

wisconsin shin usman yana sabo benue najeriya amurka kabara
Madubin Kabara
Ali Nuhu | Madubin Usman Kabara #2

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 11, 2025 12:09


Na yi hira da Ali Nuhu Mohammed jarumin fina-finan Hausa da Turanci na Najeriya a lokacin da ya ziyarci birnin Washington DC da ke Amurka,, in da na tambaye shi darussan da ya koya a cikin shekaru 20 da ya kwashe yana harkar shirya finafinai.

washington dc usman hausa najeriya amurka kabara