Podcasts about amurka

  • 16PODCASTS
  • 218EPISODES
  • 15mAVG DURATION
  • 5WEEKLY NEW EPISODES
  • Dec 20, 2025LATEST

POPULARITY

20172018201920202021202220232024


Best podcasts about amurka

Latest podcast episodes about amurka

Madubin Kabara
Nura Abubakar | MUK Na 25

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 29:43


Dalibi ne da ya ke digirin digirgir a fannin Turanci da fasahar hotunan finafinan majigi. Matashin ya bayyana yadda jin wani shiri a gidan radiyon Muryar Amurka na VOA ya ba shi kaimin neman zuwa karatu a Amurka, har ya buge da koyar da harshen Hausa tun a digirinsa na biyu a wata jami'a ta Amurka.

Madubin Kabara
Adamu Garba II | MUK Na 28

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 30:26


Adamu Garba II matashi ne mai kwarin gwiwa sannan wanda ya ke dan kasuwar da yayi iliminsa a tsakanin Najeriya har zuwa Amurka. Yana daga cikin 'yan takarar Shugaban Kasar Najeriya a shekarar 2023 mafi karancin shekaru a tsakanin masu neman wannan kujera a kasar da ta fi kowa ce kasar Afirka yawan al'umma da kuma karfin arzikin man fetur. Shine kuma wanda 'yan uwa da abokan arziki suka tara wa sama da naira miliyan 80 don yin takara a jam'iyyar APC amma kwatsam sai ya canja sheka zuwa YPP.

shine yana apc garba adamu ypp najeriya afirka amurka
Madubin Kabara
Usman Umar SojaBoy | MUK Na 31

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 35:52


Usman Umar da aka fi sani da Soja Boy mawaki ne, dan wasan kwaikwayon zahirin rayuwa da ya fito a tauraron wani shirin wasan talbijin a Amurka mai suna 90DayFiance wanda ake bibiyar saurayi da budurwa don ganin yadda alakarsu ta soyayya ke tafiya.

Madubin Kabara
Na'ima Idris Usman | MUK Na 32

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 14:14


Na'ima Idris Usman, cikakkiyar Likita ce da ke jihar Kanon Najeriya, ta yi karatun a tsakanin Najeriys da China. Ta bamu labarin rayuwarta daga kuruciya zuwa girmanta, da ma yadda aka yi ta fara ilimantar da mata ta kafafen sada zumunta game da lafiyar jikinsu duk da cewa furta kalmomin da ke da alaka da al'aura abu ne mai cike da kalubalen a kasar Hausa. Da kuma yadda karshe ta buge da zuwa shirin horar da shugabanci ga matasan Afirka a Amurka da a turance ake kira da Mandela Washington Fellowship da aka fi sani da Young African Leaders Initiative (YALI) na shekarar 2022.

china usman hausa mandela washington fellowship afirka amurka young african leaders initiative yali
Madubin Kabara
Nafisat Abdullahi | MUK Na 36

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 88:02


Na sami yin hira da shahararriyar Jarumar Fina-finan Hausa Nafisat Abdullahi a birnin Washington DC da ke Amurka, don sanin asalinta da kuma yadda take tafiyar da rayuwarta.

Mu Zagaya Duniya
Trump ya ƙaƙaba sabbin takunkuman hana shiga Amurka

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 20:07


Mu Zagaya Duniya wanda ke bitar wasu daga cikin muhimman lamurran da suka wakana  a makon da muka yi wa bankwana,shirin zai fara ne da matakin da shugaba Donald Trump ya ɗauka na ƙaƙaba sabbin takunkuman hana shiga Amurka kan wasu ƙarin ƙasashe bakwai na Afrika, ciki har da Burkina Faso da Mali da kuma Jamhuriyar Nijar a bisa dalilan da ya  ce na tsaro ne.

Madubin Kabara
Iman Al-Hassan | MUK Na 23

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 19, 2025 22:55


Karatu ne ya kai iyayen Iman Yusuf Al-Hassan zuwa Amurka, wanda su 'yan asalin jihohin Kano da Jigawa ne a Arewacin Najeriya, amma kuma kaddarar zama ta kama su har suka hayayyafa. Iman ta fada min yadda take da burin zaman Najeriya duk kuwa da cewa a Amurka aka haifeta ta girma.

iman kano jigawa najeriya amurka
Madubin Kabara
Hadiza Aliyu Gabon | MUK Na 21

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 11, 2025 16:01


Hadiza Aliyu da aka fi sani da Gabon, na daya daga cikin fitattun taurarin fina-finan Hausa mafi shahara. Ta shiga Najeriya a lokacin da bata jin Hausa, amma kuma tana son zama tauraruwar fina-finan Hausa na Kannywood. Yanzu kuma sai gashi mun da cewa tana yawan tafiye-tafiye zuwa kasashen duniya, ciki har da Amurka inda muka yi wannan hirar da ita.

gabon hausa najeriya amurka yanzu
Madubin Kabara
Maimuna Sulaiman Bichi | MUK Na 21

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 10, 2025 40:51


Maimuna Sulaiman Bichi da aka fi sani da ‘yar Bichi ko Lolo's Kitchen ‘yar asalin Najeriya ce ta suka dawo Amurka da zama tun tana shekaru 15 da haihuwa. Ta kuduri aniyar bude gidan abincin da zai kware a girke-girke musamman ma irin na gargajiyar Hausawa.

kitchen lolo sulaiman najeriya amurka hausawa
Madubin Kabara
Mohammed Ladan | MUK Na 19

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 10, 2025 33:46


Dakta Mohammed Ladan dai an fi saninsa da suna Dakta Ladan, sakamakon wani fitaccen shirin lafiya na gidan radiyon sashen Hausa na Muryar Amurka. Amma a likitance shi masanin kimiyyar hada magunguna ne wato ‘phamacist'. Dan asalin jihar Neja ne da ke Arewacin Najeriya, sannan a yanzu mazaunin Amurka fiye da shekara 40 tun bayan zuwansa.

Madubin Kabara
Yusuf Al-Hassan | MUK Na 16

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 9, 2025 61:57


Farfesa Yusuf Al-Hassan dan asalin cikin birnin Kano ne a Najeriya da ya kwashe shekaru yana koyo da koyarwa a tsakanin Najeriya da Amurka game da ilimin fasahar sana'o'in hannu inda har ya taba zama zakaran gasar malaman koyar da sana'o'i ta Amurka. Malamin ya kuduri aniyarsa ta yadda zai taimaki Najeriya ta hanyar kai Kanawa 100 zuwa Amurka don koyon ilimin sana'a.Yusuf Al-Hassan | MUK Na16

kano kanawa najeriya amurka
Madubin Kabara
Hauwa Mustapha Babura | MUK Na 13

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 8, 2025 30:54


Na yi hira da Hauwa Mustapha Babura, 'yar asalin garin Babura da ke jihar Jigawa ta Arewacin Najeriya. Ta bani labarin rayuwarta tun bayan shigarta Amurka da kuruciya, inda a yanzu haka 'yar kasa ce a can kamar yadda take a kasarta ta asali. Da kuma yadda aka yi ta zama kwararriyar malamar makaranta a bangaren ilimin kananan yara da kuma yadda ake renon kwakwalwarsu.

Madubin Kabara
Abba Zubair | MUK Na 14

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Dec 8, 2025 41:16


Farfesa Abba Zubair Chedi na asibitin Mayo Clinic da ke Amurka, dan asalin jihar Kano ne a Najeriya da ya yi kaurin suna a Amurka, musamman a lokacin da ya shiga binciken yadda za a yi amfani da kimiyyar kwayar halitta ta 'stem cell' wajen kirkirar sassan jikin bil'adama, kamar zuciya da huhu don dasa wa mutanen da sassan jikin ya lalace ba tare da jiran sai wani ya mutum a cire a saka wa wani ba.

Wasanni
Yadda aka gudanar da jadawalin gasar cin kofin duniya ta 2026

Wasanni

Play Episode Listen Later Dec 8, 2025 10:04


Shirin a wannan lokaci zayyi duba ne kan yadda rabon jadawalin gasar lashe kofin duniya da za a yi a baɗi ya gudana. A makon da ya gabata ne Hukumar Kula da Kwallon Ƙafa ta Duniya FIFA ta fidda jadawalin Gasar Kofin Duniya na shekarar 2026, wacce za ta gudana a tsakanin ƙasashen Amurka da Canada da kuma Mexico. Bikin dai ya gudana a cibiyar Kennedy da ke birnin Washington DC, ƙarƙashin jagorancin shugaban Amurka Donald Trump da shugaban FIFA Gianni Infantino.

Mu Zagaya Duniya
Bitar Labaran Mako: Naɗin sabon ministan tsaron Najeriya Janar Christopher Musa

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Dec 6, 2025 20:30


Shirin Mu Zagaya Duniya tare da Azima Bashir a wannan mako ya yi bita tare da bibiyar manyan labarai mafiya jan hankali a makon da mukayi bankwana da shi daga sassa daban-daban na duniya. Labarai mafiya jan hankali a Najeriya cikin makon da muke bankwana da shi shi ne naɗin sabon ministan tsaro Janar Christopher Musa mai ritaya bayan murabus ɗin bazata da Alhaji Badaru Abubakar ya yi daga kan kujerar bisa dalilai na rashin lafiya dai dai lokacin da matsalolin tsrao ke ci gaba da ta'azzara a wannan ƙasa. Sai kuma batun tantance ƙarin Jakadun da shugaba Tinubu ya miƙawa Majalisar dattijai kana mutuwar ɗan adawa Anicet Ekane can a Kamaru, yayinda aka ga yadda tattaunawa ta yi nisa da fatan kawo ƙarshen yaƙin Ukraine tsakanin masu shiga tsakani, a gefe guda kuma aka ƙulla yarjejeniya mai cike da tarihi tsakanin Congo da Rwanda bisa jagorancin Amurka. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

Bakonmu a Yau
Janar Sani Kukasheka kan kalubalen tsaron da ke gaban Christopher Musa

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 3, 2025 3:35


Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatar da sunan Janar Christopher Musa mai ritaya ga majalisar Dattawa domin amincewar ta ya zama ministan tsaro. Christopher Musa ya yi aiki a matsayin babban hafsan tsaron Najeriya daga ranar 23 ga watan Yunin 2023 zuwa 30 ga watan Octoban 2025, lokacin da shugaban ƙasar Bola Ahmad Tinubu ya yi masa ritaya. Idan majalisa ta amince, Janar Musa zai maye gurbin Badaru Abubakar da ya yi murabus a ranar Litinin. Bayanai sun nuna cewa fannonin da Musa ya fi ƙwarewa a kai shine fatattarkar ƴan ta'adda, da dubarun yaƙi, kasancewar ya yi aiki a matsayin jagoran rundunar sojojin Najeriya da ke kula da tsaron iyakokin Najeriya ta arewa maso gabashi da kuma yankin tafkin Chadi, haka nan ya kuma yi aiki a matsayin guda daga cikin dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya a Sierra Leone, da kuma wasu ayyukan a Amurka da Majalisar Ɗinkin Duniya.. Domin sanin tasirin wannan nadin da kuma kalubalen dake gaban Janar Musa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon kakakin rundunar sojin kasa ta Najeria, Janar Sani Usman Kukasheka mai ritaya. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

sierra leone domin sani idan duniya shiga chadi najeriya amurka majalisar bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Yadda aka tarawa Najeriya dala miliyan 30 domin samar da tsaro a makarantu

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 3, 2025 3:37


Ƴan Najeriya na ci gaba da neman bayani a kan yadda wasu kuɗaɗen da aka tara, da yawan su ya kai dala miliyan 30 domin samar da tsaro a makarantu suka shiga, sakamakon sake dawowar satar ɗalibai a yankin arewacin ƙasar. A ƙarƙashin wannan shirin da ya fara a shekarar 2014, kasashe da dama suka tallafawa Najeriya, cikin su har da ƙasar Norway da ta bada dala miliyan guda, da wata dala miliyan guda daga Bankin Raya ƙasashen Afirka na AfDB, sai kuma Fam miliyan guda daga gwamnatin Birtaniya. Gwamnatin Switzerland ta bada taimakon dala miliyan takwas, yayin da Amurka ta bada dala miliyan biyu, sai kuma Qatar da ta bada dala miliyan biyu, yayin da ƴan kasuwan Najeriya su kuma suka bada taimakon dala miliyan 10. Ganin yadda aka kasa samar da tsaron a makarantu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Abubakar sadiq Umar Gombe.  Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

norway qatar fam domin dala samar yadda tarawa shiga najeriya afirka amurka birtaniya bashir ibrahim idris
Kasuwanci
Yan Najeriya na yawaba Hasetins kan kafa kamfanin ma'adanai mafi girma a Afirka

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Dec 3, 2025 10:06


Shirin 'Kasuwa A kai Miki Dole' na wannan mako tare da Ahmed Abba ya mayar da hankali ne kan gina katafaren kamfanin tono da kuma sarrafa ƙarafu da duwatsu masu daraja da wani matashi ya ƙaddamar a jihar Nasarawa da ke arewacin Najeriya, irinsa mafi girma a Afirka, wanda zai laƙume dalar Amurka miliyan 400.

mafi kafa girma nasarawa najeriya afirka amurka ahmed abba
Bakonmu a Yau
Dakta Nasir Sani Gwarzo akan ranar HIV ta duniya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 1, 2025 3:35


Kamar dai kowace shekara, 1 ga watan Disamba ita ce ranar da Hukumar Lafiya ta Duniya ta keɓe don yaƙi da cuta mai karya garkuwar jikin ɗan Adam wato HIV ko kuma SIDA.  Bikin na bana ya zo ne a cikin wani yanayi da shugaba Donald Trump ya katse tallafin da Amurka ke bai wa ƙasashe masu tasowa ciki har da na ɓangaren yaƙi da wannan cuta. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Nasir Sani Gwarzo ƙwararren likitan yaƙi da annoba a Najeriya,  wanda ya fara da bayyana halin da ake ciki game da yaƙi da HIV a ƙasar. Ga zantawarsu.

donald trump ga hiv akan sida bikin kamar sani duniya najeriya amurka abdoulkarim ibrahim shikal
Madubin Kabara
Murtala Mai | Madubin Usman Kabara #11

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 20, 2025 56:11


Dr. Murtala likitan yara ne dan asalin jihar Adamawar Najeriya da ya rikide ya zama kwararren masanin lafiyar al'umma musamman mata da yara, wanda a yanzu haka ma'aikaci ne a wata kungiya mai zaman kanta da ta ke tallafawa harkokin lafiyar iyali a duniya ciki har da kasashen Afirka mai suna Pathfinder International da ke kasar Amurka.Murtala Mai | Madubin Usman Kabara #11

usman afirka amurka kabara
Madubin Kabara
Fadji Maina | Madubin Usman Kabara #10

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 19, 2025 45:45


‘Yar Nijar kuma masaniyar kimiyyar ruwa da doron kasa da ke aiki a hukumar sama-jannatin Amurka ta NASA. Dr. Fadji Maina tana cikin wacce mujallar tereren arziki ta Forbes ta wallafa sunanta a cikin matasan duniya guda 30 ‘yan kasa da shekara 30 da suka sami nasara a rayuwa. Yanzu haka ma'aikaciya ce a hukumar sama jannatin Amurka ta NASA da ke aiki bisa kwarewar ta a fannin ruwa da kimiyyar doron kasa.

forbes nasa usman maina amurka fadji yanzu kabara
Madubin Kabara
Sarki Abba Abdulkadir | Madubin Usman Kabara #9

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 18, 2025 61:07


A shekarar 1984 a Najeriya an sami wani saurayi dan jihar Kano da ya fi kowane dalibi a Najeriya cin makin jarrabawar gama sakandaren kasashen Afirka ta WAEC a takaice. Yanzu haka dai wannan dalibin mai suna Farfesa Sarki Abba Abdulkadir farfesa ne a bangaren haddasuwar cututtuka a Jami'ar Northwestern University da ke Chicago a Amurka.

Madubin Kabara
Adamu Hamza Bamalli | Madubin Usman Kabara #7

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 16, 2025 120:07


Adamu Hamza Bamalli ya sha gwagwarmaya a Najeriya da Amurka kama daga zama direban babbar mota zuwa rikidewa ya zama kwararren Injiniya a jihar Maryland ta Amurka.

maryland usman adamu najeriya amurka kabara
Mu Zagaya Duniya
Dambarwar siyasar da ta dabaibaye jam'iyyar adawa ta PDP a Najeriya

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Nov 15, 2025 19:39


Shirin Mu zagaya Duniya tare da Nura Ado Suleiman a wannan mako kamar yadda ya saba ya yi bitar muhimman labaran da suka faru a makon da muke bankwana da shi daga ɓangarori daban-daban na duniya. A Najeriya shirin ya faro da batun Siyasa inda a cikin makon da muka yi wa bankwana rikicin cikin gidan babbar Jam'iyyar adawar Najeriyar wato PDP ya zama ɗaya daga cikin batutuwan da suka ɗauki hankali. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

jam ku pdp duniya najeriya amurka
Madubin Kabara
Sabo Tanimu | Madubin Usman Kabara #3

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 12, 2025 29:40


Na ziyarci Dr. Sabo Tanimu a jihar Wisconsin ta Amurka. Yana daya daga cikin kwararrun likitocin kayan cikin bil'adama a kasar inda yake shugabantar bangaren cutar dajin da ta shafi kayan ciki. Dan asalin Najeriya ne daga jihar Benue a tsakiyar Arewacin Najeriya. Shin yaya aka yi Likita Sabo ya fara daga Najeriya har ya tsinci kansa a Amurka inda ya shafe shekaru da dama yana aikin Likita a can.

Madubin Kabara
Ali Nuhu | Madubin Usman Kabara #2

Madubin Kabara

Play Episode Listen Later Nov 11, 2025 12:09


Na yi hira da Ali Nuhu Mohammed jarumin fina-finan Hausa da Turanci na Najeriya a lokacin da ya ziyarci birnin Washington DC da ke Amurka,, in da na tambaye shi darussan da ya koya a cikin shekaru 20 da ya kwashe yana harkar shirya finafinai.

washington dc usman hausa najeriya amurka kabara
Bakonmu a Yau
Ambasada Abubakar Cika kan barazanar kai wa Najeriya hari da Amurka ta yi

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 4, 2025 3:37


Yayin da hukumomin Najeriya suka yi watsi da barazanar shugaban Amurka na kai wa ƙasar hari saboda zargin kashe Kiristoci, ƴan kasar da dama na ci gaba da bayyana ra'ayi a kan matsayin na shugaba Donald Trump. Daga cikin waɗanda suka bayyana ra'ayin su a kan wannan barazana har da tsohon Jakadan Najeriya a ƙasar Iran, Ambasada Abubakar Cika, kamar yadda za ku ji a tattaunawarsu da Bashir Ibrahim Idris.  

donald trump iran hari daga abubakar yayin najeriya amurka bashir ibrahim idris
Bakonmu a Yau
Dr. Abdulhakim Garba Funtuwa kan dambarwar yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Oct 29, 2025 3:37


Ga alama yajejeniyar tsagaita wutar da Isra'ila ta ƙulla tsakaninta da Hamas, wadda Amurka ta tsara ta kama hanyar rugujewa, sakamakon umarnin da Firaminista Benjamin netanyahu ya bayar na ƙaddamar da sabbin hare-hare a Gaza. Wannan ya biyo bayan abinda ya kira ƙin bada gawarwakin sauran Yahudawan da Hamas ta yi garkuwa da su. Domin tattauna wannan dambarwa, Bashir Ibrahim Idris, ya tuntuɓi Dakta Abdulhakin Garba Funtua, mai sharhi a kan harkokin Gabas ta Tsakiya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.........................

ga gaza hamas isra domin garba wannan amurka bashir ibrahim idris
Mu Zagaya Duniya
Shuban Tinubu na Najeriya ya sallami manyan hafsoshin tsaron ƙasar

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Oct 25, 2025 18:30


Daga cikin labarun da shirin 'Mu zagaya Duniya' na wannan makon ya kunsa akwai labarin matakin da shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ɗauka na yin tankaɗe da rairaya a manyan hukumomin tsaron ƙasar, inda ya sallami manyan hafsoshin tsaron ƙasar, dai dai lokacin da rundunar sojin Najeriya ta ce ta samu nasarar kashe ‘yan ta'adda fiye da 50 yayin wasu jerin hare-hare da mayaƙan Boko Haram suka ƙaddamar kusan lokaci guda a kan garuruwan daban daban a jihohin Borno da Yobe. Shirin ya waiwayi wasu daga cikin lamurran da suka wakana a Kamaru inda ake cigaba da dakoon Kotun Fasalta Kundin tsarin mulki ta tabbatar da sakamakon zaɓen shugabancin ƙasar. A yankin gabas ta tsakiya, Amurka ta hau kujerar naki kan yunƙurin wasu na ganin Isra'ila ta kwace iko ya yankin Falasɗinu na Gaɓar yamma da kogin Jordan.

Wasanni
Makomar ƙasashen Najeriya, Senegal da Afrika ta Kudu a gasar cin kofin Duniya

Wasanni

Play Episode Listen Later Oct 13, 2025 9:49


Shirin a wannan mako ya mayar da hankali ne kan wasannin neman tikitin zuwa gasar cin kofin Duniya ta 2026 da ƙasashen Amurka, Mexico da Canada za su karɓi baƙunci. A Nahiyar Afrika tuni dai wasu ƙasashe suka sami tikitin zuwa gasar da suka haɗar da Morocco da Tunisia da Aljeriya da Ivory Cost, sai dai ƙasashen Najeriya da Afrika ta Kudu da kuma Senegal na cikin halin rashin tabbas, sai dai a wannan Talata ne za su san makomarsu. Latsa alamar sauti don sauraron shirin tare da Abubakar Isah Ɗandago..................

Muhallinka Rayuwarka
Alfanun cibiyar bunƙasa noma a jihar Kano ga ci gaban samar da abinci a Najeriya

Muhallinka Rayuwarka

Play Episode Listen Later Oct 11, 2025 19:02


Shirin Muhallinka Rayuwarka tare da Michael Kuduson a wannan mako ya mayar da hankali kan yadda aka samar da wata katafariyar cibiyar bunƙasa harkokin noman Damuna dana Rani ga al'ummar jihar Kano wadda aka samar a garin Kadawa da ke ƙaramar hukuamr Garin Malam. bayanai sun ce wannan cibiyar bunƙasa noma na ƙunshe da tarin kayakin buƙata a lokacin noman walau na rani ko kuma na damuna duk dai a ƙoƙarin haɓaka harkar noma a jihar ta Arewa maso yammacin Najeriya. Bankin Musulunci da haɗin gwiwar gwamnatin jihar Kanon ne suka samar da wannan cibiya wadda ta laƙume biliyoyin dalolin Amurka ƙarƙashin shirin KSSB na haɓaka noma bisa kulawar SASAKAWA. Ku latsa alamar tsari don sauraron cikakken shirin tare da Michael Kuduson.....

Mu Zagaya Duniya
Dubban Falasɗinawa sun fara tururuwar komawa muhallansu a yankin arewacin Gaza

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Oct 11, 2025 20:02


Daga cikin labarun da shirin 'Mu zagaya Duniya' tare da Nura Ado Sulaiman, ya waiwaya a wannan makon akwai halin da ake ciki a Zirin Gaza bayan yarjejeniyar tsagaita wutar yaƙin da aka samu nasarar ƙullawa tsakanin Isra'ila da Hamas.Shirin ya kuma waiwayi zaɓen shugabancin Kamaru wanda masu fashin baƙi ke ci gaba da tofa albarkacin bankinsu a kai. A najeriya kuma akwai waiwayen afuwar da shugaba Bola Tahmed Tinubu ya yi wa wasu mutane fiye da 170 Latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin...........

Kasuwanci
Yadda Najeriya ta kashe kusan Dalar Amurka biliyan 3 wajen biyan kuɗin ruwan

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Oct 8, 2025 10:03


Shirin ‘Kasuwa A Kai Miki Dole' na wannan mako zai tattauna ne kan wasu alƙaluma da suka nuna yadda Najeriya ta Kashe Dala Biliyan 2.86 a cikin watanni 8 na farkon shekarar da muke ciki ta 2025, wajen Biyan Kuɗin Ruwan Basukan da ta karɓo daga ƙasashen ƙetare tare da Nura Ado Suleiman..... Latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin...........

yadda dalar ruwan najeriya amurka
Mu Zagaya Duniya
Faransa ta jagoranci gwamman ƙasashen Turai wajen amincewa da ƙasar Falasɗinu

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Sep 27, 2025 20:01


A cikin wannan shirin da ke waiwaye kan mahimman labaran wannan makon, za ku ji cewa:  Faransa ta jagoranci ƙarin gwamman ƙasashe wajen amincewa da Yankin Falasɗinu a mamtsayin ƙasa ‘Yantacciya a wani yunƙuri na Diflomasiya da ke zama ɗaya daga cikin mafiya girma da aka gani cikin shekaru da dama.   Shirin zai kuma waiwayi jawaban wasu daga cikin shugabannin Nahiyar Afrika a zauren babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya. Najeriya ta yi fatali da rahoton Amurka da ya zargi mahukuntan ƙasar da gazawa sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na aiwatar da ayyukan raya ƙasa da akw warewa maƙudan kuɗaɗe a kasafi duk shekara. Da dai sauran mahimman labarai.

shirin duniya asar turai najeriya amurka faransa majalisar
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyi kan shirin Amurka na hana ƴan Najeriya masu rashawa shiga ƙasar

Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Play Episode Listen Later Sep 25, 2025 9:55


Shirin Ra'ayoyin mai Saurare na wannan ranar Alhamis 25 ga watan Satumbar 2025, wanda Oumar Sani ya gabatar, ya tattauna ne kan matakin gwamnatin Amurka na hana duk wani ɗan Najeriya ciki har da jami'an gwamnati da aka samu da hannu da rashawa bisar da za ta ba su damar shiga ƙasar.

shirin asar shiga masu najeriya amurka alhamis
Bakonmu a Yau
Maitre Lirwanou Abdourahman kan ficewar Nijar Mali da Burkina Faso daga ICC

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Sep 24, 2025 3:32


Burkina Faso, Mali da kuma Nijar sun sanar da janyewar ƙasashensu daga Kotun Hukunta Laifufuka ta Duniya da ke birnin Hague. A sanarwar haɗin-gwiwa da suka fitar cikin daren litinin da ta gabata, ƙasashen uku sun ce sun ɗauki matakin saboda sun lura cewa kotun ta rikiɗe domin zama ƴar amashin ƴan mulkin mallaka. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani dokokin ƙasa da ƙasa Maitre Lirwanou Abdourahman, domin jin ko wataƙila ya yarda da dalilan da wadannan ƙasashe suka gabatar. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

mali ku burkina faso hague maitre daga duniya nijar najeriya amurka abdoulkarim ibrahim shikal
Al'adun Gargajiya
Yadda aka bar baya da ƙura a girmamawar da ka yiwa Rarara da digirin Dakta

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Sep 23, 2025 10:02


Shirin Al'adunmu na Gargajiya tare da Nura Ado Suleiman a wannan makon ya sake waiwayar fagen Waƙa guda daga cikin fannoni masu tasiri a Adabin Harshen Hausa la'akari da gudunmawar waƙoƙin da kuma mawaƙan da ke rera su wajen bunƙasa harshen. Tun cikin makon jiya masana da sauran jama'ar gari ke tofa albarkacin bakunansu akan karramawar  da wata Jami'a mai suna European-American University ta yi wa fitaccen mawaƙin siyasa a Najeriya Dauda Kahutu Rarara, wanda ta bai wa Digirin Girmamawa na Dakta. Reshen Jami'ar da bayanai a yanar gizo suka nuna cewar hedikwatarta na ƙasar Faransa ne ta yi bikin Karrama mawaƙi Raran ne a Abuja, ranar Asabar, 20 ga watan nan na Satumba, taron da ya samu halartar wasu fitattun mutane. Sai dai Kash! ‘yan sa'o'i bayan bikin da aka yi Jami'ar da ake alaƙanta da Turai da Amurka ta ce ba ta fa san zance ba, domin ba da yawunta aka miƙa wa fitaccen mawaƙin siyasar Digirin na Girmamawa ba, zalika dukkanin mutanen da suka yi iƙirarin alaƙanta kansu da ita ta barranta da su, domin sun yaudari mutane ne da sunanta domin samun damar karɓar na goro a huce. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

wa ku tun sai abuja baya yadda turai amurka faransa gargajiya
Bakonmu a Yau
Farfesa Tukur Abdulƙadir kan ƙarin ƙasashen da ke amincewa da Falasɗinu

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Sep 23, 2025 3:45


Ƙasashen duniya na ci gaba da nuna amincewarsu da samar da ƴantacciyar ƙasar Falasɗinu, a wata guguwa wadda ba'a taɓa ganin irinta ba. Ƙasashen turai da ake ganin suna da ƙyakyawar alaƙa da Amurka irinsu su Burtaniya, Canada da kuma Australia a wannan Karo sun sanar da amincewar su da baiwa Falasɗinu damar zama ƙasa mai cin gashin kanta amma bisa wasu shariɗoɗi. A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara Farfesa Tukur Abdulƙadir ya ce har yanzu da sauran rina a kaba don kuwa amincewar waɗannan ƙasashe ƙadai a fatar baki bata wadatar ba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

Wasanni
Makomar tawagar Najeriya a ƙoƙarin neman gurbin zuwa gasar lashe kofin duniya

Wasanni

Play Episode Listen Later Sep 15, 2025 9:56


Shirin a wanan mako tare Khamis Saleh, ya yi duba ne kan makomar tawagar Najeriya a ƙoƙarin neman gurbin zuwa gasar lashe kofin duniya, inda a tsakiyar makon da ya gabata aka kammala wasannin na 8 na sharen fagen zuwa gasar lashe kofin duniya da ƙasashen Canada da Mexico da kuma Amurka za su karɓi bakunci a shekara mai zuwa. Kawo yanzu dai wasanni sun ɗauki zafi ganin cewa wasu daga cikin tawagogin ƙasashen sun fara jin kanshin halartar gasar, amma kuma wasu har yanzu tana ƙasa tana dabo. Latsa alamar sauri domin sauraron cikakken shirin.....

Mu Zagaya Duniya
Shirin ƙarin albashin masu riƙe da muƙaman siyasa a Najeriya ya bar baya da ƙura

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Sep 13, 2025 20:00


A karon farko gwamnatin Najeriya ta hannun hukumarta da ke kula da sufurin jiragen ruwa a koguna ko kuma cikin gida, ta shelanta haramta jigilar duk wani jirgi ko kwale-kwale da ba a yi wa rijista da gwamnati ba, Ghana ta karɓi baƙi ‘yan Afirka ta yamma, waɗanda gwamnatin Amurka ta taso ƙeyarsu a ƙarƙashin shirin shugaba Donald Trump na korar baƙin-haure, wasu kenan daga cikin manyan labarun makon jiya da Nura Ado Suleiman zai kawo muku a cikin shirin Mu zagaya Duniya.. Latsa alamar sauti don sauraron shirin..........

Mu Zagaya Duniya
Bitar mako: Rundunar Sojin Najeriya ta samu nasarar kashe ‘yan ta'adda kusan 600

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Aug 16, 2025 19:59


Wasu daga cikin labarun makon da ya gabata da shirin 'Mu Zagaya Duniya' ya waiwaya a wannan karon sun haɗa da, nasarar da rundunar Sojin Najeriya ta samu na kashe ‘yan ta'adda kusan 600 da yarjejeniyar sayen makamai da ƙasar ta ƙulla da Amurka. Sai kuma a fannin tattalin arziƙi, inda wata tawaga ta musamman daga ƙasar Qatar ta fara ziyarar makwanni kusan 3 a wasu ƙasashen nahiyar Afrika domin ƙulla yarjeniyoyi gami da zuba hannayen jarin biliyoyin Dalar Amurka a ƙasashen aƙalla 10.

Bakonmu a Yau
Abdulhakeem Funtuwa kan yunkurin dakatar da yaƙin Ukraine wajen mantawa da Gaza

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Aug 14, 2025 3:27


A ranar Jumma'a ake saran shugaban Amurka Donald Trump zai yi wata ganawa da takwaransa na Rasha Vladimir Putin dangane da yadda za'a kawo ƙarshen yaƙin da ake gwabzawa a Ukraine. Sai dai wasu da bayyana damuwa kan yadda shugabannin suka manta da batun tsagaita wuta a yaƙin Gaza, ganin yadda ake ci gaba da asarar rayukan ɗimɓin rayuka. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr. Abdulhakeem Garba Funtuwa dangane da yunkurin ƙasashe duniyar na samaun tsagaita wuta da kuma watsi da halin da ake ciki a Gaza.

Lafiya Jari ce
Matakin Amurka ka iya haifar da koma baya ga shirin yaki da cutar HIV a Najeriya

Lafiya Jari ce

Play Episode Listen Later Aug 4, 2025 10:11


Shirin ya mayar da hankali ne kan yadda matakin Amurka na janye tallafin da take ba wa ɓangaren kula da masu fama da cuta mai karya garkuwa jiki ta HIV da ake fargabar zai iya haifar da koma baya ga shirin yaƙi da cutar. Tuni hukumomi a duniya suka fara tofa albarkacin bakinsu kan wannan mataki da shugaban Amurka, Donald Trump ya ɗauka, wanda ake ganin zai fi yin tasiri ne ga nahiyar Afirka. Tuni mujallar Lancet ta Biritaniya ta yi hasashen cewa matakin na Donald Trump na iya haifar da mutuwar mutane sama da miliyan 14 nan da shekarar 2030, ciki har da yara sama da miliyan 4.5 'yan kasa da shekaru biyar. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Azima Bashi Aminu.

Kasuwanci
Takardar kuɗin Najeriya ta samu tagomashi a kwanakinnan

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Jul 23, 2025 10:02


To kamar yadda akaji a matashiyar shirin, ra'ayoyin masana tattalin arziki sun banbanta a Najeriya, tun bayan da sananne a harkar tattalin arziki Bismark Rewane ya tabbatar cewa Naira ta daidaita tsakanin 1500 zuwa 1560 kan kowace dala a makonnin baya-bayan nan, yayin da tattalin arzikin ƙasar kuwa ya fara farfadowa sakamakon matakin babban bankin na Najeriya CBN da ya sanya zunzurutun ƙudi har dalar Amurka biliyan 4 da miliyan 100 cikin watanni shida na wannan shekara...ta 2025.

samu naira najeriya amurka
Tambaya da Amsa
Me ye dalilin Amurka da ƙawayenta na hana Iran mallakar makamin Nukiliya?

Tambaya da Amsa

Play Episode Listen Later Jul 19, 2025 20:45


Shirin Tambaya da Amsa na wanan makon tare da Nasiru Sani ya amsa wasu daga cikin muhimman tambayoyin da ku masu sauraro ku ka aiko mana. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkaen shirin....

Mu Zagaya Duniya
Yadda hare-haren ta'addanci ke ci gaba da sanadin mutuwar mutane a Najeriya

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Jul 12, 2025 19:21


Hukumar kare hakkin ɗan Adam ta Najeriya ta ce  adadin mutanen da ‘yan ta'adda suka kashe a cikin watanni shidan farko na wannan shekara, ya zarce adadin da aka lissafa a shekarar bara. Ƙungiyar direbobin motocin dakon kaya a Senegal ta koka kan matsalolin tsaro da suka fara shafar yankunan kan iyakar ƙasarsu da Mali, inda ta yi barazar dakatar zirga-zirga zuwa Malin muddin mahukunta suka gaza ɗaukar matakan da suka ɗace. Kakakin majalisar dokokin Kenyan ya goyi bayan bai wa ‘yan sandan Umranin harbe duk mai zanga-zangar da aka samu yana satar dukiyar jama'a da lalata kayan gwammnati. A Amurka kuwa Ambaliyar ce ta yi sanadin mutuwar aƙalla mutane 119 Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Nura Ado Sulaiman.

Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Alhaji Garba Suleiman Krako Madakin Saminaka kan ambaliyar Texas

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jul 10, 2025 3:33


Rahotanni daga Amurka na cewa an samu ƙaruwar yawan mutanen da suka rasa rayukansu a sakamakon Iftila'in Ambaliyar ruwan da ya afka wa Jihar Texas, inda zuwa yanzu adadin ya haura mutane 115, yayin da har aynzu aka gaza gano wasu aƙalla 160 da suka ɓace. Domin jin halin da ake ciki da kuma dalillan da suka haddasa aukuwar ambaliyar a Texas, Nura Ado Suleiman ya tattauna da mazaunin ƙasar ta Amurka, Alhaji Garba Suleiman Krako Madakin Saminaka. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....

Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Dr Idris Harbau kan taron ƙasashen BRICS a Brazil

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jul 9, 2025 3:34


A ranar Litinin ƙasashe manbobin ƙungiyar BRICS suka kammala taronsu na 17 a Brazil, inda a cikin kwanaki biyu da suka shafe suna ganawa, jagororin ƙasashen suka tattauna a kan yadda manufofin shugaba Trump ke tasiri kan tattalin arziƙi da kasuwancin Duniya. Sai dai tun kafin kammala taron, shugaba Trump ɗin ya yi barazanar lafta harajin kashi 10 kan kayayyakin ƙasashen na BRICS, da ma duk wata ƙasa da ta goyi bayan matakan adawa da manufofin Amurka. Kan wannan batu, da kuma tasirin ƙungiyar ta BRICS Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Aminu Idris Harbau, masanin tattalin arziƙi da ke Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar..

Bakonmu a Yau
Amb Abubakar Chika: cika shekaru 80 da sanya hannu kan yarjejeniyar samar da MDD

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jun 26, 2025 3:35


Yau ake cika shekaru 80 da rattaɓa hannu kan yarjejeniyar da ta samar da Majalisar Ɗinkin Duniya da aka gudanar a Birnin San Francisco da ke Amurka, a ranar 26 ga watan Yunin shekarar 1945. Bikin cika shekaru 80 din na zuwa ne a daidai lokacin da Majalisar mai wakilai 193 ke fuskantar kalubale da dama, waɗanda suka hada da makomar ta ko kuma ci gaban tasirinta baki ɗaya. Kan wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ambasada Abubakar Chika, tsohon jakadan Najeriya a Iran. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana..........

iran ku bikin chika samar sanya duniya abubakar hannu yau najeriya amurka majalisar dinkin duniya majalisar bashir ibrahim idris
Wasanni
An bude gasar lashe ƙofin duniya ta kungiyoyi a Amurka

Wasanni

Play Episode Listen Later Jun 16, 2025 9:30


Shirin Duniyar wasanni na wanan makon tare da Khamis Saleh ya maida hankali ne akan gasar lashe ƙofin duniya ta kungiyoyi da aka bude a karshen mako a ƙasar Amurka dama sauye -sauyen da aka samu a bana.  Ku shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shiri........