POPULARITY
A yau shirin tamabaya da amsa, tare da Nasiru Sani, zai kawo muku bayanai ne akan tasirin tsarin harajin da shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaƙabawa ƙasashen Canada da Mexico da kuma China akan ƙasashe Afirka. Shirin ya kuma zanta da kwararru a fannin lafiya, kan dalilan da ke sanya shan ruwa a kai.Akwai kuma cikakken bayani kan Sultan Makenga, wato jagoran ƙungiyar 'yan tawayen M23 wanda ya hana zaman lafiya a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo, musamman ma a gabashin ƙasar.Shiga alamar sauti, domin saurarin cikakken shirin.
Yau shugaban Amurka Donald Trump le cika kwanaki 100 a karagar mulkin ƙasar, tun bayan rantsar da shi a ranar 20 ga watan Janairun shekarar nan. A tsawon wannan lokaci, shugaban na Amurka ya ɗauki mabanbantan matakai da suak girgiza sassan duniya.Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Tukur Abdulkadir na Jami'ar Kaduna, don jin yadda masana ke kallon salon kamun ludayin Donald Trump ga kuma tattaunawarsu.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar..
Gwamnatin shugaba Donald Trump ta gabatar da ƙudurin daina ba da tallafi ga rundunonin wanzar da zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya, saboda gazawar da ta ce rundunonin na yi a ƙasashen Mali da Lebanon da kuma Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo.Amurka ce dai ke kan gaba wajen tallafa wa ayyukan wanzar da zaman lafiyar a sassan Duniya, inda take samar da kusan kaso 27 cikin 100 na kasafin da ake buƙata.akan haka ne, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Kamilu Sani Fagge.
Shirin Mu Zagaya Duniya tare da Nura Ado Suleiman, kamar kowannen mako kan yi bitar muhimman labaran da suka faru cikin makon da muke ban kwana da shi, kuma kamar kodayaushe a wannan karon wasu daga cikin labaran da ke ƙunshe a shirin sun ƙunshi ziyarar da Ministan Harkokin Wajen Najeriya ya kai Jamhuriyar Nijar, wadda a karon farko kenan tun bayan kifar da gwamnatin shugaba Muhammad Bazoum da sojoji suka yi. A Najeriya shirin ya leƙa Filato aka samu hasarar ɗimbin rayuka, sakamakon hare-haren da aka kai a wasu yankunan jihar, a Najeriyar za a ji yadda wata shu'umar cuta ta janyowa manoman Tumatir hasarar ɗimbin amfanin gonar, sai kuma yadda ‘yan damfara suka yi awon gaba da sama da naira tiriliyan 1 a Najeriyar.A Sudan kuwa ƙungiyar bayar da agaji ta Redcross ce ta aƙalla mutane dubu 8000 suka bace a yakin kasar.Sai kuma Kenya inda aka cafke wasu mutane da ke shirin fasa kaurin dubban tururuwa zuwa ƙasashen ƙetare.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin 'Kasuwa A kai Miki Dole' na wannan makon ya mayar da hankali kan tasirin matakin shugaban Amurka Donald Trump kan shirin sa na sanya gagarumin ƙarin haraji ga kusan ɗaukacin ƙasashen duniya, wanda ya jawo durƙushewar kasuwannin hannayen jari ta duniya da lalata alaƙa tsakanin ƙasar da ƙawayenta, duk da cewa ya yi amai ya lashe wajen dakatar da harajin da watanni uku masu zuwa. Shirin ya duba tasirinsa ga ƙasashen Afirka masamman Najeriya.
Shirin Lafiya Jari ce tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan ƙaruwar masu kamuwa da cuta mai karya garkuwar jiki ko kuma HIV AIDS ko sida tsakanin matasan Ghana a shekarun baya-bayan nan, wadda masana ke ɗora alhakin yawaitarta kan rashin ɗaukar matakai. Wannan ƙaruwar alƙaluma na zuwa a dai dai lokacin da duniya ke ganin ƙarancin magunguna rage kaifin cutar sakamakon matakin Amurka na zaftare tallafin da ta ke bayarwa ƙarƙashin ƙungiyar USAID.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shiri.
A Laraba 9 ga watan Afrilu, sabon harajin da ya kama daga kashi 10 zuwa sama, da shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaƙaba wa ƙasashen Afirka zai fara aiki, bayan da harajin da ya shafi sauran ƙasashe ya soma aiki a ranar 5 ga watan na Afrilu. Tun cikin makon jiya ne dai matakin na Trump ya soma tasiri a kasuwannin Turai da Asiya, a yayin da ƙasashen Afirka suka shiga zulumi dangane da makomarsu.Don jin tasirin da sabon harajin na Amurka zai yi a kan tattalin Arzikin arziƙin ƙasashen Afirka, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dr Ƙasim Garba Kurfi.A latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar zanatawar.
ƙasashe da dama ciki har da na Ƙungiyar EU, suka sha alwashin mayar da martanin ƙaƙaba wa kayayyakin Amurka haraji, kamar yadda shugaba Trump ya ƙaddamar da sabon tsarin karɓar harajin da ya ce ya shafi duniya baki ɗaya.
Ƙasashe da dama ciki har da na Ƙungiyar EU, sun alwashin mayar da martanin ƙaƙaba wa kayayyakin Amurka haraji, kamar yadda shugaba Trump ya ƙaddamar da sabon tsarin karɓar harajin da ya ce ya shafi duniya baki ɗaya.Sabon harajin dai ya kama ne daga kashi 10 zuwa sama, wanda ya shafi hajoji daga kowace ƙasa, matakin da Trump matakin ya ce ya ɗauka ne don kare buƙatun al'ummar Amurka. Don jin yadda masana ke kallon sabon yaƙin kasuwancin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta AbdulHakim Garba Funtua.
A yayinda aka cika shekaru 3 cif da faro yaƙi tsakanin ƙasashen Rasha da Ukraine maƙwabtan juna, dukkanin ɓangarorin biyu sun tafka gagarumar asara marar misaltuwa a wannan ɗan tsakani kama daga Sojojinsu da ke fagen daga da kuma kayakin more rayuwa da kowacce ta lalatawa ƴar uwarta. A baya-bayan nan anga yadda shugaban Amurka Donald Trump ke ƙoƙarin kawo ƙarshen wannan yaƙi ta hanyar tuntuɓar Vladimir Putin na Rasha a wani yanayi da tuni aka faro taron tattaunawa kan kawo ƙarshen wannan yaƙi a Saudiya kodayake batun bai yiwa ƙasashen Turai daɗi ba, ganin yadda basu samu goron gayyata a tattaunawar ba, haka zalika itama Ukraine.Dangane da wannan dambarwa ne kuma Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abdulhakeem Garba Funtua masanin siyasar ƙasashe ga kuma yadda zantawarsu ta gudana.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar...
Shirin na Tambaya da amsa na baiwa masana damar kawo ƙarin haske a wasu daga ciƙin tambayoyinku daga nan Rfi,shin ko wata kasa a doron duniyar nan, ta taba fusƙantar irin gobarar da ta tashi a birnin Los Angeles na Amurka kuma duk da kasancewarta babbar ƙasa mai isassun kayan aiki,ko mai ya hana ya hana Amurka samun nasarar shawo kan gobarar a cikin ƙanƙanin lokaci
Shugaban Amurka Donald Trump ya bada umarnin sanya takunkumi akan kotun duniya ta ICC da kuma haramtawa jami'anta dake binciken 'yan kasarsa ko kuma kawayen Amurka irin su Isra'ila. Abin tambayar shine, wanne irin tasiri wannan mataki zai yi?Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar Bashir Ibrahim Idris da Farfesa Shehu Abdullahi Zuru, masanin shari'a a Jami'ar Baze, da ke Nijeriya.
Ƙasashen duniya sun bayyana matukar rashin amincewarsu da buƙatar shugaban Amurka Donald Trump, na ƙwace Gaza da kuma mayar da Falasdinawa wasu ƙasashe domin gina wurin shaƙatawa a ƙasarsu. Wannan matsayi ya gamu da suka daga ƙasashen duniya da dama ciki harda Majalisar Ɗinkin Duniya. Bashir Ibrahim Idris ya tatatuna shirin da Ambasada Abubakar Cika, tsohon Jakadan Najeriya a kasar Iran. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana.........
Ƙasashen duniya na ci gaba da bayyana damuwa dangane da shirin shugaban Amurka Donald Trump na dakatar da ayyukan hukumar USAID wadda ke taimakawa ƙasashen duniya . Wannan hukuma dai na taka gagarumar rawa a bangarori da dama a ƙasashe masu tasowa irin su Najeriya.Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Abba Gambo, mai bai wa gwamnonin Najeriya shawara a kan harkokin noma dangane da tasirin matakin a kan noman ƙasar.Latsa alamar sauti domin sauraren yadda tattaunawar ta kasance....
Bayan shafe watanni 15 ana gwabza mummunan yaƙi a yankin Gaza tsakanin sojojin Isra'ila da mayaƙan Hamas da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama, shugabaan Amurka, Donald Trump ya ce yaƙin ya lalata yankin na Gaza baki daya, don haka ya bayyana wa Sarki Abdallah na Jordan buƙatar kwashe Falasɗinawa daga yankin zuwa ƙasarsa kuma ya ce ya na sa ran tattaunawa da shugaban Masar, Abdel Fattah al-Sisi a kan haka. A kan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da masanin lammuran da suka shafi Gabas ta Tsakiya, Malam Isma'il Ahmad.Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu............
A ƙasar Amurka, bayan rantsar da shi a matsayin sabon shugaba ƙasa na 47, Donald Trump, ya rattaba hannu kan wasu gomman dokokin zartawa na ikon shugaban ƙasa, ciki har da janye ƙasarsa daga Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), kamar yadda ya yi a wa'adin mulkinsa na farko, kafin magabacinsa Joe Biden ya maido da ƙasar ciki. Wasu na ganin wannan mataki zai yi illa ƙwarai ga ɗorewar hukumar wajen gudanar da ayyukan ta a duniya, duba da kaso mai tsoka da Amurka ke bayarwa wajen gudanar da ayyukan WHO ɗin.Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi...
Sabon shugaban Amurka Donald Trump ya janye kasarsa daga cikin mambobin Hukumar Lafiya ta Duniya, matakin da wasu ke ganin na iya illa ga dorewar hukumar wajen gudanar da ayyukan ta a duniya. Dangane da tasirin matakin, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Balarabe Sani Garko na Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Sabon shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana manufofin gwamnatinsa bayan karbar rantsuwar kama aiki da ya yi a matsayin shugaba na 47. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abdulhakeem Garba Funtua na Babbar kwalejin Fasaha ta Kaduna dangane da wadannan manufofi, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana a kai.
Wasu daga cikin muhimman labaran da za ku ji a wannan shiri sun ƙunshi nasarar cimma yarjejeniya tsakanin Isra'ila da Hamas sai kuma wutar dajin Los Angeles wadda ta cinye faɗin yankin da ya zarta girman birnin Washington DC fadar gwamnatin Amurka akwai yadda
Daga cikin labarun da shirin wannan makon ya waiwaya akwai yadda ɗaruruwan mutane mazauna ƙauyuka aƙalla 50 suka tsere daga muhallansu saboda barazanar da ƙasurgumin ɗan ta'adda Bello Turji yayi na kai musu farmaki, a ranar 1 ga watan Janairun da ya gabata. Sai kuma waiwayar rawar da tsohon shugaban Amurka marigayi Jimmiy Carter ya taka wajen samar da zaman lafiya a Yankin Gabas ta Tsakiya.
Ana ci gaba da jimamin mutuwar tsohon shugaban Amurka Jimmy Carter wanda ke shan jinjina saboda irin gagarumar rawar da ya taka wajen samar da zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya da kuma ingantan rayuwar talakawa a ƙasashen Afrika da suka haɗa da Najeriya da Nijar. Ambasada Abdullahi Bindawa, na ɗaya daga cikin jami'an da suka yi aiki kut da kut tare da Jimmy Carter, ga kuma abin da yake cewa kan marigayi a hirarsa da Abdurrahman Gambo AhmadKu latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu
A yayin da ake bankwana da shekarar 2024 shuwagabanni daga kasashen Duniya na fuskantar tarin kalubale da suka hada da rikice-rikice,yake-yake harma da wasu matsalolin da suka shafi sauyin yanayi da matsin tattalin Arziki da sauran su. Wasu abubuwa ne baza ku iya mantawa ba kuke tsoron dakon su zuwa sabuwar shekara?Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin, tare da Hauwa Garba Aliyu Zaria.
Wani rahoton Bankin Duniya ya nuna cewa Najeriya ce ƙasa ta uku a yawan basususun kasashen ketare, bayan da ta ƙarbi sama da dalar Amurka biliyan 16.5 kwankwacin naira Triliyan 27 da biliyan 700. Da wannan matsayi Najeriya ta na biye ne da ƙasashen Bangladesh mai matsayi na ɗaya da Pakistan ta biyu a yawan basussuka a duniya.Sabon ranceHakan na zuwa ne kwanaki kadan bayan da majalisar dattawan najeriyar ta sahalewa shugaba Tinubu karbo sabon rancen naira Tiriliyan 1 da biliyan 700, duk da ikirarin ƙasar na samun ƙudin haraji mai yawa daga hukumar kwastom da sauransu.Yawan basussukaBayaga bankin duniya duniya, jummular basussukan da Najeriya ta ƙarbo ya kai naira triliyan 138, wanda hasashe ma ke cewa zai kai dala biliyan 45 kafin karshen wannan shekara ta 2024.
Ana ci gaba da samun martani daban daban dangane da umarnin kotun duniya ta ICC na bada sammacin kama Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu da tsohon ministan tsaronsa Yoav Gallant da kuma shugaban Hamas Mohammed Deir saboda aikata laifuffukan yaki. Yayin da wasu ke murna da matakin, wasu kuma irinsu Amurka na watsi da shi. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin harkar shari'a Farfesa AShehu Abdullahi zuru, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Shirin mu zagaya Duniyaya yi dubi da yadda zaben Amurka ya gudana. Karibullah Abdulhamid na Madobi ya gabatar.
Yau Amurkawa ke kaɗa ƙuri'a a zaɓen ƙasar da bayanai ke cewa fiye da mutum miliyan 180 za su jefa ƙuri'unsu don zaɓen guda cikin ƴan takara biyu da ke fafatawa wato tsohon shugaban ƙasar Donald Trump na jam'iyyar Republican da Kamala Harris ta Jam'iyyar Democrat wadda mataimakiyar shugaban ƙasa ce kuma ƴar takarar mace baƙar fata ta farko a tarihin ƙasar. Domin jin tasirin wannan zaɓe da ya ɗauki hankalin duniya Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Shehu Abdullahi Zuru na Jami'ar Baze.
Yau Amurkawa ke kaɗa ƙuri'a a zaɓen ƙasar da bayanai ke cewa fiye da mutum miliyan 180 za su jefa ƙuri'unsu don zaɓen guda cikin ƴan takara biyu da ke fafatawa wato tsohon shugaban ƙasar Donald Trump na jam'iyyar Republican da Kamala Harris ta Jam'iyyar Democrat wadda mataimakiyar shugaban ƙasa ce kuma ƴar takarar mace baƙar fata ta farko a tarihin ƙasar. Domin jin tasirin wannan zaɓe da ya ɗauki hankalin duniya Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Shehu Abdullahi Zuru na Jami'ar Baze.
Shirin Mu Zagaya Duniya na wannan mako tare da Ƙaribullah Abdulhamid Namadobi kamar ko yaushe ya yi duba kan muhimman labaran da suka faru a makon da muke shirin bankwana da shi, ciki kuwa har da batun matsalar wutar lantarkin da yankin Arewacin Najeriya ya yi fama da shi, sai kuma shirye-shiryen tunƙarar zaɓen Amurka da ke tafe a makon gobe. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin wanda ya taɓo ɓangarori daban-daban na duniya kama daga Afrika da nahiyar Turai, Asiya da kuma tashe-tashen hankulan da ake fama da su a sassan duniyar musamman gabas ta tsakiya.
Kamar yadda wata kila kuka ji a cikin labaran duniya, Ministan harkokin wajen Najeriya, Ambassada Yusuf Tuggar ya bayyana manyan dalilan da ya kamata a yi dubi da su domin sanya kasar a matsayin mambar kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya. Shugaban Sashen Hausa na RFI, Mr Joseph Penney ya tattauna da ministan a zauren Majalisar dake ci gaba da gudanar da taronta a New York ta kasar Amurka, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Shirin Mu zagaya Duniya da ke bitar labaran mako tare da Nura Ado Suleiman ya taɓo yadda ambaliyar ruwa ke ci gaba da ɓarna a sassan arewacin Najeriya a wani yanayi da hukumar NEMA ke gargaɗi kan yiwuwar ambaliyar ta shafi mutane fiye da miliyan 3 a jihar Kano kaɗai.
Tsohon shugaban ƙasar Amurka Donald Trump, wanda ke takarar shugabancin ƙasar a ƙarƙashin jam'iyyar Republican a zaɓe mai zuwa ya tsallake rijiya da baya, bayan da wani mutum mai shekaru 20 ya ya yi yunƙurin kashe shi ta hanyar harbin bindiga, yayin da ya ke yaƙin neman zaɓe a jihar Pennsylvania a ranar Asabar, al'amari da ya ta'azzara rarrabuwar kawuna mai muni da a ke da ita a fagen siyasar Amurka. Ko wane tasiri ne hakan zai yi ga siyasar wannan ƙasa, wadda ke zama a matsayin abin koyi, kuma ke da'awar kare dimokaradiyya a faɗin duniya. A kan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da masanin siyasar ƙasa da ƙasa, Farfesa Kamilu Sani Fagge.
GwamnatIn Najeriya ta magantu, Bayan ganin yadda al'umman Najeriya suka hasala kan yarjejeniyar da ta rattaba wa hannu da ƙungiyar Tarayyar Turai, wadda ake ta zargin cewa akwai sharaɗin sai ƙasa ta amince da batun auren jinsi kafin a ba ta rancen wasu kuɗaɗe da suka kai dalar Amurka biliyan 150, inda ta ce babu gaskiya a cikin lamarin, tana mai cewa hasali ma babu wani abin da ya shafi rance na kuɗi a wannan yarjejeniya. A kan haka ne wakilinmu na Abuja Mohammed Sani Abubakar ya nemi ƙarin bayani a tattaunawarsa da ministan kasafi da tsare-tsaren tattalin arziki na Najeriyar, Abubakar Atiku Bagudu.
Amurka ta yi gargadin cewa, bayan ficewar dakarunta daga Jamhuriya Nijar a tsakiya watan Septumbar wannan shekara, akwai yiyuwar za a fuskanci tarin matsaloli a cikin kasashen Yammacin Afirka. Domin jin yadda masana ke kallon wannan gargadi na Amurka, Umar Sani ya tattauna da Malam Sanoussi Mahamane, masani kan lamurran da suka shafi tsaro a Jamhuriyar Nijar.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu.
Ƴan Majalisar Amurka sun fara shirin bada damar hukunta alkalan kotun duniya da suka bada damar tuhumar Isra'ila da aikata laifuffukan yaki. Danna alamar saurare don jin cikakkiyar tattaunawar tare da Bashir Ibrahim Idris
Kungiyar tarayyar Turai da Amurka sun gargadi Isra'ila a shirin da take yi na kai hari Rafah, duk da cewa alamu sun nuna cewa kasar bata da shirin dakatar da kudurin nata. Danna alamar saurare don jin cikakkiyar tattaunawar tare da Bashir Ibrahim Idris
Bayan yin bazata wajen farfaɗowa daga faɗuwar da yayi a watannin baya, kuɗin Najeriya ya fuskanci koma baya musamman a makon jiya, inda a kasuwar canjin bayan fage aka sayar da dala guda kan Naira 1,400. Sai dai a wannan makon Nairar ta sake samun tagomashi inda aka sayar dalar Amurka guda kan kasa da naira dubu 1,300.Ko me ya janyo rashin tsayuwar karfin Nairar, duk da irin matakan da bankin Najeriya ya ɗauka domin ba ta kariya? Tambayar kenan da muka yi Dr Ƙasim Kurfi, masanin tattalin arziƙi a Najeriyar.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
Bayan yin bazata wajen farfaɗowa daga faɗuwar da yayi a watannin baya, kuɗin Najeriya ya fuskanci koma baya musamman a makon jiya, inda a kasuwar canjin bayan fage aka sayar da dala guda kan Naira 1,400. Sai dai a wannan makon Nairar ta sake samun tagomashi inda aka sayar dalar Amurka guda kan kasa da naira dubu 1,300.Ko me ya janyo rashin tsayuwar karfin Nairar, duk da irin matakan da bankin Najeriya ya ɗauka domin ba ta kariya? Tambayar kenan da muka yi Dr Ƙasim Kurfi, masanin tattalin arziƙi a Najeriyar.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirar da muka yi da shi
Ƙasashen duniya da kuma ƙungiyoyi kaƙƙin aikin jarida da kuma ‘yancin bayyan ra'ayi, sun yi tir a game da matakin rufe wasu kafafen yaɗa labarai da gwamnatin mulkin sojin Burkina Faso ta dauka. Baya ga kafafen yada labaran Faransa ciki har da RFI da kuma France24, matakin rufe kafafen yaɗa labaran ya shafi na Amurka, Birtaniya Faransa da dai sauransu domin kawai wallafa rahoton kungiyar HRW da ke zargin dakarun gwamnati da yi wa fararen hula kisan gilla.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkeen shirin.
Wasu gwamnonin arewacin Najeriya 10 da ke fuskantar matsalolin tsaro, sun kammala taron da suka je Amurka kan matsalar da kuma hanyoyin samar da zaman lafiya. Gwamnonin sun ce sun samu bayanan sirrin tsaron jihohinsu a Amurkar fiye da yadda suke samu a Najariya.Ahmad Abba ya tattaunawa da gwamnan jihar Katsina Mallam Dikko Ummaru Radda, wanda ya fara da yi masa bayani kan nasarar taron.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Shirin Kasuwa A Kai Miki Dole a wannan makon ya maida hankali ne kan batun korafin ‘yan Najeriya ke yi game da rashin ganin sauyi a farashin kayan amfanin yau da kullum, bayan karyewar farashin ƙudaden ƙetare masamman dalar Amurka da sanadin tashin ta ne ya haddasa mummunan tashin farashin kayayyaki a kasar, wanda har hukumar ƙididdiga ta ƙasar ta ce lamaarin ya yi muni. Ko da ya ke a wasu manyan biranen Najeriya irinsu Legas da Abuja, an fara ganin sauƙi a wasu kayayyakin abinci irinsu shinkafa da man girki da dai sauransu.Ku latsala alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Ahmed Abba........
Daga cikin muhimman batutuwan da shirin ya waiwaya a wannan makon akwai matakin Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar na kawo karshen yarjejeniyar tsaro da ke tsakanin kasar da Amurka. A Najeriya kuwa hukumar kare hakkin dan Adam ta kasar ce ta kawo karshen binciken da take gudanarwa kan zargin da ake yi wa rundunar sojin kasar na tilasta wa mata akalla dubu 10 zubar da juna biyun da suka samu a bisa tilas daga mayakan Boko haram
Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken ya sake komawa a Yankin Gabas ta Tsakiya a ci gaba da kokarin da kasashen duniya ke yi don samar da tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas. Daga farkon wannan rikici wanda ya barke a ranar 7 ga watan Oktoban bara zuwa yanzu, sau da dama Amurka na cewa tana yunkuri domin samar da tsagaita wuta a wannan yaki da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane kusan dubu 35 da kuma raba sama da milyan biyu da gidajensu. Farfesa Tukur Abdulkadir malami a jami'ar jimi'ar jihar Kaduna, na ganin cewa, da dagaske Amurka ke yi, da tuni an kawo karshen wannan yaki.Ku latsa alamar sauti don jin zantawarsa da Abdoulkarim Ibrahim Shikal.......
Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar ta sanar da kawo karshen yarjejeniyar tsaro da ke tsakanin kasar da Amurka, tare da zargin cewa dakarun Amurka wadanda adadinsu ya zarta dubu daya na zaune a kasar ne ba a kan ka'ida ba. Sanarwar ta zo ne kwana guda bayan da wata babbar tawagar Amurka ta kamma ziyarar da ta kai Nijar ta tsawon kwanaki uku. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Farfesa Dicko Abdourahmane, masani tsaro kuma malami a jami'ar Damagaram Zinder, wanda da farko ya fara yin bayani a game da dalilan da suka sa mahukuntan Nijar suka dauki wannan mataki.Ku latsa alamar sauti don jin zantawarsu.......
Gwamnatin Najeriya ta fara kai samame zuwa kasuwar musayar kudaden waje na bayan fage, yayin farashin dalar Amurka ke ci gaba da turmushe darajar kudin kasar. Wannan na zuwa ne, yayin da al'ummar kasar ke ci gaba da kokawa bisa tsadar rayuwa da ke neman jefa su cikin mummunan yanayi, musamman talakawa.A shekarar bara ne, shugaban kasar, Bola Ahmed Tinubu ya sanar da najye tallafin man fetur, a lokacin da yake gabatar da jawabi a taron rantsar da shi.Wannan sanarwar ta shugaba Tinubu ta haifar da cece-kuce, musamman daga masana tattalin arziki da ke hasashen illar da hakan zai haifar ga tattalin arzikin kasar.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin, tare da Nasiru sani.
Rikicin siyasa ya barke a Senegal sakamakon dage zaben kasar da shugaba Macky Sall ya yi a karshen mako. Matakin ya haifar da zanga zanga da kuma arangama da 'yan sanda, yayin da kungiyoyi da manyan kasashen duniya irin su ECOWAS da AU da EU da kuma kasashen Faransa da Amurka suka bukaci daukar matakin gudanar da zaben kamar yadda dokar kasa ta tanada. Dangane da wannan rudanin siyasa da ya mamaye kasar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Moussa Tchangari na kungiyar Alternative a Nijar
Darajar kudin Najeriya na naira na ci gaba da durkushewa a hada hadar kudade ta duniya, abin da ya kai ga yanzu haka ana sayar da dalar Amurka guda a kan naira 1,500. Tuni wannan matsalar ta haifar da tsadar kayayyakin masarufi a tsakanin al'umma, yayin da kungiyar masu masana'antu ke barazanar kara farashin kayan da suke sarrafawa.
Shirin 'Ra'ayoyin Masu Sauraro' na wannan rana ya bayar da damar tattaunawa akan sanar da masu masa'antu suka fitar a Najeirya, inda suka yi gargadi a game da yiwuwar samun hauhawar farashin kaya sakamakon yadda kudin kasar Naira ke ci gaba da rasa daraja kasuwa canji. Matsalar cigaba da faduwar darajar Nairar na zuwa ne duk ikirarin kokarin da gwamnati ke yi wajen kawo karshenta, inda a baya bayan nan, babban bankin Najeriya ya sanar da ware biliyoyin dalar Amurka don ceto kudin kasar daga durkushewar da yayi.
Sakataren harkokin wajen Amurka, Antony Blinken na ci gaba da ziyarar wasu kasashen Afirka da suka hada da Cape Verde da Cote d'Ivoire da Najeriya da kuma Angola. Da yammacin ranar Talata Blinken ya gana da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu dangane da bukatar hadin kan kasashen biyu.Dangane da wannan ziyarar da kuma tasirinta, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abdulhakeem Garba Funtua na Babbar kwalejin Fasaha ta Kaduna.
Na'ima Idris Usman, cikakkiyar Likita ce da ke jihar Kanon Najeriya, ta yi karatun a tsakanin Najeriys da China. Ta bamu labarin rayuwarta daga kuruciya zuwa girmanta, da ma yadda aka yi ta fara ilimantar da mata ta kafafen sada zumunta game da lafiyar jikinsu duk da cewa furta kalmomin da ke da alaka da al'aura abu ne mai cike da kalubalen a kasar Hausa. Da kuma yadda karshe ta buge da zuwa shirin horar da shugabanci ga matasan Afirka a Amurka da a turance ake kira da Mandela Washington Fellowship da aka fi sani da Young African Leaders Initiative (YALI) na shekarar 2022. --- This episode is sponsored by · Anchor: The easiest way to make a podcast. https://anchor.fm/app --- Send in a voice message: https://anchor.fm/usmankabarahausa/message Support this podcast: https://anchor.fm/usmankabarahausa/support
Usman Umar da aka fi sani da SojaBoy mawaki ne, dan wasan kwaikwayon zahirin rayuwa da ya fito a tauraron wani shirin wasan talbijin a Amurka mai suna 90DayFiance wanda ake bibiyar saurayi da budurwa don ganin yadda alakarsu ta soyayya ke tafiya. --- This episode is sponsored by · Anchor: The easiest way to make a podcast. https://anchor.fm/app --- Send in a voice message: https://anchor.fm/madubinkabara/message Support this podcast: https://anchor.fm/madubinkabara/support