Madubin Kabara

Follow Madubin Kabara
Share on
Copy link to clipboard

Saurari yadda ni dan jarida Usman Kabara nake tattaunawa da kwararrun 'yan Afirka don jin gwagwarmayar rayuwarsu a gida da kasashen waje. Support this podcast: https://anchor.fm/madubinkabara/support

Usman Kabara


    • Dec 22, 2025 LATEST EPISODE
    • weekdays NEW EPISODES
    • 40m AVG DURATION
    • 71 EPISODES


    Search for episodes from Madubin Kabara with a specific topic:

    Latest episodes from Madubin Kabara

    Solomon Dalung | MUK Na 39

    Play Episode Listen Later Dec 22, 2025 31:30


    Na sami zama tare da Lauya Dan Gwagwarmaya Barrister Solomon Dalung, tsohon Ministan Matasa Da Wasanni a lokacin mulkin Marigayi Shugaba Muhammadu Buhari. Inda na tattauna da shi don kallon rayuwarsa a cikin shirin Madubin Usman Kabara Podcast domin daukar darasi ga ‘yan baya.

    Usman SojaBoy | MUK Na 38

    Play Episode Listen Later Dec 22, 2025 40:24


    Na ziyarci Usman Umar (SojaBoy), domin yin hira da shi ido da ido a kokarina na jin dalilan salon wakokinsa da mafiya yawan mutane musamman 'yan Arewacin Najeriya, ba su yarda da salon nasa ba, suna ma kallon abin a matsayin rashin tarbiyya da rushe al'ada da addini.

    usman sojaboy
    Nazir Hausawa (Ziriums) | MUK Na 37

    Play Episode Listen Later Dec 22, 2025 59:34


    Nazir Ahmed Hausawa (Ziriums), yana daya daga cikin ‘yan masana'antar finafinan Kannywood, Makadin Fiyano, Mawakin gambarar Hausa HipHop, Tsohon malamin koyar da kida, Tsohon ma'aikacin BBC World Service Trust da VOA Hausa, Masanin harkokin gidajen alfama na Amurka. A cikin hirarsa da Madubin Usman Kabara a Amurka, ya bayyana min darussan da ya koya a zamansa na shekaru a Amurka.

    nazir amurka hausawa
    Nafisat Abdullahi | MUK Na 36

    Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 88:02


    Na sami yin hira da shahararriyar Jarumar Fina-finan Hausa Nafisat Abdullahi a birnin Washington DC da ke Amurka, don sanin asalinta da kuma yadda take tafiyar da rayuwarta.

    Barau I. Jibrin | MUK Na 35

    Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 55:56


    Na yi hira da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa ta Najeriya, Mai Girma Sanata Barau I. Jibrin (Maliya) game da rayuwarsa da kuma gudunmawarsa a siyasance, musamman ga 'yan Arewacin Najeriya.

    najeriya
    Kamaluddeen Kabir | MUK Na 34

    Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 57:40


    Kamaluddeen Kabir, dan asalin jigar Katsina ne mai digirin digirgir wanda yayi karatunsa a tsakanin Najeriya da Birtaniya sannan kuma Malami ne yanzu haka a jami'ar Umaru Musa 'YarAdua da ke jihar ta Katsina.

    katsina najeriya malami birtaniya
    Aminu Waziri Tambuwal | MUK Na 33

    Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 29:02


    Mun sami tattaunawa Aminu Waziri Tambuwal gwamnan jihar Sokoto, kuma shugaban tawagar yakin neman zaben Alhaji Atiku Abubakar a matsayin shugaban Najeriya a 2023 da ke tafe. Inda ya bamu labarin kuruciyarsa har zuwa girma da shiga fagen siyasa. Ba mu bar shi ba sai da ya fada mana dalilinsa na janye wa daga takarar shugabancin Najeriya don mara wa Atikun a karkashin jam'iyyar PDP.

    Na'ima Idris Usman | MUK Na 32

    Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 14:14


    Na'ima Idris Usman, cikakkiyar Likita ce da ke jihar Kanon Najeriya, ta yi karatun a tsakanin Najeriys da China. Ta bamu labarin rayuwarta daga kuruciya zuwa girmanta, da ma yadda aka yi ta fara ilimantar da mata ta kafafen sada zumunta game da lafiyar jikinsu duk da cewa furta kalmomin da ke da alaka da al'aura abu ne mai cike da kalubalen a kasar Hausa. Da kuma yadda karshe ta buge da zuwa shirin horar da shugabanci ga matasan Afirka a Amurka da a turance ake kira da Mandela Washington Fellowship da aka fi sani da Young African Leaders Initiative (YALI) na shekarar 2022.

    china usman hausa mandela washington fellowship afirka amurka young african leaders initiative yali
    Usman Umar SojaBoy | MUK Na 31

    Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 35:52


    Usman Umar da aka fi sani da Soja Boy mawaki ne, dan wasan kwaikwayon zahirin rayuwa da ya fito a tauraron wani shirin wasan talbijin a Amurka mai suna 90DayFiance wanda ake bibiyar saurayi da budurwa don ganin yadda alakarsu ta soyayya ke tafiya.

    Aisha Hassan | MUK Na 30

    Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 30:57


    Aisha Hassan matashiya ce 'yar asalin jihar Neja a Najeriya da ta girma a Ingila, sannan ta yi karatu mai zurfi a fannin hada-hadar kasuwanci. Bugu da kari ba a barta a baya ba wajen shiga fagen kafafen sadarwar zamani inda take koyar da salon sa sutura da daurin dan-kwali a shafukanta na yanar gizo.

    neja najeriya ingila
    Halima Ali Shuwa | MUK Na 29

    Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 71:52


    An karrama Halima Ali Shuwa da lambar yabon gama digirin digirgir a matsayin dalibar da ta yi wa sa'o'inta fintinkau a fanni binciken sojojin garkuwar jikin bil'adama. Bugu da kari kuma sai ga wani babban kamfanin hada magunguna a duniya ya bata aiki sakamakon fahimtar amfanin abin da ta kware a fannin binciken kwayar halitta.

    Adamu Garba II | MUK Na 28

    Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 30:26


    Adamu Garba II matashi ne mai kwarin gwiwa sannan wanda ya ke dan kasuwar da yayi iliminsa a tsakanin Najeriya har zuwa Amurka. Yana daga cikin 'yan takarar Shugaban Kasar Najeriya a shekarar 2023 mafi karancin shekaru a tsakanin masu neman wannan kujera a kasar da ta fi kowa ce kasar Afirka yawan al'umma da kuma karfin arzikin man fetur. Shine kuma wanda 'yan uwa da abokan arziki suka tara wa sama da naira miliyan 80 don yin takara a jam'iyyar APC amma kwatsam sai ya canja sheka zuwa YPP.

    shine yana apc garba adamu ypp najeriya afirka amurka
    Mua'wiya Sa'idu Abdullahi | MUK NA 27

    Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 24:19


    Mu'awiya Said Abdullahi, ya yi karatu ne a fannin zanen gidaje da kuma tsara birane. An haifeshi ne a garin Kaduna, sannan iyayensa Lauyoyi ne. Ya fara digirinsa ne daga jami'ar Ahmadu Bello ta Zaria, ya kuma kammala a daya daga jami'o'in kasar Malaysia. Yayi digirinsa na biyu da na uku a Korea ta Kudu, inda yanzu haka ya ke aiki a matsayin shugaban bangaren kula da bangaren tsara biranen kasashen waje a wani babban kamfani a kasar ta Koriya ta Kudu mai suna WithWorks da ke birnin Seoul.

    Ibrahim Sherif | MUK Na 26

    Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 36:47


    Ibrahim Sherif bakano ne dan Najeriya da ya bar gida tun yana dan saurayi zuwa Birtaniya domin aikin sa kai. Inda daga baya ya nausa Afirka ta Kudu inda ya cika burinsa na zama matukin jirgin sama, har ma ya buge da tsere keke a can.

    sherif inda kudu najeriya afirka birtaniya
    Nura Abubakar | MUK Na 25

    Play Episode Listen Later Dec 20, 2025 29:43


    Dalibi ne da ya ke digirin digirgir a fannin Turanci da fasahar hotunan finafinan majigi. Matashin ya bayyana yadda jin wani shiri a gidan radiyon Muryar Amurka na VOA ya ba shi kaimin neman zuwa karatu a Amurka, har ya buge da koyar da harshen Hausa tun a digirinsa na biyu a wata jami'a ta Amurka.

    Marzuq Ungogo | MUK Na 24

    Play Episode Listen Later Dec 19, 2025 38:22


    Muhammad Marzuq Abubakar Ungogo wani hazikin matashin likitan dabbobi ne da yake digirin-digirgir a birtaniya, tare da yin binciken a fanni kwayoyin cututtukan dabbobin da kuma gano dalilan da ke hana wasu magungunan dabbobin aiki da ya kamata su yi. Ya bayyana mana tarihin rayuwarsa da ma yadda aka yi yayi digiri na biyu a Turai da ma ci gaba da digirinsa na uku. Ya tabo batun yadda yake ganin noma da kiwo a kasashe kamar Najeriya.

    turai najeriya
    Iman Al-Hassan | MUK Na 23

    Play Episode Listen Later Dec 19, 2025 22:55


    Karatu ne ya kai iyayen Iman Yusuf Al-Hassan zuwa Amurka, wanda su 'yan asalin jihohin Kano da Jigawa ne a Arewacin Najeriya, amma kuma kaddarar zama ta kama su har suka hayayyafa. Iman ta fada min yadda take da burin zaman Najeriya duk kuwa da cewa a Amurka aka haifeta ta girma.

    iman kano jigawa najeriya amurka
    Hadiza Aliyu Gabon | MUK Na 21

    Play Episode Listen Later Dec 11, 2025 16:01


    Hadiza Aliyu da aka fi sani da Gabon, na daya daga cikin fitattun taurarin fina-finan Hausa mafi shahara. Ta shiga Najeriya a lokacin da bata jin Hausa, amma kuma tana son zama tauraruwar fina-finan Hausa na Kannywood. Yanzu kuma sai gashi mun da cewa tana yawan tafiye-tafiye zuwa kasashen duniya, ciki har da Amurka inda muka yi wannan hirar da ita.

    gabon hausa najeriya amurka yanzu
    Maimuna Sulaiman Bichi | MUK Na 21

    Play Episode Listen Later Dec 10, 2025 40:51


    Maimuna Sulaiman Bichi da aka fi sani da ‘yar Bichi ko Lolo's Kitchen ‘yar asalin Najeriya ce ta suka dawo Amurka da zama tun tana shekaru 15 da haihuwa. Ta kuduri aniyar bude gidan abincin da zai kware a girke-girke musamman ma irin na gargajiyar Hausawa.

    kitchen lolo sulaiman najeriya amurka hausawa
    Binta Aliyu Zurmi | MUK Na 20

    Play Episode Listen Later Dec 10, 2025 47:54


    Binta Aliyu Zurmi da aka fi sani da Elbynt, ‘yar jarida ce daga Najeriya mazauniyar kasar Jamus kuma ma'aikaciya a daya daga fitattun gidajen radiyon Hausa da ke kasashen waje. Ku biyo mu don kallo ko sauraron tattaunawar da muka yi da ita game da tarihin rayuwarta a gida da kasahen waje.

    Mohammed Ladan | MUK Na 19

    Play Episode Listen Later Dec 10, 2025 33:46


    Dakta Mohammed Ladan dai an fi saninsa da suna Dakta Ladan, sakamakon wani fitaccen shirin lafiya na gidan radiyon sashen Hausa na Muryar Amurka. Amma a likitance shi masanin kimiyyar hada magunguna ne wato ‘phamacist'. Dan asalin jihar Neja ne da ke Arewacin Najeriya, sannan a yanzu mazaunin Amurka fiye da shekara 40 tun bayan zuwansa.

    Bello Sisqo | MUK Na 18

    Play Episode Listen Later Dec 10, 2025 40:00


    Bello haifaffen birnin Maiduguri ne amma girman Kano a tarayyar Najeriya, wanda ya ci karo da kalubalen rayuwa a dalilin basirarsa ta waka wanda har korarsa daga gidansu aka yi. Amma maimakon ya saduda, sai ma ya tsalleke kasar zuwa Jamus a tarayyar Turai inda a yanzu haka yake zaune a matsayin mawaki kuma mai koyar da rawai.

    Aisha Rimi | MUK Na 17

    Play Episode Listen Later Dec 10, 2025 18:25


    Aisha Rimi ‘yar kasar Birtaniya ce wacce iyaiyenta ‘yan asalin Arewacin Najeriya ne. Duk da fadawa hatsarin da ya yi sanadiyyar rabata da kafarta daya, to amma hakan bai canza komai a samun nasararta a rayuwa ba.

    duk rimi birtaniya
    Yusuf Al-Hassan | MUK Na 16

    Play Episode Listen Later Dec 9, 2025 61:57


    Farfesa Yusuf Al-Hassan dan asalin cikin birnin Kano ne a Najeriya da ya kwashe shekaru yana koyo da koyarwa a tsakanin Najeriya da Amurka game da ilimin fasahar sana'o'in hannu inda har ya taba zama zakaran gasar malaman koyar da sana'o'i ta Amurka. Malamin ya kuduri aniyarsa ta yadda zai taimaki Najeriya ta hanyar kai Kanawa 100 zuwa Amurka don koyon ilimin sana'a.Yusuf Al-Hassan | MUK Na16

    kano kanawa najeriya amurka
    Aliyu Mustapha Lawal | MUK Na 15

    Play Episode Listen Later Dec 9, 2025 26:17


    Aliyu Mustapha Lawal, ya fito daga jihar Kano ne a Najeriya, wanda ya shiga gasar duniyar kasida ko waken-baka da larabci mai taken 'Gasar Yariman Sha'iran Larabawa' da aka yi a Birnin Abu Dhabi da ke hadaddiyar daular larabawa. Ya tattauna damu game da rayuwarsa tsakanin Najeriya da Misira da kuma yadda aka yi ya sami shiga gasar larabawa a matsayinsa na bahaushe.

    Abba Zubair | MUK Na 14

    Play Episode Listen Later Dec 8, 2025 41:16


    Farfesa Abba Zubair Chedi na asibitin Mayo Clinic da ke Amurka, dan asalin jihar Kano ne a Najeriya da ya yi kaurin suna a Amurka, musamman a lokacin da ya shiga binciken yadda za a yi amfani da kimiyyar kwayar halitta ta 'stem cell' wajen kirkirar sassan jikin bil'adama, kamar zuciya da huhu don dasa wa mutanen da sassan jikin ya lalace ba tare da jiran sai wani ya mutum a cire a saka wa wani ba.

    Hauwa Mustapha Babura | MUK Na 13

    Play Episode Listen Later Dec 8, 2025 30:54


    Na yi hira da Hauwa Mustapha Babura, 'yar asalin garin Babura da ke jihar Jigawa ta Arewacin Najeriya. Ta bani labarin rayuwarta tun bayan shigarta Amurka da kuruciya, inda a yanzu haka 'yar kasa ce a can kamar yadda take a kasarta ta asali. Da kuma yadda aka yi ta zama kwararriyar malamar makaranta a bangaren ilimin kananan yara da kuma yadda ake renon kwakwalwarsu.

    Saratitin Baba | MUK Na 12

    Play Episode Listen Later Dec 8, 2025 30:00


    Na yi hira da Saratu Garba Abdullahi wacce aka fi sani da Saratitin Baba, ‘yar jihar Jigawa ce da ke Arewacin Najeriya, shiga cikin hirar don jin yadda ta sha alwashin cika burin mahaifinta.

    Murtala Mai | Madubin Usman Kabara #11

    Play Episode Listen Later Nov 20, 2025 56:11


    Dr. Murtala likitan yara ne dan asalin jihar Adamawar Najeriya da ya rikide ya zama kwararren masanin lafiyar al'umma musamman mata da yara, wanda a yanzu haka ma'aikaci ne a wata kungiya mai zaman kanta da ta ke tallafawa harkokin lafiyar iyali a duniya ciki har da kasashen Afirka mai suna Pathfinder International da ke kasar Amurka.Murtala Mai | Madubin Usman Kabara #11

    usman afirka amurka kabara
    Fadji Maina | Madubin Usman Kabara #10

    Play Episode Listen Later Nov 19, 2025 45:45


    ‘Yar Nijar kuma masaniyar kimiyyar ruwa da doron kasa da ke aiki a hukumar sama-jannatin Amurka ta NASA. Dr. Fadji Maina tana cikin wacce mujallar tereren arziki ta Forbes ta wallafa sunanta a cikin matasan duniya guda 30 ‘yan kasa da shekara 30 da suka sami nasara a rayuwa. Yanzu haka ma'aikaciya ce a hukumar sama jannatin Amurka ta NASA da ke aiki bisa kwarewar ta a fannin ruwa da kimiyyar doron kasa.

    forbes nasa usman maina amurka fadji yanzu kabara
    Sarki Abba Abdulkadir | Madubin Usman Kabara #9

    Play Episode Listen Later Nov 18, 2025 61:07


    A shekarar 1984 a Najeriya an sami wani saurayi dan jihar Kano da ya fi kowane dalibi a Najeriya cin makin jarrabawar gama sakandaren kasashen Afirka ta WAEC a takaice. Yanzu haka dai wannan dalibin mai suna Farfesa Sarki Abba Abdulkadir farfesa ne a bangaren haddasuwar cututtuka a Jami'ar Northwestern University da ke Chicago a Amurka.

    Munira Sulaiman Tanimu | Madubin Usman Kabara #8

    Play Episode Listen Later Nov 17, 2025 45:00


    Munira Sulaiman Tanimu na daya daga cikin zaratan matasan mata a Arewacin Najeriya da ta ciri tuta a bangaren ilimi, sana'o'i, siyasa, tallafawa ilimin ‘ya'ya mata ‘yan talla. Mun tattauna da ita don jin tarihin rayuwarta da kalubalen da ta fuskanta.

    Adamu Hamza Bamalli | Madubin Usman Kabara #7

    Play Episode Listen Later Nov 16, 2025 120:07


    Adamu Hamza Bamalli ya sha gwagwarmaya a Najeriya da Amurka kama daga zama direban babbar mota zuwa rikidewa ya zama kwararren Injiniya a jihar Maryland ta Amurka.

    maryland usman adamu najeriya amurka kabara
    Imrana Alhaji Buba | Madubin Usman Kabara #6

    Play Episode Listen Later Nov 15, 2025 45:01


    Imrana matashi ne danye shataf daga jihar Yobe, wanda har yanzu bai shekara talatin da haihuwa ba, sannan ba dan masu kudi ko mulki ba ne, amma ya sami nasararorin rayuwar da har Sarauniyar Ingila sai da ta karrama shi saboda wasu dalilan da matashin ya bayyana a wannan tattaunawa da mu ka yi dashi game da tarihin rayuwarsa.

    Halima Djimrao | Madubin Usman Kabara #5

    Play Episode Listen Later Nov 14, 2025 60:55


    Halima Djimrao tsohuwar ma'aikaciyar sashen Hausa na Muryar Amurka, ta yi doguwar hira game da rayuwarta tun daga haihuwa har zuwa girmanta da karatunta na addini dana zamani, da ma yadda aka yi ta sami aiki a Muryar Amurka da ke birnin Washington DC da kuma dalilin yin ritayarta a lokacin da duniyar aikin radiyo ke yayinta.

    Abubakar Malami - Madubin Usman Kabara #4

    Play Episode Listen Later Nov 13, 2025 17:26


    Lauya Abubakar Malami (SAN) ya fada mana tarihin rayuwarsa tun daga kuriciya har zuwa girmansa da kuma gwagwarmayarsa ta zama Lauya da kuma mai shari'a a matsayinsa na dan gado, da ma yadda ya sake rikide zuwa Lauya mai zaman kansa har ya sami lambar girma ta Senior Advocate of Nigeria a turance.

    Sabo Tanimu | Madubin Usman Kabara #3

    Play Episode Listen Later Nov 12, 2025 29:40


    Na ziyarci Dr. Sabo Tanimu a jihar Wisconsin ta Amurka. Yana daya daga cikin kwararrun likitocin kayan cikin bil'adama a kasar inda yake shugabantar bangaren cutar dajin da ta shafi kayan ciki. Dan asalin Najeriya ne daga jihar Benue a tsakiyar Arewacin Najeriya. Shin yaya aka yi Likita Sabo ya fara daga Najeriya har ya tsinci kansa a Amurka inda ya shafe shekaru da dama yana aikin Likita a can.

    Ali Nuhu | Madubin Usman Kabara #2

    Play Episode Listen Later Nov 11, 2025 12:09


    Na yi hira da Ali Nuhu Mohammed jarumin fina-finan Hausa da Turanci na Najeriya a lokacin da ya ziyarci birnin Washington DC da ke Amurka,, in da na tambaye shi darussan da ya koya a cikin shekaru 20 da ya kwashe yana harkar shirya finafinai.

    washington dc usman hausa najeriya amurka kabara
    Usman Kabara

    Play Episode Listen Later Aug 6, 2024 2:49


    Shirin da zai dinga yin tsokaci a kan yadda al'amuran yau da kullum da suka shafi rayuwarmu suka samo asali.

    KAMALUDDEEN KABIR: Yadda ya sami karatu a Birtaniya

    Play Episode Listen Later Feb 17, 2023 58:20


    Dakta Kamaluddeen Kabir, dan asalin jigar Katsina ne mai digirin digirgir wanda yayi karatunsa a tsakanin Najeriya da Birtaniya sannan kuma Malami ne yanzu haka a jami'ar Umaru Musa 'YarAdua da ke jihar ta Katsina. --- This episode is sponsored by · Anchor: The easiest way to make a podcast. https://anchor.fm/app --- Send in a voice message: https://anchor.fm/usmankabara/message

    sami yadda katsina najeriya malami birtaniya
    NA'IMA IDRIS: Ta shiga sahun manyan gobe a Afirka

    Play Episode Listen Later Aug 1, 2022 14:53


    Na'ima Idris Usman, cikakkiyar Likita ce da ke jihar Kanon Najeriya, ta yi karatun a tsakanin Najeriys da China. Ta bamu labarin rayuwarta daga kuruciya zuwa girmanta, da ma yadda aka yi ta fara ilimantar da mata ta kafafen sada zumunta game da lafiyar jikinsu duk da cewa furta kalmomin da ke da alaka da al'aura abu ne mai cike da kalubalen a kasar Hausa. Da kuma yadda karshe ta buge da zuwa shirin horar da shugabanci ga matasan Afirka a Amurka da a turance ake kira da Mandela Washington Fellowship da aka fi sani da Young African Leaders Initiative (YALI) na shekarar 2022. --- This episode is sponsored by · Anchor: The easiest way to make a podcast. https://anchor.fm/app --- Send in a voice message: https://anchor.fm/usmankabarahausa/message Support this podcast: https://anchor.fm/usmankabarahausa/support

    china hausa gobe shiga mandela washington fellowship afirka amurka young african leaders initiative yali
    AISHA HASSAN: 'Yar Najeriya da Birtaniya gwanar daurin dan-kwali

    Play Episode Listen Later Aug 1, 2022 31:36


    Aisha Hassan matashiya ce 'yar asalin jihar Neja a Najeriya da ta girma a Ingila, sannan ta yi karatu mai zurfi a fannin hada-hadar kasuwanci. Bugu da kari ba a barta a baya ba wajen shiga fagen kafafen sadarwar zamani inda take koyar da salon sa sutura da daurin dan-kwali a shafukanta na yanar gizo. AISHA HASSAN: 'Yar Najeriya da Birtaniya gwanar daurin dan-kwali --- This episode is sponsored by · Anchor: The easiest way to make a podcast. https://anchor.fm/app --- Send in a voice message: https://anchor.fm/usmankabarahausa/message Support this podcast: https://anchor.fm/usmankabarahausa/support

    neja kwali najeriya birtaniya ingila
    SOJABOY: Bahaushen da Amurkawa suka fi sani

    Play Episode Listen Later Jul 25, 2022 36:37


    Usman Umar da aka fi sani da SojaBoy mawaki ne, dan wasan kwaikwayon zahirin rayuwa da ya fito a tauraron wani shirin wasan talbijin a Amurka mai suna 90DayFiance wanda ake bibiyar saurayi da budurwa don ganin yadda alakarsu ta soyayya ke tafiya. --- This episode is sponsored by · Anchor: The easiest way to make a podcast. https://anchor.fm/app --- Send in a voice message: https://anchor.fm/madubinkabara/message Support this podcast: https://anchor.fm/madubinkabara/support

    suka 90dayfiance sani sojaboy amurka
    Yar Najeriya ta sami lambar yabo a Birtaniya

    Play Episode Listen Later Jul 1, 2022 71:52


    HALIMA ALI SHUWA: An karrama ta da lambar yabon gama digirin digirgir a matsayin dalibar da ta yi wa sa'o'inta fintinkau a fanni binciken sojojin garkuwar jikin bil'adama. Bugu da kari kuma sai ga wani babban kamfanin hada magunguna a duniya ya bata aiki sakamakon fahimtar amfanin abin da ta kware a fannin binciken kwayar halitta. --- Send in a voice message: https://anchor.fm/madubinkabara/message Support this podcast: https://anchor.fm/madubinkabara/support

    sami yabo najeriya birtaniya
    MUAWIYA SAIDU: Masanin tsara birane a Koriya ta Kudu

    Play Episode Listen Later Mar 28, 2022 24:19


    Muawiya Saidu Abdullahi, ya yi karatu ne a fannin zanen gidaje da kuma tsara birane. An haifeshi ne a garin Kaduna, sannan iyayensa Lauyoyi ne. Ya fara digirinsa ne daga jami'ar Ahmadu Bello ta Zaria, ya kuma kammala a daya daga jami'o'in kasar Malaysia. Yayi digirinsa na biyu da na uku a Korea ta Kudu, inda yanzu haka ya ke aiki a matsayin shugaban bangaren kula da bangaren tsara biranen kasashen waje a wani babban kamfani a kasar ta Koriya ta Kudu mai suna WithWorks da ke birnin Seoul. --- Send in a voice message: https://anchor.fm/usmankabarashowhausa/message Support this podcast: https://anchor.fm/usmankabarashowhausa/support

    I SHARIF: Dan Najeriya matukin jirgi a Afirka ta Kudu

    Play Episode Listen Later Mar 5, 2022 36:47


    Kaftin Ibrahim Sharif bakano ne dan Najeriya da ya bar gida tun yana dan saurayi zuwa Birtaniya domin aikin sa kai. Inda daga baya ya nausa Afirka ta Kudu inda ya cika burinsa na zama matukin jirgin sama, har ma ya buge da tsere keke a can. --- Send in a voice message: https://anchor.fm/usmankabarashowhausa/message Support this podcast: https://anchor.fm/usmankabarashowhausa/support

    sharif inda kudu najeriya afirka birtaniya
    NURA ABUBAKAR: Koyar da Hausa ya kai shi Amurka

    Play Episode Listen Later Feb 17, 2022 29:43


    Nura Abubakar dalibi ne da yake digirin digirgir a fannin Turanci da fasahar hotunan finafinan majigi. Matashin ya bayyana yadda jin wani shiri a gidan radiyon Muryar Amurka na VOA ya ba shi kaimin neman zuwa karatu a Amurka, har ya buge da koyar da harshen Hausa tun a digirinsa na biyu a wata jami'a ta Amurka. --- Send in a voice message: https://anchor.fm/usmankabarahausa/message Support this podcast: https://anchor.fm/usmankabarahausa/support

    MARZUQ UNGOGO - Likitan Dabbobi

    Play Episode Listen Later Jan 16, 2022 38:22


    Marzuq Ungogo wani hazikin matashin likitan dabbobi ne da yake digirin-digirgir a birtaniya, tare da yin binciken a fanni kwayoyin cututtukan dabbobin da kuma gano dalilan da ke hana wasu magungunan dabbobin aiki da ya kamata su yi. Ya bayyana mana tarihin rayuwarsa da ma yadda aka yi yayi digiri na biyu a Turai da ma ci gaba da digirinsa na uku. Ya tabo batun yadda yake ganin noma da kiwo a kasashe kamar Najeriya. --- Send in a voice message: https://anchor.fm/usmankabarahausa/message Support this podcast: https://anchor.fm/usmankabarahausa/support

    turai najeriya
    IMAN AL-HASSAN - 'Yar Amurka mai son dandana rayuwar Najeriya

    Play Episode Listen Later Dec 31, 2021 22:54


    Karatu ne ya kawo iyayenta 'yan asalin jihohin Kano da Jigawa zuwa Amurka daga a Najeriya, amma kuma kaddarar zama ta kama su har suka hayayyafa. Iman ta fada min yadda take da burin zaman Najeriya duk kuwa da cewa a Amurka aka haifeta ta girma. --- Send in a voice message: https://anchor.fm/usmankabarahausa/message Support this podcast: https://anchor.fm/usmankabarahausa/support

    iman kano jigawa najeriya amurka
    HADIZA ALIYU GABON: Abinda ke kaita kasashen waje

    Play Episode Listen Later Nov 18, 2021 16:00


    Hadiza Aliyu da aka fi sani da Hadiza Gabon, na daya daga cikin fitattun taurarin fina-finan Hausa mafi shahara. Ta shiga Najeriya a lokacin da bata jin Hausa, amma kuma tana son zama tauraruwar fina-finan Hausa na Kannywood. Yanzu kuma sai gashi mun da cewa tana yawan tafiye-tafiye zuwa kasashen duniya, ciki har da Amurka inda muka yi wannan hirar da ita. --- Send in a voice message: https://anchor.fm/usmankabarashowhausa/message Support this podcast: https://anchor.fm/usmankabarashowhausa/support

    gabon hausa waje najeriya amurka yanzu
    MAIMUNA ‘YAR BICHI: Ta yi damarar kafa shagon abincin Najeriya a Amurka

    Play Episode Listen Later Aug 29, 2021 40:50


    Maimuna Sulaiman Bichi da aka fi sani da ‘yar Bichi ko Lolo's Kitchen ‘yar asalin Najeriya ce ta suka dawo Amurka da zama tun tana shekaru 15 da haihuwa. Ta kuduri aniyar bude gidan abincin da zai kware a girke-girke musamman ma irin na gargajiyar Hausawa. --- Send in a voice message: https://anchor.fm/madubinkabara/message Support this podcast: https://anchor.fm/madubinkabara/support

    kitchen lolo kafa najeriya amurka hausawa

    Claim Madubin Kabara

    In order to claim this podcast we'll send an email to with a verification link. Simply click the link and you will be able to edit tags, request a refresh, and other features to take control of your podcast page!

    Claim Cancel