POPULARITY
Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali ne kan al'adar nan ta dalilin aure, guda cikin al'adun Hausawa da aka shafe tsawon lokaci ana amfani da ita da nufin haɗin aure walau tsakanin ƴammata da Samari ko kuma Zawara. Kamar yadda kusan kowanne lamari ke tafiya da zamani itama al'adar ta juye, ta yadda ta koma cikakkiyar sana'a da wasu ɗaiɗaikun mutane ke da gogewa akanta, har ta kai ga ake buɗe ofisoshi don gudanar da ita.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.
Kamar yadda aka saba, shirin yakan yi dduba ne akan al'adun al'ummar Hausawa da sauran su, waɗanda suka gushe ko kuma ake ganin wanzuwan su a yanzu.Al'adar tashe dai na daga cikin al'adun da aka fara ganin yaɗuwarsu a ƙasar Hausa tun a ƙarni na 16, al'ada ce da ta ƙunshi wasannin barkwanci, waɗanda ake gudanar da su da zarar a kammala azumin goman farko na watan Ramadana. Sai dai wannan al'ada ta fara gushewa. Ko menene dalilin haka? Abin da shirin wannan makon zai yi nazari a kai kenan.
Shirin ya duba yadda Hausawa mazauna kasar Senegal kei cudanya da 'yan asalin kasar duk da cewa suna daraja al'adunsu da ke da matikar muhimmanci a gare su.
Shirin Al'adun mu na Gado a wannan makon ya mayar da hankali ne kan yadda Hausawa ke ƙoƙarin mancewa da al'adar amfani da kwarya, wacce ke cikin daɗaɗɗun kayan amfanin gida na Malam Bahaushe. To sai dai duk da irin tasirin Kwarya a cikin al'ummar ta Hausawa, sannu a hankalin wannan al'ada tana neman gushewa a tsakanin al'ummar ta Hausawa har ma da Fulani da suka rungumi al'adar daga baya. Masu harkar sayar da ƙore a yankin Arewacin Nigeria, na kokawa sosai kan rashin garawar sana'ar tasu sakamakon yadda Hausawa da Fulani suka rage amfani da Kwarya.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa........
Shirin 'Al'adunmu na Gado' na wannan makon tare da Abdoulaye Issa ya tattauna dangene da gushewar a'adar tatsuniya wadda ke zama hanyar da al'ummar Hausawa ke amfani da ita wajen ilmantarwa, fadakarwa da kuma tarbiyantar da yara ta hanyar shirya kagaggun labarai masu kunshe da darussa.
Shirin al'adunmu na Gado tare da Abdoulaye Issa kamar yadda ya saba a wannan makon ma ya leƙo wasu daga cikin masarautun Hausawa don jin tarihi da kuma tasirinsu ga al'umma. A wannan karon shirin ya yi duba kan tasirin al'adun gargajiya a matsayin jigon tafiyar da shugabanci bayan ficewar turawan Mulkin mallaka a Najeriya.Haka zalika za kuji hira ta musamman da sarkin Keffi a jihar Nassarawa wato Mai martaba Alhaji Shehu Usman Shindo Yamusa.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.....
Shirin al'adunmu na gado tare da Aboulaye Issa, ya mayar da hankali ne kan al'adar gaɗa da ke ƙoƙarin gushewa tsakanin al'ummar Hausawa duk da tasirinta a shekarun baya musamman tsakanin matasa.
Shirin Al'adun mu na Gado a wannan makon ci gaba ne game da jerin shirye-shiryen da muka faro kan zuwan Turawan mulkin mallaka zuwa ƙasar Hausa. Turawan sha mamakin abinda suka tarar, kasancewar sun samu al'ummar Hausawa da cikakkiyar wayewar addini, sarauta, sutura, karatu da rubutu da kuma wayewar kasuwanci da sauran harkoki na rayuwa. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare ta Abdoulaye Issa.......
Sana'ar Wanzanci da a baya ta shahara musamman yankin Arewacin Najeriya yanzu ta fara gushewa saboda yadda masu aski na zamani su fito su ka mamaye sana'ar tsakanin Hausawa.
Shirin Al'adun Gargajiya na wannan makon ya ziyarci masarautar Sarkin Hausan Turai Alhaji Surajo Jankado Labbo da ke kasar Faransa, inda Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da shi kan wasu batutuwa da suka shafi Hausawa. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa........
Daya daga cikin matsalolin da suka addabi nahiyar Turai a wannan lokaci, shine batun bakin haure, ganin yadda matasa daga nahiyar Afirka ke tafiya mai hadari cikin kwale kwale da zummar zuwa nahiyar, abinda ke kai ga rasa rayuka da dama. Dangane da wannan matsala da kuma matakan da magabata ke dauka wajen fadakar da al'umma illar irin wannan tafiya, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Sarkin Hausawa Turai Alhaji Sirajo Jankado a fadarsa da ke kasar Faransa, kuma ga yadda zantawar su ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tasu......
Daga cikin tambayoyin da za mu amsa a yau, akwai wadda ke neman sanin tarihin Hausawa ‘yan asalin kasar Mali. Danna alamar saurare don jin cikakken shirin tare da Micheal Kuduson.
Shirin ya duba bikin Hausa Kirista da aka saba gudanarwa a duk ranar 26 ga watan disambar kowace shekara sakamakon kirisimeti. Za mu ji yadda bikin ya samo asali a cikin bukukuwan al'adun Hausawa da ma yadda aka gudanar da shi.
Yadda al'umma a yankin Hausawa suke fadin sunayen yaransu na farko sabanin yadda aka sani a baya.
Shirin Al'adun mu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan makon ya yi duba ne kan sana'ar wanzanci, wacce ke cikin sana'oin gargajiya na Hausawa da ke cike da abubuwa na al'ajabi. Mafi yawancin wanzamai gadon sana'ar suke yi daga iyayensu, amma wani lokacin, ana samun wasu daga waje da suke sha'awar koyon sana'ar don su samu hanyar cin abici. Duk kuwa da yadda bincike ya nuna cewa sana'ar ba abar da mutum zai koya cikin sauki da sauri ba ce. Sakamakon yanda ake samun sauyin zamani, yanzu wanzamai sun fara fuskantar kalubale na rashin tabbas a sana'arsu saboda fara bacewar sana'arsu. Ku danna alamar sauti don sauraron cikakken shirin........
Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali ne kan bikin kidan Duma, guda cikin al'adun jihar Maradi da ke kokarin gushewa. A wani kokari na dakile gushewar al'adu, gwamnatin jamhuriyyar Nijar ta kaddamar da wani gangamin horar da matasa kidan Duma, salon kidan da ke da shahara a tsakanin garuruwan Hausawa.Akwai dai salo kala kala na kidin Duma da yanzu ke zama inda mata sun fi son gargajiya yayin bukukuwansu abin da ake kira Partyn kauyawa Tasi'u Bakwai ya mana filla filla ma'anar kidi irinsu adamulmula, yar sahabi da sauransu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin..............
Shirin ya yi nazari kan yadda ske yin watsi da al'adun Hausawa na iyayen da kakanni a yayin bikin aure a Najeriya.
Shirin 'Al'adunmu na Gado' tare da Abdoulaye Issa a wannan makon ya mayar da hankali ne kan yadda aka gudanar da bikin masarautar Hausawar Afrika a jahar Kano da ke tarayyar Najeriya, kuma a lokacin taron an gudanar da nade-nade da bama da akayi da zummar hada kan al'ummar Hausawa da ke kasashe daban daban. Toh domin jin yadda taron ya gudana sai ku latsa alamar sauti don jin cikakken shirin......
Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa ya mayar da hankali ne kan al'adun al'ummar yankin Kumasi da ke kasar Ghana, yankin da ke kunshe da tarin al'ummar Hausawa a kasar ta yammacin Afrika. A cikin shirin na wannan mako za kuma kuji yadda cefane ke wakana a tsari na al'adun Hausa wanda a wasu lokutan ke cin karo da matsalar al'mubazzaranci wato rashin tattali daga Mata a dai dai lokacin da ake fama da matsin rayuwa.Wadannan dama muhimman batutuwan da suka shafi al'adun Malam Bahaushe na kunshe a cikin wannan shiri.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shiri..........
Shirin 'Al'adunmu Na Gado' ya mayar da hankali ne a kan tanade-tanaden al'adun Bahaushe, wadanda akasarinsu suka rungumi addinin Musulunci a game da tamakekeniya a lokacin azumin watan Ramadan. Shirin ya leka kasar Togo, inda ya tattauna da Hausa da ke zaune a wannan kasa tare da wasu kabbilu a game da hakan.
Shirin "Al'adunmu na Gado" a wannan makon ya yi duba ne akan yadda wasan gargajiya na Tabastaka ke ta ka rawa wajen abinda ya shafi zaman lafiya a yankunan Damagaram da kuma Zindar.Haka nan kuma, shirin ya duba yadda al'ummar Hausawa suka rungumi abincin al'adar al'ummar kasar Ghana.Shirin bai tsaya nan ba sai da ya leka tarayyar Najeriya, inda ya kawo yadda aka gudanar da bikin nadin sabon Sarkin Kwantagora a jahar Niger da ke tsakiyar kasar.
A wannan makon shirin ya mayar da hankali ne kan taron da cibiyar bincike kan harsunan Najeriya, fassara da hikimomin al'umma ta Jami'ar Bayero da ke Kano a arewacin Najeriya ta shirya, domin tunawa da gudummawar wani Shehin Malami marigayi Farfesa Ibrahim Yaro Yahaya wajen bunkasa ilmin a yankin Hausawa.
Shirinmu na wanna makon ya yi dubi ne da yadda raayuwar mata take a fadodin sarakuna musamman a yanunan Hausawa. Shirin ya yi la'akari da yadda al'adun suke daga masarauta zuwa masarauta.
Shirin Al'adunmu na Gado na wannan makon tare da Abdoulaye Issa ya kai ziyara ne can fadar mai martaba Sarkin Machina da ke jihar Yobe ta Najeriya da kuma Masarautar Hausawa a garin Port-Novo na kasar Benin. Masarautar ta Machina ta yi bayani kan yadda take tattalin al'adun da al'ummarta ta gada tun fil azal. Kazalika shirin ya ziyarci garin Ajase na birnin Port-Novo da ke Jamhuriyar Benin, inda Hausawa suka shafe fiye da shekaru 150 a wannan yanki tare da kafa Masarautarsu.
Shirin al'adunmu na Gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali kan lalacewar tarbiyya a tsakanin al'umma matsalolin da ake dora alhakinsu kan kwaikwayon dabi'un ketare a kasashen Hausawa.
Shirin ya duba yadda zamani ya sauya tunanin al'ummar Hausawa da dama kan kyamar mahauta masu sana'ar sayar da nama da kuma auren 'ya'yansu.
Zamani ya taho da abubuwa da dama, kuma wannan shirin ya fito da bambancin yanayin zamantakewar al'ummar Hausawa a can baya da kuma na wannan zamanin.
Daruruwan al'ummar Hausawa ne suka gudanar da zanga-zanga a birane daban-daban na kasar Sudan, inda suke neman a yi musu adalci bayan barkewar rikicin kabilanci da ya yi sanadiyar kashe musu mutane da dama a yakin kogin Nilu. Akalla mutane 79 suka mutu, wasu 199 suka samu raunuka bayan barkewar rikicin tsakanin Hausawa da 'yan kabilar Barti Larabawa a ranar Litinin din makon jiya. Malam Umar Hamza Abdullaye na daga cikin wadanda suka halarci zanga-zangar kuma ya yi wa Bashir Ibrahim Idris karin bayani. Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu.
Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya dora kan shirin makon jiya da ya mayar da hankali kan tarihin masarautar Hausawan Lukusa, karkashin jagorancin mai martaba sarkin Hausawa kuma sarkin musulmin yankin Alhaji Abdu Nuhu.
Shirin Al'adunmu na Gado tare da Abdoulaye Issa ya yada zango a yankin Lokossa na Jamhuriyar Benin, inda wata takadama ta kuno kai a unguwar zongo dangane da wata masarauta karkashin shugabancin Nuhu Abdou .
Sutura ko kayan sawa, suna daga cikin abubuwan da suka bambanta tsakanin 'Yan adam da dabbobi. Kamar yadda aka sani, al'ummomi dabam dabam, na da irin nau'i ko kalan kayan da suka fi sawa. Da zarar ka ga mutum da irin wannan kaya, zaka fara tunanin cewa dan kabila ko kuma dan yanki kaza ne. A cikin shirin a'adun mu na gado daga nan Rfi ,Abdoulaye Issa ya duba halin da ake Mallam Bahaushe ke rayuwa a wannan zamani a cikin wannan shiri,kamra dai yada za a ji. Baya ga al'amarin sutura,Abdoulaye Issa ya jiyo ta bakin mai sana'ar kunun gyade a Jihar Bauchi dake Najeriya.
An gudanar da bikin nadin sababbin sarautu, a masarautar Hausawan Turai. Karin bayani cikin Taba Ka Lashe.
Shirin al'adunmu na gado ya mayar da hankali kan kokarin farfado da wakokin gargajiya tsakanin matasan Hausawa. Ayi saurare lafiya.
Shirin Ilimi Hasken Rayuwa na wannan makon ya tattauna ne game da sabuwar jaridar Tabarau wadda ake rubuta cikin ajami domin bunkasa yaduwar ilimi tsakanin al'ummar Hausawa musamman makaranta Al-Kur'ani mai girma.
Maimuna Sulaiman Bichi da aka fi sani da ‘yar Bichi ko Lolo's Kitchen ‘yar asalin Najeriya ce ta suka dawo Amurka da zama tun tana shekaru 15 da haihuwa. Ta kuduri aniyar bude gidan abincin da zai kware a girke-girke musamman ma irin na gargajiyar Hausawa. --- Send in a voice message: https://anchor.fm/madubinkabara/message Support this podcast: https://anchor.fm/madubinkabara/support
Ko kun san cewa akwai fadar Hauasawa har ma da sarkinsu a Turai? Shirin Taba Ka Lashe ya yi nazari kan batun wannan sarauta.
Shirin rayuwata na wannan makon tare da Zainab Ibrahim, ya tabo yadda dabi'ar rawa a matsayin sana'a ke gamuwa da kalubale tsakanin al'ummar Hausawa.
Shirin al'adunmu na gado tare da Mahaman Salissou Hamissou ya yi duba kan koma bayan da ake samu a cikin al'ummar musulmi musamman a lokacin Ramadan ta yadda masu galihu ke gaza taimakawa marasa karfi.
Sheikh Ja'afar Mahmoud Adam ya kawo wata magana da Hausawa ke yi. Ya ce "Sai dai a ce ƙaryar mutum ta ƙare ba dai gaskiya ba"
Shirin yayi nazari kan zamantakewar Fulani da Hausawa tun bayan fuskantar barazana ta asarar rayuka da dukiya a wasu jihohin kudu maso yammacin Najeriya.
Kalubalen da iyaye 'yan asalin kasashen nahiyar Afirka dama yaran da suka haifa a kasar Amirka suke fuskanta a yayin da aka ce yaran sun kai minzanin yin aure.
Shirin al'adu na wannan mako tare da Mahaman Salissou Hamissou ya dora kan na makon jiya game da yadda hukumomin Ilimi a Najeriya suka amince da shigar da Tatsuniyoyi cikin manhajar Ilimin kasar, dai dai lokacin da tatsuniyoyin ke kokarin gushewa tsakanin hausawa duk da kasancewar su wani bangare na al'adun Hausawa.
Shirin Al'adunmu na Gado a wannan makon tare da Mohamane Salissou Hamissou ya duba yadda Larabawa suka shafe tsawon lokaci suna fataucin bayi a kasar Hausa.
Shirin Al'adunmu na gado a wannan makon tare da Salissou Hamissou ya duba yadda Larabawa suka yi shafe tsawon lokaci suna fatauci a kasar Hausa.
A makon da ya gabata ne wani rikicin kabilanci ya tashi tsakanin Yarabawa da Hausawa a kasuwar Sasa dake jihar Oyo a Najeriya, lamarin da ya yi sanadin barnar rayuka da dukiyoyi. Sai dai an yi ta nuna wa kafofin yada labarai da na sadarwar zamani yatsa a kan ruruta wutar rikicin, inda ake ganin da dama sun saki layi, sun hau dokin zuciya, suka yi ta yada labarai masu tada hankali. A ka haka ne Michael Kuduson ya tattauna da sakataren kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya, Malam Shuaibu Liman, wanda ya fara bayani kamar haka:
Shirin da Al'adunmu na Gado a wannan karon tare da Salissou Hamissou ya tabo yadda wasu al'adun malam Bahaushe ke barazanar bacewa saboda zamani, Ayi saurare Lafiya.
Shirin zai leka Tarayyar Najeriya, inda zai yi nazarin wani abu guda da ya hada manyan kabilun kasar wato Hausawa da Igbo da kuma Yarabawa, wannan abu kuwa shi ne: "Goro."
RFI
Kabilun Atyap da Fulani da Hausawa dake rikici a Zangon Kataf dake Jihar Kaduna a Najeriya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a tsakanin su. Wannan ya biyo bayan taron zaman lafiyar da Basaraken yankin, Agwatyap, Dominic Gambo Yahya ya jagoranta tare da tsohon hafsan sojin sama mai ritaya, Air Marshall Stephen Shekari da kuma wakilan al’ummomin 3 dake yankin. Dangane da wannan nasarar da aka Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Barista Francis Kozah daya daga cikin mahalarta taron, kuma ga yadda tattaunawar ta kaya.
Kilishi, wani abincine na kasaita a kasar Hausa, wanda yake da sunaye daban daban misali a turanci ana kiransa da "Beef Jerky". Kasan cewar Amurka bata bari a shigo da nama Hausawa mazauna yammacin duniyar na fama da rashin Kilishi, Hakan yasa Balkisu Aliyu mai kamfanin Alsutra Kitchen ta fara yin Kilishin ana saida shi a kasashe da dama. Hakan yasa muka gayyato ta shirin Barka da Warhaka don tattaunawa da ita.
Wanne irin abincin gargajiya na kasar Hausa kuka sani? Ya aka yi abincin gargajiya ke bacewa sannu a hankali a kasar Hausa? Ku biyo mu cikin Shirin Taba Ka Lashe.
Al'adar karance-karance ta ja baya a wannan zamanin musamman ma a tsakanin Hausawa ta la'akari da yadda mafi akasarin jama'a suka fi karkata zuwa ga kallo da sauraro. Wannan shi ne batun da shirin Taba ka Lashe ya duba.