POPULARITY
Yayin da aka buɗe babban taro kan alkinta tekunan duniya a birnin Nice na Faransa, Majalisar Ɗinkin Duniya ta buƙaci a sake rattaba hannu kan sabbin yarjejeniyoyi da za su mayar da hankali kan alkinta tekuna da kuma kare hallittun ƙarƙashin ruwa. To sai dai duk da kasancewar Nahiyar Africa yankin da yafi fama da matsalolin muhalli ciki har da gurgusowar tekun, da alama taron bai yiwa yankin tanadin komai ba. Kan haka muka tattauna da Dr Mustapha Zakari Karkarna. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Rukayya Abba Kabara................
Majalisar dokokin ƙungiyar ƙasashen ECOWAS ta gudanar da taron ta a Lome da ke ƙasar Togo, wanda ya mayar da hankali kan tsadar sufurin jiragen sama a yankin. Bayan taron, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Sanata Ali Muhammed Ndume, daya daga cikin shugabannin taron. Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar tattaunawar tasu.............
Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya UNICEF, ya ce an samu ɓullar sabon nau'in cutar Polio a ƙananan hukumomi 18 da ke wasu jihohin Najeriya 9 ciki har da Kano. Rahoton ya ce zuwa yanzu an samu rahotanni daban daban aƙalla 18 kan ɓullar sabon nau'in cutar ta Shan Inna, kuma an tattara bayanan ne a cikin watanni uku da suka gabata zuwa yanzu.Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Sadiq Isa Abubakar, shugaban cibiyar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa na asibitin Malam Aminu Kano da kuma jami'ar Bayero.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu
Gwamnatin shugaba Donald Trump ta gabatar da ƙudurin daina ba da tallafi ga rundunonin wanzar da zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya, saboda gazawar da ta ce rundunonin na yi a ƙasashen Mali da Lebanon da kuma Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo.Amurka ce dai ke kan gaba wajen tallafa wa ayyukan wanzar da zaman lafiyar a sassan Duniya, inda take samar da kusan kaso 27 cikin 100 na kasafin da ake buƙata.akan haka ne, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Kamilu Sani Fagge.
Ƙungiyoyin mata daban daban na ci gaba da gudanar da zanga zanga dangane da zargin cin zarafin da Sanata Natasha Uduaghan ke yi kan shugaban Majalisar dattijan ƙasar Godwill Akpabio na neman yin lalata da ita, wanda ya sanya matan miƙa buƙatar murabus ɗinsa, kodayake jami'an tsaro sun yi amfani da hayaƙi mai sanya ƙwalla wajen tarwatsa dandazonsu. Dangane da yadda tarin mata ke fuskantar cin zarafi walau a wuraren ayyuka koma a tsakar gari, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hajiya Khadija Suleiman Saulawa wata mai rajin kare haƙƙoƙin mata a Najeriya ga kuma yadda zantawarsu ta gudana.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
Majalisar dokokin Ƙungiyar ECOWAS ta sake kafa wani sabon kwamiti da zai ziyarci ƙasashen Nijar da Mali da kuma Burkina Faso, domin tattaunawa da hukumomin sojin dake mulki a ƙasashen 3 waɗanda suka samar da ƙawancen AES. Mataimakin shugaban Majalisar Ɗattawan Najeriya, Sanata Barau Jibril ya bayyana haka bayan wani zaman na musamman da Majalisar ECOWAS ta gudanar a birnin Lagos, dangane da wannan ne kuma suka zanta da Bashir Ibrahim Idris.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
Daga cikin labarun da shirin Mu Zagaya Duniya na wannan makon ya ƙunsa akwai gargaɗin da Majalisar Ƙoli kan Shari'ar Musulunci ta Najeriya ta yi wa Malamai kan cewa su yi taka tsan-tsan yayin gabatar da wa'azi, musamman a cikin watan Azumin Ramadana mai alfarma. Sojojin Somaliya sun halaka mayaƙan Al Shebaab a ƙalla 70.Muna kuma ɗauke da bitar rahoton da ya gano yadda wata muguwar ƙwaya mai ta kashe dubban mutane (Tare da ci gaba da aika wasu dubban zuwa asibiti) a wasu ƙasashen yammacin Afirka.
Ƙasashen duniya sun bayyana matukar rashin amincewarsu da buƙatar shugaban Amurka Donald Trump, na ƙwace Gaza da kuma mayar da Falasdinawa wasu ƙasashe domin gina wurin shaƙatawa a ƙasarsu. Wannan matsayi ya gamu da suka daga ƙasashen duniya da dama ciki harda Majalisar Ɗinkin Duniya. Bashir Ibrahim Idris ya tatatuna shirin da Ambasada Abubakar Cika, tsohon Jakadan Najeriya a kasar Iran. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana.........
Hukumar da ke kula da al'adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta UNESCO ta damƙawa Najeriya takaddar shaidar sanya bikin hawan Daba na Kano cikin manyan al'adun duniya masu matukar tasiri. Jim kaɗan bayan kammala miƙa shaidar wakilinmu a Abuja Isma'il Karatu Abdullahi ya tattanna da ministar al'adu ta Najeriya Hajiya Hannatu Musawa kan tasirin da wannan zai yi wa ƙasar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar ta su......
Majalisar Ɗinkin Duniya ta shiga sahun ɓangarorin da suka fara nuna goyon baya ga sabuwar gwamnatin Syria, a wani yanayi da shugaba Abu Mohammad al-Julani da Firaminista Mohammed al-Bashir suka faro shugabancin riƙon kwarya gadan-gadan, kodayake kiraye-kiraye na ci gaba da tsananta don ganin jagororin sun yi taka-tsan-tsan a salon mulkinsu don kaucewa sake faɗawar ƙasar a yaƙi. Dangane da wannan Azima Bashir Aminu ta tuntuɓi masanain alaƙar ƙasashen ƙetare Abdulhakeem Garba Funtua, don jin ko wannan gwamnati za ta samu cikakken goyon bayan yammacin duniya.Ku latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawarsu
Kamar yadda aka saba, RFI Hausa na bai wa masu saurare damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwa da dama da ke ci musu tuwo a ƙwarya. Majalisar dattawar Najeriya ta amince da wani kuɗirin doka da ya haramta fitar da duk wata masara mai yawa da ba'a sarrafa ta ba daga ƙasar zuwa ƙasashen waje, kuma ta tanadi hukuncin ɗaurin shekara guda ga duk wanda ya yi kunnen ƙashi.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau.Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyin mabanbanta..
Shirin Al'adun mu na Gado a wannan makon ya mayar da hankali ne kan matakin da Hukumar Raya Al'adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya UNESCO, na sanya hawan Dabar Kano a arewacin Najeriya cikin kundinta na al'adun duniya.Bincike ya nuna cewar an fara gudanar da al'adar hawa Daba a lokutan bikin ƙaramar Sallah da Babba tun kafin jihadin Shehu Usman Dan fodio zamanin Sarkin Kano Rumfa. Masana a fannin tarihi sun ce zamanin Sarkin Kano Abbas, ya yi wa tsarin sauye-sauye wanda akan sa ake tafiya har zuwa wannan lokaci.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa........
Kamar yadda aka saba, RFI Hausa na bai wa masu saurare damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwa da dama da ke ci musu tuwo a kwarya. Majalisar Ɗinkin Duniya ta ware ranar 3 ga watan Disambar kowacce shekara a matsayin ranar masu buƙata ta musamman, wato mutane da ke rayuwa da wata naƙasa a fadin duniya.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau.Ku latsa alamar sauti domin sauraren shirin tare da Hauwa Halliru Gwangwazo:
Yau ce ranar da Majalisar ɗinkin duniya ta ware domin tunawa da halin da masu buƙata ta musamman ke ciki da kuma duba hanyoyin da za a inganta rayuwarsu. Karibullahi Abdulhamid Namadobi ya yi tattaki zuwa wani gida a jihar Lagos mai ɗauke da irin waɗannan mutanen sama da dubu 3 da suka fito daga yankunan arewacin Najeriya. Ga yadda zantawarsa ta gudana da guda cikin shugabanninsu Muhammad Dahiru Dan Adam.
Shugabannin ƙasashen Musulmi da na Larabawa, sun kammala taronsu da gabatar da buƙatar korar Isra'ila daga Majalisar Ɗinkin Duniya da kuma gudanar da bincike mai zaman kansa kan kisan gillar da ta yi a Gaza. Taron ya kuma amince da wasu ƙudurori daban daban da su kai ga tabbatar da ƙasar Falasɗinu. Dangame da matakan da shugabannin suka ɗauka, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ambasada Abubakar Chika, tsohon jakadan Najeriya a Iran. Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar tattaunawar ta su..........
A babban taron zauren Majalisar Ɗinkin Duniya kuwa, shugaban Senegal ne ya ɓare kwamitin tsaron majalisar, a bisa yadda yake gaza ɗaukar matakan warware matsalolin tsaron da ke haddasa hasarar rayukan da ɗimbin duniya a yankin Sahel.
Kamar yadda wata kila kuka ji a cikin labaran duniya, Ministan harkokin wajen Najeriya, Ambassada Yusuf Tuggar ya bayyana manyan dalilan da ya kamata a yi dubi da su domin sanya kasar a matsayin mambar kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya. Shugaban Sashen Hausa na RFI, Mr Joseph Penney ya tattauna da ministan a zauren Majalisar dake ci gaba da gudanar da taronta a New York ta kasar Amurka, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Kasashen duniya sun fara mayar da martani dangane da kazamin hare haren da Isra'ila ke kai wa a yankin kudancin Lebanon wanda a jiya kawai ya kai ga hallaka mutane kusan 300. Cikin wadanda suka bayyana damuwa da yadda yakin Isra'ilar ke fadada har da Sakatare Janar na Majalisar dinkin duniya Antonio Guterres. Dangane da wannan yaki Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abdulhakeem Garba Funtua na Babbar Kwalejin Fasaha dake Kaduna, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Yau ake fara taron babban zauren Majalisar dinkin duniya karo na 79, wanda ake saran ya gudanar da mahawara a kan batutuwa da dama cikin su harda sabon daftarin majalisar wanda ya kunshi sauyin yanayi da rikice rikice da matsalar sauyin yanayi da rashin shugabanci na gari tare da matsalar yunwa. Dangane da wannan taro Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ambasada Abubakar Chika, tsohon jakadan Najeriya a kasar Iran, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Majalisar Ɗinkin Duniya ta koka kan yadda aka samu ƙaruwar kashi 20 cikin 100 kan hare-haren da ake kai wa makarantu da sauran cibiyoyin ilimi da kuma ɗalibai a tsakanin shekarun 2022 zuwa 2023 da ta gabata, musamman a ƙasashen da yaƙi ya ɗaiɗaita. Cikin rahoton da ta fitar, hukumar kula ilimi, da raya al'adu ta Majalisar Dinkin Duniya UNESCO, ta ce sau dubu 6,000 aka kai wa dalibai da malamansu da kuma cibiyoyin ilimi hari, ciki har da hare-hare dubu 1,000 inda sojoji ke mayarda makarantun sansani. Ganin cewa Najeriya na daga cikin ƙasashen makarantu da dama ke fuskantar barazanar hare-haren ta'addanci ya sa Nura Ado Suleiman tattauna wa da Kwamrade Audu Titus Amba, shugaban ƙungiyar malaman Najeriyar.
Ƴan Najeriya sun fara bayyana damuwa kan yadda majalisar dattawa ke ɗaukar matakai akan mambobinta da suka bayyana ra'ayoyinsu akan halin da ƙasar ke ciki, wannan ya biyo bayan tuɓe sanata Ali Ndume daga muƙaminsa na mai tsawatarwa a Majalisa, wanda ke zuwa bayan dakatarwar da aka yi wa Sanata Abdul Ningi. Dangane da wannan matsala Bashir Ibrahim ya tattauna da tsohon Sanata kuma tsohon Minista Ambasa Ibrahim Kazaure. Kuna iya latsa alamar sauti domin jin yadda zantawar ta su ta gudana...
Nasarar lashe zagayen farko na zaɓen ‘yan majalisar Faransa da jam'iyyar RN ta masu ra'ayin riƙau ta samu da kashi 33 cikin 100 a ranar Lahadi, ya tayar da hankalin sauran jam'iyyu masu ra'ayoyin sassauci da na tsaka-tsaki bazama, waɗanda a yanzu haka suke laluben hanyar da za su bi domin hana jagorar masu zafin kishin ƙasar wato Marine Le Pen lashe zaɓen ‘yan majalisar zagaye na biyu da ke tafe a mako mai zuwa. Ko yaya masana ke kallon yanayin da siyasar Faransa ta samu kanta ciki? Da kuma dalilan da suka janyo hakan? Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna Farfesa Kamilu Sani Fagge na Jami'ar Bayero da ke Kano a Najeriya. Kuna iya latsa alamar sauti domin jin tattaunawar...
Daga cikin Labarun da shirin ya waiwaya a wannan mako akwai matakin mahukuntan sojin Jamhuriyar Nijar na cirewa hamabararren shugaban ƙasar Bazoum Muhd rigar kariyar, abinda ya bude kofar samun damar gurfanar da shi gaban kotu.A Najeriya kuwa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce zai ci gaba da yi wa tattalin arzikin ƙasar garambawul duk kuwa da yadda hakan ke ta'azzara wahlhalun da al'ummar kasar ke sha. Sai Kuma Senegal inda shugaban kasar Basirou Diomaye Faye ya sassauta farashin kayayyakin masarufi don saukaka wa jama'a tsadar rayuwar da suke ciki.Majalisar Ɗinkin Duniya ta sanar da ƙaruwar mutanen da rikici ke tilastawa barin matsugunansu a sassan duniya, adadin da zuwa yanzu ya kai mutum miliyan 120.
Shirin Mu zagaya duniya bisa al'ada kan yi bitar muhimman labaran da suka gudana a makon jiya, a wannan makon shirin tare da Nasrudden Muhammad, ya duba kan dambarwar yajin aikin NLC a Najeriya sai kuma yadda Jam'iyyar ANC a Afrika ta kudu ke laluben kafa gwamnatin haɗaka. Duk dai a cikin shirin za kuma kuji yadda ta ke ci gaba da kayawa a Gaza, bayan da Isra'ila ta ci gaba da kai hare-hare sassan Rafah ciki har da makarantar da ke ƙarƙashin kulawar Majalisar Ɗinkin Duniya.Waɗannan da ma sauran muhimman labarai na ƙunshe a cikin shirin.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin..
Shirin al'adun gargajiya na wannan mako ya yi duba ne a kan yadda Jama'a ke koken game da rikon sakainar kashi da hukumomi ke yi wa abubuwan tarihi, kamar Makon jiya yau ma shirin ya yi tattaki ne har Kanon Dabo da ke tarayyar Najeriya, inda ya tattauna da shugaban kwamitin raya Al'adun Gargajiya na Majalisar dokokin Jihar, Hon. Sarki Aliyu Daneji.Ku latsa alamar sauti don jin yadda shirin ya kasance....
Majalisar Dinkin Duniya ta ce shekarar da ta gabata ita ce mafi zafi da duniya ta gani, sai dai ta yi gargadin cewa 2024 za ta fi bara muni. A wani rahoton shekara-shekara da Majalisar ta fitar, ta ce dukannin binciken da ta gudanar ya nuna cewa 2023 itace mafi zafi a tarihin duniya.Rahoton binciken ya kuma ce shekaru biyun da suka gabata, sune mafi tsananin zafi cikin shekaru 10 da suka gabata, yayin da ake fargabar zafin zai ci gaba da tsananta a bana.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Nasirudden Muhammad.
Yan Majalisar dokokin Senegal sun amince da kudirin shugaba Macky Salla na jinkirta zaben shugaban kasa da a baya aka tsaida za a yi a ranar 25 ga watan Fabrairu da karin watanni 10, lamarin da ya janyo zanga-zanga da hatsaniya a zauren majalisar. Don jin tasirin hakan ga mutuncin shugaban Senegal da kuma siyasar kasar, Michael Kuduson ya zanta da Barista Ibrahim Bello Rigachukun, tsohon dan majalisar wakilan Tarayya a Najeriya, da kuma Majalisar dokokin nahiyar Afrika.
Majalisar dokokin Faransa ta amince da kudirin dokar da ke neman tsaurara dokokin bakin hauren da ke shiga kasar ciki har da masu neman mafaka, kudirin da bai samu tsallakewa Majalisa ba har sai da aka yi hadaka tsakanin Jam'iyyar shugaba Macron da ta masu tsattsauran ra'ayi karkashin jagorancin Marine Le Pen. Ita dai wannan doka za ta saukaka wa bakin-hauren da suke aiki a fannoni ko ma'aikatun da suke da karancin ‘yan kwadago, samun takardar izinin zama a Faransa, ko da ya ke a hannu guda kudurin zai kuma saukaka damar korar bakin a duk sanda aka so yin hakan, batun da ya sha bamban da ra'ayin jam'iyya mai shugabancin kasar.Tuni dai wasu ministocin gwamnatin ta Macron da daidaikun ‘yan jam'iyyarsa suka fara juya baya ga shugaban, kuma kan hakan ne muka tattauna da Dr Abba Sadiq mazaunin birnin Paris wanda ya yi mana karin haske kan dokar.
Majalisar dinkin duniya ta bi sahun kungiyoyi da daidaikun jama'ar dake gabatar da bukatar gudanar da bincike na gaskiya a kan kisan gillar da aka yiwa mutanen kauyen Tudun Biri a Najeriya, sakamakon harin sama da sojoji suka kai wanda yayi sanaduyar salwantar rayukan mutane da dama. Ko a jiya sanda aka gudanar da zanga zangar lumana a Abuja da kuma Zaria domin kara matsin lamba ga gwamnati. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hajiya Naja'atu Muhammad, mai sharhi a kan al'amuran yau da kullum a Najeriya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Kungiyar agaji ta OXFAM ta bayyana farin cikin ta da nasarar da aka samu wajen kafa asusun da manyan kasashen duniya zasu zuba kudade, domin tallafawa kasashe masu tasowa dake fuskantar matsalar sauyin yanayi. Wannan mataki ya biyo vayan amincewar da wakilan kasashe sama da 175 suka cimma a wajen taron sauyin yanayin Majalisar dinkin duniyar dake gudana a Dubai. Bashir Ibrahim Idris ya tatatuna da Daraktar kungiyar dake kula da nahiyar Afirka, Fati Nzi Hassan.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
A Najeriya, Kungiyar CISLAC da ke bin diddigir ayyukan Majalisar da yaki da rashawa ta gudanar da wani taron karawa juna sani a birnin Legas dangane da kokarin samar da sauye sauye a harkokin zaben Najeriya da kuma kyautata nagarta a bangaren shari'un bayan zabe. Shugaban kungiyar Auwal Musa Rafsanjani ya bayyana mana muhimammancin taron a zantawarsa da Ahmed Abba
Majalisar Dinkin Duniya, ta bukaci a gaggauta tsagaita wuta a Zirin Gaza, tare da gargadin cewa lokaci na kurewa kasashe kan bukatar dakile yi wa Falasdinawa kisan kare dangi a yankin na Gaza. Shugaban Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya, Filpipo Grandi ya bukaci mambobin Kwamitin Tsaro na Majalisar da su kawo karshen rarrabuwar kawunan da ke tsakaninsu, don tabbatar da an tsagaita wutar da za ta dakatar da salwantar rayukan Falasdinawa a Zirin Gaza.
Malaman addinin Islama a Najeriya sun bi sahun wasu ‘yan kasar da Majalisar dokoki da ta dattawa, wajen bukatar ganin gwamnatin Najeriya ta bude iyakokin ta da Jamhuriyar Nijar domin sakin mara ga talakawan dake tsakanin kasashen biyu, sakamakon takunkumin karya tattalin arzikin da aka kakabawa kasar bayan juyin mulkin soji. Rahotanni sun ce mazauna iyakokin kasashen biyu na Najeriya da Nijar na fuskantar mawuyacin hali wajen katsewar harkokin kasuwanci da kuma na yau da kullum. Dangane da haka Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Khalid Aliyu, Sakataren kungiyar Musulmin Najeriya ta JNI kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Majalisar zartaswar Najeriya ta amince da ware kusan naira triliyan uku a matsayin kari kan kasafin kudin bana, duk da janye tallafin man fetur. Majalisar ta ce za'a yi amfani da wadannan kudade ne wajen habbaka bangaren tsaro da kuma gyaran wasu manyan gadoji a biranen kasar. Wannan kari dai ya zo wa ‘yan Najeriya a bazata la'akari da yadda suka yi tsammanin rarar da aka samu bayan janye tallafin man fetur za su shiga cikin irin wadannan bangarori. Dr Kasim Garba Kurfi masanin tattalin arziki ne a Najeriya, ya ce akwai bukatar gwamnatin Najeriya ta sake duba wannan batu, ga dai tattaunawar sa da Rukayya Abba Kabara kan wannan al'amari da sauran batutuwan tattalin arziki a kasar.
Majalisar Wakilan Tarayyar Najeriya, ta zargi gwamnatin da ta gabata da aikata damfara, ta hanyar kaddamar da jiragen saman Nigeria Air kwanaki biyu kafin Shugaba Muhammadu Buhari ya sauka daga karagar mulkin kasar. Majalisar ta yi wannan zargi ne bayan da Mukaddashin Babban Daraktan sabon kamfanin ya tabbatar ma ta da cewa, jirgin da aka nuna wa duniya dauke da tambarin Nigeria Air, an yi hayarsa ne daga kamfanin Jirage na Ethiopan Airlines. Ko wanne mataki ya kamata sabuwar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta dauka dangane da wannan lamari? Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin da Nasiru Sani ya gabatar.
A wannan shirin na Muhallin ka Rayuwar ka, shirin dake tattauna wa da masu ruwa da tsaki kan sauyi ko dumamar yanayi da kuma uwa uba fannin noma da kiwo, wanda Nasiru Sani ke jagoranta.Shirin na wannan mako zaiyi dubi ne kan wani rahoto da Majalisar dinkin duniya ta bayana cewar kudin da ake kashewa wajen sayen ruwan roba ya kai ayi amfani dasu wajen samar da wadataccen ruwan sha a fanfunan daukacin al'uma a duniya.
Ganin irin gagarumar nasarar da Hukumar NDLEA dake yaki da masu mu'amala da miyagun kwayoyi keyi a Najeriya, Majalisar zartarwar kasar ta amince da a baiwa hukumar sama da naira miliyan 580 domin sayen motocin soji dan ci gaba da yakin da suke yi. Wannan na zuwa ne kasa da mako biyu da Hukumar ta kama hodar ibilis a Lagos da kudin sa ya zarce sama da naira biliyan 193. Dangane da nasarorin da Hukumar ke samu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Alhaji Muhammadu Awwal, daya daga cikin masu sanya ido akan yaki da miyagun kwayoyin a Najeriya. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Yau ake kammala taron Hukumar kare hakkin Bil Adam ata Majalisar Dinkin Duniya a Geneva, wanda yake tattauna batutuwan da suka shafi kare hakkin Bil Adama a kasashen duniya daban daban. Taron na kwanaki 3 ya samu halartar wakilai daga sassan duniya. Dangane da wannan taro, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Kalla Muntari, dan Majalisar dokoki kuma shugaban kwamitin kula da walwalar 'yan kasa a Jamhuriyar Nijar. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Mutane a Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo sun gudanar da zanga zangar adawa da zaman sojojin Majalisar dinkin Duniya dake aikin samar da zaman lafiya a kasar, saboda abinda suka kira yadda Yan tawaye ke ci gaba da kai hari suna kashe fararen hula. Yayin zanga zangar an kashe sojoji 3 da kuma mutum goma sha biyu daga cikin masu zanga-zangar. Akalla sojojin Majalisar 18,000 ke aikin wanzar da zaman lafiya a kasar ta Congo. Latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawar Bashir Ibrahim Idris da kuma Janar Sani Usman Kukasheka mai ritaya, masanin tsaro a Najeriya.
Gwamnatin Jihar Zamfara da ke Najeriya ta sanar da sauke manyan Sarakunan Jihar guda biyu da Magajin Gari guda saboda samun su da hannu wajen ayyukan ta'addancin da suka addabi Jihar. Majalisar zartawar jihar ta amince da rahotan binciken da akayi akan Sarkin Zurmi Atiku Abubakar da na Dansadau Hussaini Umar tare da Suleiman Ibrahim Danyabi a matsayin Magajin Garin Birni Tsaba. Mun tattauna da Kwamishinan yada labaran Jihar Ibrahim Dosara kuam ga bayanin da ya mana akan matakin.
Kasar Amurka ta sake fitar da wani sabon hasashe wanda ke cewa Najeriya ta kama hanyar rugujewa, kamar yadda wasu kwararrun kasar suka yi Nazari akai. Rahotan wannan hasashe ya tada hankalin jama'ar kasar da dama, musamman lura da matsalolin da suka addabi kasar da kuma tashe tashen hankula. Dangane da wannan rahoto, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Haruna Yarima na Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria, kuma tsohon dan Majalisar wakilan Najeriya. Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu
YAU ce ranar da Majalisar Dinkin Duniya ta ware a matsayin ranar yaki da cutar AIDS ta duniya, da zummar nazari da kuma fadakar da jama'a halin da ake ciki game da cutar. A wannan shekarar Majalisar ta bukaci samun daidaito ne wajen kawo karshen cutar nan da shekara ta 2030. Dangane da wannan rana, mun tattauna da Dr Aliyu Gambo, shugaban hukumar yaki da cutar a Najeriya, kuma ga tsokacin da yayi mana akai.
Shirin 'Mu Zagaya Duniya' tare da Garba Aliyu Zaria da ke bitar muhimman labarai, ko lamurran da suka wakana a makon da ya kare, ya maida hankali kan harin baya-bayan nan da wuka da aka akaiwa wani dan majalisar dokokin Birtaniya, wanda jami'an tsaro suka tattabar da cewa ta'addanci.
Batun wasu hukunce-hukunce masu cin karo da juna da wasu Alƙalai shida suka yanke wanda Majalisar Ƙoli ta Harkokin Shari'a ke bin ba'asi a kai da kuma labarun wasanni.
Majalisar wakilan Najeriya ta bai wa gwamnati shawarar amfani da sojin haya wajen shawo kan matsalar boko haram da ‘Yan bindigar da suka addabi kasar. Wannan na daga cikin kudirori guda 19 da Majalisar ta amince da su bayan taron da ta gudanar akan matsalolin tsaron da suka addabi Najeriya da niyyar shawo kansu, inda ta mikawa shugaban kasa Muhammadu Buhari. Dangane da wannan shawara Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin harkar tsaro Dr Yahuza Getso, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
Majalisar Wakilan Najeriya ta tantance sabon babban hafsan sojin kasa Janar Faruq Yahaya da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada domin maye gurbin Janar Ibrahim Attahiru da ya rasu. Dangane da kalubalen dake gaban sabon shugaban sojin da kuma tabarbarewar matsalar tsaro a kasar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hon. Abdurazaq Namdas, shugaban kwamitin sojin kasa, na Majalisar, kuma kuna iya latsa alamar sauti domin sauraron hirar da akayi da shi.
A Jiya Laraba ne majalisar dokokin kasar Jamhuriyar Nijer ta kawo karshe wa’adin aikinta na tsawon shekaru 5. Majalisar da aka zaba a 2016 zuwa 2021, ta rufe kofofinta ne tare da jawabin da shugabanta Husaini Tinni ya yi a zauren majalisar dake birnin Yamai. To domin jin Irin muhimman ayuka na gari da za a shaidi majalisar da aikatawa, Mahaman Salisu Hamisu ya tattauna da dan majalisar dokoki Murtala Alhaji Mamuda.
8 ga watan Maris rana ce da Majalisar dinkin Duniya ta ware a matsayin ranar mata ta duniya, wadda ake amfani da ita wajen nazarin rayuwar mata da kuma halin da suke ciki, musamman matsalolin da suke fuskanta. Kuma dangane da wannan rana Bashir Ibrahim idris ya tattauna da Hajajiya Maryam Muhammad, Malama kuma mai bincike a kasar Amurka, kan rayuwar ‘ya mace a kasashe maso tasowa irin Najeriya da kuma matsalolin dake hana su samun ilimi.
An yi bikin rantsar da zababben shugaban Amurka Joe Biden a matsayin shugaban kasa na 46, tare da mataimakiyar sa Kamala Harris a Majalisar dokokin Amurka. Bikin da ya gudana a Majalisar dokoki Amurka kamar yadda aka saba, shine irin sa na farko da shugaba mai barin gado yaki halarta a cikin shekaru 150, ganin yadda shugaba Donald Trump ya haure takalman sa ya tashi zuwa Florida, bayan yayi jawabi a cibiyar soji ta ‘Joint Base Andrews’ inda ya shaidawa magoya bayan sa cewa zai sake dawowa ta wata hanyar, bayan nasarorin da yace ya samu. Garba Aliyu Zaria a cikin shirin Mu zagaya Duniya ya mayar da hankali kan rantsar da sabon Shugaban Amurka Joe Biden,Shugaba na 46.
Hukumar tsaron FBI a Amurka ta ce Magoya bayan Donald Trump na shirin gudanar da zanga-zanga a wasu jihohin kasar 50. Bayan tsige Shugaba Donald Trump na Amurka da majalisar wakilan kasar ta yi jiya laraba, a yanzu haka masu ruwa da tsaki game da dorewar siyasar kasar sun maida hankula ne wajen samun nasarar rantsuwar kama aiki na sabon Shugaba Joe Biden. Jamian tsaron kasar dai sun karfafa matakan tsaro don gudun kada a mamaye su. Majalisar wakilan kasar dake da rinjayen ‘yan jam’iyar Democrat ta kada kuri’ar amincewa da tsige shugaban, a karo na 2, kuma irinsa na farko a tarihi da yawan kuri’u 232 a kan 197 na wakilan dake goyon bayansa. A zauren majalisar, ‘yan jam’iyyar Republican 10 ne suka goya wa takwarorinsu na Democrat baya, cikinsu har da kusa a jam’iyyar, Sanata Liz Cheney. An zargi hamshakin attajiri, kuma shugaban Amurka mai barin gado, mai shekaru 74 wanda zai mika ragamar mulki a ranar 20 ga wannan wata na Janairu, da tunzura masu zanga zangar da suka mamaye majalisar dattawan kasar a ranar 6 ga wata domin hana tabbatar da zaben Joe Biden mai shekaru 78, al’amarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 5, ya kuma zubar da mutuncin demokradiyar Amurka. Garba Aliyu Zaria ya tuntubi Farfesa Khamilu Sani Fagge na Jamiar Bayero dake Kano don jin yadda yake kallon dambarwar siyasar Amurkan.
Shirin 'Mu Zagaya Duniya' kamar yadda ya saba, yayi waiwaye kan wasu daga cikin muhimman abubuwan da suka auku a makon da ya kare, ciki har da siyasar kasar Amurka, inda shugaba mai barin gado Donald Trump ya tunzura magoya bayansa da suka tayar da tarzoma a zauren majalisar dattijan kasar.
Majalisar dattijan Najeriya ta yi karatun na biyu kan Kudurorin kafa sabbin rundunonin jami’an tabbatar da zaman lafiya na ‘peace corps’ da kuma rundunar mafarauta domin taimakawa jami’an tsaro wajen kawo karshen matsalolin tsaron da suka addabi sassan kasar ta Najeriya. Matakin na zuwa a daidai lokacin da shugaban kasa Muhammadu Buhari gami da manyan hafsoshin rundunonin tsaron kasar ke cigaba da shan caccaka kan kalubalen da ya dabaibaye sha’anin tsaro a sassan kasar. Kan haka muka tattauna da masanin tsaro a Najeriya, Aminu Bala Sokoto (Squadron Leader mai ritaya).
Bayan kisan gillar da aka yiwa manoman shinkafa 110 a jihar Borno da ke yankin Arewa maso gabashin Najeriya, tawagar ‘yan Majalisar Tarayya da suka fito daga jihar sun ziyarci garin Zabarmari yau Litinin don jajantawa mutanen yankin dangane da ibtila’in da ya afka musu. Bayan kammala ziyarar ta yau, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hon Ahmed Satomi dan majalisar wakilai da ke wakiltar yankin da harin ya afku ga kuma yadda zantawarsu ta gudana.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bai wa karamin ministan ayyukan kasar Festus Keyamo umarnin cigaba da shirin dibar ma’aikata dubu 774 bayan takaddamar da ta kaure tsakanin sa da 'yan Majalisun kasar da suka nemi a dakatar da aikin. Ministan ya ce shugaba Buhari ya bashi umurnin cigaba da aikin kamar yadda doka ta tanada, yayin da kungiyoyi daban daban za su taka rawa wajen dibar ma’aikatan a matakan kananan hukumomi 774 da ke fadin Najeriya a shirin da ake saran ya lakume naira biliyan 52. Dangane da wannan cigaba mun tattauna da Mallam Abdullahi Umar, kuma ga tsokacin da ya yi akai.
Shugaban Kwamitin Noma a Majalisar Wakilan Najeriya Mukhtar Dan Dutse ya bukaci sanya hukuncin kisa kan 'yan bindigar da suka addabi yankin Arewacin kasar da kuma makiyayan da ke kashe manoma. Dan Majalisar ya ce rashin daukar mataki mai tsauri kan irin wadannan mutane na barazanar jefa Najeriya cikin yunwa ganin yadda manoma suka kauracewa gonakin su saboda fargabar hallaka su. Dangane da wannan matsayi, mun ji ta bakin masanin shari’a Farfesa Shehu Abdullahi Zuru na Jami’ar Abuja, kuma ga tsokacin da yayi akai.
Majalisar dinkin Duniya ta bayyana takaicinta kan rikicin siyasar Mali, sakamakon hasarar rayukan da aka samu a zanga-zangar kin jinin shugaban kasar Ibrahim Bubakar Kaita, yayin da ita kuma kungiyar gamayyar tattalin arzikin kasashen Afrika ta yamma ECOWAS ko CEDEAO ta bukaci ama kan tuburin sulhu tsakanin gwamnati da ‘yan adawa domin kawo karshen rikicin. A kan haka Mahaman Salisu Hamisu ya tattauna da Dr Sani Yahaya Janjuna mai sharhi kan siyasa da zamantakewar alúmma a Jamhuriyar Nijar, kan sanin abinda ya kara gurbata rikicin.
Hukumar zaben Jamhuriyar Nijar, ta ce ba za ta iya gudanar da zabe domin bai wa ‘yan kasar dake zaune a kasashen ketare damar samun wakilci a Majalisar dokokin kasar ba, sannan kuma ba za ta iya gudanar da zaben kananan hukumomi ba duk da cewa wa’adinsu ya kawo ya kawo karshe. A baya dai cikin watanni masu zuwa aka tsara gudanar da sabbin zabuka a kasar ta Nijar, sai dai hukumar zabe ta ce ba ta da lokacin yi wa masu kada kuri’u rijista a kasashen ketare, matakin da tuni ya samu amincewar kotun tsarin mulkin kasar. Wannan shi ne batun da muka baiwa masu sauraro damar tattaunawa akai.
Yau shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' tare da Bashir Ibrahim Idris zai mayar da hankali kan kokarin da Majalisar Dattawar Najeriya ke yi na samar da dokar da za ta sa ido kan amfani da kafofin sadarwar intanet.
Shirin ra'ayoyin ku masu sauraro na wannan lokaci tare da Zainab Ibrahim, ya tattauna matakin Majalisar Dattawan Amurka na kada kuri’ar kin amincewa da matakin kiran masu bada shaida da kuma tattara sabbin hujjoji dangane da tsige shugaban kasar Donald Trump. Ana ganin matakin da Majalisar Dattawan mai rinjayen ‘yan Jam’iyar Republican ta dauka, zai kai ga wanke Trump daga zarge-zargen amfani da karfin ikonsa ta hanyar da ba ta dace ba. Tuni Majalisar Wakilan kasar ta tsige shugaban daga karagarsa.
Majalisar dokokin Najeriya ta gabatar da kudirin dokar hukunta duk wanda aka kama da laifin yada kalaman kiyayya, da daurin shekaru 10 a gidan yari ko biyan tarar naira miliyan 10. Matakin ya haifar da suka daga bangarorin adawa, alkalai da kuma kungiyoyin fararen hula, inda suka ce kudurin dokar ya yi tsanani. Kan wannan al'amari a wannan karon muka baiwa masu sauraro damar bayyana ra'ayoyi akai.
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya yi nazari kan kiran da Majalisar Tarayyar Najeriya ta yi shugaba Muhammadu Buhari don yi mata bayani kan tabarbarewar tsaro a kasar.
Shirin dandalin siyasa a wannan makon ya sake yin duba kan dambarwar neman shugabancin Majalisar Najeriyar karo na 9 da sabbin zababbun 'yan Majalisar wakilan kasar ke tafkawa. A yi sauraro lafiya.
Shirin Dandalin Siyasa ya tattauna game da batun yin watsi da amincewa da jekadu 46 da Majalisar Dattiajan Najeirya ta yi da rikicin shugabannin Jamiyyar PDP mai adawa a Najeriya da ta dare gida biyu inda wasu ‘yan jam’iyyar ke neman a raba-gari wasu kuma ke bukatar sake lale.
Shirin Dandalin Siyasa ya yi nazari kan shirin babban zaben kasar Ghana da za a gudanar a watan Disemba. Shirin kuma ya leka Najeriya game da batun fasa kwan da Hon Abdulmumin Jibril ke yi a Majalisar dokokin kasar.