POPULARITY
Shirin al'adun mu na Gado na wannan mako zai Dora kan ci gaban Muhawara a tsakanin Masana kan kwarewar waƙa a tsakanin mawaki Shata da kuma Rarara Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin, tare a Nasiru Sani
Shirin na yau, ya ɗora ne akan kashi na farko da muka gabatar a makon jiya, wanda ya yi duba game da yadda harshen Hausa ya bunkasa a lokutan baya, da muhimmacinsa, baya ga matsalolin da yake fuskanta da ma kalubalen da Rubutun Hausa ke fuskanta a kafofin sada zumunta. Masana sun bayyana ka'idojin rubutun Hausa, a matsayin wani yanayi na lura tare da kiyaye ka'idojin harshen Hausa a rubuce domin samun damar isar da sakon da marubuci ke nufi zuwa ga mai karatu daidai ba tare da dungushe ko sauya ma'anar da marubuci ke nufi ba. A cewar masanan kiyaye ƙa'idodin rubutun yana kuma samar da saukin fahimtar karatu daga mai karantawa.Ko da a kafafen yada labarai, rashin kiyaye ka'idojin rubutun Hausa yakan taka rawa wajen sauya ma'anar labari, to ko ya masu bibiyar shafukan yanar gizo na kafafen watsa labarai ke ji idan suka ga ba a yi amfani da harufa masu lanƙwasa ba kamar Ɓ da Ɗ da kuma Ƙ? Ga abinda wasu ke cewa.
Shirin Ilimi hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan makon shirin ya sauya salo zuwa mai dogon zango ta yadda zai tattauna da masu ruwa da tsaki a kan bunƙasar harshen Hausa da matsalolin da ya ke fuskanta da dalilan da suka haifar da matsalolin, da dai sauran muhimman batutuwa da suka shafi harshen na Hausa. Harshen Hausa, harshe ne da yake da tsohon tarihi wanda ya shafe ɗaruruwan shekaru ana magana da shi, wanda alƙaluma suka tabbatar da cewar zuwa yanzu miliyoyin mutane ne ke magana da harshen a sassan duniya.Wani rahoto da aka wallafa a shekarun baya bayan nan ya nuna cewar a halin yanzu Harshen Hausa ne Harshe na 11 da aka fi amfani da shi a duniya, zalika an yi ƙiyasin cewar mutane miliyan 150 ne ke magana da shi a sassan Duniya.Masana na kallon waɗaccan alƙaluma a matsayin dallilan da suka sanya harshen na Hausa yin shaharar ta kai ya yi gogayya da dukkanin manyan harsunan duniya, lura da yadda harshen ke da yalwar kalmomi da za a iya sarrafa su gami da bayyana kowanne irin tunani da su, walau a litattafai, kafofin yaɗa labarai da sauran hanyoyi.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin 'Lafiya Jari Ce' na wannan makon ya mayar da hankali ne akan cutar sankarau, wanda ke yin ƙamari a cikin yanayi na zafi da ake ciki, musamma a ƙasashenmu na nahiyar Afrika. Tuni aka samu ɓullar cutar sankarau a sassa daban-daban na Najeriya inda ta kashe gomman mutane a jihohin Kebbi da Sokoto, wadda aka bayyana ta da annoba. Masana a ɓangarorin lafiya da kuma yanayi, na ci gaba da gargaɗi kan yiwuwar ɓullar tarin cutuka sakamakon tsananin zafin da ake fuskanta a wasu daga cikin jihohin Najeriya, a wani yanayi da ake ci gaba da azumin watan Ramadana,, wannan shi ne maudu'in da shirin lafiya jari ce na wannan mako zai mayar da hankali akai sai ku biyomu.
Shirin, ‘Muhallinka Rayuwarka' na wannan makon ci gaba ne daga shirin da kuka ji a makon jiya. Idan a wannan kashi na uku wanda shi ne na ƙarshe, ya mayar da hankali ne kan tasirin ruwan Tekuna da Tafkuna da kuma Koguna ga kyautatuwar muhalli ko gurbatarsa, da kuma hanyoyin magance ƙalubalen da muhalli ka iya fuskanta. Masana kimiyyar muhalli sun haƙiƙance cewa tabbas waɗannan nau'ika na ruwa guda uku suna da ɗumbin tasiri akan muhalli. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Michael Kuduson..........
Shirin kasuwa a kai miki dole na wannan makon ya yi duba ne akan hasashen masana game da makomar tattalin arzikin Najeriya a shekarar nan ta 2025. Masana dai sun daɗe da bayyana wasu hanyoyi da ake amfani da su wajen hasashen makomar tattalin arziƙin ko wacce kasa, yanki ko nahiya a faɗin duniya.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin....
A wannan mako shirin ya tattauna ne kan rawar da kasuwancin Intanet ke takawa wajen bunkasar tattalin arzikin kasashe irinsu Najeriya. Kasuwanci ta internet da ake kira da e-commerce a turance, na taka muhimmiyar rawa wajen sauya yadda ake gudanar da harkokin siye da siyarwa a duniya tare da habakar tattalin arziki.A Najeriya, masana sun yi ittifakin cewa kasuwanci internet wato e-commerce na kawo sauyi ga tattalin arzikin kasar, tare da samar da ci gaba ta fuskoki da dama, da kuma samar da ayyukan yi a tsakanin al'ummar kasar.Duk da cewa an hakkikance kasuwanci ta internet na bunkasa tattalin arziki a Najeriya, akwai tulin kalubale da ya kamata a magance, masamman karancin wayewa game da harkokin kasuwanci ta Internet ga jama'a, da wargajewar kasuwa.Masana sun yi nuni da cewa, kasuwanci ta internet na bayar da damar da za ta iya haifar da ci gaban tattalin arziki a Najeriya, amma hakan na bukatar tallafi da aiwatar da wasu manufofi, wandanda za su samar da kyakkyawan yanayi ta fuskar kasuwanci da tattalin arziki ta yadda al'ummar kasar za su dara.
Ƙungiyar Amnesty International ta danganta haɗrin tankin man da ya hallaka kusan mutane 100 a jihar Neja ta tsakiyar Najeriyar a matsayin talaucin da ya yiwa jama'ar ƙasar katutu, inda daraktan ƙungiyar a Najeriyar Malam Isa Sanusi ke cewa akwai buƙatar mahukunta su sassauta matakan da suke ɗauka a lamurran da suka shafi tattalin arziƙi. Matsalar ta haɗari ko kuma gobarar tankar mai na neman zama ruwan dare a Najeriya, inda ko a baya-bayan nan aka ga yadda fiye da mutane 100 suka mutu can a jihar Jigawa sakamakon gobarar da ta tashi lokacin da suke tsaka da kalen man da ya malala akan titi bayan tuntsirewar wata tanka.Masana irin daraktan ƙungiyar ta Amnesty International mai rajin kare haƙƙin ɗan adam, Isa Sanusi na kallon talauci a matsayin babban dalilin da ke sanya mutane kai kansu ga irin wannan haɗarin wanda ke nuna buƙatar da ke akwai ga mahukunta wajen sun samar da sassauci ga jama'a don kaucewa fuskantan makamantan wannan matsaloli.Yayin wata zantawarsa da editan sashen Hausa na RFI Bashir Ibrahim Idris, Isah Sanusi ya miƙa ga roƙo ga mahukuntan Najeriya.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.
Masana tsaro na ci gaba da tsokaci kan harin da mayakan Boko Haram suka kai sansanin sojin Damboa a jihar Bornon Najeriya wanda ya yi sanadiyyar mutuwar sojoji da ƴan sa kai. Kan hakan ne wakilinmu Ƙaribullah Abdulhamid Namadobi ya tuntuɓi masanin tsaro Kyaftin Abdullahi Bakoji mai ritaya.Shiga alamar sauti, domin sauraron ciakkiyar tattaunawar.
Shirin Al'adun mu na Gado a wannan makon ya mayar da hankali ne kan matakin da Hukumar Raya Al'adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya UNESCO, na sanya hawan Dabar Kano a arewacin Najeriya cikin kundinta na al'adun duniya.Bincike ya nuna cewar an fara gudanar da al'adar hawa Daba a lokutan bikin ƙaramar Sallah da Babba tun kafin jihadin Shehu Usman Dan fodio zamanin Sarkin Kano Rumfa. Masana a fannin tarihi sun ce zamanin Sarkin Kano Abbas, ya yi wa tsarin sauye-sauye wanda akan sa ake tafiya har zuwa wannan lokaci.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa........
Shirin Lafiya Jari ce a wannan makon tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan matsalar mace-macen mata masu juna biyu da jarirai walau a lokacin haihuwa ko kuma goyon ciki, matsalar da ke tsananin ta'azzara a Jamhuriyyar Nijar bayan da alƙaluma suka nuna yadda matsalar ke kwan-gaba-kwan-baya sakamakon dawowarta a baya-bayan nan bayan daƙileta a shekarun baya. Masana sun alaƙanta matsaloli masu alaƙa da rashin cin abinci mai gina jiki ko kuma rashin kulawar lafiya baya da rashin garkuwa mai ƙwari ga matan a jerin manyan dalilan da kan sabbaba mace-macen matan masu juna.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin Lafiya Jari ce tare da Azima Bashir Aminu a wannan makon ya mayar da hankali kan yadda cutar Cancer ko kuma Daji ko Najeriya ke ta'azzara a Najeriya a wani yanayi da ake da ƙarancin wayar da kai kan cutar duk kuwa da illar da ta ke ci gaba da yiwa jama'a. Hankulan masana a ɓangaren kiwon lafiya ya tashi ne matuƙa bayan hasashen da ke nuna yiwuwar alƙaluman masu kamuwa da cutar duk shekara a Najeriyar da yawansu ya kai dubu 70 ya iya ruɓanyawa fiye da ninki 10 nan da shekaru ƙalilan masu zuwa a ƙasar, a wani yanayi da har yanzu jama'a ke jahiltar cutar.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Mazauna yankin arewacin Najeriya na bayyana damuwa kan yadda kamfanoni da ƴan kasuwa ke rige rigen sayen kayan abinci a hannun manoma. Masana na bayyana fargabar cewar matakin zai sanya kayan abincin ya yi tsada a daidai lokacin da jama'a ke fama da tsadar rayuwa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Alhaji Muhammadu Magaji, Sakataren tsare tsare na ƙungiyar manoman Najeriya dangane saye kayan abincin. Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar tattaunawar ta su........
Masu masana'antu a arewacin Najeriya sun bi sahun sauran jama'ar yankin wajen bayyana damuwarsu a kan halin da suka samu kansu na rashin wutan lantarki sama da kwanaki goma. Kan haka Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mataimakin shugaban ƙungiyar masu masana'antu ta ƙasa MAN, Ali Safiyanu Madugu.
Shirin lafiya jari ce a wannan makon ya mayar da hankali ne game da matsalar shaye-shayen magunguna ba bisa ka'ida ko kuma shawarwarin masana kiwon kiwon lafiya ba, wadda hakan ke haifar da matsaloli da dama a jikin dan'adam. 14/10/2024
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasashen Afirka ta Yamma, wato GIABA ta shirya wani taron fadakar da 'yan kasuwa da masu masana'antu da kuma lauyoyi a kan hakkin da ya rataya a kansu na kin bada dama ga masu halarta kudaden haramun ko kuma 'yan ta'adad su yi amfani da su wajen boye kudaden sata. Taron na kwanaki 2 na gudana ne a birnin Lagos. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai magana da yawun GIABA Mr Timothy Melaye, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Jamhuriyar Nijar inda tsuntsaye irinsu Angulu da Mikiya da ake samu a mayanka da bayan gari, inda ake jefar da gawawwakin dabbobi a yanzu sun zama tarihi. Za mu duba dalilan ɓacewarsu. Masana a faɗin duniya sun yi ittifakin cewa ɓacewar waɗannan tsuntsaye, musamman ungulu ba karamin koma baya ba ne ga lafiyar muhalli. Kafin mu tafi jihar Maraɗi a Jamhuriyar Nijar, za mu ji ƙarin bayani a game da ungulu da mahimancinsa ga muhalli da lafiyar al'umma, da kuma dalilan da su ka sa su ke ɓacewa daga doron ƙasa, daga bakinmasanin namun daji da abin da ya shafi halayyarsu.
Shirin Lafiya Jari ce a wannan karo ya mayar da hankali ne game da alfanun Azumi ga lafiyar jikin dan Adam. Masana kiwon lafiyar dai na bayyana cewar Azumi na taimakawa wajen rage kaifin wasu cutuka a jikin dan adam. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu.....
Shirin na wanna makon zai yi dubi ne akan katafaren shirin zamanantar da aikin noma da gwamnatin jihar Nejan Najeriya ta kaddamar. Masana na ganin Jihar a matsayin wadda idan aka tattala kasar noma da take da ita, a cikinta kadai za a iya noma abincin da zai iya ciyar da kasar har ma a iya fitarwa zuwa kasashen ketare. A wannan aikin da aka kaddamar, gwamnatin jihar ta ce ta samar da kayan aikin fasahar noma na zamani tare da tanadar da dabarun noma daga kwararru.Ku latsa alamar sauti dn sauraron cikakken shirin tare da Nasiru Sani.......
Shirin Lafiya Jari ce a wannan karo ya mayar da hankali ne kan irin cutukan da ke karuwa a lokutan Azumi musamman yadda a wannan karon ake gudanar da ibadar a cikin yanayi na tsananin zafi, wanda masana ke ganin akwai wasu naukan cutukan da ka iya bijorowa. Masana kiwon lafiya dai sun gargadi masu dauke da wasu nau'ukan cutuka kan irin matakan da ya kamata su dauka don kula da lafiyarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu.....
Masana harkar noma da samar da abinci sun bayyana cewar Najeriya na da duk abinda take bukata wajen ciyar da kan ta muddin ta inganta harkar noman kasar, amma kuma sakaci daga hukumomi da matsalar tsaro na ci gaba da yiwa kasar tarnaki. Wasu na danganta matsalolin da ake fuskanta daga sakacin gwamnati, yayin da wasu ke zargin jama'ar kasar da kauracewa rungumar aikin noman.Dangane da wannan matsala na gazawar kasar wajen ciyar da kan ta, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Sakataren tsare tsare na kungiyar manoman Najeriya, Alhaji Muhammadu Magaji.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Masana a Najeriya na zargin wasu bankunan kasa da da taimakawa wajen bunkasar ayyukan masu garkuwa da mutane domin karbar diyya, saboda yadda ake amfani da su wajen sarrafa kudaden da ake biyan diyyar da su. Masanan sun ce ya dace a samu hadin kai tsakanin jami'an tsaro da kuma bankunan domin dakile ayyukan 'yan ta'addan wanda ke ci gaba da ta'azzara yanzu haka.Dangane da wannan zargi, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin harkar tsaro, Dr Yahuza Getso.
Kasar Saudiyya ta ce zata zuba jari a matatun man Najeriya guda 4 da yanzu haka ake gyarawa domin ganin sun dawo aikin tace mai gadan gadan, domin rage dogaro da man da ake shigo da su daga kasashen ketare. Saudiyar ta sanar da haka ne bayan tattaunawar da aka yi tsakanin Yarima Muhammad bin Salman da shugaba Bola Ahmed Tinubu a birnin Riyadh, inda aka gudanar da taron Saudiya da shugabannin Afirka. Baya ga zuba jarin a matatun man, Saudiyar ta kuma ce zata taimakawa Najeriya da kudaden dala domin rage karancinsa da ake fuskanta da kuma ceto naira dake ci gaba da faduwa. Dangane da wannan ci gaba, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin harkar mai da iskar gas a Najeriya, Injiniya Kelani Muhammad, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Kwanaki 26 bayan barkewar yakin dake ci gaba da gudana ba tare da kaukautawa ba tsakanin Isra'ila da kungiyar Hamas, wanda yayi sanadiyar mutuwar mutane kusan dubu 10, ana fargabar yakin na iya fadada musamman ganin yadda kungiyoyi irin su Hezbollah da Houthi suka fara harba makamai a kan Israila. Masana na bayyana cewar ganin yadda Majalisar Dinkin Duniya kuma kasashen dake da karfin fada aji suka gaza samar da Shirin tsagaita wuta, yakin na iya daukan dogon lokaci. A kan haka, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Bashir Nuhu Mabai na Jami'ar Dutsinma da ke Katsinan Najeriya.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Shirin 'Kasuwa Akai Miki Dole' na wannan mako tare da Ahmed Abba ya mayar da hankali ne kan jan hankali da kungiyoyi irinsu CISLAC ke yi a Najeriya, wajen ganin gwamnati ta maida hankali kan gibi da ake samu a fannin tara haraji domin samun kudaden shiga. Masana sun yi ittifakin cewar Najeriya na da dimbin arzikin da bai kamata ace sai ta ciyo bashin kudade kafin biyan bukatun ta ba, amma sakaci da kuma cin hanci da rashawa da ya yi wa kasar katutu ke mayar da ita baya.Wannan yasa kungiyar CISLAC mai zaman kanta da ke sa ido kan ayyukan majalisar dokoki da kuma yaki da rashawa, da hadin guiwan cibiyar horar da ‘yan majalisun dokoki da demokuradiyya, suka shirya taro don horarwa da nunawa ‘yan majalisu rawar da za su taka wajen yin dokoki da saka ido a hanyoyin samar da haraji ga kasa.
A makon da ya gabata ne shugaban hukumar kulada kwallon kafa ta duniya FIFA Gianni Infantino, ya bayyana shirin da hukumar ke yi don gudanar da bikin cika shekaru dari da fara gudanar da gasar lashe kofin duniya ta maza, daga cikin tsarin na hukumar FIFA ke yi, ta sanar da yadda za ta gudanar da gasar ta shekarar 2030. A cewar shugaban hukumar ta FIFA Gianni Infantino, a nahiyoyi 3 ne za a buga gasar da suka hada da Kudancin Amurka da Turai da kuma Afrika, inda kasashen Morokko da Spain da Portugal da Uruguay da Argentina da kuma Paraguay za su amshi bakunci. Masana harkar wasan kwallon kafa i na ganin damar da Morocco ta samu a yanzu sake bude wata kofa ce ga sauran kasashen Afrika na amsar damar karbar bakuncin gasar.
Shirin Kasuwa A Kai Miki Dole na wannan makon ya yi nazari ne kan yadda ake ci gaba da samun hau-hawan farashin kayayyakin abinci a kasashen duniya musamman nahiyar Afrika. Masana sun bayyana cewa, yakin da ake fama da shi Ukraine na daya daga cikin manyan dalilan da suka haddasa tsadar farashin abinci a kasashen duniya, yayin da matsalar ke ci gaba da kamari a nahiyar Afrika saboda karin dalilai da suka hada da hare-haren ta'addanci da suka hana manoma zuwa gona ballantana shuka da girbi.Ku latsa alamar sautin da ke kasa domin sauraren cikakken shirin tare da Ahmed Abba.
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya rattaba hannu akan wata sabuwar doka wadda zata samar da banki Wanda zai dinga baiwa dalibai rance domin biyan kudin makarantu. Masana harkar ilimi da dama sun bayyana cewar wannan sabuwar dokar zata taimaka gaya musamman ga ‘yayan marasa galihu domin samun ilimin da ya dace. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Idris Hamza Yana na Jami'ar Jigawa akai, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Shirin Kasuwa akai miki Dole tare da Ahmed Abba ya mayar da hankali kan noman albasa da tafarnuwa a jihar Sokoto ta arewacin Najeriya, jihar da ke matsayin kan gaba wajen noman albasar da tafarnuwa a kasar. Wani kalubale ga manoman na Albasa da Tafarnuwa a jihar ta Sokoto shi ne yadda ake fuskantar lalacewarta musamman a lokacin bozonta, wannan dalili ya sanya samar da wasu dabarun adana ta don kaucewa asarar da manomanta ke fuskanta.Ku latsa alamar sauti don saurarin cikakken shirin..........
La Generalitat va organitzar el passat 9 de maig un acte de reconeixement als cuidadors de senders de Catalunya. Entre ells hi ha en Xavi Masana, que en nom del Centre Excursionista de Sitges té cura dels dos senders de gran recorregut de Sitges -marcats amb les clàssiques marques blanca i vermella-, la primera etapa del GR5 entre Sitges i Olesa de Bonesvalls, i el GR92 entre el poble de Garraf i Vilanova. L'entrada Xavi Masana és des de fa 20 anys el cuidador dels senders de Gran Recorregut de Sitges ha aparegut primer a Radio Maricel.
En este nuevo Episodio del Podcast "La Hora de la Nostalgia", analizamos vida y obra del Fundador de Les Luthiers: Gerardo Masana. Formulario para inscribirse a la grabación de Septiembre: https://tinyurl.com/bp7thhuf El Podcast es conducido por Leandro Devecchi, Sebastián Padilla, Sebastián Saravia y Juan Vargas Eguinoa. Participa con nosotros, como columnista estrella, el señor Carlos Núñez Cortés Apoyá el proyecto con un café en: https://cafecito.app/lahoradelanostalgia También podés ser parte desde Patreon en: https://www.patreon.com/lahoradelanostalgia Y tenés nuestras remeras en: https://lahoradelanostalgia.flashcookie.com Si vivís fuera de Argentina, podés conseguir las remeras acá: https://lhdln.redbubble.com También podés ser parte del Foro de la Comunidad del Podcast: http://www.lahoradelanostalgia.com.ar Acordate de seguirnos en nuestro instagram: https://www.instagram.com/horadelanostalgia y en nuestros canales en YouTube y Spotify. Suscribite y dejanos tus comentarios!
Shirin Lafiya Jari ce tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan cutukan da ke tasiri a lokacin azumun watan Ramadan dama nau'ikan abincin da ya kamata masu irin cutukan su rika ma'amala da su. Shirin ya tattaro shawarwarin masana kiwon lafiya dana kwararru a bangaren abincin mai gina jiki game da abin da ya shafi nau'ikan abincin da basu da hadari da kuma wadanda ka iya ta'azzara wasu nau'ikan cuta a jikin dan adama musamman a irin wannan lokaci na azumin watan Ramadana.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin......
Shirin Ilimi Hasken Rayuwa na wannan lokaci ya tattauna da masana ne a Najeriya akan wani littafi da aka wallafa domin taimakawa wajen kula da lafiyar mata da kannan yara.
Shirin na wannan lokaci ya duba Harshen Hausa da ya kasance daya daga cikin harsuna da ke samun karbuwa da yaduwa a sassan duniya wanda hakan ya sa manyan kasashen duniya ke bude kafafan yada labarai dan isar da sakonni ga alummar da ke amfani da shi. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin da Shamsiyya Haruna ta gabatar.
Yayin da shugabannin kasashen Afirka ke kokarin ganin an samar da kyakkyawan yanayi na siyasa da ke bayar da samar zuba jari don habaka masana'antu a nahiyar, wasu ‘yan kasuwa a Jamhuriyar Nijar sun bukaci mahukuntan kasar da su yi nazari a game da dalilan da suka haddasa mutuwar masana'antun da ake da su a kasar saboda kauce wa kura-kurai a nan gaba. A game da wannan matsala da masana'antu ke fuskanta a kasar ta Nijar, Mahaman Salissou Hamissou ya zanta da Alhaji Boukari Sani Zilly, dan kasuwa kuma dan siyasa. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Majalisar Dinkin Duniya da manyan kasashe da dama cikinsu har da Amurka da Birtaniya sun yaba da rawar da kungiyar kasashen Afirka ta dauka na sasanta rikicin kasar Habasha, wanda tsohon shugaban kasar Najeriya Olusegun Obasanjo ya jagoranta a Afirka ta Kudu. Masana na bayyana cewar wannan ya dada tabbatar da cewar 'yan Afirka na iya sasanta rikicin su ba tare da sanya hannu kasashen Yammacin duniya ba. Dangane da wannan nasara, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Abbati Bako, mai sharhi akan siyasar duniya. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Barakar da aka samu tsakanin gwamnan babban bankin Najeriya da ministar kudin kasar akan shirin sake fasalin naira ya haifar da cece kuce a fadin kasar dangane da abinda ake kira banbanci tsakanin manyan hukumomin dake kula da tattalin arzikin kasar guda biyu. Masana na bayyana damuwa akan yadda baraka tsakanin wadannan hukumomi ke iya yiwa tattalin arzikin Najeriya rauni, kamar yadda darajar naira a wannan lokaci ke ci gaba da faduwa a kasuwar musayar kudade. Dangane da wannan matsala, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki, Alhaji Shuaibu Idris Mikati. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Masana harkar tsaro na bayyana daya daga cikin matsalolin dake yiwa yaki da ta'addanci tarnaki, a matsayin zagon kasar da ake samu daga wasu bata garin jami'an tsaro. Wannan matsala dai na ci gaba da haifar da tufka da warwarar da ake gani wajen yakin da kasashen Afirka ke fafatawa domin tabbatar da zaman lafiya. Dangane da wannan matsala, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon hafsan sojin Najeriya, Air Commodore Tijjani Baba Gamawa mai ritaya. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Masana a duniya sun danganta yawan ruwan saman da ake samu wanda ke haifar da ambaliya ga sauyin yanayin da ake fuskanta. Yanzu haka kasashen duniya da dama na fama da matsalar ambaliya saboda yawan ruwan saman da ake samu, cikin su harda kasashen dake Afirka ta Yamma. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin sauyin yanayi, Malam Nazifi Alaramma dake Jami'ar Jihar Kano. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
[…]
Kasashen duniya da dama, ciki harda nahiyar Afirka, ke fuskantar matsalar ambaliyar ruwa wadda ta kaiga rasa rayuka da lalata kadarori. Masana na danganta wannan matsalar da sauyin yanayi. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin da Halima Sani Jumare ta shirya
Kasashen da dama a Afirka ta yamma da na Sahel za su fuskanci ruwan sama masu yawan gaske da ambaliya ,wannan hasashe daga masana na zuwa a dai-dai lokacin da ake kawo karshen taron hukumar kulla da yanayi na kasa a Najeriya Nimet a Abuja.Nasiru sani ya samu tattaunawa da masana dangane da wannan hasashe a cikin shirin Muhalinka rayuwarka daga Rfi.
Masana tattalin arziki dai na ci gaba da yin kashedi dangane da yadda wannan yaki da ake gwabzawa tsakanin Rasha da Ukraine ke neman haifar da talauci da wasu matsaloli musamman ga kasashe masu tasowa. A yau alhamis aka cika wata hudu da shiga yakin Ukraine da Rasha,sai dai duk kokarin manyan kasashe na kawo karshen wannan rikici ya cutura. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Farfesa Kabiru Isah Dandago, masani tattalin arziki kuma malami a jami'ar Bayero da ke Kano, domin jin yadda wannan yaki ke shafar kasashe musamman na Afirka.
Shirin 'Muhallinka Rayuwarka' ya duba batun noman zamani, inda wani matashi a jihar Adamawa da ke Najeriya ya samar da masana'antar samar da madarar shanu a zamanance. Shirin ya tattauna da kwararru a wannan fannin tare da shi kansa matashin da ya yi wannan hobbasa.
Shirin Lafiya Jari Ce na wannan mako tare da Azima Bashir Aminu ya tattaunawa kan Cutar Sankarau dake addabar al'umma a Arewacin Najeriya masamman a irin wannan lokaci da yankin ke fuskanctar tsananin zafi ko kuma farkon zubar ruwan sama, yanayin da kan haddasa bullar cutuka daban-daban kama daga Sankarau, kyanda kwalara da kuma zazzabin cizon sauro wadanda a lokuta da dama kan haddasa asarar dimbin rayuka. Yau shirin ya maida hankali kan cutar Sankarau.
Shirin Lafiya Jari Ce na wannan makon tare da Azima Bashir Aminu ya tattaunawa ne kan ranar 23 ga watan Mayun da Majalsar Dinkin Duniya ta ware amatsayin ranar yaki da cutar yoyon Fitsari da nufin kawo karshen matsalar a cikin al'umma.
Vigésimo sexta transmisión en vivo del Podcast "La Hora de la Nostalgia", donde tuvimos el agrado de charlar con Sebastián Masana, que respondió preguntas de los oyentes! Recuerden que este Episodio es una bajada en audio de una transmisión en vivo, así que quizás algunas cosas puedan no ser claras para el oyente. De todos modos, pueden ver esto mismo aquí: https://www.youtube.com/watch?v=c5RIgvOEZ-4 El Podcast es conducido por Leandro Devecchi, Sebastián Padilla, Sebastián Saravia y Juan Vargas Eguinoa. Participa con nosotros, como columnista estrella, el señor Carlos Núñez Cortés Apoyá el proyecto con un café en: https://cafecito.app/lahoradelanostalgia También podés ser parte desde Patreon en: https://www.patreon.com/lahoradelanostalgia Y tenés nuestras remeras en: https://lahoradelanostalgia.flashcookie.com Si vivís fuera de Argentina, podés conseguir las remeras acá: https://lhdln.redbubble.com También podés ser parte del Foro de la Comunidad del Podcast: http://www.lahoradelanostalgia.com.ar Acordate de seguirnos en nuestro instagram: https://www.instagram.com/horadelanostalgia y en nuestros canales en YouTube y Spotify. Suscribite y dejanos tus comentarios!
En este nuevo Episodio del Podcast "La Hora de la Nostalgia", tenemos una charla profunda y emotiva con Sebastián Masana, el hijo del fundador de Les Luthiers: Gerardo Masana. El Podcast es conducido por Leandro Devecchi, Sebastián Padilla, Sebastián Saravia y Juan Vargas Eguinoa. Participa con nosotros, como columnista estrella, el señor Carlos Núñez Cortés Apoyá el proyecto con un café en: https://cafecito.app/lahoradelanostalgia También podés ser parte desde Patreon en: https://www.patreon.com/lahoradelanostalgia Y tenés nuestras remeras en: https://lahoradelanostalgia.flashcookie.com Si vivís fuera de Argentina, podés conseguir las remeras acá: https://lhdln.redbubble.com También podés ser parte del Foro de la Comunidad del Podcast: http://www.lahoradelanostalgia.com.ar Acordate de seguirnos en nuestro instagram: https://www.instagram.com/horadelanostalgia y en nuestros canales en YouTube y Spotify. Suscribite y dejanos tus comentarios!