POPULARITY
A makon da ya gabata ne dai Hukumar Ƙwallonn Kafar Afirka CAF ta gudanar da zaɓenta, inda aka sake zabar Patrick Motsepe a matsayin shugaba a karo na biyu. Bayan haka ne aka gudanar da zaɓen wakilan nahiyar a Hukumar Ƙwalllon Ƙafa ta Duniya, FIFA, inda Afirka ke da wakilai 6, har da shugaban CAF mai kujerar kai-tsaye..
A wannan makon shirin ya mayar da hankali ne kan yadda ake kara samun saukar farashin kayan masarufi a sassan Najeriya. Bayanai da muka tattaro na nuni da cewa yawancin kayayyakin da farashin su ya sauka na amfanin gona ne da kuma na kamfanonin kasashen waje, amma na kamfanonin cikin gida har yanzu suna nan a yadda suke.A makon jiya Hukumar ƙididdiga ta Najeriya NBS, ta ce an samu sauƙin matsalar hauhawar farashin kayayyakin masarufi a ƙasar da a ƙalla kashi 10.3.Cikin sanarwar da ta fitar a Talatar wancan makon, hukumar ta NBS ta ce hauhawar farashin kayayyaki a Najeriyar ya sauka ne zuwa kashi 24.4 a watan Janairun wannan shekara, saɓanin kashi 34.8 da aka gani a watan Disambar shekarar bara ta 2024.
Hukumar Ƙayyade Farashin Wutatar Lantarki a Najeriya, sanar da sabon tsarin biyan tara a kan waɗanda ke satar makamashin lantarki a ƙasar. Tarar ta kama daga Naira dubu 100 zuwa dubu 300 daidai da irin salon da mutum ya yi wajen sada gidansa da wannan makamashi.
Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa a Najeriya, ta ce farashin kayan abinci ya sauka a cikin watan Janairun da ya gabata da 10% idan aka kwatanta da na wata Disamba. To waɗannan dai bayanai da hukuma ta fitar, saboda haka za mu so jin ra'ayoyinku a game da wannan rahoto.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin tare da Abida Shu'abu Baraza...
Hukumar ƙididdiga ta Najeriya NBS, ta ce an samu sauƙin matsalar hauhawar farashin kayayyakin masarufi a ƙasar da a ƙalla kashi 10.3. Cikin sanarwar da ta fitar a jiya Talata, hukumar NBS ɗin ta ce hauhawar farashin kayayyaki a Najeriyar ya sauka zuwa kashi 24.4 a watan Janairun wannan shekara, saɓanin kashi 34.8 a watan Disambar shekarar bara ta 2024. Domin jin halin da ake ciki....la'akari da wannan rahoto, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Musa Idris daga jihar Jigawa, magidanci kuma ɗan kasuwa.Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu..........
SHirin na wannan ya mayar da hankali ne akan ƙarin kuɗin kira da damar shi internet wato Data, da kmafnonin sadarwa suka yi a Nijeriya. Bayan da Hukumar dake kula da kamfanonin sadarwa NCC ya amince. Sai a latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin.
Kamar yadda labari ya karaɗe kafafen yada labarai, ƙaasa da mako guda bayan da hukumar kwastan a Najeriya ta sanar da buɗe shafin yanar gizo don aikewa da takardun neman ɗaukar jami'ai kimanin dubu 4, sama da masu neman wannan aiki dubu dari 5 ne suka gabatar da buƙatunsu. Wannan al'amari ne da ke faruwa a kowace ma'aikata a duk lokacin da aka sanar da buƙatar ɗaukar ma'aikata.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Abida Shu'aibu Baraza.
Shirin Duniyar Wassani a wannan makon ya yi duba ne game da kyautar gwarzon ɗan wasan Afrika da aka bayar. A ranar Litinin din da ta gabata ne dai Hukumar da ke kula da kwallon ƙafar nahiyar Afrika wato CAF, ta bayar da kyautar gwarzon nahiyar Afrika wanda yafi bajinta a wannan shekarar da muke bankwana da ita. Ɗan wasan gaba na tawagar Super Eagles ta Najeriya Ademola Lookman ne ya samu nasarar lashe wannan kyauta, biyo bayan irin bajintar da ya nuna ga ƙasar da kuma ƙungiyarsa ta Atlanta. Samun nasarar lashe wannan kyauta da ɗan wasan yayi dai ta sanya zamowa cikin jerin ƴan wasa 6 na Najeriya da a tarihi suka taɓa lashe ta.Ku latsa alamar sauti don jin cikakken shirin tare da Khamis Saleh........
Hukumar da ke kula da al'adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta UNESCO ta damƙawa Najeriya takaddar shaidar sanya bikin hawan Daba na Kano cikin manyan al'adun duniya masu matukar tasiri. Jim kaɗan bayan kammala miƙa shaidar wakilinmu a Abuja Isma'il Karatu Abdullahi ya tattanna da ministar al'adu ta Najeriya Hajiya Hannatu Musawa kan tasirin da wannan zai yi wa ƙasar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar ta su......
Shirin Mu Zagaya Duniya na wannan mako tare da Nura Ado Sulaiman kamar ko yaushe ya yi duba kan muhimman labaran da suka faru a makon da ya gabata, ciki kuwa har da batun yadda Hukumar Kula da Al'adu ta Majalisar Dinkin Duniya UNESCO, ta sanya hawan Dabar jihar Kano dake Najeriya cikin manyan Al'adun Duniya masu dimbin Tarihi.Da kuma sauran rahotanni da suka gabata.Sai a latsa alamar sauti domin samun cikakken shirin.
Hukumar ƙididdiga ta Najeriya NBS, ta ce tattalin arzikin Najeriya ya bunƙasa da kashi 3.46 a rubu'i na uku na wannan shekarar ta 2024, wato tsakanin watan Yuli zuwa Satumba. A rahoton da ta fitar ranar Litinin, NBS ta ce yawan masara aikin yi ma ya ragu a Najeriya. Kan haka ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki Dr Kasum Garba Kurfi.
Shirin Duniyar Wasanni a wannan makon ya yi duba ne kan irin gudummawar da cibiyoyin horar da matasa wasan kwallon ƙafa ke bayarwa wajen zakulo matasan ƴan wasa da horar da su a Nigeria. Wannan dai wani bangare ne na gudummawarsu ga ci gaban wasan kwallon ƙafa a Nigeria, tsofin ƴan wasan tawagar Super Eagles na ƙasar, sun fara kafa cibiyoyi masu zaman kan su, da su ke zakulowa tare da horar da matasa don yin fice a harkar ta kwallon kafa. Irin wadannan cibiyoyin horar da matasa wasan na kwallon kafa da a turance ake kira Football Academy, kan shiga birane da karkara don tuntubar ƙanana da matsakaitan club-club, domin samun ƴan wasan daga wajen su da za a yi rijistarsu a wannan cibiya.Pascal Patrick, tsohon ɗan wasan Super Eagles kuma shugaban Hukumar kwallon kafa ta NFA a jihar Bauchi kana co-odinetan tawagar Super Eagles na Nigeria, na daya daga cikin tsofaffin ƴan wasan ƙasar da suka kafa irin wannan cibiya a jihar Bauchi.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh.......
Shirin ‘Muhallinka Rayuwarka' da ke nazari kan abin da ya shafi muhallli, canjin yanayi, noma da kiwo, ya yi tattaki zuwa Kamaru, inda ya duba shirin tallafa wa manoma wajen noman dawa mai jure fari da kasa mara kyau. Hukumar kula da samar da albarkatun gona a arewacin Kamaru IRAD ce ke jagorantar aiwatar da shirin na sake fasalin bunkasa noman dawa 'yar rani, wato moskowari.
A dai-dai lokacin da ake ci gaba da shirye-shiyen wasannin sharen fagen samun gurbi a gasar lashe kofin Afrika, Hukumar Kula Ƙwallon kafar Afrika CAF ta ce filayen wasan ƙasar Ghana ba su da ingancin da ya kamata a ce an gudanar da manyan wasanni na kasa da kasa a cikin, matakin da ke kara nuna gazawar ƙasar. Ita dai hukumar CAF ta ce ba komai ya sanyata daukar wannan mataki ba, face yadda ta ce aƙwai rashin wadatatciyar ciyawa da rashin magudanun ruwa da dai sauransu a filin wasa na Baba Yara da ke birnin Kumasi, haka ta ce abin ya ke a sauran filayen wasanni irin na Cape Coast da kuma na Accra.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh......
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasashen Afirka ta Yamma, wato GIABA ta shirya wani taron fadakar da 'yan kasuwa da masu masana'antu da kuma lauyoyi a kan hakkin da ya rataya a kansu na kin bada dama ga masu halarta kudaden haramun ko kuma 'yan ta'adad su yi amfani da su wajen boye kudaden sata. Taron na kwanaki 2 na gudana ne a birnin Lagos. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai magana da yawun GIABA Mr Timothy Melaye, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Shirin namu na wannan mako zai yi dubi ne kan yadda hukumar kula da harkar jarabawan shiga jami'o'i a Najeriya wato JAMB da hadin guiwan kungiyar zabiya na kasa ta shirya taron nahiyar Afrika na farko kan baiwa nakasassu ko masu larura ta musamman dangane da harkar ilimi kamar kowani dan adam. Taron an shirya shi ne dai la'akari da irin kalubalen da masu larura ta musamman ke fama da ita a kasashe masu tasowa kamar Najeriya,kama daga kyama,nuna musu banbanci da dai sauransu.
Hukumar tara kudaden haraji a Najeriya tace masu masana'antu a kasar sun yi asarar kudin da ya kai kusan naira triliyan 2 bara sakamakon faduwar darajar naira. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Hukumar kididdiga ta kasar ke cewa ma'aikata dubu 30 ne suka rasa ayyukansu saboda durkushewar ma'aikatun da suke aiki. Dangane da wanan labarai mai tada hankali, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ahaji Ali Madugu, mataimakin shugaban kungiyar masu masana'antu a Najeriya. Kuna iya latsa alamar sauti domin jin yadda zantawar ta su ta gudana...
Shirin na wannan mako ya mayar da hankali ne kan karuwar matasan da basa zuwa makaranta a Ghana. Hukumar kididdiga ta kasar GSS ta gano cewa kusan matasa miliyan biyu ne ba sa karatun Boko ko aikin yi ko kuma samun horon sana'o'in dogaro da kai.Ku danna alamar saurare don jin cikakken shirin tare da Abdulkadeer Haladu Kiyawa.
Hukumar Yaƙi da Cututuka Masu Saurin Yaɗuwa a Najeriya, ta ce kawo yanzu adadin waɗanda suka kamu da cutar Amai da gudawa wato Cholera sun kai dubu 1 da 579, kuma tuni 54 daga cikinsu suka riga mu gidan gaskiya. Hukumar ta yi gargaɗi ga jama'a da su kiyaye ta hanyar ɗaukar matakan kariya, domin kuwa tuni cutar ta shiga jihohi 32 na ƙasar.Waɗanne irin matakai mahukunta ke ɗauka a yankunanku domin hana yaɗuwar wannan cuta?A naku ɓangare, waɗanne matakai ku ke ɗauka domin kare kanku?Kuri ka aiko mana da ra'ayoyinku a lambarmu ta WhatsApp +234 70 66 35 66 41 da kuma shafinmu na Facebook.
Shirin 'Tambaya Da Amsa' wanda ya ke zuwa duk mako a wannan tasha zai amsa tambayar da ke neman bayanni a kan ayyukan Hukumar Lafiya ta Duniya,,musamma inda take samun kuɗaɗen gudanar da ayyukanta da kuma yadda taa ke ɗaukar ma'ikata.
Daga cikin labarun da shirin karshen makon ya waiwaya akwai neman tsohon gwamnan jihar Kogi yahya Bello da hukumar EFCC ke yi ruwa a jallo, lamarin da ya kai ga daukar matakin dakile duk wani yunkurinsa na ficewa daga Najeriya Shirin ya kuma leƙa gabas ta tsakiya inda Iran ta ƙi fusata kan makamai masu linzamin da na'urorin tsaron sararin samaniyarta suka kakkaɓo a birnin Isfahan, waɗanda wasu majiyoyi suka ce Isra'ila ce ta yi yunkurin kai mata hari da su.
‘Tambaya Da Amsa' shiri ne da ke kawo amsoshin tambayoyin da wasu daga cikin masu sauraronmu suka aiko mana. Bayan janye tallafin lantarki a Najeriya, hukumar samar da wutar ta yi bayani game da rukunnai dabam dabam na masu amfani da wuta da abin da za su biya a matsayin kudin wuta. A yi mun ƙarin bayani a kan wadannan rukunnai. Menene ya sa dole sai an kasa al'umma zuwa rukuni -rukuni?
Hukumar alhazai a Najeriya, ta sanar da karin kusan Naira milyan biyu a kan kujerar aikin hajjin bana ga maniyatan da suka riga suka zuba kudadensu. Wannan dai mataki ne da ya yi matukar bai wa jama'a mamaki, tare da kara haifar da fargar cewa dubban maniyata ba za su iya sauke faralin na shekarar bana ba.Abin tambayar shine, wane tasiri wannan mataki zai yi a kan maniyatan Najeriya na shekarar bana?Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.
A wannan Juma'a ake kammala yakin neman zaben shugaban Senegal, kasar da rikicin siyasa da ya auku a cikinta a baya-bayan nan ya gaza yin mummunan tasiri a kanta duk kuwa da jan hankalin duniya da lamarin ya yi. Hukumar zaben kasar ta ce kimanin mutane miliyan 7 ne suka yi rajistar kada kuri'a a zaben da ‘yan takara 19 suka raba rana.Masu sharhi da dama sun lura da yadda duk da rikice-rikicen siyasa da suka taso ba a samu wani tashin hankali da ya taka wa shirin zaben birki ba.Kan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da Dakta Mukhtar Bello, malami a bangaren kimiyyar siyasa a jami'ar Bayero da ke Kano a Najeriya.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Gwamnatin Najeriya ta bayyana aniyarta ta samar da hukumar da zata dinga daidaita farashin kayan masarufi kamar yadda aka saba yi a shekarun baya, wanda ake kira 'Commodity Board', sakamakon kiraye kirayen 'yan kasar ganin yadda 'yan kasuwa ke cin karen su babu babbaka. Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya sanar da haka wajen wani taro a Abuja. Dangane da tasirin wannan mataki, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin harkar noma, Farfesa Mohammed Khalid Othman na Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
Shirin wannan mako zai yi dubi ne yadda Hukumar da ke kula da harkokin hasashen yanayi ta Nigeria, ta yi hasashen samun wani gagarumin sauyin yanayi a yankunan arewa maso gabas da arewa ta tsakiya cikin ‘yan kwanaki masu zuwa. Bugu da kari hukumar, ta bayyana cewa shima yankin kudancin Nigeria zai shiga yanayi na zafin rana da wasu alamun hadari, kana yankunan da ke kusa da ruwa, za su shiga yanayi na hazo da ganin alamun hadari. Jihohin kudancin Nigeria irin su Lagos, Delta, Rivers da Bayelsa, ana sa ran samun yanayin hadari da tsawa a wadannan kwanaki.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Nasiru Sani ............
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya ta sake bude wani sabon babin bincike a kan wasu tsoffin gwamnoni da ministoci 13 da take zargi da aikata laifukan almundahana na sama da naira biliyan 853 da miliyan 800. Wannan na zuwa ne jim kadan bayan da gwamnatin kasar ta dakatar da wata minister da aka zarga da karkata akalar wasu makudan kudade, tare da kaddamar da bincike a kanta.A kan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da Awwal Musa Rafsanjani n kungiyar farar hula ta CISLAC a Najeriya.
Hukumar bada agajin gaggawa ta Najeriya reshen shiyar Arewa maso yamma, ta ce mutane 85 ne suka rasa ransu a harin bom din da sojoji suka kai, sannan akwai wasu 66 da ke samun kulawa a asibiti. Mafi yawan wadanda lamarin ya shafa dai mata ne da kananan yara da kuma dattijai a lokacin da suke gudanar da Mauludi, a kauyen Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi da ke Jahar Kaduna.'Yan Najeriya na ci gaba da cece-kuce kan wannan ibtila'i da ba wannan ne karon farko da yake faruwa akan fararen hula ba.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.
‘Yan Najeriya na ci gaba da bayyana damuwa a kan yadda kotuna ke karbe hurumin da kundin tsarin mulki ya bai wa Hukumar zabe na bayyana wadanda suka samu nasarar zabubbukan da jama'a suka yi, wajen bayyana wasu daban a matsayin halartattun wadanda suka yi nasara. Wannan ya biyo bayan yadda kotunan suka sauya sunayen wadanda hukumar zabe ta sanar sun samu nasara a zabbubukan gwamnoni da kuma ‘yan majalisun kasar. Ko a wannan mako, kotuna sun soke zabubbukan gwamnonin Zamfara da Kano, yayin suka tabbatar da na jihohin Lagos da Bauchi. Dangane da wannan korafi, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hajiya Naja'atu Muhammad, ‘yar siyasa, kuma mai sharhi akan harkokin Najeriya.Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Hukumar Kula da Gidajen Gyara Halinka a Najeriya, ta ce akalla fursunoni dubu 5 ne aka yanke wa hukuncin kisa, abin da suke jira kawai shi ne zartarwa. Hukumar ta ce an gaza zartar da hukuncin ne saboda rashin samun sahlaewar gwamnonin jihohi ko kuma wasu hukumomi da ke da alhakin rattaba hannu kafin zartarwar. Shin yaya kuke fatan ganin an bullo wa wannan lamari domin rage cunkoson gidajen yari a Najeriya? Shin ko kuna goyon bayan aiwatar da hukuncin kisa a kasashenku ko kuma sauya irin wannan hukunci zuwa na dauri? Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayiyin jama'a a kan wannan maudu'in.
Hukumar da ke kula da kwallon kafa a Najeriya ta NFF ta dakatar da wasu alkalan wasan da ke busa gasar firimiya league su 14 daga aiki, saboda abinda ta kira kura kuran da suka tafka wajen gudanar da alkalancin wasannin da ke gudana a wannan kaka. Irin wadannan kura kurai na daga cikin dalilan da suka saka hukumar kwallon kafa ta Afirka wato CAF kan tsallake alkalan wasan Najeriya lokacin zabo wadanda za su busa wasannin Afirka. Ko gasar da za a gudanar a Abidjan shekara mai zuwa, babu alkalin wasa koda guda daga Najeriya. A kan wannan ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da shugaban alkalan wasan Najeriya, Malam Zubairu Sani.Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tasu....
Hukumar kula da hasashen yanayi ta tarayyar Nigeria NIMET, ta ankarar da mazauna wasu jihohin arewacin kasar dangane da mamakon ruwan saman da ake sa-ran zubawa nan da ‘yan kwanaki masu zuwa. A cewar hukumar, wacce kan yi hasashen yadda yanayi zai kasance a kasar, tuni na'urorinta suka hango alamomin tsawa da walkiya a yankunan jihohin Borno, Taraba, Gombe, Bauchi da kuma Kano.Wannan hasashe na zuwa ne yayinda har yanzu, wasu al'ummomin kasar, ba su gama farfadowa daga barnar da ambaliya ta yi musu a daminar bara ba.
Kamar yadda aka saba, shirin 'Tambaya Da Amsa' tare da Michael Kuduson na zuwa muku ne duk mako da amsoshin tambayoyin da wasu daga cikin masu sauraronmu suka aiko mana. Daga cikin taambayoyin da aka amsa a shirin wannan makon, har da karin bayani kan yadda hukumar kididdiga ke aikinta masamman na tattara farashi.
Hukumar bada agajin gaggawa ta Najeriya NEMA, ta ce sun fara tattaunawa da mahukuntan kasar Masar a birnin Alkahira, kan yadda za a kwaso daliban kasar daga Sudan, yayin da bangarori biyu ke ci gaba da gwabza yaki a kasar da ke Gabashin Afirka. Wannan ya zo ne, bayan da dubban dalibai 'yan Najeriyar da ke karatu a Sudan suka mika koken su ga gwamnatin kasar, game da mummunan yanayin da suke ciki, saboda tashe-tashen hankula a Khartoum, babban birnin ƙasar.Sojojin gwamnati da kuma dakarun RSF sun shafe sama da mako guda suna rikici da juna, lamarin da ya jefa fararen hula da dama cikin mummunan yanayi.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin da Shamsiyya Haruna ta gabatar.
Hukumar sa-ido game da yadda ake hada-hadar kudade a Najeriya wato NFIU, ta ce daga ranar 1 ga watan Maris mai zuwa Gwamnatin Tarayya, jihohi da kuma kananan hukumomi, ba su da izinin fitar da tsabar kudi daga asusun ajiyarsu, amma suna da hurumin yin hakan daga bakin zuwa. A cewar shugaban hukumar ta NFIU Modibbo Tukur, ya ce wadanda suka karya wannan ka'ida za su iya fuskantar hukuncin daurin shekaru 3 a gidan yari. Domin jin tasirin wannan tsari, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Kasimu Garba Kurfi, shugaban cibiyar hada-hadar hannayen jari na APT Securities and Fund Ltd da ke Lagos, ga kuma zantawarsu.
Hukumar kula da afuwa a Najeriya ta bukaci rundunar ‘yan sandar kasar ta dauki tubabbun ‘yan tsagerun yankin Neja Delta aikin dan sanda, don taimakawa wajen samar da tsaron kasa. Shugaban hukumar, Janar barry Ndiomu ne ya mika wannan bukata, wanda ke zuwa a daidai lokacin da sufeto janar na ‘yan sandan kasar, Usman Baba Alkali ke korafin cewa kan yadda matasa daga yankin Neja Delta ba sa iya cika gurbin da aka ware musu a lokacin dibar sabbin ‘yan sanda. Kan haka ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauanwa da Muhammad Wakili tsohon kwamishinan 'yan sanda.
Yau aka shiga rana ta 5 a gasar cin kofin duniya da ke gudana a kasar Qatar, inda ake ci gaba da fafatawa da kuma samun sakamako masu bada mamaki. Wannan na zuwa ne bayan korafe-korafen da suka biyo bayan shirin daukar nauyin gasar da kuma barazanar da wasu kasashen yammacin duniya suka yi na kauracewa wasannin. Dangane da yadda wasannin ke gudana, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin harkar kwallon kafa, Hon Sani Ahmed Toro, tsohon Sakatare Janar na Hukumar kwallon kafar Najeriya. Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu.
Hukumar EFCC mai yaki da rashawa a Najeriya kaddamar da bincike dangane da aikin gida cibiyar samar da wutar lantarki ta Mambilla wadda aka ware dala bilyan 6 domin ginawa. A lokacin da yake karba tambayoyi a gaban kwamitin hadin-gwiwa mai kula da harkar wutar lantarki na majalisun tarayyar kasar, ministan wuta ya tabbatar da cewa duk da irin makudan kudaden da aka ware, amma har yanzu ba wani aikin da aka yi a wurin. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.
Shirin ya maida hankali ne kan zaben sabbin shugabannin gudanarwar hukumar kwallon kafar Najeriya wato NFF, da ya gudana makon jiya a birnin Benin na jihar Edo da ke kudancin kasar, inda aka zabi Alhaji Ibrahim Musa Gusau a matsayin sabon shugaba, bayan karewar wa'adin Mr Amaju Pinnick wanda ya kwashe tsahon zango biyu yana shugabancin hukumar.
Ganin irin gagarumar nasarar da Hukumar NDLEA dake yaki da masu mu'amala da miyagun kwayoyi keyi a Najeriya, Majalisar zartarwar kasar ta amince da a baiwa hukumar sama da naira miliyan 580 domin sayen motocin soji dan ci gaba da yakin da suke yi. Wannan na zuwa ne kasa da mako biyu da Hukumar ta kama hodar ibilis a Lagos da kudin sa ya zarce sama da naira biliyan 193. Dangane da nasarorin da Hukumar ke samu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Alhaji Muhammadu Awwal, daya daga cikin masu sanya ido akan yaki da miyagun kwayoyin a Najeriya. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Hukumar lafiya ta duniya tace cututtukan da basa yaduwa irin su bugun zuciya da shanyewar wani bangare na jiki da sarkewar numfashi da sankara da kuma hawan jini na kashe mutane akalla miliyan 41 kowacce shekara, sabanin cututtuka masu yaduwa da a baya suka fi kashe mutane. Rahotan binciken da Hukumar ta gudanar yace a kowanne dakika 2, mutum guda dake kasa da shekara 70 na mutuwa sakamakon irin wadannan cututtuka, kuma kashi 86 na masu mutuwar na fitowa ne daga kasashe matalauta ko kuma masu tasowa. Dangane da wannan rahoto, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Balarabe Sani Garko, na Jami'ar Ahmady Bello dake Zaria. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Ganin yadda ake ci gaba da ruwan sama ba tare da kaukautawa ba, da kuma yadda ruwan ke haifar da matsalar ambaliya, Hukumar bada agajin gagggawa a Najeriya ta NEMA, ta aike da sakon gargadi ga jihohi 14 wadanda ta bayyana cewar a kwanaki masu zuwa zasu fuskanci matsalar ambaliya. Hukumar ta kuma gargadi mazauna gefen kogin dake fitowa daga Kamaru a Najeriya da su shirya domin gwamnati zata bude madatsar ruwan Labdo, wanda shima ke tattare da hadari. Dangane da wannan gargadi, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Aminu Muhammed, shugaban Hukumar bada agajin gaggawa a jihar Adamawa. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Ana ci gaba da cece-kuce a Najeriya kan yadda ake zargin Hukumar Kula da Kudaden Fansho wato PENCOM da biyan kowanne ma'aikacinta albashin akalla Naira miliyan 2 da dubu 400 a kowanne wata. Wani faifan bidiyo ya nuna yadda shugabar hukumar A'isha Dahiru Umar ta gaza kare kanta kan wannan batu a gaban Majalisar Wakilan kasar. A game da wannan al'amari, Abdurrahman Gambo Ahmad ya tattaunawa da Dr. Kabiru Danladi Lawanti, malami a Jami'ar ABU da ke Zaria.
Yau ake kammala taron Hukumar kare hakkin Bil Adam ata Majalisar Dinkin Duniya a Geneva, wanda yake tattauna batutuwan da suka shafi kare hakkin Bil Adama a kasashen duniya daban daban. Taron na kwanaki 3 ya samu halartar wakilai daga sassan duniya. Dangane da wannan taro, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Kalla Muntari, dan Majalisar dokoki kuma shugaban kwamitin kula da walwalar 'yan kasa a Jamhuriyar Nijar. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Hukumar UNESCO ta bayyana jerin kasashen da akafi samun yaran da basa zuwa makaranta a Duniya, inda ta saka Najeriya a matsayi ta 3, bayan Pakistan da Afghanistan. Alkaluman hukumar sun nuna cewar yara miliyan 20 ne yanzu haka basa zuwa makaranta a Najeriya. Ganin girmar wannan matsala, Bashir Ibrahim Idris ya zanta da Farfesa Peter Lassa, tsohon shugaban Hukumar kula da manyan kwalejojin ilimi a Najeriya, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
Hukumar zaben Kenya ta bayyana mataimakin shugaban kasar William Ruto a matsayin wanda ya yi nasarar lashe zaben shugabancin kasar da aka yi ranar talatar. Ruto dai ya doke Rahila Ondiga ne wanda ya tsaya neman shugabancin kasar har sau biyar ba tare da ya nasara ba, duk da cewa a wannan karo ya samun goya bayan shugaban kasar mai ci Uhuru Kenyatta. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin
Hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa a Najeriya ta bayyana samun karin mutanen dake harbuwa da cutar monkeypox ko kuma kyandar biri, inda tace a makon jiya, mutane 24 aka tabbatar sun harbu da cutar. Hukumar ta bukaci mutane da su kiyaye wajen kaucewa kamuwa da ita. Farfesa Kabir Sabitu, na Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria, yayi bayani akan matakan kare kai daga kamuwa da wannan cuta. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
'Yan Najeriya na ci gaba da mayar da martani dangane da faifan bidiyon da ke nuna yadda 'yan bindiga ke dukan mutanen da suka yi garkuwa da su da kuma barazanar da shugaban su ke yi na kaiwa shugaban kasa Muhammadu Buhari da Gwamnan Kaduna Nasir El Rufai hari. Wannan hari ya tayar da hankalin jama'ar kasar da kuma tausayawa mutanen da ake garkuwa da su sama da watanni 4 da suka gabata. Dangane da wannan bidiyo, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hajiya Naja'atu Muhammad, kwamishiniya a Hukumar kula da ayyukan 'yan sandan Najeriya, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
A karo na 2 a cikin wata guda ake samun katsewar wutar lantarki a fadin Najeriya sakamakon lalacewar wutar baki daya wanda kuma ya durkusar da ayyukan jama'a. Hukumar kula da hasken lantarkin ta kasa tace an samu lalacewar wutar ce ranar Laraba da misalin karfe 12 na rana, wanda shine irin sa na 5 da aka gani a cikin wannan shekara. Dangane da wannan matsala, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Comrade Musa Ayiga, tsohon jami'in hukumar PHCN a Najeriya, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
Hukumar Bada lamuni ta Duniya IMF ta gargadi Najeriya cewar yadda kudaden shigar kasar ke raguwa da kuma basukan da take ci, daga shekarar 2026 kasar zata koma amfani da kudaden harajin da take tarawa wajen biyan kudin ruwan bashin da ta ciwo. Jami'in Hukumar a Najeriya Ari Asien ya kuma bayyana cewar ganin yadda gwamnatin kasar ke kashe naira biliyan 500 kowanne wata a matsayin tallafin man fetur, tallafin na iya kaiwa naira triliyan 6 a karshen wannan shekara. Dangane da wannan gargadi, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Isa Abdullahi, masanin tattalin arziki a Jami'ar Kashere. Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu.
Hukumar kula da tsara jarrabawar kammala karatun sakandare ta afrika ta yamma WAEC ta bayyana cewan jihohin Sokoto da Zamfara a tarayyar Najeriya ba su biyawa yara a makarantun gwamnati kudin rubuta jarabawan karshe ta bana da za a fara ranar 16 ga wannan wata ba. Shekara ta biyu kenan a jihar Sokoto yara basa iya samun zarafin rubuta jarabawar WAEC makarantun gwamnati. Kan hakan Mohammed Sani Abubakar ya zanta da kwamishinan ilimin bai daya na jihar Mohammad Bello Abubakar ga kuma zantawarsu.
Hukumar Kula da Ayyukan Sadarwa a Najeriya, ta bayyana sunayen kamfanoni biyu wato MTN da kuma Mafab a matsayin wadanda suka cancanci fara aiki da sabuwar fasahar sadarwa ta 5G a kasar. Hukumar ta NCC, ta bayyana 24 ga watan Agustan wannan shekara a matsayin ranar da kamfanonin za su fara amfani da sabuwar fasahar. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Adamu Garba, na kamfanin IPI Solutions Group wanda yak ware a fannin ayyukan sadarwa, wanda da ya fara da yi masa bayani game da abin da ake nufin 5G.
Hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi a Najeriya wato NDLEA, ta bukaci a fara yi wa masu neman tsayawa takarar neman wasu mukaman siyasa ciki har na shugaban kasar gwaji domin tabbatar da cewa ba sa mu'amala da miyagun kwayoyi. Shugaban hukumar ta NDLEA Janar Buba Marwa mai ritaya ne ya bukaci a fara wannan gwaji a wasikar da ya aika wa jam'iyyun siyasar kasar. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Sule Ammani Yari, mai bin diddigin lamurran siyasar kasar domin jin yadda yake kallon wannan shawara da NDLEA ta gabatar.
Hukumar 'yan sandan farin kaya ta DSS a Najeriya, ta bayyana gano shirin kai hari akan wuraren ibada da wuraren shakatawa da kuma wasu kadarorin gwamnati musamman lokacin bikin Sallah da bayan sa. Mai Magana da yawun Hukumar Peter Afunanya ya bayyana haka a sanarwar da ya rabawa manema labarai, inda yake zargin mutanen cewar suna shirin mayar da kasar irin halin da ta samu kanta kafin shekarar 2015 inda ake samun fashe fashen makamai. Dangane da wannan gargadi Bashir Ibrahim Idris ya ttauna da masanin harkar tsaro Malam Yahuza Getso, kuma ga yadda zantawar su ta gudana
Shirin Muhallinka Rayuwarka na wannan mako tare da Nasiru Sani ya maida hankali ne sanarwar da Hukumar kula da yanayi ta Najeriya NIMET ta yi na gargadi dangane da yanayin zafi da za'a fuskanta a Najeriya musaman jihohin arewacin kasar.
Shirin Duniyar wasanni na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya mayar da hankalin kan dambarwar rikicin shugabancin da ya dabaibaye hukumar kula da gasar Polo a Najeriya, Ayi saurare Lafiya.
Hukumar kwallon kafar Afrika ta sanar da dage haramci da ta yi na soke wasanni a filin wasa na Olembe biyo bayan mutuwar mutane 8 da aka samu ranar litinin 24 ga watan janairu 2022. Masar ta yi waje da kungiyar Morrocco da ci 2 da 1, wasar da aka bayyana cewa an baiwa hammuta iska tsakanin yan wasan na Masar da Morrocco jim kadan da kammala ta ,bayan da yan wasan suka fice daga fili. Kungiyar kwallon kafar Sanegal ta samu tsallakawa mataki na ga ba ,bayan doke kungiyar kwallon kafar Equatorial Guinee da ci 3 da 1,Sadio Mane da abokanin tafiyar sa za su kara da kungiyar kwallon kafar Burkina Faso ranar laraba. A bangaren kungiyar kwallon kafar Burkia Faso,mai horar da wannan kungiya mai suna Kamou Malo,da samun nasara a faffatawa da kungiyar Tunisia,ya na mai cewa al'amari ne yan kasar ga baki, jajircewa da juriya suka yan wasan ga samun wannan nasara,abin farin ciki ne ga Burkina Faso. Abdurahamane Gambo daga Yaounde ya hada mana shirin Duniyar wasanni.
Hukumar Yaki da cututtuka a Najeriya ta tabbatar da cewar kasar ta fada zagaye na 4 na annobar korona, yayin da ake ci gaba da samun hauhawar masu harbuwa da cutar kowacce rana. Hukumar ta bayyana jihohin Lagos da Rivers da Abuja a matsayin inda aka fi samun yawan masu harbuwa da ita. Dangane da wannan matsalar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr. Abdu Misau na Jami‘ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi. Ku latsa alamar sauti domin saurare cikakkiyar hirarsu
Hulumar kwallon kafar Najeriya NFF ta sallami Gernot Rhor mai horar da kungiyar kwallon kafar Super Eagles. Sallamar dake zuwa a wani lokaci da ya kasa kawo sauyi a tafiyar kungiyar ga baki daya. a cikin shirin Abdurahaman Gambo Ahmad ya ji ta bakin ma'abuta kwallon kafa da kuma irin fatan su bayan nadin sabon mai horar da Super Eagles a cikin shirin Duniyar wasanni.
Sharhi a kan babban labarin Jaridar LEADERSHIP ta yau Laraba 14/10/2021
A cikin shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' Bashir Ibrahim Idris ya kawo yada hukumar sadarwar Najeriya ta tashi tsaye don magance dukkannin matsalolin da ke addabar bangaren.
Cikin shirin Tambaya da Amsa na wannan makon tare da Michael Kuduson, za ji karin bayani kan ko wata hukumar tsaron wata kasa na da damar ta bukaci a mika mata wani mai laifi daga wata kasar da take zargi, kamar yadda FBI ta nemi a mika mata shahararren dan sandan nan na Najeriya Abba Kyari.
Shirin 'Lafiya Jari Ce na wannan mako tare da Azima Bashir Aminu ya duba fagabar da al'umma a Najeriya suka shiga sakamakon sake bayyanar cutar Polio ko Shan'inna a wasu sassan kasar, shekara guda bayan da Hukumar lafiya ta Duniya ta wanke kasar daga wannan cuta.
Shirin 'Mu Zagaya Duniya' a wannan makon ya soma da waiwaye ne kan shirin hukumar kare hakkin dan Adam ta Majalisar Dinkin Duniya na soma bincike kan zargin sojojin Isra'ila da aikata laifukan yaki yayin hare-haren da ta kaddamar kan birnin Gaza tsawon kwanaki 11 a cikin watan Mayu na wannan shekara.
Shirin 'Tambaya da Amsa a wannan makon yana dauke da amsoshin wasu daga cikin tambayoyin masu saurare ciki har da neman karin bayani kan mukamin sojoji na Field Marshal da kuma matakan da ake bi kafin samun mukamin.
Shirin Duniyar Wasanni na wannan makon ya yi nazari kan zaben hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afrika CAF da ake tunkara.
Shirin Kasuwa akai Miki Dole na wannan mako tare da Ahmed Abba ya maida da hankali ne kan nadin da Hukumar Kasuwanci ta Duniya WTO ta yi wa Dakta Ngozi Okonjo Iweala a matsayin shugabanta, Mace ta farko bakar fata kuma 'yar Najeriya da ta taba darewa Kujerar a tarihi.
Hukumar kididdiga ta Najeriya ta bayana cewa kasar ta fita daga masassarar tatalin arziki da ta fada a shekarar data gabata. Dr Isah Abdullahi. Masani tatalin arziki ne a Najeriya ya gana da Usman Ibrahimm Tunau a kan lamarin.
Kalaman Ministan tsaron Najeriya cewar 'yan kasar su kare kan su daga hare haren Yan bindiga ya haifar da cece kuce a fadin kasar. Wannan na zuwa ne bayan sace daliban kwalejin sakandaren Kagara da Yan bindiga suka yi jiya. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hajiya Naja’atu Muhammad, kwamishiniya a Hukumar kula da ayyukan 'yan Sandan Najeriya, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
Gwamnatin Jihar Niger dake Najeriya ta sanar da rufe daukacin makarantun kwanan dake kananan hukumomi 4 dake Jihar sakamakon kashe wani dalibi da kuma sace wasu da dama a makarantar Sakandaren Kagara da ‘yan bindiga suka yi da asubahin ranar Laraba 17 ga watan Fabarairu. Gwamna Abubakar Sani Bello ya bayyana Kananan hukumomin da umurnin ya shafa da suka hada da Kagara da Munya da Mariga da kuma Shiroro. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Musa, jami’in yada labaran karamar hukumar Kagara.
Shirin Ilimi hasken rayuwa tare da Bashir Ibrahim Idris ya duba yadda hukumar shirya jarabawar BAC ta OBM a jamhuriyyar Nijar ta samar da wasu tarin sauye-sauye ga daliban da za su zauna jarabawar a bana.
Hukumar tsaron FBI a Amurka ta ce Magoya bayan Donald Trump na shirin gudanar da zanga-zanga a wasu jihohin kasar 50. Bayan tsige Shugaba Donald Trump na Amurka da majalisar wakilan kasar ta yi jiya laraba, a yanzu haka masu ruwa da tsaki game da dorewar siyasar kasar sun maida hankula ne wajen samun nasarar rantsuwar kama aiki na sabon Shugaba Joe Biden. Jamian tsaron kasar dai sun karfafa matakan tsaro don gudun kada a mamaye su. Majalisar wakilan kasar dake da rinjayen ‘yan jam’iyar Democrat ta kada kuri’ar amincewa da tsige shugaban, a karo na 2, kuma irinsa na farko a tarihi da yawan kuri’u 232 a kan 197 na wakilan dake goyon bayansa. A zauren majalisar, ‘yan jam’iyyar Republican 10 ne suka goya wa takwarorinsu na Democrat baya, cikinsu har da kusa a jam’iyyar, Sanata Liz Cheney. An zargi hamshakin attajiri, kuma shugaban Amurka mai barin gado, mai shekaru 74 wanda zai mika ragamar mulki a ranar 20 ga wannan wata na Janairu, da tunzura masu zanga zangar da suka mamaye majalisar dattawan kasar a ranar 6 ga wata domin hana tabbatar da zaben Joe Biden mai shekaru 78, al’amarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 5, ya kuma zubar da mutuncin demokradiyar Amurka. Garba Aliyu Zaria ya tuntubi Farfesa Khamilu Sani Fagge na Jamiar Bayero dake Kano don jin yadda yake kallon dambarwar siyasar Amurkan.
A yayinda Gwamnatin Najeriya ta dage wajen ganin an samar da katin dan kasa ga dukkan al’ummarta musamman da zummar taimaka wajen inganta tsaro, sai gashi kwatsam ma’aikatan hukumar kula da ke samar da katin sun tsunduma yajin aiki bisa rashin kayan kare lafiya yayin gudanar da aikisu da kuma batun karin kudaden su. Dangane da wannan dambarwa wakilinmu na Abuja Mohammed Sani Abubakar ya tattauna da Malam Nura Sale, wani kwararren a harkar kimiyyar sadarwa zamani.
Rahotanni daga Najeriya na nuna yadda matsalar cin hanci ta dabaibaye dibar 'yan Sandan da ya gudana a wannan shekara, inda ake zargin wasu jami’an hukumar da karbar makudan kudade suna sauya sunayen mataşan da suka samu nasara. Wannan matsala ta haifar da cece-kuce a cikin kasar, musamman a wannan lokaci da matsalar tsaro ta dabaibaye Najeriya baki daya. Muhammad Sani Abubakar ya tattauna da Haj Naja’atu Muhammad, kwamishiniya a Hukumar kula da aikin Yan Sanda dake Najeriya, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
Rohatanni daga jihar Legas a Najeriya na cewa gwamnatin jihar ta yi asarar kimanin Naira miliyan 400 sakamakon rikicin da ya barke a jihar, biyo bayan zanga-zangar EndSars da ake yi, duk da cewa har yanzu ba'a kammala bincika ba, yayin da Juma’an nan gwamnan Jihar Babajide Sanwo-Olu ya aki rangadin gani da ido na wuraren da aka yi ta'adi sakamakon tarzomar. Shugaban Cibiyar Kasuwanci Ta Legas, Muda Yusuf, ya shaidawa manema Labarai, cewa har yanzu ba'a kai ga tattara alkaluma kan kiyasin asarar da wannan tarzoma ta jawo ba, amma an yi asarar kimanin naira biliyan 400. Tarzomar da ta barke a Legas ta haifar da matsaloli da ta kai ga kona gine-ginen gwamnati da na al’umma. Cikin wuraren da aka kona tun a daren Talata kafin wayewar Laraba, sun hada da wani Babban Otel da wani asibiti baya ga ofisoshin ‘yan sanda. Yayin da ranar Laraba aka cinna wuta a cibiyar Hukumar kula da tashoshin jiragen ruwa ta Najeriya NPA, da kuma gidan talabijin na TVC da ke Legas din, tare da ofishin Hukumar kiyaye haddura da wani sashe na sakatariyar Legas. Kazalika, fusatattun masu zanga-zangar sun bankawa tashar motocin BRT na gwamnatin Lagas dake Oyingbo wuta, inda motocin Bus na safa-safa da dama suka kone, yayin da aka kai hari kan bankuna a wasu sassan birnin. A bangare daya, bayanai sunce ankuma kona gidan mahaifiyar gwamnan jihar Baba Jide Sanwo – Olu, yayin da suka farma gidan sarkin Lagas, wanda yasha da kyar, inda aka wawure kayayyakinsa da dukiyoyi. Dangane da wannan batu, Garba Aliyu Zaria ya tuntubi Dr. Kasimu Garba Kurfi masanin tattalin arziki a Najeriya don jin yadda suke kallon irin hasarar da aka tafka.
Majalisar Dinkin Duniya tace kasashen Afirka sun yi asarar kudaden da suka kai Dala biliyan 836 ta hanyar fitar da su zuwa kasashen duniya ba bisa ka'ida ba a cikin shekaru 15. Hukumar dake kula da kasuwanci da kuma cigaba ta gabatar da rahoto akai, inda take cewa kudaden sun zarce Dala biliyan 770 da ake bin nahiyar baki daya a shekarar 2018.Dangane da wannan rahoto, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki, Dr Isa Abdullahi na Jami’ar Kashere, kuma ga yadda zantawarsu ya gudana.
Hukumar bunkasa matsakaita da kananan sana’o’I ta Najeriya SMEDAN, ta ce yanzu haka fanninta ne ke kan gaba wajen samar da ayyukan yi a kasar da kashi 76.5, inda kimanin mutane miliyan 59 da dubu 647, ke cin abinci a fannin. Hukumar ta bayyana wadannan alkaluma ne yayin kaddamar da shirin tallafa wa matasa kusan dubu 1 da 500 a jihohin kasar 11, wanda wasu daga ciki suka hada da, Katsina, Zamfara, Delta, Rivers, sai kuma Legas, inda bikin ya gudana. Nura Ado Suleiman da halarci taron, ya zanta da babban daraktan hukumar bunkasa matsakaita da kananan masana’antun na Najeriya SMEDAN Dr Dikko Umaru Radda.
A Najeriya Sakamakon wani rahoton da Hukumar hana fasakwauri ta yada tun a jiya lahadi, game da bankado sirrin yunkurin kai wa Abuja babban birnin kasar kazamin hari Hedquatan sojan kasar ta ce shege ka fasa. Major- Gen John Enenche jami'in kula da manema labarai na maaikatar Tsaron kasar ya bada wannan tabbaci, inda yake cewa sun dade zaman cikin shiri. Akan haka muka tuntubi Farfesa Mohammed Kabir Isa na Jamiar Ahmadu Bello dake Zaria wanda yasha bincike-bincike dangane da ayyukan ‘yan Boko Haram don jin yaya suke kallon wannan sirri.
Hukumar Lafiya ta Duniya tayi shelar cewar Afirka ta rabu da cutar polio bayan kwashe dogon lokaci ana yaki da cutar a fadin duniya. Hukumar tace tayi nasarar kare yara miliyan guda da dubu 800 daga zama guragu, yayin da ceto rayukan mutane 180,000 wajen yaki da cutar. Yaya kuke kallon wannan nasara? Wane irin darasi ya dace Afirka ta koya daga wannan yakin ? Ta yaya kuke ganin Afirka zata yaki wasu cututtukan da suka rage ?
Yanzu haka wata takaddama ta kaure tsakanin Hukumar raba wasiku a Najeriya da Hukumar tara kudaden haraji kan wanda yake da hurumin karbar harajin kan Sarki ko kuma ‘Stamp Duty’ da ake kira a turance. Hukumar tara kudaden haraji tace ita take da hurumi, yayin da Hukumar tara haraji tace ita doka ya baiwa hurumi. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Dauda Muhammad Kontagora masanin tattalin arziki, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
Yayin da Majalisar Dattawan Najeriya ke shirin fara gudanar da bincike kan almundahana a Hukumar kula da Naija Delta sakamakon korafin da aka gabatar mata na bacewar kudaden da suka kai naira biliyan 80, wasu mazauna yankin na zargin shugabannin su da gazawa wajen gina yankin duk da makudan kudaden da gwamnatin Najeriya ke ware masa. Wani mawallafi da ya fito daga Yankin, Mr Agba Jalingo ya zargi shugabannin yankin da sace kudaden da ake warewa ma’aikatar kula da Naija Delta da kudaden Amnesty da kashi 13 na arzikin mai da wasu kudade kuma da gwamnatin tarayya ke turawa yankin, yayin da suke zargin wasu yankuna da jefa yankin cikin koma baya. Ga tattaunaawarsa da Bashir Ibrahim Idris.
Hukumar zaben Jamhuriyar Nijar, ta ce ba za ta iya gudanar da zabe domin bai wa ‘yan kasar dake zaune a kasashen ketare damar samun wakilci a Majalisar dokokin kasar ba, sannan kuma ba za ta iya gudanar da zaben kananan hukumomi ba duk da cewa wa’adinsu ya kawo ya kawo karshe. A baya dai cikin watanni masu zuwa aka tsara gudanar da sabbin zabuka a kasar ta Nijar, sai dai hukumar zabe ta ce ba ta da lokacin yi wa masu kada kuri’u rijista a kasashen ketare, matakin da tuni ya samu amincewar kotun tsarin mulkin kasar. Wannan shi ne batun da muka baiwa masu sauraro damar tattaunawa akai.
Hukumar samar da abinci ta Majalisar Dinkin Duniya tace akalla mutane sama da miliyan 40 dake zaune a Yammacin Afirka zasu fuskanci karancin abinci a watanni masu zuwa sakamakon illar annobar coronavirus wadda ta tilasata killace mutane a cikin gidajen su. Wannan ya biyo bayan matakan da gwamnatoci suka dauka na tilastawa mutane zama a gida domin dakile yaduwar annobar coronavirus wadda ta shafi manoma da masu harkar samar da abinci. Dangane da wannan rahoto Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Sakataren yada labaran kungiyar manoman Najeriya kuma kwamishinan Gona a Jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Magaji.
Shirin Duniyar Wasanni na wannan lokaci yayi nazari kan Jadawalin da hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ke fitarwa kan matakin kwarewar tawagogin kwallon kafar kasashe.
A taron birnin Rabat na kasar Morocco da ya hada hukumar Fifa da ta Caf,Gianni Infantino Shugaban hukumar Fifa ya bukaci hukumar Caf da ta yi nazari tareda dage gasar cin kofin nahiyar Afrika kama daga shekaru biyu zuwa hudu. Shawarar shugaban ta Fifa na zuwa ne a wani lokaci da kwallon kafa a Afrika ke fama da matsalolli. Abdoulaye Issa a cikin shirin Duniyar wasanni ya duba halin da ake ciki kamar dai yadda za a ji.