POPULARITY
Taron Jam'iyyar PDP a ƙarshen makon da ya gabata, ya amince da bai wa yankin kudancin ƙasar damar gabatar da ɗan takarar zaɓen shugaban ƙaasr da za ayi a shekarar 2027, ya yin da ya haramtawa waɗanda suka fito daga arewacin ƙasar tsayawa takara. Tuni aka bayyana cewar wasu kusoshin jam'iyyar na zawarcin tsohon shugaban ƙasar Goodluck Jonathan da Peter Obi domin tsaya musu takara. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon Sakataren jam'iyyar, Sanata Umar Ibrahim Tsauri game da lamarin. Ku latsa alamar sauti don sauraron yadda zantawarsu ta gudana.................
Ƙungiyar Fulani ta Miyetti Allah a Najeriya, ta nesanta kan ta daga goyan bayan ayyukan ta'addancin da wasu ɗai-ɗaikun ƴaƴanta keyi, tare da bayyana cewar ita ta fi jin raɗaɗin matsalar. Shugaban ƙungiyar Baba Usman Ngelzerma ya ce aƙalla Fulani 20,000 aka kashe, yayin da suka yi asarar shanu sama da miliyan 4 ga ayyukan ta'addancin a shekaru 5 da suka gabata. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Bashir Ibrahim Idris.............
Majalisar Dattawan Najeriya ta bayyana cewar ya zama dole ta yi dokokin da za su takaita yadda kafofin sada zumunta ke neman haifar da tashin hankali a cikin kasar. Shugaban masu rinjaye a Majalisar Bamidele Opeyemi ya bayyana haka, sakamakon zargin neman jefa kasar cikin tashin hankalin da matasa ke yi ta wadannan kafofi. Dangane da wannan yunkuri, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin harkar sadarwa,Malam Umar Saleh Gwani. Latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana...
Gwamnatin Najeriya ta bayyana shirin amfani da malaman addini wajen wayar da kan jama'a wajen rungumar amfani da abincin da aka sauyawa kwayar halitta da ake kira GMO. Shugaban hukumar kula da irin wadannan abinci Farfesa AbdullahI Mustapha ya bayyana haka a tattaunawarsa da RFI Hausa. Ganin yadda jama'a ke dari darin amfani da irin wannan abinci, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin kula da harkar lafiya, Farfesa Yusuf Abdu Misau, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Shirin a wannan makon zayyi duba ne kan karramawar da gwamnatin Najeriya ta yi wa tawagar Super Falcons na lashe gasar WAFCON. A makon da ta gabata ne shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya karrama ƴan wasan tawagar ƙungiyar kwallon ƙafa ta mata ta ƙasar Falcons, bayan nasarar lashe kofin WAFCON karo na 10 daga cikin 13 da aka yi. Cikin kyautukan da gwamnati ta baiwa waɗannan ƴan wasa akwai lambar girmamawa na ƙasa wato OON da shugaban Tinubu ya baiwa dukkan ƴan wasan da masu horar dasu, hakazalika kowacce ƴar wasa ta samu dalan amurka dubu 100, da kuma karin naira miliyan goma-goma daga ƙungiyar gwamnonin Najeriya. Tuni dai shugaban hukumar wasani a Najeriya Shehu Dikko ya yaba da wannan nasarar da kuma irin karramawar da shugaban ƙasar ya yiwa ƴan wasan. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh.
Shirin Mu zagaya Duniya na wanan makon tare da Ibrahim Mallam Tchilla yayi waiwaye kan gudunmawar da tsofan shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayer wajen hada kai da samar da cigaba ga al'umma Najeriya. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin....
Shugaban Kamaru Paul Biya ya bayyana aniyar sa ta sake tsayawa takarar shugabancin ƙasar a karo na 8 yana mai shekaru 92 da haihuwa, inda ya yi iƙirarin cewa matasa da mata ne zai fi bai wa fifiko idan ya samu ya zarce. Wani saƙo da Biya mai shekaru 92 ya wallafa a shafinsa na Twitter ne ke sanar da wannan mataki wanda ya kawar da jita-jitar da ke nuna cewa shugaban a wannan karon bashi da sha'awar tsayawa takara don neman wa'adi na gaba. Fiye da shekaru 40 kenan Paul Biya ke jagorancin Kamaru kasancewarsa shugaba na biyu da ya jagoranci ƙasar tun bayan samun ƴancinta daga Faransa wato bayan murabus ɗin shugaba Amadou Ahidjo. Idan har Paul Biya ya yi nasarar lashe zaɓen da zai bashi damar sake yin shekaru 7 a karagar mulki, kenan shugaban mafi daɗewa kan mulki, zai tasamma shekaru 100 na rayuwarsa a karagar mulki karon farko da ake ganin irin hakan a tarihi. Shiga alamar sauti, domin sauraro cikakken shirin tare da Abida Shu'aibu Baraza.
A jiya Lahadi, 13 ga watan Yulin nan ne Allah ya yi wa tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari rasuwa yana da shekaru 82 a duniya. Bayan kasancewa shugaban gwamnatin sojin Najeriya daga shekarar 1983 zuwa da 1985, ya sake dawowa a matsayin farar hula, inda ya mulki ƙasar daga shekarar 2015 zuwa 2023. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Faruk Adamu Aliyu, ɗaya daga cikin makusantan Buhari akan wannan rasuwa da irin rayuwar da yayi. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar....
Hukumar kula da jarabawar shiga manyan makarantu a Najeriya ta JAMB ta nemi gafarar jama'ar kasar saboda matsalolin da aka samu wajen jarabaswar bana, wadda ta kai ga dalibai sama da miliyan guda da rabi suka kasa samun makin da ake bukata. Shugaban hukumar Farfesa Ishaq Oloyede cikin hawaye ya nemi gafarar jama'a da kuma daukar alhakin lamarin.Dangane da wannan matsala, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Umar Saleh Gwani masanin harkar sadarwa.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
A yau shirin tamabaya da amsa, tare da Nasiru Sani, zai kawo muku bayanai ne akan tasirin tsarin harajin da shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaƙabawa ƙasashen Canada da Mexico da kuma China akan ƙasashe Afirka. Shirin ya kuma zanta da kwararru a fannin lafiya, kan dalilan da ke sanya shan ruwa a kai.Akwai kuma cikakken bayani kan Sultan Makenga, wato jagoran ƙungiyar 'yan tawayen M23 wanda ya hana zaman lafiya a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo, musamman ma a gabashin ƙasar.Shiga alamar sauti, domin saurarin cikakken shirin.
A Gabon, ana ci gaba da yakin neman zabe a yau da ke jajuburin zaben Shugaban kasar,wanda ya hada 'yan takara takwas. Gwamnati ta ayyana ranar zaben gobe a matsayin ranar hutu, domin baiwa masu rajista a larduna damar yin balaguro. Ƴan adawa sun bayyana damuwarsu ganin ta yada shugaban majalisar sojin kasar ke amfani da kadarorin gwamanti a yakin zaben. A game da zaɓen, Abdoulaye Issa ya tattauna da Janjouna Ali Mahaman Sani, masanin siyasar ƙasar ta Gabon da kewaye.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu
A kasar Gabon, ana ci gaba da yakin neman zabe a yau da ke jajiberin zaɓen Shugaban ƙasar,wanda ya haɗa 'yan takara takwas. Gwamnati ta ayyana ranar zaben gobe a matsayin ranar hutu, domin baiwa masu rajista a larduna damar yin balaguro.Ƴan adawa sun bayyana damuwarsu ganin ta yada shugaban majalisar sojin kasar ke amfani da kadarorin gwamanti a yakin zaben.Abdoulaye Issa ya tattauna da Janjouna Ali Mahaman Sani, masani siyasar kasar ta Gabon da kewaye.Ga kuma yada zantawar tasu ta gudana.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
Hukumar EFCC dake yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya ta sanar da kwato kuɗaɗen da suka kai naira Triliyan guda a shekarar da ta gabata, abinda ke nuna irin nasarar da ta samu, baya ga samun nasara a kotu a shari'o'in da suka kai sama da 4,000.Dangane da wannan nasarar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Isa Sanusi, Daraktan Ƙungiyar Amnesty a Najeriya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiya hirar...........
Shugaban Ƙasar Ghana John Dramani Mahama ya ƙaddamar da wani shirin diflomasiya domin shawo kan ƙasashen Nijar da Mali da Burkina Faso, wadanda suka fice daga cikin ƙungiyar ECOWAS.A ƙarshen makon da ya gabata, shugaban ya ziyarci waɗannan ƙasashe guda uku, inda ya gaba da shugabannin su.Dangane da tasirin wannan ziyarar, Bashir Ibrahim Idris ya tatauna da Dr Elharun Muhammad na Cibiyar kula da manufofin ci gaban ƙasashe dake Kaduna, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Majalisar Dattawan Najeriya ta kaddamar da bincike domin gano yadda bindigogi dubu 178,459 suka bata daga rumbun aje makaman 'yansanda daga shekarar 2018 zuwa yanzu. Shugaban kwamitin binciken, Sanata Samuel Godwin ya ce daga cikin bindigogin, dubu 88,078 manya ne kirar AK-47, yayin da dubu 3,097 kuma kanana ne.Dangane da wannan labari mai tayar da hankali, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Alhaji Sule Ammani, Yarin Katsina.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Shirin Muhallinka Rayuwarka na wannan mako ya yi duba ne kan fitar da amfanin gona da aka noma a damunar bara da Kungiyar Gwamnonin Najeriya ta ce a ke yi sakamakon karyewar darajar kuɗin ƙasar, lamarin da su ka ce ya sanya su suma su ka tsunduma cikin masu ribibin sayen amfanin gonar, su na adanawa a rumbunansu domin maganin gobe. A farkon makon watan Janairun wannan shekarar, a yayin ziyarar gaisuwar sabuwar shekara da kungiyar gwamnonin Najeriya ta ka kai wa Shugaban ƙasar, Bola Ahmed Tinubu, Shugaban Ƙungiyar gwamnonin, kuma gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq ya yi bayani tare da ƙarin haske a kan aniyar gwamnonin.Sai dai kungiyar Manoman ƙasar wato AFAN, ta bakin kakakinta Muhammad Magaji, ta bayyana cewa ba sabon abu bane yadda ake fitar da kayan amfanin gona zuwa ƙasashen waje domin neman riba, amma ta ce ƴan kasuwa da ke sayen kayan a hannun manoman ne ke yin hakan ba manoman da kansu ba.Kasancewar matakin da gwamnonin su ka ce sun fara ɗauka na sayen kayan abinci su na adanawa na da buƙatar fashin baƙi daga masana, mun tuntuɓi Malam Abubakar Lawal Kafinsoli na sashen nazarin noma a Jami'ar Tarayya da ke Dutsinma a jihar Katsina dangane yadda hakan zai taimaka wa manoma da kuma harkar noma a ƙasar, wanda ya ce wannan ba hanya ba ce mai bullewa ba, musamman ga talakawan kasar.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Michael Kuduson.
A yau shirin tamabaya da amsa zai fara ne da kawo muku takaitaccen tarihi ne akan zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Ghana wato John Dramani Mahama da tasirin sa ga lamuran ƙasar.
Daga cikin abubuwan da shirin Mu Zagaya Duniya na wanan makon ya yi waiwaye akai akwai yadda gobarar daji ce ke cigaba da tafka barna a birnin Los Angeles inda ta raba mutane kusan dubu 200 da muhalansu bayan kone fadin kasa da gine-gine masu yawan gaske.
A wannan talatar ce aka rantsar da John Mahama a matsayin shugaban Ghana, cikin yanayi na tarin kalubale da suka hada da na matsin tattalin arziki biyo bayan lashe zaben da aka yi cikin kwanciyan hankali da lumana. Masu bibiyar siyasa a kasar sunyi ittifakin cewa duk da cewa Mahaman ya taba jagorancin kasar, ya dawo ne a lokacin da lamura suka sauya ainun.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Abida Shu'aibu Baraza.
Ƴan Najeriya na fatan ganin samun sauƙi a wannan shekara ta 2025, bayan da suka shiga wani yanayi na matsalin tattalin arziki a shekarar 2024 da muka yi bankwana da ita, sakamkon wasu matakai da gwamnatin shugaba Tinubu ta ɗauka, masamman janye tallafin man fetur da kuma barin naira ta ceci kanta a kasuwar canjin kuɗaɗe. Shugaban ƙasar Bola Tinubu dai ya ce gwamnatinsa za ta rage hauhawar farashi a shekarar 2025 ta hanyar haɓaka noma da tallafa wa masana'antu, danage da fatan da ƴan Najeriyar ke da shi da kuma hasashen masana dangane da farfadowa tattalin arziki a wannan shekara, Ahmad Abba ya tattauna da Farfesa Kabiru Isa Dandago na jami'ar Bayaro da ke Kano, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
A ranar Laraba ne shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatar da kasafin kudin ƙasar na shekarar 2025 na naira Tiriliyan 47.9. Sai dai wani batu da ya haifar da muhawara a tsakanin ‘yan Najeriya dangane da kasafin kuɗin na baɗi, shi ne yadda aƙalla kaso 30 zuwa 32 na yawan kuɗaɗen za su tafi a biyan basuka ko kuma kudin ruwan basukan, kwatankwacin naira tiriliyan 15 da biliyan 800, adadin da ya zarce yawan kudaden da aka warewa tsaro, ilimi, lafiya da manyan ayyuka.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin tare da Kabiru Mohammed Dan Bauchi...
Shirin Tambaya da Amsa tare da Nasiru Sani a wannan mako kamar yadda ya saba ya amsa wasu jerin tambayoyi da masu sauraro suka aiko, ciki kuwa har da amsar tambaya kan tarihin Marigayi shugaba Ibrahim Ra'isi na Iran da Allah ya yi rasuwa sakamakon haɗarin jirgin sama cikin shekarar nan.
Daga cikin Labarun da suka fi ɗaukar hankali a makon da ya ƙare akwai jerin makamai masu linzamin da Iran ta kai wa Isra'ila hari da su, a yayin da ita kuma Isra'ilar ta karkatar da hare-haren da take kai wa a Gaza zuwa Kudancin Lebanon, h da zummar murkushe mayakan Hezbolla A Najeriya kuwa ɗimbin Iyallai ne suka shiga alhinin rashin da suka yi, biyo bayan nuutsewar da wani jirgin ruwa yayi ɗauki da fasinjoji sama da 300 da ke ƙoƙarin tsallaka kogin Kwara domin zuwa taron Maulidi.
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana shirin gudanar da wani taron matasa na kasa domin basu damar tattauna matsalolin da suka addabe su da zummar share musu hawaye. Ana saran wannan mataki ya kwantar da hankalin fusatattun matasan wadanda ke korafi a kan yadda ake gudanar da mulkin Najeriya.Dangane da wannan yunkuri, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Alhaji Muntaqa Abdulhadi Dabo, daya daga cikin fitattun matasan kasar, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Shugaban majalisar gudanarwar Kungiyar tintiba ta arewacin Najeriya wato ACF, Alhaji Bashir Dalhatu ya nemi gafarar 'yan arewacin kasar saboda abinda ya kira gazawar su ta kare yankin daga fadawa rikici mafi muni a tarihinsa. Dalhatu ya ce suna ci gaba da lalubo hanyar shawo kan wadannan matsaloli da suka yiwa yankin kamun kazar kuku. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu tare da Bashir Ibrahim Idris.......
A jawabin da ya gabatar ga al'ummar ƙasar biyo bayan soma zanga-zangar nuna rashin amincewa da tsadar rayuwa, shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya yi buƙaci a jingne zanga-zanga tare da bayyana aniyar tattaunawa da waɗanda suka shirya zanga-zangar. Sai dai an yi ta mayar da martani a game da jawabin nasa, wanda masu sharhi ke cewa bai taɓo inda ake so ya taɓo ba, hasali ma tamkar bai fahimci bukatun al'ummar ƙasar ba.A kan haka ne Aisha Shehu Kabara ta tattauna da Kwamared Bello Basi Fagge, wani mai fafutuka, kuma mai sharhi kan al'amuran yau da kulluma Kano, Najeriya.
Kamfanin Dangote ya yi watsi da zargin samar da man da bashi da inganci da kuma fara aiki ba tare da lasisis ba da hukumomin Najeriya suka masa, inda ya sake jaddada cewar tabbas wasu mutane na neman yiwa matatar tasa zagon kasa. Shugaban hada hadar kasuwanci na kamfanonin Dangoten Rabiu Umar ya bayyana haka a tattaunawarsu da Bashir Ibrahim Idris. Kuna iya latsa alamar sauti domin jin yadda zantawar tasu ta gudana...
Tsohon shugaban ƙasar Amurka Donald Trump, wanda ke takarar shugabancin ƙasar a ƙarƙashin jam'iyyar Republican a zaɓe mai zuwa ya tsallake rijiya da baya, bayan da wani mutum mai shekaru 20 ya ya yi yunƙurin kashe shi ta hanyar harbin bindiga, yayin da ya ke yaƙin neman zaɓe a jihar Pennsylvania a ranar Asabar, al'amari da ya ta'azzara rarrabuwar kawuna mai muni da a ke da ita a fagen siyasar Amurka. Ko wane tasiri ne hakan zai yi ga siyasar wannan ƙasa, wadda ke zama a matsayin abin koyi, kuma ke da'awar kare dimokaradiyya a faɗin duniya. A kan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da masanin siyasar ƙasa da ƙasa, Farfesa Kamilu Sani Fagge.
Shugaban gudanarwar kungiyar ECOWAS Omar Alieu Touray yace kungiyar tana fuskantar baraznar rugujewa sakamakon ficewar kasashen Mali da Burkina Faso da kuma Jamhuruyar Nijar, wadanda tuni suka kafa kungiya a tsakanin su. Tourey yace ficewar su zata raunana kungiyar ta fuskar kasuwanci da zirga zirgar jama'a da kuma yaki da ta'addanci. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ambasada Abubakar Cika, masanin harkar diflomasiya, kuma ga yadda hirar su ta gudana. Danna alamar saurare don jin cikakkiyar tatttaunawar
Shirin 'Kasuwa akai Miki Dole na wannan makon ya maida hankali da kan kiranda wasu kungiyoyi suka yi wa gwamnatin Najeriya da ta yi wa Allah ta farfado da harkokin noma da sarrafa manja kamar yadda aka san ƙasar a baya. Kungiyar ɗalibai ta ƙasar ta yi kira ga shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya farfado da harkokin sarrafa manja da Allah ya wadata ƙasar da shi, ta yadda hajar zata wadata ƴan Najeriya da ma fitar da shi ƙasashen waje kamar yadda lamarin yake a baya. Kirin ƙungiyar ta NANS na zuwa ne bayan da Shugaban ƙungiyar masu samar da manja ta Najeriya Mista Alphonsus Inyang, ya ce Najeriya na kashe sama da daka miliyan 600 duk shekara wajen shigo da Manja daga katare duk da cewa Allah ya albarkaci ƙasar da kwakwan Manja.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Ahmed Abba......
Shirin tamabaya da amsa na wannan mako zai kawo muku tarihin shugaban kasar Iran Ebrahim Raisi, wanda Allah Ya yi wa rasuwa a ranar 19 ga watan Mayun shekarar 2024, tare da bayani akan ma'askin dare kamar yadda aka aiko mana da tambayoyi akansu, sai a kasance tare da mu a cikin shirin.
A cikin shirin Mu Zagaya Duniya akwai cikar shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu shekara guda a kan karagar Mulki.sai kuma yadda asusun Tallafawa Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, yayi A wadai da KARUWAR cin zarafi da take hakkin kananan yara a kasashen Mali da Burkina Faso da kuma Nijar a dalilin ta'azzarar ayyukan kungiyoyin ‘yan ta'adda. da kuma sauran rahotanni da ke biye dasu.
A ranar Talata ne aka rantsar da sabon shugaban kasar Senegal, Bassirou Diomaye Faye, wanda ya lashe zaben kasar a makon da ya gabata da kaso sama da 54 cikin 100 na yawan kuri'u sama da miliyan 7 da aka kada. Faye shine shugaba mafi kankantar shekaru a Afrika, kuma ya lashe zaben ne a wani yanayi da kasar ke cikin chukumurdar siyasa.Matashin ya zama shugaban kasa ne kasa da makonni biyu bayan fitowar sa daga gidan yari.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.
Kungiyar ‘Yan Nijar mazauna Cote d'Ivoire ta bukaci a cirewa Nijar takunkumai da aka kakaba mata sakamkon juyin mulki da sojoji suka yi, saboda halin kunci da hakan ya jefa su ciki. Shugaban kungiyar ta Ho consei de Nijar a Cote d'Ivoire Alhaji Abdou Jibo ya yi wannan kira, yayin zantawa ta musamman da sashin hausa na RFI a Abidjan.Amma ya fara yi wa Ahmad Abba bayani kan zamantakewarsu a kasar da ke mamba a ECOWAS.Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar
Sabon Babban Daraktan RFI, Mr Jean-Marc Four yanzu haka yana ziyarar aiki a Najeriya dokin ganin yadda RFI Hausa ke gudanar da ayyukansa tare da ganawa da ma'aikatan sashen. Yayin ziyarar Mr Four ya bayyana gamsuwa da kwararrun ma'aikatan dake aiki da RFI Hausa tare da gabatar da sabon albishir a kan shirin da yake da shi ga sashen da kuma sauran sassan da ake amfani da karsunan Afirka. Ga yadda zantawarsu ta gudana da Bashir Ibrahim Idris.
Maudu'in na wannan rana ya mayar da hankali ne, kan rahoton da kwamitin shugaban Najeriya ya fitar game da badakalar da aka samu tsohon shugaban babban bankin kasar, Godwin Emefile, da aikatawa na bude asusun bankuna sama da 500 a kasashen waje. Sai dai, Godwin Emefiele, ya yi watsi da rahoton binciken da ya bayyana cewar ya bude asusun bankuna har guda 593, wadanda yayi amfani da su wajen boye makudaden kudaden gwamnati da niyyar yin kwanciyar magirbi akansu.Cikin sanarwar da ya fitar a ranar Lahadi, Emefiele, wanda aka bayar da belinsa a ranar Juma'a, ya ce tuni ya bai wa lauyoyinsa umarnin shigar da kara kan rahoton da yace babu abinda ya kunsa sai karairayi domin bata masa suna.SHiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin da Nasiruddeen Muhammad ya gabatar.
A Najeriya, Kungiyar CISLAC da ke bin diddigir ayyukan Majalisar da yaki da rashawa ta gudanar da wani taron karawa juna sani a birnin Legas dangane da kokarin samar da sauye sauye a harkokin zaben Najeriya da kuma kyautata nagarta a bangaren shari'un bayan zabe. Shugaban kungiyar Auwal Musa Rafsanjani ya bayyana mana muhimammancin taron a zantawarsa da Ahmed Abba
Bayan share tsawon watanni ana zaman tankiya, daga karshe dai shugaban Senegal Macky Sall ya sanar da cewa ba zai tsaya takarar neman shugabancin kasar karo na uku a zaben da za a yi cikin watan fabarairun shekaru mai zuwa ba. Shugaba Sall, ya ce ya yanke shawarar kin tsaya takarar ce duk da cewa Kundin Tsarin Mulki ya ba shi dama, sannan kuma akwai masoyansa da dama da ke fatan ganin ya tsaya a zaben mai zuwa. Shin me za ku ce a game da mataki da shugaban na Senegal na ya dauka? Shin anya ya yi hakan ne saboda nuna kishin kasa ko kuma saboda jajircewar masu adawa da tsayawarsa a zaben? Ku latsa alamar ssauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a.
Al'amurran yau da kullum sun fara daidaita a birnin Moscow fadar gwamnatin kasar Rasha, bayan da jagoran kamfanin Wagner Yevgeny Prigozhin ya sanar da dakatar da boren da yake yi wa gwamnatin Vladimir Putin. Shugaban kasar Belarusse Alexander Loukochanko ne ya yi nasarar shawo kan shugaban Wagner domin jingine yunkurinsa na afka wa birnin Moscow, tare da amince wa ya bar Rasha zuwa Belarusse. Domin jin dalilin da suka haddasa tsamin dangantaka tsakanin Putin da Prigozhin, da kuma yadda hakan zai shafi makomar yakin Rasha da Ukraine? Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Janar Idris Bello Dambazau mai ritaya. A latsa alamar sauti don jin tattaunawar ta su.......
Babbar kwalejin horar da likitoci ta duniya, wato ‘International College of Surgeons' reshen Najeriya, ta ce likitoci dubu 6 da 221 ne suka koma aiki Birtaniya daga Najeriya a cikin shekaru 6 da suka gabata, saboda neman rayuwa mai inganci. Cibiyar horar da ma'aikatan lafiyar ta ce wannan rige rigen da likitoci ke yi na barin Najeriya, ya dada haifar da matsala da kuma sanya mutane sama da miliyan 40 basa iya ganin likita guda da zai duba halin lafiyarsu. Shugaban kwalejin, Farfesa Akanimo Essiet ya gabatar da wadannan alkaluma bayan kammala taron masanan kwalejin karo na 56, inda ya bayyana cewar matsalar ta yi matukar illa wajen rage yawan ma'aikatan lafiya a Najeriya. Essiet ya ce kafin shekarar 2022, likita guda ne ya ke kula da marasa lafiya dubu 4 a Najeriya, sabanin ka'idar da Hukumar Lafiya ta Duniya ta gindaya wadda ta ce ana bukatar likita guda domin ya kula da marasa lafiya 600. Essiet ya ce an samu gibi sosai wajen jami'an da ke aikin kula da lafiya a Najeriya, yayin da adadin likitocin da ke aiki a Birtaniya ya tashi daga 4,765 a shekarar 2017, zuwa 10,986 a wannan shekarar. Dangane da dalilan da suka sa ma'aikatar lafiyar ke barin Najeriya zuwa Turai, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Kamaluddeen Garba, ‘dan Najeriya da ke aiki a Birtaniya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Hukumar kula da afuwa a Najeriya ta bukaci rundunar ‘yan sandar kasar ta dauki tubabbun ‘yan tsagerun yankin Neja Delta aikin dan sanda, don taimakawa wajen samar da tsaron kasa. Shugaban hukumar, Janar barry Ndiomu ne ya mika wannan bukata, wanda ke zuwa a daidai lokacin da sufeto janar na ‘yan sandan kasar, Usman Baba Alkali ke korafin cewa kan yadda matasa daga yankin Neja Delta ba sa iya cika gurbin da aka ware musu a lokacin dibar sabbin ‘yan sanda. Kan haka ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauanwa da Muhammad Wakili tsohon kwamishinan 'yan sanda.
Gwamnatin Nijar ta kammala taron kwanaki biyu da ta shirya domin gabatar da shirin raya kasar da take da shi ga manyan ‘yan kasuwa da zuba jari daga kasashen duniya. Shugaban kasar Bazoum Muhammad da manyan jami'an gwamnati ne suka halarci taron na kwanaki biyu a birnin Paris na kasar Faransa Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da ministan lafiya na kasar, Dakta Ilyasu Idi Mai-Nasara wanda ya kasance daga cikin tawagar da suka yiwa shugaban rakiya. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Shugaban kwamitin zaman lafiya a Najeriya, Janar Abdusalami Abubakar ya bayyana matukar damuwa dangane da irin zafafan kalamun da 'yan siyasa ke amfani da su a dai dai lokacin da ake shirin zaben shekara mai zuwa. Tsohon shugaban kasar ya bukaci Yan takarar shugaban kasar da su ja kunnen masu magana da yawunsu domin kaucewa kalaman da zasu tinzira tashin hankalin da zai kaiga rasa rayukan jama'a. Abdusalami ya bukaci yan siyasar da su mutunta alkawarin da suka dauka lokacin da suka rattaba hannu akan yarjejeniyar da aka gabatar musu. Dangane da wannan gargadi, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Usman Muhammed, na Cibiyar bunkasa dimokiradiya dake Abuja kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Shirin 'Tarihin Afrika' na wannan mako tare da Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya ci gaba da kawo muku tarihin fiitaccen shugaban kasar Ghana dan gwagwarmaya John Jerry Rawlings da ya mulki kasar na gajartaccen wa'adi a shekarar 1979 gabanin sake shugabantar kasar a wa'adi na 2 daga 1981 zuwa 2001.
Shirin 'Tarihin Afrika' na wannan mako tare da Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya ci gaba da kawo muku tarihin fiitaccen shugaban kasar Ghana dan gwagwarmaya John Jerry Rawlings da ya mulki kasar na gajartaccen wa'adi a shekarar 1979 gabanin sake shugabantar kasar a wa'adi na 2 daga 1981 zuwa 2001. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.
Shirin 'Tarihin Afrika' na wannan mako tare da Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya ci gaba da kawo muku tarihin fiitaccen shugaban kasar Ghana dan gwagwarmaya John Jerry Rawlings da ya mulki kasar na gajartaccen wa'adi a shekarar 1979 gabanin sake shugabantar kasar a wa'adi na 2 daga 1981 zuwa 2001.
Lauyan dake kare shugaban haramcaciyar kungiyar dake fafutukar kafa kasar Biafra a Najeriya, Nnamdi Kanu, wato Mike Ozekome, ya rubutawa shugaban kasar Muhammadu Buhari wasika, inda yake bukatar gagaguta sakin Kanu ta hanyar siyasa. Lauyan yace sakin Kanu zai kawo karshen durkushewar tattalin arzikin Yankin Kudu maso Gabas, saboda tilasta zaman gida kowacce litinin da magoya bayan sa suka yi. Dangane da wannan bukata, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Barista Abdullahi Jalo, lauya mai zaman kansa a Najeriya. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Shirin ya maida hankali ne kan zaben sabbin shugabannin gudanarwar hukumar kwallon kafar Najeriya wato NFF, da ya gudana makon jiya a birnin Benin na jihar Edo da ke kudancin kasar, inda aka zabi Alhaji Ibrahim Musa Gusau a matsayin sabon shugaba, bayan karewar wa'adin Mr Amaju Pinnick wanda ya kwashe tsahon zango biyu yana shugabancin hukumar.
Sabon Shugaban Kasar Kenya, William Ruto yayi gargadi dangane da matsalar sauyin yanayi da farin da Kenya ke fama da shi, wanda ya shafi wasu kasashen Afirka ta Gabas, inda miliyoyin mutane ke fuskantar barazanar yunwa. Shugaban ya kuma tabo batun tashin hankalin da ake samu a Habasha da kuma dalilin da ya sa ya nada tsohon mai gidan sa Uhuru Kenyatta a matsayin mai shiga Tsakani domin sasanta rikicin. Latsa alamar sauti domin sauraron fassarar kalaman nasa.
Shirin tarihin Afrika tare da Abdoulkarim Ibrahim Shikal a wannan makon ya ci gaba da kawo muku tarihin fitaccen shugaban kasar Ghana dan gwagwarmaya John Jerry Rawlings da ya mulki kasar na gajartaccen wa'adi a 1979 gabanin sake shugabantar kasar a wa'adi 2 na daga 1981 zuwa 2001.