POPULARITY
Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International a Najeriya ta yi zargin cewa jirgin sojin saman ƙasar ya yi ruwan bamai-bamai kan jami'an sakai tare da kashe akalla 20 da jikkata wasu da dama a ƙauyukan Maraya da Wabi da ke ƙaramar hukumar Maru na jihar Zamfara. Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar jiya Litinin, ta ce lamarin kai tsaye ya shafi jami'an sakai da suka taru domin tunkarar ƴan bindiga da suka kai hare-hare a ƙauyukan nasu ranar Asabar. A tattaunawarsa da Ahmad Abba, Daraktan Amnesty International a Najeriya, Malam Isa Sunusi, ya fara da bayani kan yadda lamarin ya auku.
A yau shirin tamabaya da amsa zai kawo muku bayanai ne akan wasu dalilai dake haifar da rashin samun isasshen barci a cikin dare. Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Micheal Kuduson, don jin sauran tambayoyin da kwararru suka amsa a wannan mako.
Shirin Mu Zagaya Duniya na wanan makon tareda Nura Ado Suleimane, ya yi duba ne kan mai'aikata a sassan Duniya suka gudanar da bikin rana ta musamman da aka ware musu a daidai lokacin da wani adadi da dama daga cikinsu ke fuskantar ƙalubale iri-iri. Ku latsa alamar sauti domin jin cikakken shirin......
Shirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan makon ya mayar da hankali kan tasirin masu horarwa na cikin gida a ci gaban ƙwallon ƙafar nahiyar Afirka. A baya-bayan nan ƙasashen na nahiyar Afirka sun mayar da hankali wajen ɗaukar masu horarwa na cikin gida tun bayan rawar da Morocco ta taka a gasar cin kofin Duniya ta 2022 karon farko da aka ga irin hakan daga wata ƙasa a nahiyar ta Afrika.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin Muhallinka Rayuwarka na wanan makon tareda Micheal Kuduson wanda kashi na uku ne ya dora akan kashi na biyu wanda ya gabata a makon jiya. Idan ba a manta ba, a makon da ya gabata shirin ya mayar da hankali ne kacokam akan yadda masu aiki a cikin teku ke rayuwa har ma da yadda za a yi amfani da teku, tafki, rafi ko kogi domin gudanar da harkokin noma da kuma kyautatawar muhalli.
A wannan makon shirin ya mayar da hankali ne kan yadda ake kara samun saukar farashin kayan masarufi a sassan Najeriya. Bayanai da muka tattaro na nuni da cewa yawancin kayayyakin da farashin su ya sauka na amfanin gona ne da kuma na kamfanonin kasashen waje, amma na kamfanonin cikin gida har yanzu suna nan a yadda suke.A makon jiya Hukumar ƙididdiga ta Najeriya NBS, ta ce an samu sauƙin matsalar hauhawar farashin kayayyakin masarufi a ƙasar da a ƙalla kashi 10.3.Cikin sanarwar da ta fitar a Talatar wancan makon, hukumar ta NBS ta ce hauhawar farashin kayayyaki a Najeriyar ya sauka ne zuwa kashi 24.4 a watan Janairun wannan shekara, saɓanin kashi 34.8 da aka gani a watan Disambar shekarar bara ta 2024.
Shirin Lafiya jari ce a wannan mako tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan yadda fasahar cire ɗa ta hanyar CS ke taimakawa wajen ceto rayukan uwa da ɗa da nufin rage asarar rayukan da ake fuskanta a lokacin haihuwa. Duk da cewa haihuwa 3 cikin 100 ce kaɗai ake yi ta hanyar tiyata ko kuma CS a Najeriya bisa alƙaluman 2019, amma a baya-bayan nan ana ganin yawaitar matan da ake yiwa CS gabanin haihuwa kama daga nau'in matan da basa zuwa asibiti da kuma mata masu shekaru da yawa ko waɗanda suka yi haihuwa da dama, duk dai a ƙoƙarin kange yawaitar mace-macen mata ko kuma asarar jariran da ake gani a sassan ƙasar mafi yawan jama'a a nahiyar Afrika.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.
Hukumar ƙididdiga ta Najeriya NBS, ta ce an samu sauƙin matsalar hauhawar farashin kayayyakin masarufi a ƙasar da a ƙalla kashi 10.3. Cikin sanarwar da ta fitar a jiya Talata, hukumar NBS ɗin ta ce hauhawar farashin kayayyaki a Najeriyar ya sauka zuwa kashi 24.4 a watan Janairun wannan shekara, saɓanin kashi 34.8 a watan Disambar shekarar bara ta 2024. Domin jin halin da ake ciki....la'akari da wannan rahoto, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Musa Idris daga jihar Jigawa, magidanci kuma ɗan kasuwa.Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu..........
Daga cikin labarun da shirin ya sake waiwaya a wannan makon, akwai cikar wa'adin ficewar kasshen Mali da Burkina Faso da kuma Nijar daga cikin ƙungiyar kasashen yammacin Afirka CCOWAS, da kuma abinda ya biyo baya.
Cikin makon da ya ƙare, Zaratan sojin Najeriya dake fatattakar ‘yan ta'adda a yankin arewa maso yammacin ƙasar, suka samu nasarar kashe kwamandojin riƙaƙken ɗan fashin dajin nan Bello Turji wanda ya zame wa jama'a Batoyi. Jami'in kula da watsa labaran rundunar ta ‘Operation Fansan Yamma' Lafatanar Kanar Abubakar Abdullahi yayi mana ƙarin bayani kan nasarorin da suka samu.
Ƙungiyar kare hakkin bil Adama ta ‘Amnesty International', ta fitar da sakamakon binciken da ta gudanar akan zarge-zargen da ake yi wa Isra'ila na aikata kisan ƙare dangi a Gaza. Cikin rahoton wanda aka fitar da shi a birnin Kano dake arewacin Najeriya, Amnesty tace Isra'ila ta kashe mutane sama da dubu 40, ciki harda kananan yara dubu 13 a cikin shekara guda.Wakilinmu na Kanon Abubakar Abdulƙadir Ɗangambo ta tattauna da Daraktan kungiyar ta Amnesty a Najeriya Isa Sunusi.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Ƙasashen AES da suka haɗa da Nijar, Mali da kuma Burkina Faso sun yi watsi da ƙarin wa'adin watanni shidda da ECOWAS ta yi musu a makon jiya, kan lokacin ficewarsu daga cikin ƙungiyar a hukumance, rangwamen da zai fara aiki a watan Janairun dake tafe. Cikin sanarwar da suka fitar, ƙasashen uku sun sanar da baiwa rundunonin sojinsu umarnin zama cikin shirin kar ta kwana. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Ambassada Abubakar Cika tsohon Jakadan Najeriya a ƙasar Iran. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawarsu..................
Hukumar da ke kula da al'adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta UNESCO ta damƙawa Najeriya takaddar shaidar sanya bikin hawan Daba na Kano cikin manyan al'adun duniya masu matukar tasiri. Jim kaɗan bayan kammala miƙa shaidar wakilinmu a Abuja Isma'il Karatu Abdullahi ya tattanna da ministar al'adu ta Najeriya Hajiya Hannatu Musawa kan tasirin da wannan zai yi wa ƙasar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar ta su......
Shirin Al'adun mu na Gado a wannan makon ya mayar da hankali ne kan matakin da Hukumar Raya Al'adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya UNESCO, na sanya hawan Dabar Kano a arewacin Najeriya cikin kundinta na al'adun duniya.Bincike ya nuna cewar an fara gudanar da al'adar hawa Daba a lokutan bikin ƙaramar Sallah da Babba tun kafin jihadin Shehu Usman Dan fodio zamanin Sarkin Kano Rumfa. Masana a fannin tarihi sun ce zamanin Sarkin Kano Abbas, ya yi wa tsarin sauye-sauye wanda akan sa ake tafiya har zuwa wannan lokaci.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa........
Shirin 'Al'adunmu na Gado' na wannan makon tare da Abdoulaye Issa ya tattauna dangene da gushewar a'adar tatsuniya wadda ke zama hanyar da al'ummar Hausawa ke amfani da ita wajen ilmantarwa, fadakarwa da kuma tarbiyantar da yara ta hanyar shirya kagaggun labarai masu kunshe da darussa.
Masu sauraro Assalamu alaikum, barkanmu da sake haduwa cikin sabon shirin Mu Zagaya Duniya, wanda ke waiwayar wasu daga cikin muhimman lamuran da suka faru a makon da ya ƙare.......Akwai tsokaci ko kuma martani daga ɓangarori daban daban dangane da umarnin kotun duniya ta ICC na bada sammacin kama Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu da tsohon ministan tsaronsa da kuma ɗaya daga cikin Jagororin Mayakan Hamas.
Yau shekaru tara kenan da zama Sarkin masarautar keffi da mai martaba Dr alhaji shehu usman chindo yamusa,bayan rasuwar mahaifinsa mai martaba alhaji Chindo Yamusa na uku 3.A cikin shirin al'adu za ku ji tarihin Sarkin na Keffi.
Shirin Lafiya Jari ce a wannan makon ya mayar da hankali kan matsalar damuwa mai dankwafarwa ko tsananin damuwa da ake kira Depression, cutar da ake ganin ta'azzararta a baya-bayan nan tsakanin ƙasashe masu tasowa musamman waɗanda ke fama da matsi ko kuma ƙuncin rayuwa. Wasu bayanan ƙwararru yayin bikin ranar lafiyar ƙwaƙwalwa da ya gudana a farkon watan nan, ya nuna yadda matsi da ƙunchin rayuwa ya jefa miliyoyin ƴan Najeriya a tsananin damuwar ko kuma damuwa mai dankwafarwa, matsalar da likitoci suka yi gargaɗin cewa ka iya kaiwa ga taɓin ƙwaƙwalwa.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu........
A cikin wannan shirin ,Nasir Sani ya tattaro tambayoyin ku masu sauraren Rfi hausa,wandada a cikin wannan shirin za ku ji amsoshin wasu daga cikin su.Masu saurare sun bukaci samun karin haske dangane da yarjejeniya a bangaren da ya shafi yankinn Neja Delta da Gwamnatin Najeriya.Shirin Tambaya da amsa na zuwa maku ne a duk karshen mako daga sashen hausa na Rfi.
Yayin da ‘Yan Najeriya da dama ke jin jiki kan matsin rayuwar da suka shiga tun bayan janye tallafin man fetur da kuma fara aiwatar da wasu matakai da sabuwar gwamnatin ƙasar ta yi, Bankin Duniya yayi gargaɗin cewar, matsalar da ake ciki samin taɓi ce, muddin aka kuskura aka janye ko dakatar da manufofin tattalin arziƙin da shugaba Tinubu ke aiwatarwa.
Najeriya ta yi sabon ƙarin farashin mai da akalla kashi 15%, wanda kuma shi ne karo na 4 a cikin watanni 16 da shugaba Bola Tinubu ya shafe kan karagar mulki. Babu dai wani dalili da kamfanin NNPCL da ke matsayin wakilin gwamnati a harkar mai ya bayar dangane da wannan farashi, illa kawai jama'a sun gan shi ne haka kwatsam.Kan wannan batu shirin 'Ra'ayoyin Masu Sauraro' na ranar Alhamis ɗin nan ya bayar da damar tattaunawa akai.
MU KOMA ZEREFAT
Kasashen duniya sun fara mayar da martani dangane da kazamin hare haren da Isra'ila ke kai wa a yankin kudancin Lebanon wanda a jiya kawai ya kai ga hallaka mutane kusan 300. Cikin wadanda suka bayyana damuwa da yadda yakin Isra'ilar ke fadada har da Sakatare Janar na Majalisar dinkin duniya Antonio Guterres. Dangane da wannan yaki Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abdulhakeem Garba Funtua na Babbar Kwalejin Fasaha dake Kaduna, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Kamar dai kowane mako, a yau juma'a ma jaridar Aminiya da ake wallafa ta a Najeriya ta sake fitowa ɗauke da dimbin labarai da suka shafi fannoni daban nan na rayuwa. Kuma Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Muƙaddashin Editan jaridar Muhammad Amin Ahmed domin jin karin bayani dangane da labaran da suke ɗauke da su a wannan karo. domin sauraron cikakken shirin, a latsa alamar sauti.
Majalisar Ɗinkin Duniya ta koka kan yadda aka samu ƙaruwar kashi 20 cikin 100 kan hare-haren da ake kai wa makarantu da sauran cibiyoyin ilimi da kuma ɗalibai a tsakanin shekarun 2022 zuwa 2023 da ta gabata, musamman a ƙasashen da yaƙi ya ɗaiɗaita. Cikin rahoton da ta fitar, hukumar kula ilimi, da raya al'adu ta Majalisar Dinkin Duniya UNESCO, ta ce sau dubu 6,000 aka kai wa dalibai da malamansu da kuma cibiyoyin ilimi hari, ciki har da hare-hare dubu 1,000 inda sojoji ke mayarda makarantun sansani. Ganin cewa Najeriya na daga cikin ƙasashen makarantu da dama ke fuskantar barazanar hare-haren ta'addanci ya sa Nura Ado Suleiman tattauna wa da Kwamrade Audu Titus Amba, shugaban ƙungiyar malaman Najeriyar.
A yau shirin zai waiwai kasar Ghana, inda basusukan da ake bin kasar ya karu da dala biliyan 47.4 / Cidi biliyan 658.6 a cikin watanni biyun farko na shekarar 2024.Babban Bankin ƙasar ta Ghana ne ya fitar da wadandan alkaluma cikin wani rahoton da ya fitar na taƙaitaccen Bayanan Tattalin Arziki da Kuɗi na watan Mayun shekarar 2024. A cewar babban bankin na Ghana, bashin da ake bin ƙasar ya karu ne zuwa Cidi biliyan 658.6 a watan Fabrairun wannan shekarar, tsabanin Cidi biliyan 611.2 da yake a ƙarshen shekarar 2023.
Shirin ra'ayoyin ku masu saurare na wannan rana ya duba yadda rashin tsrao da kuma garkuwa da mutane ke kara yawaita a arewacin Najeriya, inda a baya-bayan nan kwamishin yan sandan jihar Zamfara da ke arewacin Najeriya ya sanar da cafke 'dan majalisar dokoki da hakimi tare da tsohon shugaban karamar hukumar Kaurar Namoda bisa zarginsu da hannu dumu dumu cikin ayyukan garkuwa da mutane domin karbar kuɗin fansa. Wannan al'amari ya sake tabbatar da zargin da ake yi wa wasu daga cikin shugabanni a Najeriya dangane da taka muhimmiyar rawa a matsalolin tsaron da suka addabi al'ummar ƙasar.Me za ku ce kan wannan lamari?Wane darasi ya kamata al'umma su koya?Wace mafita ce mafi dacewa a bi wajen magance matsalolin tsaron dake tagayyara jama'a?Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin, tare da Nasiruddeen Muhammad
A wannan mako shirin ya mayar da hankali ne kan wani rahoto da hukumar ƙididigar ta Najeriya ta fitar cewa an sake samun hauhawan farashin kayayyaki wanda ƙasar ba ta taɓa gani ba cikin shekaru 30, daidai lokacin da gwamnatin ƙasar ke faɗi tashin kawowa al'umma sauƙi kan tsananin rayuwa da suke ciki, tare da amincewa da Naira dubu 70 a amatsayin mafi ƙarancin albashin ma'aikata. Shin ko hakan zai kawo sauƙi kan halin da ake ciki a ƙasar? Kuna iya latsa alamar sauti don jin amsar wannan tambaya tare da masana ta cikin shirin...
Shirin 'Lafiya Jari Ce' na wannan makon zai mayar da hankalli ne a kan gargaɗin da hukumar kiyaye ingancin abinci da magunguna a Najeriya, wato NAFDAC ta yi a kan hatsarin da ke tattare da amfani da maganin kashe ƙwari na Sniper a wajen adana kayan abinci domin kare su daga ƙwari. NAFDACdai ta jaddada haramcin da ta yi a kan amfani da wannan magani da ma sshigowa da shi Najeriya, bayan da ce bincikenta ya tabbatar da cewa maganin yana haddasa cutuka da suka haɗa da cancer.
A ranar Alhamis da ta gabata, shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da naira dubu 70 a matsayin mafi ƙarancin albashi a ƙasar, inda yayi alƙawarin sake nazari kan yiwuwar wani ƙarin a duk bayan shekaru uku, a cikin shirin mu Zagaya Duniya ,Nura Ado Suleiman ya zaɓo wasu daga cikin muhimman labarun lamurran da suka wakana a makon da ya ƙare domin bitarsu.
Shirin 'Duniyar Wasanni' na wannan mako tare da Khamis Saleh ya mayar da hankali ne kan nasarar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta El-Kanemi Warriors ta lashe kofin kalubale na Najeriya na shekarar 2024. A karshen watan da ya gabata ne dai ƙungiyar ta Jihar Borno ta samu nasarar lashe kofin kalubale na Najeriya, bayan da doke Abia Warriors da ci 2 - 0 a filin wasa na Mobolaji Johnson da ke Lagos.
Shirin tambaya da amsa na wannan makon ya amsa tambayoyi da dama da masu saurare suka aiko mana su. Danna alamar saurare don jin masoshin tambayoyin ta cikin shirin tare da Nasiru Sani
Ganin yadda annobar cutar Kwalara ta yaɗu a sama da jihohi 30, gwamnatin Najeriya ta bada umarnin ɗaukar matakan tabbatar da kawo ƙarshen cutar cikin makwanni 6.An dai ɗora nauyin ne akan hukumar duba gari ta kasa.Wakilinmu na Abuja Mohd Sani Abubakar ya zanta da shugaban hukumar Dakta Yakubu Mohd Baba don jin ta yadda za su tunkari wannan aiki. Kuna iya latsa alamar sauti domin sauraron zantawar ta su...
A cikin shirin Duniyarmu a yau,Michael Kuduson ya tattauna Mustapha Salisu Fernandez dan siyasa kuma mai sharhi kan lamuran yau da na kullum a Najeriya.
A wannan mako, shirin ya yi duba ne a kan yadda hare-haren ‘yan ta'adda suka kassara harkokin ilimi a arewacin Najeriya, shekara 10 kenan da 'yan ta'adda suka fara kai hari kan makarantu a Najeriya, lamarin da ya fara faruwa a shekarar 2014 a makarantar sakandaren ‘yan mata ta garin Chibok da ke jihar Borno a Arewa maso gabashin kasar. Bincike ya nuna cewa, tun bayan harin na 2014, 'yan ta'adda sun ci gaba da kai makamancinsa a kimanin makarantu 17, waɗanda suka haɗa da makarantun Firamare da sakandare da ma manyan makarantun gaba da sakandare, inda suka yi garkuwa da dalibai da dama, an sako wasu bayan biyan kuɗin fansa, wasu kuwa suna rike a hannunsu har zuwa yanzu. Cikin shekaru goma da fara ƙaddamar da irin wannan ta'addanci kan makarantu da ɗalibai, masana sun bayyana shakku kan gwamnatin Najeriya tare da zarginta da nuna halin ko in kula kan ilimi tare da rayukan al'ummar kasar musamman ɗalibai. Kuna iya latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin...
Shirin Mu zagaya duniya bisa al'ada kan yi bitar muhimman labaran da suka gudana a makon jiya, a wannan makon shirin tare da Nasrudden Muhammad, ya duba kan dambarwar yajin aikin NLC a Najeriya sai kuma yadda Jam'iyyar ANC a Afrika ta kudu ke laluben kafa gwamnatin haɗaka. Duk dai a cikin shirin za kuma kuji yadda ta ke ci gaba da kayawa a Gaza, bayan da Isra'ila ta ci gaba da kai hare-hare sassan Rafah ciki har da makarantar da ke ƙarƙashin kulawar Majalisar Ɗinkin Duniya.Waɗannan da ma sauran muhimman labarai na ƙunshe a cikin shirin.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin..
Mahukunta a Nijar sun ce ba za su bari motocin da ke ɗauke da lambar Jamhuriyar Benin damar tsallaka iyakar ƙasar da Najeriya domin shiga ko kuma fita daga Nijar ba, a maimakon haka, sai dai su zagaya zuwa cikin Burkina Faso da kuma Togo kafin komawa gida. Wannan dai alama ce da ke ƙara tabbatar da cewa alaƙa ta yi tsami a tsakanin ƙasashen biyu tun daga lokacin da aka kifar da gwamnati Mohamed Bazoum. Dan gane da wannan mataki, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Hima Barkire, sakataren tsare-tsare na ƙungiyar masu motocin dakon kaya a Nijar.Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawar ta su......
Shirin a wannan mako zai ba da hankali ne akan noman auduga,a shekarun baya, Nigeria ta kasance daya daga cikin kasashe masu tinkaho da noman auguda a nahiyar Afrika da duniya baki daya.Sai dai hankalin mahukuntan kasar ya koma ga bangaren man petur bayanda Allah ya albarkaci kasar da mai.Jihohin da suka yi fice a noman auduga a kasar, sun hada da Zamfara, Katsina, Kano, Adamawa, Bauchi da kuma Gombe.
Yau Musulmin duniya ke cika kwanaki 30 da fara azumin watan Ramadana, yayin da ake shirin bukukuwan Sallar Eid el Fitr daga gobe Laraba. Azumin na dauke da darussa da dama da Musulmi ke dauka.Ibrahim Malam Goje ya tambayi Farfesa Mansur Isa Yelwa na Jami'ar Abubakar tafawa Balewa dake jihar Bauchi a arewacin Najeriya, dangane da darussan da ya kamata musulmi ya yi amfani da su.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Za a ji yadda aka sake zabar sabuwar ranar gudanar da zaben shugabancin kasar Senegal,Al'ummar Sudan ta Kudu sun tsallake rijiya da baya, domin kuwa aniyar wani sabon mugu da ya bayyana ce ta watse bayanda ya yi kokarin shirya juyin mulki a kasar, duk da cewar har yanzu basu gama murmurewa daga kazamin yakin basasar da ya tagayyara su ba, wato dai ana kukan targade karaya kuma na neman kunno kai.
A cikin shirin na wannan mako,Michael Kuduson ya duba wasu daga cikin tambayoyin,ko wadanan hanyoyi ne ake bi domin samun tikiti kujerar wakili a Kwamity tsaro na MDD.Ya kuma duba wasu tambayoyi da suka jibanci bangaren tsaro da sauren su.
Al'ummar Jihar Kano dake Najeriya sun tashi da labarin murabus din da shugaban hukumar Hisbah, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya yi daga mukamin sa, sakamakon abinda ya kira sanyaya masa gwuiwar da gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi, wajen sukar yadda suke gudanar da aikin su.Wannan murabus din ta haifar da mahawara mai zafi a ciki da wajen jihar Kano, tare da hudubobi a Masallatan Juma'a dangane da muhimmancin hukumar da kuma rawar da take takawa.Nasirudeen Muhammed zai jagoranci shirin.
Hauhawar farashin kayan masarufi a Najeriya ya jefa rayuwar marasa karfi cikin halin kakanikayi, musamman yadda darajar kudin kasar na naira ke ci gaba da faduwa, yayin da kayan masarufi suka yi tashin gauron zabi. A halin yanzu dai farashin kayan abinci ya yi tashin da ba'a taba gani ba, yayin da gwamnati ke ci gaba da yi wa talakawa albishir cewar rayuwa za ta inganta nan gaba kadan. Dangane da irin wannan rayuwa ta kunci da talakan ke ciki, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Alhaji Shehu Ashaka, daya daga cikin dattawan kasar
Cikin shirin 'Mu Zagaya Duniya' na wannan makon tare da Nura Ado Suleiman, ya fara ne daga Kano a Najeriya, inda a ranar Juma'ar da ta gabata, kotun koli ta tabbatar da gwamna Abba Kabir Yusuf Abba na jam'iyyar NNPP a matsayin halastaccen gwamnan jihar. Shirin ya kuma sake waiwayar matakin jagoran mulkin Sojin Sudan, Janar Abdel Fattah al-Burhan na gindaya sharudda gabanin amincewa da shiga tattaunawa da bangaren jagoran dakarun RSF Mohamed Hamdan Dagalo da suka shafe fiye da watanni 9 suna gwabza yaki.
A Najeriya wata babbar matsala da ake fama da ita a kasar ita ce yawaitar satar kananan yara musamman a yankin arewacin kasar, inda bayanai ke cewa bayan sace su, ana safarar su ne zuwa wasu yankuna da ke kudancin kasar. Malam Ibrahim Yunusa Ibrahim da ke zaune a Gwagwalada kusa da Abuja, daya ne daga cikin gungun iyalai fiye da 50 wadanda aka sace ‘yayansa, kuma yanzu haka suke ci gaba da nema, ya yi wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal karin bayani a game da wannan matsalar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
Fira Ministan Jamhuriyar Nijar Ali Mahaman Lamine Zaine ya bukaci sauya lokacin da za su sake ganawa da ECOWAS kan shirin maida Mulki ga farar hula daga 10 zuwa ranar 25 ga watan nan na Janairu.Cikin wasikar da ya aika, Fira Ministan ya ce sauya lokacin zai bai wa Nijar damar gudanar da tattaunar kasa don karbar ra'ayoyin jama'a dangane da tsara makomar kasar a nan gaba.Dangane da wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Ambassada Abubakar Cika, tsohon jakadan Najeriya a Iran.
Gwamnatin Najeriya ta dakatar da amincewa da shaidar karatu daga kasashen Benin da Togo, sakamakon bankado asirin yadda wasu jami'o'in kasashen ke bayar da shaidar kammalla karatun digiri cikin wata guda. Tuni ‘yan kasar suka fara yaba wa gwamnatin la'akari da yadda wannan matsala ke kara kamarai.Umar Shehu Audu, shi ne dan jaridar da ya yi shigar burtu wajen bankado yadda ake gudanar da wannan kasuwanci mai riba, kuma yayin tattaunawarsa da RFI Hausa, ya ce, tabbas burinsa ya cika.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar zantawarsa da Rukayya Abba Kabara.
Maudu'in na wannan rana ya mayar da hankali ne, kan rahoton da kwamitin shugaban Najeriya ya fitar game da badakalar da aka samu tsohon shugaban babban bankin kasar, Godwin Emefile, da aikatawa na bude asusun bankuna sama da 500 a kasashen waje. Sai dai, Godwin Emefiele, ya yi watsi da rahoton binciken da ya bayyana cewar ya bude asusun bankuna har guda 593, wadanda yayi amfani da su wajen boye makudaden kudaden gwamnati da niyyar yin kwanciyar magirbi akansu.Cikin sanarwar da ya fitar a ranar Lahadi, Emefiele, wanda aka bayar da belinsa a ranar Juma'a, ya ce tuni ya bai wa lauyoyinsa umarnin shigar da kara kan rahoton da yace babu abinda ya kunsa sai karairayi domin bata masa suna.SHiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin da Nasiruddeen Muhammad ya gabatar.
Daga cikin labarun da Shirin ya kunsa akwai batun yadda yan ta'adda a Najeriya ke gina ramu suna boyewa, saboda barin wutar da suke sha daga sojojin kasar, sai kuma batun kammala ficewar sojojin Faransa a Nijer da dai sauran manyan labaran da suka hada da Burkina Faso, jamhuriyar Benin, yakin Isra'ila da Hamas, tare da dokar yan ci rani da Faransa ta amince da ita.