Podcasts about abdoulaye issa

  • 5PODCASTS
  • 89EPISODES
  • 9mAVG DURATION
  • 1EPISODE EVERY OTHER WEEK
  • Apr 15, 2025LATEST

POPULARITY

20172018201920202021202220232024


Best podcasts about abdoulaye issa

Latest podcast episodes about abdoulaye issa

Al'adun Gargajiya
Al'adar dalilin aure ta sauya sabon salo tsakanin al'ummar Hausawa

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Apr 15, 2025 9:47


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali ne kan al'adar nan ta dalilin aure, guda cikin al'adun Hausawa da aka shafe tsawon lokaci ana amfani da ita da nufin haɗin aure walau tsakanin ƴammata da Samari ko kuma Zawara. Kamar yadda kusan kowanne lamari ke tafiya da zamani itama al'adar ta juye, ta yadda ta koma cikakkiyar sana'a da wasu ɗaiɗaikun mutane ke da gogewa akanta, har ta kai ga ake buɗe ofisoshi don gudanar da ita.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.

Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Janjouna Ali Mahaman Sani kan zaɓen Gabon na gobe Asabar

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Apr 11, 2025 3:24


A kasar Gabon, ana ci gaba da yakin neman zabe a yau da ke jajiberin zaɓen Shugaban ƙasar,wanda ya haɗa 'yan takara takwas. Gwamnati ta ayyana ranar zaben gobe a matsayin ranar hutu, domin baiwa masu rajista a larduna damar yin balaguro.Ƴan adawa sun bayyana damuwarsu ganin ta yada shugaban majalisar sojin kasar ke amfani da kadarorin gwamanti a yakin zaben.Abdoulaye Issa ya tattauna da Janjouna Ali Mahaman Sani, masani siyasar kasar ta Gabon da kewaye.Ga kuma yada zantawar tasu ta gudana.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

ga ku gabon sani gobe shugaban abdoulaye issa
Bakonmu a Yau
Janjouna Ali Mahaman San: Kan zaɓen shugaban ƙasa a Gabon

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Apr 11, 2025 3:24


A Gabon, ana ci gaba da yakin neman zabe  a yau da ke jajuburin zaben Shugaban kasar,wanda ya hada 'yan takara takwas. Gwamnati ta ayyana ranar zaben gobe a matsayin ranar hutu, domin baiwa masu rajista a larduna damar yin balaguro. Ƴan adawa sun bayyana damuwarsu ganin ta yada shugaban majalisar sojin kasar ke amfani da kadarorin gwamanti a yakin zaben.  A game da zaɓen,  Abdoulaye Issa ya tattauna da Janjouna Ali Mahaman Sani, masanin siyasar ƙasar ta Gabon da kewaye.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu

ku gabon shugaban abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Aikin ƙwado da linzami na fuskantar barazanar disashewa

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Mar 25, 2025 10:18


shirin Al'adun Mu na Gado na wanan makon tareda Abdoulaye Issa ya  leka Jihar  Maradin Jamhuriyar Nijar inda al'adar aikin kwado da lizzami da aka share shekaru ana yin sa da hannu ke fuskantar barazanar samun babban koma baya sakamakon wasu sabbin na'urori ko teloli na zamani da aka samu masu aiki da Computer wadanda ke zuba wannan aiki ga riguna cikin gaggawa. Ku shiga cikin alamar sauti domin sauraron shirin....

Al'adun Gargajiya
Dawowar tsafe-tsafe a tsakanin al'umma kashi na biyu

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Mar 18, 2025 10:00


Shirin Al'adun Mu na Gado a wannan makon ya kawo muku ci gaban tattaunawa da Dakta Tahir da ake kira da Babba Impossible, wanda a makon daya gabata ya fara fashin baƙi a lamarin da yashafi tsafe-tsafe. Haka nan shirin ya leka Jamhuriyar Benin, inda gwamnatin ƙasar ta sanar da rusa wasu masarautu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa............

mu ku gado haka kashi abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Yadda Gwamnan Adamawa Alhaji Umaru Fintiri ya ƙara yawan Masarautun jihar

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Feb 25, 2025 10:02


Shirin ''al'adunmu na gado'' tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya leƙa jihar  Adamawa ta yankin arewa maso gabashin Najeriya don duba yadda gwamnatin Jihar ta ƙara yawan Masarautu a wannan jiha tun cikin shekarar da ta gabata. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.

ku shirin yadda umaru adamawa najeriya abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Tasirin naɗin da wasu Masarautu ke yiwa waɗanda ba ƙabilunsu ba

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Feb 18, 2025 10:04


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali kan al'adar nan ta naɗin sarauta da wasu masarautun gargajiya ke yi ga  ƙabilun da ba su ke da masarautar ba, wanda hakan ya biyo bayan sabbin naɗe-naɗe da ɗaya daga cikin manyan masarautun ƙabilar gwari a arewacin Najeriya ta yi wa wasu manyan shuwagabannin al'ummar fulani a jihar Neja. Wannan dai ba shi ne karon farko ba da ake samun masarautun Hausa da Fulani da ma wasu masarautun a yankin kudanci da kuma arewacin Najeriya ke baiwa ƙabilun da ke zaune a masarautar sarauta ba, abin da shirin Al'adu na wannan mako ya yi nazari akai tare da jin inda hakan ya samo asali da kuma alaƙar da ke tsakanin al'adun ƙabilar gwari da fulani daga masana al'adu da masarautu.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.

Al'adun Gargajiya
Yadda tsamin alaƙar gwamnati da Sarakuna ke raunata Masarautun gargajiya

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Feb 11, 2025 9:14


Shirin 'Al'adunmu na Gado' tare da Abdoulaye Issa a yau mayar da hankali kan rashin jituwar dake faruwa tsakanin gwamnoni a Najeriya da kuma ɓangaren Sarakunan gargajiya wanda har takai ga wasu jihohin na rushe Masarautu suna kuma kirkirar sababbi. A ‘yan shekarun nan, an sami irin wanann takun saka a jihohi irin Kano da Sokoto da Adamawa da kuma Katsina dukkaninsu a sassan Arewacin Najeriyar, inda masana tarihi da al'adu ke kallon al'amarin a matsayin barazana ga tsarin Sarautar mai dogon tarihi.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

ku kano gado yadda sokoto katsina adamawa najeriya gargajiya abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Ƴan China da ke Najeriya sun gudanar da bikin sabuwar shekararsu

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Jan 28, 2025 9:53


Shirin Al'adun mu na gado na wannan makon ya mayar da hankali ne ga bukuwan sabuwwar shekara na ƴan ƙasar China, bukukuwan da aka gudanar  a sassa daban daban na duniyar. A Najeriya, ƴan China ba su yi ƙasa a gwiwa ba wajen gudanar da wannan biki a biranen Abuja da kuma Lagas, wanda ya samu halarta  jama'a baki daga ciki da waje. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa.........

china ku bikin abuja najeriya abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Yadda al'adar shaɗi ko kuma Charo ke gudana tsakanin al'ummar fulani a baya

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Jan 21, 2025 9:59


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali ke kan al'adar shaɗi ko kuma Charo na sahun manyan al'adun ƙabilar fulani a ƙasashen Afrika ta yadda har sai wanda ya iya karɓaɓɓen shaɗi ke iya samun matar aure, yayinda a wasu lokutan ake gudanar da wannan al'adu a shagulgula don nishaɗi kuma jajirtacce shi ne jarumi.

Al'adun Gargajiya
Yadda Hausawa ke ƙoƙarin yin watsi da al'adar amfani da kwarya

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Dec 17, 2024 9:56


Shirin Al'adun mu na Gado a wannan makon ya mayar da hankali ne kan yadda Hausawa ke ƙoƙarin mancewa da al'adar amfani da kwarya, wacce ke cikin daɗaɗɗun kayan amfanin gida na Malam Bahaushe. To sai dai duk da irin tasirin Kwarya a cikin al'ummar ta Hausawa, sannu a hankalin wannan al'ada tana neman gushewa a tsakanin al'ummar ta Hausawa har ma da Fulani da suka rungumi al'adar daga baya. Masu harkar sayar da ƙore a yankin Arewacin Nigeria, na kokawa sosai kan rashin garawar sana'ar tasu sakamakon yadda Hausawa da Fulani suka rage amfani da Kwarya.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa........

ku gado arin fulani yadda masu watsi hausawa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
UNESCO ta sanya hawan Dabar Kano cikin kundinta na al'adun duniya

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Dec 10, 2024 10:35


Shirin Al'adun mu na Gado a wannan makon ya mayar da hankali ne kan matakin da Hukumar Raya Al'adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya UNESCO, na sanya hawan Dabar Kano a arewacin Najeriya cikin kundinta na al'adun duniya.Bincike ya nuna cewar an fara gudanar da al'adar hawa Daba a lokutan bikin ƙaramar Sallah da Babba tun kafin jihadin Shehu Usman Dan fodio zamanin Sarkin Kano Rumfa.  Masana a fannin tarihi sun ce zamanin Sarkin Kano Abbas, ya yi wa tsarin sauye-sauye wanda akan sa ake tafiya har zuwa wannan lokaci.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa........

unesco ku kano gado sanya daba duniya dabar sallah babba najeriya cikin masana majalisar abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Gushewar al'adar tatsuniya a cikin al'ummar Hausawa

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Nov 26, 2024 10:11


Shirin 'Al'adunmu na Gado' na wannan makon tare da Abdoulaye Issa ya tattauna dangene da gushewar a'adar tatsuniya wadda ke zama hanyar da al'ummar Hausawa ke amfani da ita wajen  ilmantarwa, fadakarwa da kuma tarbiyantar da yara ta hanyar shirya kagaggun labarai masu kunshe da darussa.

gado najeriya cikin hausawa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Tasirin al'adun gargajiya wajen tafiyar da mulki bayan ficewar turawa

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Nov 6, 2024 10:23


Shirin al'adunmu na Gado tare da Abdoulaye Issa kamar yadda ya saba a wannan makon ma ya leƙo wasu daga cikin masarautun Hausawa don jin tarihi da kuma tasirinsu ga al'umma. A wannan karon shirin ya yi duba kan tasirin al'adun gargajiya a matsayin jigon tafiyar da shugabanci bayan ficewar turawan Mulkin mallaka a Najeriya.Haka zalika za kuji hira ta musamman da sarkin Keffi a jihar Nassarawa wato Mai martaba  Alhaji Shehu Usman Shindo Yamusa.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.....

ku gado haka shirin bayan najeriya gargajiya hausawa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Sarkin Damagaram ya naɗa ɗan Najeriya a matsayin Talban masarautarsa

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Oct 8, 2024 9:55


Shirin Al'adu na wannan makon ya duba irin yanda masarautunmu na gargajiya ke kama hanyar zama ƙasa da ƙasa ta yanda sarakunan wasu masarautun ke nada ƴan wasu ƙasashe don basu mukamin a fadodinsu da sunan ƙarfafa zumunci da kyautata rayuwar jama'ar ƙasashen. A baya-bayan nan, mai Martaba Sarkin Damagaram da ke Jamhuriyar Nijar ya naɗa Alhaji Idriss Ousmane Kwado, a matsayin Talban Damagaram, bikin ya samu halartar gwamnonin jahar Zinder da na Katsina da wasu manyan sarakunan Arewacin Nigeria.  Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa.......

ku katsina najeriya jamhuriyar nijar damagaram abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Yadda aka gudanar da bikin Sallar Gani a Najeriya da Nijar

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Oct 1, 2024 10:19


Shirin Al'adun mu na Gado a wannan makon yayi duba ne kan yadda ake gudanar da bikin Sallar Gani. ita dai wannan sallar na daga cikin dadadun al'adar mallam Bahaushe, kuma har yanzu ana gudanar da wannan biki a  wasu masarautu a Arewacin Najeriya da kuma Jamhuriyar Nijar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa.......

ku bikin gado gani yadda nijar najeriya jamhuriyar nijar abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Shirye-shirye na musamman kan tarihin zuwan Turawa ƙasar Hausa

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Sep 17, 2024 9:56


Shirin Al'adun mu na Gado a wannan makon ci gaba ne game da jerin shirye-shiryen da muka faro kan zuwan Turawan mulkin mallaka zuwa ƙasar Hausa. Turawan sha mamakin abinda suka tarar, kasancewar sun samu al'ummar Hausawa da cikakkiyar wayewar addini, sarauta, sutura, karatu da rubutu da kuma wayewar kasuwanci da sauran harkoki na rayuwa. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare ta Abdoulaye Issa.......

ku gado asar hausa tarihin hausawa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Jerin shirye-shirye kan tarihin zaman takewar ƙasar Hausa kafin zuwan Turawa

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Sep 10, 2024 9:41


Shirin a wannan makon ya maida hankali ne yadda tsarin shugabanci ya ke a kasar Hausa kafin zuwan Turawan mulkin mallaka. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa.........

Al'adun Gargajiya
Irin rawar da masarautu ke takawa wajen kawo sauye-sauyen da suka kamata kashi na 2

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Jun 11, 2024 9:42


Shirin al'adun gargajiya na wannan mako ci gaba ne akan na makon daya gabata wanda ya duba muhimancin sarakunan mu da kuma irin rawar da za su iya takawa a wannan lokaci da ake fuskantar sauye-sauye a fanoni da dama. inda shirin ya tattauna da sarakunan masarautun Macina da kuma ta Nupe. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa.........

Al'adun Gargajiya
Irin rawar da ya kamata masarautu su taka wajen kawo sauye-sauyen da suka kamata

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Jun 4, 2024 10:42


Shirin al'adun gargajiya na wannan mako ya yi duba ne a kan muhimancin sarakunan mu da kuma irin rawar da za su iya takawa a wannan lokaci da ake fuskantar sauye-sauye a fanoni da dama. shirin ya tattauna da sarakunan masarautun Macina da kuma ta Nupe. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa.........

Al'adun Gargajiya
Yadda masarautar Hausawan Turai ke gudanar da ayyukanta

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Mar 19, 2024 10:17


Shirin Al'adun Gargajiya na wannan makon ya ziyarci masarautar Sarkin Hausan Turai Alhaji Surajo Jankado Labbo da ke kasar Faransa, inda Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da shi kan wasu batutuwa da suka shafi Hausawa.  Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa........

ku yadda turai faransa gargajiya hausawa bashir ibrahim idris abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Shiri na musamman kan marigayi Salissou Hamissou

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Feb 20, 2024 10:51


Shirin "Al'adunmu na gado" a wannan makon na musamman ne, wanda ya yi duba akan irin gudunmuwar da marigayi Salissou Hamissou ya bayar a bangaren al'adu, musamman a lokacin da ya ke gabatar da wannan shiri na Al'adunmu na gado.  Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa.....

ku shiri nijar abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Yadda al'adar auren Zaga ke shudewa tsakanin kabilar Sayawa a Najeriya

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Feb 13, 2024 9:28


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya yi duba kan yadda auren Zaga tsakanin al'ummar Sayawa ke komawa tarihi, salon al'adar da ke bayar da damar gadon mace ko kuma bayar da kyautar ta da sunan aure. Duk da tarin kabilun da ake da su a cikin jihohin Najeriya, kowace kabila na da irin nau'o'in al'adunta na gargajiya a fannonin rayuwa dabam dabam.Al'adun kan bambanta ne ta fuskar tsarin zamantakewa, ko ta fuskar auratayya da makamantarsu.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.....

ku shirin zaga duk yadda auren najeriya abdoulaye issa
Bakonmu a Yau
Abba Seidick kan cewa Faransa ta gaggauta aiwatar da sauyi a dangantakar ta da kasashen Afirka

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Nov 9, 2023 3:49


Yan majalisun dokokin Faransa sun bukaci gwamnatin kasar da ta gaggauta aiwatar da sauye sauye domin inganta dangantakar ta da kasashen Afirka, lura da yadda kasashen Rasha da China ke fadada karfin fada aji a yankin.    Dangane da haka Abdoulaye Issa ya tattauna da Abba Seidick masanin siyasa,zamantakewar kasar Faransa. 

china abba yan tada rasha afirka faransa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Bikin cika shekara daya da sarkin Katsinar Maradi yayi da hawa kan karagar mulki

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Nov 7, 2023 10:48


Shirin Al'adun mu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan makon, ya maida hankali ne kan cika shekara daya da sabon sarkin Katsinar Maradi,Mai Martaba Ahmad Ali Zaki Maremawa yayi kan karagar mulki. A dai ranar Asabar 5 ga watan Nuwambar shekarar da ta gaba ne aka nada Mai Martaba  Ali Zaki a matsayin Sultan na 2 na Katsinar Maradi. Shirin ya tabo batun nasarorin da sarkin ya samu a wannan lokaci da yayi yana jagoranci.Ku danna alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa....

Al'adun Gargajiya
Bafaranshiya ta lashe kyautar iya gasa biredi ta duniya

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Oct 31, 2023 10:31


Shirin Al'adun mu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan makon, ya tabo batun kyautar da matashiya 'yan Farsans ta lashe, inda ta zamo ta daya a duniya a wannan shekarar wajen iya gasa biridi. Tarihi dai ya nuna wannan ne karo na faro da mace ta taba lashe wannan kyauta. Haka nan, shirin ya kuma tattauna da masu ruwa da tsaki a bangaren kan wannan al'amari.Ku danna alamar sauti don sauraron cikakken shirin........ 

Al'adun Gargajiya
Yadda sauyin zamani ke shirin batar da sana'ar wanzanci

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Oct 10, 2023 10:11


Shirin Al'adun mu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan makon ya yi duba ne kan sana'ar wanzanci, wacce ke cikin sana'oin gargajiya na Hausawa da ke cike da abubuwa na al'ajabi. Mafi yawancin wanzamai gadon sana'ar suke yi daga iyayensu, amma wani lokacin, ana samun wasu daga waje da suke sha'awar koyon sana'ar don su samu hanyar cin abici. Duk kuwa da yadda bincike ya nuna cewa sana'ar ba abar da mutum zai koya cikin sauki da sauri ba ce.  Sakamakon yanda ake samun sauyin zamani, yanzu wanzamai sun fara fuskantar kalubale na rashin tabbas a sana'arsu saboda fara bacewar sana'arsu. Ku danna alamar sauti don sauraron cikakken shirin........ 

sana ku shirin mafi zamani duk yadda batar hausawa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
An kaddamar da shirin farfado da salon kidan Duma a Nijar

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Aug 31, 2023 10:12


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali ne kan bikin kidan Duma, guda cikin al'adun jihar Maradi da ke kokarin gushewa.  A wani kokari na dakile gushewar al'adu, gwamnatin jamhuriyyar Nijar ta kaddamar da wani gangamin horar da matasa kidan Duma, salon kidan da ke da shahara a tsakanin garuruwan Hausawa.Akwai dai salo kala kala na kidin Duma da yanzu ke zama inda mata sun fi son gargajiya yayin bukukuwansu abin da ake kira Partyn kauyawa Tasi'u Bakwai ya mana filla filla ma'anar kidi irinsu adamulmula, yar sahabi da sauransu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin..............

Al'adun Gargajiya
Yadda babban taron masarautar Hausawar Afrika ya gudana a Kano

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Jun 27, 2023 10:15


Shirin 'Al'adunmu na Gado' tare da Abdoulaye Issa a wannan makon ya mayar da hankali ne kan yadda aka gudanar da bikin masarautar Hausawar Afrika a jahar Kano da ke tarayyar Najeriya, kuma a lokacin taron an gudanar da nade-nade da bama da akayi da zummar hada kan al'ummar Hausawa da ke kasashe daban daban. Toh domin jin yadda taron ya gudana sai ku latsa alamar sauti don jin cikakken shirin......

afrika kano gado toh taron yadda najeriya hausawa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Tasirin fasahar AI wajen samar da sauyi ga al'adun gargajiya

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Jun 16, 2023 10:24


Shirin Al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa ya mayar da hankali game da tasirin da sabuwar fasahar AI ta sanya na'urori basirar dan adam za ta yi ga tsarin al'adun gargajiya. Baya ga gudunmawar da fasahar ta AI ko kuma Artificial Intelligence za ta bayar wajen adana kayakin tarihi ana ganin za kuma ta taimaka matuka wajen dakile tarin al'adu ko kuma harsuna daga bacewa.Bayanai na nuna cewa wannan fasaha da ake sanya na'urori basirar dan adam za ta bunkasa sassan da suka shafi musayar al'adu tsakanin kabilu daban.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin............

Al'adun Gargajiya
Al'adun Auren kabilar Bugaje a Jamhuriyyar Nijar

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Jun 6, 2023 10:06


Shirin al'adunmu na Gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali ne kan al'adar auren Bugaje a Jamhuriyyar Nijar guda cikin al'adun da ke mutunta bukukuwan gargajiya da kuma dokokin hada zuriya. A cikin shirin za ku ji yadda Auratayya ta ke a cikin kabilar ta Bugaje, wadanda aurensu ke da matukar tsada musamman idan za su hada zuriya da wani yare daban.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.........

Al'adun Gargajiya
Al'adu da sarautun gargajiyar Hausawa a garin Kumasi na kasar Ghana

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later May 30, 2023 9:37


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa ya mayar da hankali ne kan al'adun al'ummar yankin Kumasi da ke kasar Ghana, yankin da ke kunshe da tarin al'ummar Hausawa a kasar ta yammacin Afrika. A cikin shirin na wannan mako za kuma kuji yadda cefane ke wakana a tsari na al'adun Hausa wanda a wasu lokutan ke cin karo da matsalar al'mubazzaranci wato rashin tattali daga Mata a dai dai lokacin da ake fama da matsin rayuwa.Wadannan dama muhimman batutuwan da suka shafi al'adun Malam Bahaushe na kunshe a cikin wannan shiri.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shiri..........

Al'adun Gargajiya
Kananun Kabilu na hadewa da juna don kaucewa barazanar gushewa

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later May 16, 2023 9:56


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya yi duba ne kan yadda kananan kabilu ke dunkulewa a sassan Najeriya a wani yunkuri na habaka al'adunsu, wannan mataki na zuwa a dai dai lokacin da kananun kabilun ke fuskantar mamaya daga manya. A baya-bayan nan wasu kabilu 8 daga arewacin Najeriya suka sanar da dunkulewa waje guda don habaka al'adunsu na gargajiya da kuma dakile barazanar shudewa.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.........

ku shirin juna najeriya abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Mabanbantan abincin gado a kasashen Afrika

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later May 9, 2023 9:56


Shirin Al'adunmu na Gado na wannan makon ya yi nazari kan mabanbantan nau'ukan abinci da ake ci a wasu kasashen Afrika ta yamma kamar Ghana, Najeriya da Nijar. Kasashen Afrika na da ire-iren abincin da suka gada daga iyaye da kakanni wanda watakila har duniya ta nade ba za su iya yin watsi da su ba.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa.

ghana afrika ku gado nijar najeriya abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Gasar musayar al'adu da harsuna tsakanin masoya tashar Radiyo Faransa

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Apr 4, 2023 9:49


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan karon ya mayar da hankali kan gasar da masoya tashar radiyon Faransa RFI da aka fi sani da ''Club RFI'' suka shirya a birnin Lagos na Najeriya, wadda ke da nufin musayar al'adu da yaruka tsakanin mabanbantan masu sauraron tashar. Gasar wadda ita ce karon farko da aka taba gudanar da makamanciyarta na da nufin fadada fahimtar yaruka tsakanin al'ummomi, tare da bayar da kyautukan kara kwarin gwiwa ga wadanda suka yi nasara.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.......

lagos ku shirin najeriya faransa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Tarihin masarautar Fulani a jihar Lagos ta Najeriya

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Feb 14, 2023 9:52


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan makon ya mayar da hankali ne kan gidan sarautar, Sarkin Fulani a jihar Lagos ta Najeriya, Alhaji Abubakar Muhammad Banbado. Ayi saurare Lafiya. 

lagos shirin fulani tarihin ayi najeriya abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Nadin Sarautar madakin Kanem a jihar Pulato ta Najeriya

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Feb 7, 2023 10:13


Shirin Al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa wanda a ke tabo mana batutuwa masu alaka da al'adun gargajiya ko bukukuwan al'adu ko masarautun gargajiya a kasar Hausa, a wannan mako ma shirin ya yi duba kan Sarautar Madakin Kanem a jihar Pulato ta Najeriya.

nadin hausa najeriya abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Tasirin bikin al'adu na tunawa da dokin iska dan Filinge

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Jan 31, 2023 10:18


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya sake yin duba kan tasirin gasar tseren doki da ya samo asali daga bikin al'adun tunawa da dokin iska dan Filinge karo na 6, Ayi saurare Lafiya.

Al'adun Gargajiya
Nadin sabon Sarki a garin Mayahe a Maradi karon farko a shekaru 70

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Jan 17, 2023 10:20


Shirin Al'adun mu na gado a wannan mako tare da Abdoulaye Issa ya yi tattaki zuwa garin Maradi na Jamhuriyyar Nijar inda ya yi mana duba kan bikin nadin Isa Gado a matsayin sabon sarkin Mayahe, nadin da ke zuwa bayan mutuwa Mai martaba Sarki Gado Sabo da ya shafe shekaru 71 a karagar mulki. A yi saurare Lafiya.

Al'adun Gargajiya
Yadda aka kafa Masarautar Hausawa a Benin

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Nov 29, 2022 9:33


Shirin Al'adunmu na Gado na wannan makon tare da Abdoulaye Issa ya kai ziyara ne can fadar mai martaba Sarkin Machina da ke jihar Yobe ta Najeriya da kuma Masarautar Hausawa a garin Port-Novo na kasar Benin. Masarautar ta Machina ta yi bayani kan yadda take tattalin al'adun da al'ummarta ta gada tun fil azal. Kazalika shirin ya ziyarci garin Ajase na birnin Port-Novo da ke Jamhuriyar Benin, inda Hausawa suka shafe fiye da shekaru 150 a wannan yanki tare da kafa Masarautarsu.

benin gado machina kafa yadda yobe najeriya hausawa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Taron bajekolin zane-zanen gargajiya na yammacin Afrika a Lagos

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Nov 8, 2022 10:02


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali kan taron bajekolin fasahohin kere-kere da zane-zanen gargajiya na yammacin Afrika da ya gudana a birnin Lagos na kudu maso yammacin Najeriya wanda aka yiwa lakabi da Art X. Ayi saurare Lafiya.

afrika lagos shirin taron zanen najeriya gargajiya abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Lalacewar tarbiyya a tsakanin matasan Hausawa saboda kwaikwayon al'adun ketare

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Nov 1, 2022 10:02


Shirin al'adunmu na Gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali kan lalacewar tarbiyya a tsakanin al'umma matsalolin da ake dora alhakinsu kan kwaikwayon dabi'un ketare a kasashen Hausawa.

gado shirin hausawa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Tarihin kafuwar Zabarmawa a Najeriya da kuma barazanar gushewarsu

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Oct 5, 2022 10:22


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa ya mayar da hankali kan tasirin kabilar Zabarmawa a Najeriya, da kuma kokarin da ake na hana gushewarta a sassan kasar duk da cewa kabilar ta fi yawa a jamhuriyar Nijar.

shirin kuma tarihin nijar najeriya abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Bikin ranar nuna al'adun kabilar Tubawa a sassan Duniya- 2

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Sep 28, 2022 10:13


Shirin al'adunmu na gado da ke zuwar muku kowanne mako tare da Abdoulaye Issa a wannan karon ya dora ne kan bikin kabilar tubawa da ya zo muku a makon jiya, kabilun da ke da matukar tasiri a kasashen Najeriya da Nijar.

Bakonmu a Yau
Alkasoum Abdourrahmane a kan caccakar da Mali ta wa Faransa da MDD

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Sep 26, 2022 4:16


Firaministan Mali da sojoji suka nada ya caccaki Faransa da kuma Majalisar Dinkin Duniya a wani jawabin da ya gabatar mai cike da koke kan tabarbarewar tsaro a kasarsa. A makon da ya gabata ne aka nada Kanar Abdoulaye Maiga, a matsayin Firaministan rikon kwaryar Mali, wanda ya zargi Faransa da zamewa kasar sa kayar kifi a wuya. Abdoulaye Issa ya tattauna da Alkassoum  Abdourahamane, mai sharhi kan lamuran zamantakewa da siyasar kasashen yammacin Afrika dangane  da  jawabin  Firaministan  kasar  ta Mali.

afrika mali faransa majalisar dinkin duniya abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Tasirin Masarautar Birtaniya ga Masarautun nahiyar Afrika

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Sep 13, 2022 10:12


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa ya yi duba kan tasirin Sarauniyar Ingila Elizabeth ta biyu ga masarautun nahiyar Afrika, la'akari da kasancewar masarautarta daddiya kuma abar koyi ga galibin masarautun Duniya ta fuskar rike al'adu da dabbaka su.

afrika shirin duniya birtaniya abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Yadda aka gudanar da bikin ranar Hausa cike kayatarwa fiye da shekarun baya

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Aug 30, 2022 10:06


Shirin Al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa ya mayar da hankali kan yadda aka gudanar da bikin ranar Hausa ta Duniya wanda a wannan karon ya gudana a kusan dukkanin kasashen yammacin Afrika da na Sahel baya ga Hausawan da ke zaune a wajen nahiyar Afrika da suka gudanar da nasu bikin na musamman.

Al'adun Gargajiya
Yadda harshen hausa ke mamaye kananan yaruka a Najeriya

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Aug 23, 2022 9:54


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa ya yi duba kan yadda harshen Hausa ke hadiye kananan yaruka tare da mamayar manyan yaruka a Najeriya da sauran kasashen makwabta.

shirin hausa yadda najeriya abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Tarihin al'adar Sallar Biannu a garin Agadez na Jamhuriyar Nijar

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Aug 16, 2022 10:26


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya yi duba kan bikin Biannu a jihar Agadez ta Jamhuriyyar Nijar, bikin da ya juye zuwa Sallah mai dogon tarihi a yankin na abzinawa da kusan kowa ke mararin isowarsa.

shirin garin tarihin sallah agadez jamhuriyar nijar abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Yadda ake fuskantar bacewar kayakin tarihi a Najeriya

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Aug 9, 2022 9:34


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali bacewar gidaje da sauran muhimman kayakin tarihi a sassan Najeriya duk da kiraye-kirayen da ake yiwa mahukunta don alkinta irin wadannan kayaki.

shirin tarihi yadda najeriya abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Yadda aka kulla yarjejeniyar kawo karshen zaman kayakin tarihin Benin a Faransa

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Aug 2, 2022 10:02


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan makon ya yi duba kan ziyarar shugaban Faransa a kasashen yammacin Afrika 3 ciki har da Jamhuriyyar Benin inda yayin zantawar shugabannin biyu wato Patrice Talon na Benin da Emmanuel Macron na Faransa sun rattaba hannu kan yarjejeniyar kawo karshen zaman kayakin tarihin kasar a Paris. A yi saurare Lafiya.

Bakonmu a Yau
Tahiru Gimba: Kan katse yarjejeniyar gina layin dogo a Nijar da Benin

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jul 26, 2022 3:43


Kasashen Jamhuriyar Nijar da Benin sun kawo karshen yarjejeniyar gina layin dogon da ke tsakaninsu da kamfanin Bollore na Faransa, da aka bai wa kamfanin gina layin dogon da zai hada kasashen biyu. Matakin dai na zuwa ne bayan da kamfanin ya gaza kammala aiki a kan lokacin da aka kulla yarjejeniya tun farko da shi, abin da ya janyo cikas ta fannin dangantakar kasashen biyu. To Dangane da haka Abdoulaye Issa ya tattauna da Tahiru Guimba, dan siyasa, wanda a lokacin suka bayyana adawarsu  da wannan aiki. Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu

ku benin dogo layin katse nijar gimba bollore faransa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Tarihin Masarautar Maradin Katsina

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Jul 26, 2022 9:42


Shirin Al'adunmu na Gado na wannan makon tare da Abdoulaye Issa ya yi nazari ne kan tarihin Masarautar Maradin Katsina da ke Jamhuriyr Nijar.

gado tarihin katsina abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Ci gaban tarihi da takaddamar da ta dabaibaye Masarautar Lokassa a Benin

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Jul 5, 2022 10:41


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya dora kan shirin makon jiya da ya mayar da hankali kan tarihin masarautar Hausawan Lukusa, karkashin jagorancin mai martaba sarkin Hausawa kuma sarkin musulmin yankin Alhaji Abdu Nuhu.

benin shirin tarihi hausawa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Bikin nadin Wazirin Katsina Sanata Ibrahim Inda

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Jun 28, 2022 9:38


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan makon ya mayar da hankali ne kan bikin nadin wazirin masarautar Katsina Sanata Ibrahim Inda wanda mai martaba Alhaji Abdulmuminu Kabir Usman ya nada a ranar 11 ga watan da muke ciki na Yuni. Ayi saurare Lafiya.

Al'adun Gargajiya
Tarihin Masarautar Lokossa da Hausawa ke shugabanci a jamhuriyar Benin

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Jun 21, 2022 9:55


Shirin Al'adunmu na Gado tare da Abdoulaye Issa ya yada zango a yankin Lokossa na Jamhuriyar Benin, inda wata takadama ta kuno kai a unguwar zongo dangane da wata masarauta karkashin shugabancin Nuhu Abdou .

benin gado tarihin hausawa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Bikin gargajiya na kabilar fulani Unaru Ja'e a jamhuriyyar Nijar

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later May 10, 2022 9:51


A kowacce shekara ne ake wannan biki na Unaru Ja'e ko da ya ke an samu tsaiko tsawon shekaru ba tare da gudanar da shi ba, gabanin dawo da shi a wannan shekara. Bikin wanda al'adun Fulani akan gudanar da shi a garin hawan dawaki a Jamhuriyyar Nijar na kunshe da kowa, dambe da shadi baya ga nuna bajinta ko zaben sarauniyar kyau da sauran muhimman al'adu, Ayi saurare Lafiya tare da Abdoulaye Issa.  

bikin fulani ayi nijar gargajiya abdoulaye issa
Bakonmu a Yau
Issaka Manzo a kan shirin girke dakarun Turai a iyakar Nijar

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Apr 20, 2022 3:37


Majalisar Dokokin Jamhuriyar Nijar a jiya Talata ta fara muhawara kan shirin girke dakarun kasashen Turai na Faransa a kan iyakar kasar domin taimaka mata wajen yaki da ‘yan ta'adda. Matakin na zuwa ne bayan janyewar da dakaru Faransa na Barkhane suka yi daga Mali, sakamakon tabarbarewar da dangantaka ta yi tsakanin kasashen biyu, saboda yarjejeniyar tsaron da kasar ta Mali ta kulla da kasar Rasha. A game da haka, Abdoulaye Issa ya tuntubi …Issaka Manzo tsohon Dan majalisa a jam'iyyar  RDR CANJI.

mali shirin manzo rasha barkhane nijar turai talata faransa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Gushewar al'adar suturar hausawa 1

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Apr 19, 2022 10:43


Sutura ko kayan sawa, suna daga cikin abubuwan da suka bambanta tsakanin 'Yan adam da dabbobi. Kamar yadda aka sani, al'ummomi dabam dabam,  na da irin nau'i ko kalan kayan da suka fi sawa. Da zarar ka ga mutum da irin wannan kaya, zaka fara tunanin cewa dan kabila ko kuma dan yanki kaza ne. A cikin shirin a'adun mu na gado daga nan Rfi ,Abdoulaye Issa ya duba halin da ake Mallam Bahaushe ke rayuwa a wannan zamani a cikin wannan shiri,kamra dai yada za a ji. Baya ga al'amarin sutura,Abdoulaye Issa ya jiyo ta bakin mai sana'ar kunun gyade a Jihar Bauchi dake Najeriya.

yan rfi kamar baya sutura najeriya hausawa abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Nadin Sarkin matasa a masarautar Abzin dake Agadez

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Apr 12, 2022 10:35


A cikin shirin al'adun mu na gado, Abdoulaye Issa ya tattauna da sarkin matasan Arewa biyo bayan nadin da aka yi masa a fadar sarkin Abzin dake jihar Agadez a Jamhuriyar Nijar. Shirin ya bai wa Sarkin matasa Abdoul Wahid Ayouba damar sanar da masu sauraren mu  muhimancin wannan mukami da kuma kawo karin haske dangane da irin rawar da ya dace ya taka a masarautar Abzin dake Agadez.

shirin dake nadin agadez arewa matasa jamhuriyar nijar abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Yadda 'yan mata ke sauya halittar lebensu don kara kyau a Kamaru

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Apr 5, 2022 10:34


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali kan wata al'ada da mata kan yi a Kamaru wajen sauya halittar lebbansu zuwa bakake duk a yunkurin kawata kyawunsu, ayi saurare lafiya.

Al'adun Gargajiya
Rawar da sarakunan gargajiya ke takawa wajen samar da zaman lafiya

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Mar 15, 2022 10:05


Shirin Al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa ya yi dubi kan rawar da sarakunan gargajiya kan taka cikin al'umma don samar da zaman lafiya mai dorewa, bugu da kari shirin wanda bisa al'ada a farkonsa kan tabo batun girke-girken gargajiya, a wannan karonma akwai zantawa da wata mai abincin siyarwa kamar yadda za ku ji a cikin shirin. Ayi saurare Lafiya.

zaman samar ayi gargajiya abdoulaye issa
Al'adun Gargajiya
Tattaunawa da dan galadiman dogon dutse kan tarihin arawa a Nijar

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Mar 8, 2022 10:53


Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa ya mayar da hankali kan tarihin arawa da sarautar kwanawa a dogon dutse na Jamhuriyyar Nijar.

Al'adun Gargajiya
Bikin baje kolin kayayyakin tarihi da Benin ta karbo daga Faransa

Al'adun Gargajiya

Play Episode Listen Later Feb 22, 2022 10:30


Shirin  'Al'adunmu Na Gado' ya ziyarci wajen bkin baje kolin kayayyakin tarihi da Jamhuriyar Benin ta karbo daga Faransa. A cikin shirin, Abdoulaye Issa ya gana da ma'aikatan gidan ajiyar kayayyakin tarihi.

Mu Zagaya Duniya
Bitar wasu daga cikin muhiman labarai na shekara ta 2021 a jamhuriyar Nijar

Mu Zagaya Duniya

Play Episode Listen Later Jan 1, 2022 20:20


A cikin wannan shirin ,Abdoulaye Issa ya mayar da hankali tareda duba wasu daga cikin muhiman labarai na Jamhuriyar Nijar na shekara ta 2021 daga nan sashen hausa na rediyon Faransa rfi.

bitar daga wasu cikin jamhuriyar nijar faransa abdoulaye issa
Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Ibrahim Halifa kan gayyatar ministan tsaro nijar da Majalisa ta yi

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 8, 2021 3:02


A Jamhuriyar Nijar 'yan Majalisun dokoki sun gayyacin Ministan tsaron kasar domin amsa wasu  tambayoyi, biyo bayan hare-haren ta'addanci da suka yi sanadiyyar mutuwar da dama daga cikin yan kasar. Dan Majalisa Ibrahim Halifa na daga cikin yan majalisun da suka gayyato Ministan tsaron Jamhuriyar Nijar, kuma Abdoulaye Issa ya samu tattaunawa da shi,ga dai yada zantawar ta su ta gudana.

nijar jamhuriyar nijar abdoulaye issa
Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Issaka Manzo kan taron kasa da kasa game da tsaro a Senegal

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Dec 7, 2021 3:44


A taron kasa da kasa dangane da sha'anin da ya shafi tsaro da ke gudana a birnin Dakar na Senegal, Shugaban Nijar Bazoum Mohammed ya bayyana kuskuren da kasashe suka yi a sha'anin da ya shafi yaki da  fataucin makamai da aka yi ta kwasa daga Libya zuwa sauren yankunan Sahel. Kalaman Shugaban da ke zuwa a dai-dai lokacin da lamarin rashin tsaro ke ciwa jama'a tuwo a kwariya. Dangane da haka Abdoulaye Issa ya tattauna da Issaka Manzo tsohon dan Majalisa a Jamhuriyar Nijar.

game senegal libya dakar sahel manzo kasa taron jamhuriyar nijar abdoulaye issa
Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - Shugaban Faransa Emmanuel Macron na ganawa da 'Yan Afrika a Montpellier

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Oct 8, 2021 3:48


Shugaba Emmanuel Macron ya  karbi bakuncin wani taro kan Afirka a yau  Juma'a tareda matasan Nahiyar Afrika a birnin Montpellier dake kudancin kasar ta Faransa. Daga cikin zantukan da Shugaba Macron zai tattaunawa da matasan sun hada da yanayin siyasa tsakanin Faransa da Afrika. Abdoulaye Issa ya samu tattaunawa da Abba Seidik  wanda ya mayar da hankali tareda duba alfanun taron dake gudana a Monpellier,Abba Seidik mai sharhin ne kuma dan Jarida dake zaune a kasar ta Faransa. Shugaban Faransa ya gayyaci matasan ne ba tareda baiwa Shugabanin kasashen Afrika damar halartar taron na Montpellier ba.

afrika emmanuel macron montpellier daga afirka faransa shugaban abdoulaye issa
Wasanni
Wasanni - An fara gasar kwallon kafar mata ta Aisha Buhari a Lagos

Wasanni

Play Episode Listen Later Sep 17, 2021 9:50


Shirin 'Duniyar Wasanni' tare da Abdoulaye Issa ya duba gasar kwallon kafa ta mata wadda uwargidan shugaban Najeriya, Aisha Buhari ta dauki nauyin shiryawa, wadda ta samu halartar manyan masu ruwa da tsaki a harkar kwallon kafa a duniya har da shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA Gianni Infantino.

mata lagos buhari najeriya abdoulaye issa
Wasanni
Wasanni - Yiwuwar canza shekar Mbappe daga PSG zuwa Real Madrid

Wasanni

Play Episode Listen Later Aug 27, 2021 10:02


A cikin shirin 'Duniyar Wasanni' na yau, Abdoulaye Issa ya duba batun yiwuwar komawar dan wasan gaban PSG, Kylian Mbappe zuwa Real Madrid. Rahotanni ma na cewa Real Madrid ta kara yawan kudin da ta taya dan wasan zuwa Yuro miliyan 180.

Wasanni
Wasanni - Jadawalin kasashen da za su fafata a gasar nahiyar

Wasanni

Play Episode Listen Later Aug 20, 2021 10:44


Shirin Duniyar Wasanni na wannan makon tare da Abdoulaye Issa ya tattauna ne kan jadawalin kasashen da za su fafata a gasar cinn kofin kasashen Afrika da za a gudanar a Kamaru.

afrika kamaru abdoulaye issa
Wasanni
Wasanni - Lionel Messi a kungiyar PSG ta kasar Faransa

Wasanni

Play Episode Listen Later Aug 13, 2021 10:15


Kungiyar PSG ta sanar da cewar Lionel Messi ya sanya hannu a kwangilar shekaru biyu bayan barin  kungiyar Barcelona inda ya kwashe shekaru 21 yana mata wasa.PSG za ta dinga biyan sa Euro milyan 40,Abdoulaye Issa a cikin shirin  Duniyar wasanni ya duba alfanun zuwa Messi PSG da ma irin kalubalen dake gaban sa.

barcelona euro lionel messi psg faransa duniyar abdoulaye issa
Wasanni
Wasanni - Yadda kasashen Turai suka kara da juna a gasar Euro rukunin kasashe 16

Wasanni

Play Episode Listen Later Jul 2, 2021 10:52


Shirin Duniyar Wasanni tare da Abdoulaye Issa na kawo muku muhimman batutuwan da suka shafi wasanni a sassa daban-daban na Duniya, inda shirin a wannan makon ya mayar da hankali kan yadda zango wasannin kasashe 16 na gasar cin kofin Turai ta Euro 2020 ya gudana.  

Wasanni
Wasanni - Nijar ta kaddamar da filin wasan damben kokwawa mafi girma a Afrika

Wasanni

Play Episode Listen Later Jun 25, 2021 10:05


Shirin Duniyar Wasanni tare da Abdoulaye Issa na wannan makon ya mayar da hankali kan yadda bikin bude katafren filin wasan kokwawa mafi girma a yammacin Afrika da Nijar ta kaddamar ya gudana a jihar Maradi ta kasar.

Wasanni
Wasanni - Halin da ake cikin a game da wasan tseren keke a Nijar

Wasanni

Play Episode Listen Later Jun 4, 2021 10:33


A cikin shirin 'Duniyar wasanni' Abdoulaye Issa ya yi mana nazari a game da halin da wasan tseren keke ke ciki a Jamhuriyar NIjar, da kuma yadda wasu ke kokarin farfado da wasan da yayi likimo.

game keke nijar cikin jamhuriyar nijar abdoulaye issa
Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - Tattaunawa da masanin harkokin siyasa Abba Sadik kan ziyarar Macron a Rwanda

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later May 27, 2021 3:50


A yau alhamis ne Shugaban Faransa  Emmanuel Macron ya kai ziyara kasar Rwanda,Shugaba Macron da sunan Faransa ya amsa cewa Faransa ta aikata ba dai-dai ba. To dangane da haka Abdoulaye Issa ya tattauna da Abba Sadik dan jarida kuma manazarcin harkokin siyasar kasashen Afrika.

Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - Tattaunawa kan rayuwar Shugaban kasar Tanzaniya Marigayi John Magufuli

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Mar 20, 2021 3:34


Da yammacin jiya Laraba 17 ga watan maris 2021  ne mataimakiyar shugaban kasar Tanzania ,  da za ta dana kujeran shugabancin kasar  Samia Hassan, ta sanar da mutuwar shugaban kasar John Magufuli . Shugaban na Tanzania da yan kasar ke  yi wa lakabi da  Bulldozer ‘ Sarkin aiki ya rasu ne ya na dan shekaru 61 a Duniya. To domin jin irin rawar da marigayin ya taka a rayuwarsa Abdoulaye Issa ya tattauna  da Abba Seidik mai sharhin kan siyasar duniya daga birnin Paris.  Ga kuma  yada firar ta su ta kasance.

ga tanzania duniya magufuli shugaban abdoulaye issa
Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - Tattaunawa da Alzubayr Abubabakr a kan koma baya da aka samu a yaki da rashawa a Najeriya

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jan 28, 2021 3:53


Kungiyar Transparency International a rahoton shekara-shekara da take fitarwa,ta ce Najeriya ta samu koma baya a yakin da take da rashawa Dangane da haka, Abdoulaye Issa ya  tattauna da Barrista Alzubyr Abubakar dake Najeriya, wanda ya bayyana mana irin illar da cin hantsi ke yi wa tattalin arzikin kasashen mu.

samu koma baya yaki najeriya abdoulaye issa
Wasanni
Wasanni - Nazari kan gasar CHAN 2021 da ke gudana a Kamaru

Wasanni

Play Episode Listen Later Jan 25, 2021 11:01


A  cikin shirin 'Duniyar Wasanni' Abdoulaye Issa ya yi nazari a kan gasar ci kofin nahiyar Afrika ta 'yan wasa masu murza tamaula a gida, wato CHAN, wanda ke gudana a Kamaru a halin yanzu.

chan afrika kamaru abdoulaye issa
Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - Kamaru ta shiga jerin kasashe masu matsalar rashin yiwa yara takardun haihuwa

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Jan 25, 2021 3:25


Kamaru ta shiga jerin kasashe da akasarin yara basu da takardun shaidar haihuwa, zalika bincike ya nuna cewar tsawon shekaru an daina baiwa jama’a takardun shaidar zama dan kasa. Wannan kalubale ya haifar da fargaba kan makomar yaran da suka rasa shaidar haihuwa, la’akari da cewar da shaidar ake rajistar shiga makarantu. Dangane da wannan batu, Abdoulaye Issa ya tattauna da Barista Hamza Mohammed kuma mai sharhi a kasar ta Kamaru.

Wasanni
Wasanni - Gasar cin kofin Afrika na Confederation a Kamaru

Wasanni

Play Episode Listen Later Jan 23, 2021 10:25


A cikin shirin Duniyar wasanni daga nan sashen hausa na Rfi za mu yi tattaki zuwa kasar Kamaru, inda kasashe 16 da suka hada da Kamaru mai masaukin baki, Zimbabwe, Mali ,Burkina Faso, Libya,Nijar, Jamhuriyar dimokuradiyyar Congo, Morroco, Togo, Rwanda, Uganda, Zambia, Tanzania, Guinea sai Namibia za su fafata a tsakanin su a gasar cin kofin kasashe Afrika na Confederation. Abdoulaye Issa ke farin cikin gabatar muku da shirin na wannan lokaci. Sai ku biyo mu.

Wasanni
Wasanni - Hasashen masana dangane da harkar wasannin kwallon kafa a cikin wannan shekara ta 2021

Wasanni

Play Episode Listen Later Jan 18, 2021 10:49


Shirin Duniyar Wasanni na wannan mako tare da Abdoulaye Issa ya maida hankali ne kan hasashen masana dangane da harkar wasannin kwallon kafa a cikin wannan shekara ta 2021, bayan da coronavirus ta dakushe harkokin a shekarar 2020 da ta gabata.

kafa wannan cikin masana abdoulaye issa
Bakonmu a Yau
Bakonmu a Yau - 'An fi muzgunawa 'yan jarida a nahiyar Africa - UNESCO

Bakonmu a Yau

Play Episode Listen Later Sep 14, 2020 3:59


14 ga kowane watan Satumbar duk shekara ce ranar da hukumar UNESCO ta ware don yin kira ga mahakunta a game da kare hakkokin manema labarai dake fuskantar barazana a aikin su a kasashen Duniya. Nahiyar Afrika na daga cikin yankunan dake fama da irin wadanan matsalloli,kamar dai yada za ku ji a tattaunawa da Abdoulaye Issa ya yi da Abbas Ibrahim ,shugaban manema labarai ta NUJ reshen Kano.

Wasanni
Wasanni - Wasannin dalibai na shekara-shekara a Nijar

Wasanni

Play Episode Listen Later Sep 11, 2020 10:07


A duk shekara dai ana hada daliban makarantu a Nijar don su fafata a wasannin shekara na dalibai don a fitar da zakaru tsakanin jahohin kasar ta Nijar. Ana shirya wannan kwambala dai ne mafi yawa a watan Maris a dai dai lokacin da dalibai ke zuwa karamin hutu ista ko paques. Abdoulaye Issa a cikin shirin Duniyar wasanni ya duba halin da ake ciki a Jamhuriyar Nijar.

nijar jamhuriyar nijar duniyar abdoulaye issa
Wasanni
Wasanni - Tasirin rufe makarantu kan harakokin wasannin dalibai a makarantu

Wasanni

Play Episode Listen Later Jul 10, 2020 10:33


Tun bayan shelanta bullar cutar COVID 19 a duniya, hukumomi a Nigeria suka yi ta bijiro da matakai don dakile yaduwar cutar a tsakanin al’umma. Daga cikin matakan da aka dauka har da rufe dukkan makarantun kasar daga matakin firamari zuwa manyan makarantu, matakin da ya yi tasiri kan harakokin wasannin motsa jiki na dalibai a wadanan makarantu. Abdoulaye Issa a cikin shirin Duniyar wasanni ya duba halin da ake ciki a kasar ta Najeriya.

covid-19 nigeria tun rufe daga najeriya duniyar abdoulaye issa
Wasanni
Wasanni - Yadda aka yi watsi da kwallon kafa a makarantun Najeriya

Wasanni

Play Episode Listen Later Mar 9, 2020 10:50


Shirin Duniyar Wasanni na wannan makon tare da Abdoulaye Issa ya yi nazari ne kan yadda aka yi watsi da wasanni tsakanin daliban makarantu a Najeriya.

kafa yadda najeriya watsi abdoulaye issa
Wasanni
Wasanni - Matsalolin da suka sanya dakatar da wasannin Polo a Nijar

Wasanni

Play Episode Listen Later Feb 28, 2020 10:35


A Jamhuriyar Nijar ana fuskanatar koma baya a Duniyar sukuwar dawakai a dai dai lokacin da Najeriya ke ta kokarin ganin an samu ci gaba a wannan sashe. Wasu daga cikin jihohin Jamhuriyar Nijar da aka samu koma baya dangane da sukuwar dawakai sun hada da birnin Yameh, Maradi, Zinder. Abdoulaye Issa ya duba mana halin da ake ciki yanzu haka a cikin shirin Duniyar wasanni.

polo suka sanya wasu maradi nijar najeriya jamhuriyar nijar duniyar abdoulaye issa
Wasanni
Wasanni - Fifa na fatan hukumar CAF ta canza lokuta na shirya gasar Afrika

Wasanni

Play Episode Listen Later Feb 7, 2020 10:13


A taron birnin Rabat na kasar Morocco da ya hada hukumar Fifa da ta Caf,Gianni Infantino Shugaban hukumar Fifa ya bukaci hukumar Caf da ta yi nazari tareda dage gasar cin kofin nahiyar Afrika kama daga shekaru biyu zuwa hudu. Shawarar shugaban ta Fifa na zuwa ne a wani lokaci da kwallon kafa a Afrika ke fama da matsalolli. Abdoulaye Issa a cikin shirin Duniyar wasanni ya duba halin da ake ciki kamar dai yadda za a ji.

fifa morocco afrika rabat fatan hukumar duniyar abdoulaye issa
Kasuwanci
Kasuwanci - Rikicin yan kasuwa a kasar Ghana

Kasuwanci

Play Episode Listen Later Nov 20, 2019 9:49


Kungiyar Kwadagon Ghana GHUTA ta sanar da shirin ta na gudanar da gagarumin aikin rufe shagunan ‘yan kasashen waje da ke birnin Accra. Lamarain da ya samo asali yau da shekaru kusan 20 a kasar ta Ghana. Abdoulaye Issa da ya ziyarci kasar ta Ghana ya jiyo ta bakin wasu yan kasuwa da wakilan kungiyar ta Ghuta a Ghana.

ghana accra abdoulaye issa ghuta