POPULARITY
Shirin 'Duniyar Wasanni' a wannan makon ya yi duba ne kan wasan ƙarshe na gasar zakarun Turai da aka yi a ƙarshen mako tsakanin PSG ta Faransa da kuma Inter Milan, inda PSG ta samu nasarar lashe gasar bayan da ta zazzaga wa Inter Milan ƙwallaye biyar. Wannan ne dai karon farko da PSG ta lashe wannan kofi, kuma karo na farko da wata ƙungiya daga Faransa ta lashe shi tun bayan Marseille a shekarar 1993.Ku latsa alamar sauti don sauraron shirin tare da Khamis Saleh............
Shirin Mu Zagaya Duniya tare da Nura Ado Suleiman, kamar kowannen mako kan yi bitar muhimman labaran da suka faru cikin makon da muke ban kwana da shi, kuma kamar kodayaushe a wannan karon wasu daga cikin labaran da ke ƙunshe a shirin sun ƙunshi ziyarar da Ministan Harkokin Wajen Najeriya ya kai Jamhuriyar Nijar, wadda a karon farko kenan tun bayan kifar da gwamnatin shugaba Muhammad Bazoum da sojoji suka yi. A Najeriya shirin ya leƙa Filato aka samu hasarar ɗimbin rayuka, sakamakon hare-haren da aka kai a wasu yankunan jihar, a Najeriyar za a ji yadda wata shu'umar cuta ta janyowa manoman Tumatir hasarar ɗimbin amfanin gonar, sai kuma yadda ‘yan damfara suka yi awon gaba da sama da naira tiriliyan 1 a Najeriyar.A Sudan kuwa ƙungiyar bayar da agaji ta Redcross ce ta aƙalla mutane dubu 8000 suka bace a yakin kasar.Sai kuma Kenya inda aka cafke wasu mutane da ke shirin fasa kaurin dubban tururuwa zuwa ƙasashen ƙetare.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Tsoffin shugabannin Najeriya guda 2 wato Olusegun Obasanjo da Muhammadu Buhari sun gurfana a wata kotun sasanta rikicin kwangilla domin bada ba'asi a kan soke kwangilar gina tashar samar da wutar lantarki ta Mambila da ministan Obasanjo ya bayar bada saninsa ba, da kuma kin biyan kudin sasanta matsalar da gwamnatin Buhari ta ki. Dangane da wannan dambarwa Bashir Ibrahim Idris ya tatauna da daya daga cikin dattawan kasar Alhaji Sule Ammani, Yarin Katsina.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyartattaunawar.
A ranar Asabar ce Faransa ta mika sansanin sojinta na biyu a kasar Chadi ga mahukuntan kasar a wani bangare na janye sojojinta a karshen watan Janairu.Kimanin sojoji Faransa 100 ne suka bar sansanin Abéché a ranar Asabar, kafin janye na Djamena su kusan 1000.A tattaunawarsa da Ibrahima Timbi Bah, Editan sashin Fulatanci na RFI, kwamandan dakarun Faransa a Afrika Janar Pascal Lanni ya yi karin haske kan ficewarsu daga Afirka.
Rundunar Tsaron Najeriya ta mayar da martani kan kalaman shugaban soji na Nijar, bisa zarge-zargen da ya yi kan ƙasar na cewa tana haɗa kai da Faransa domin yi mata maƙarƙashiya. Latsa alamar sauti domin sauraren ƙarin bayanin da kakakin rundunar tsaron Najeriya Birgediya Janar Tukur Gusau ya yi wa wakilinmu na Abuja Mohd.Sani Abubakar...
Shirin 'Mu Zagaya Duniya' na wannan makon tare da Nura Ado Suleimaza ya mayar da hankali ne kan mayan labarai da suka fi ɗaukar hanhali a makon da muka yi bankwana da shi, masamman halin da ake ciki a Najeriya bayan da shugaban ƙasar ya gabatar da kasafin kuɗin shekarar 2025.
Shirin lafiya jari ce a wannan makon ya mayar da hankali kan ta'azzarar cutar Tamowa ko kuma rashin sinadaran abinci mai gina jiki da ke addabar ƙananan yara a Najeriya, a wani yanayi da asusun UNICEF ke cewa duk yaro 1 cikin 3 na fama da matsalar ƙarancin abinci a ƙasar, wanda ke wakiltar kashi 37 cikin 100 na yawan yaran ƙasar ko kuma adadin yara miliyan 6. Duk da cewa tsawon lokaci wannan cuta ta ɗauka ta na addabar yara a Najeriyar, a wannan karon cutar ta tsananta a jihohin arewacin ƙasar wanda masana suka alaƙanta da matsaloli masu alaƙa da rashin tsaron da ya hana jama'a noma da kuma gushewar damunar bana da wuri, lamarin da ya ƙara yawan yaran da ke fama da cutar ta Tamowa ko kuma yunwa, dalilin da ya ja hankali ƙungiyoyin agaji da dama ciki har da ALIMA wato Alliance for International Medical Action ta Faransa wadda ke bayar da agajin lafiya a ƙasashe 13 ciki har da Najeriya.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu.....
Shirin 'Duniyar Wasanni' na wannan makon ya yi dubi ne akan yadda aka gudanar da bikin bada kyautar Ballon d'Or ta shekarar 2024.
Shirin Ilimi Hasken Rayuwa na wannan makon ya duba yadda wasu manyan jami'o'i a Najeriya ke neman tallafin ƙasashen da suka ci gaba kan yadda za a inganta ƙirƙirarriyar fasaha ta AI. Tuni kuma suka gabatar da wannan buƙata tasu a wajen taron da ƙungiyar bunkasa ilimi ta ƙasashen Turai kan shirya duk shekara, inda a wannan shekara Faransa ta karbi baƙuncin irin wannan taro da ya samu halartar jami'oi 6 da aka zabo daga Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Shamsiyya Haruna.......
Shirin 'Mu zagaya Duniya' na wannan mako tare da Rukayya Abba Kabara ya taɓo halin da aka shiga a Najeriya bayan da mahukunta suka kara farashin man fetur, sai kuma taron Afirka da China da kuma sabon fraministan Faransa.
Wasannin guje-guje da tsalle-tsalle da ke gudana a nan birnin Paris na tafiya yadda aka tsara, inda kawo yanzu an kammala wasu wasanni da dama wasu kuma ana daf da kammala su. 'Yan wasan tawagar kwallon kwando ta Mata ta Najeriya na ci gaba da fatan ganin a wannan karon ta samu nasarar tsallake matakin rukuni, ganin yadda suka dage wajen lashe wasansu na farko da Austrelia amma sai dai sunsha kashi a hannun Faransa a wasa na biyu inda a yanzu fatansu shine samun nasara a wasan da zasu yi da Kanada don tsallakawa matakin dab da na kusa da na karshe a wannan gasa.
Shirin duniya kamar yadda aka saba na duba manyan labaran da suka faru a sassan duniya A cikin shirin zaku ji cewa..............Gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin janye biyan kudaden haraji kan wasu muhimman kayayyakin abinci da ta dage haramcin shigar da su kasar, don saƙaƙawa jama'a raɗaɗin tsadar raywar da suke ciki.Matakin sojojin da suka yi juyin mulkin a Nijar, Mali da kuma Burkina Faso na tabbatar da ballaewarsu daga ECOWAS ya tayar da hankalin kungiyar kasashen ta yammacin Afirka, a yayin da kwararru ke cigaba da bajakolin ra'ayoyinsu kan matakin.A Kenya kuwa, shugaban ƙasar William Ruto ne ya kori rankatakaf din ministocinsa sai fa ƙwaya biyu rak da ya bari, ‘yan kwanaki bayan zanga-zanga kan tsadar rayuwa da dubban matsasan kasar suka gudanar.Danna alamar saurare don jin gundarin shirin tare da Nura Ado Sulaiman.
Cikunan ƴan siyasa sun ɗuri ruwa a Faransa, bayan da masu tsattsauran ra'ayi suka lashe sama da 33% na ƙuri'un da aka kaɗa a zaɓen shiga Majalisar Dokokin Ƙasar, tare da yiyuwar samun gagarumar nasara a zagaye na biyu na zaɓen da za a yi ranar Lahadi mai zuwa. Ana matuƙar nuna fargaba dangane da abin da zai faru matuƙar masu wannan ra'ayi suka samu rinjaye a majalisar, saboda tsauraran manufofinsu da suka haɗa da ƙyamar baƙi da kuma neman rage duk wani taimako da ake bai wa ƙasashe masu tasowa.Shin ko yaya kuke kallon wannan lamari da ke faruwa a fagen siyasar ƙasar ta Faransa?Wannan shi ne abin da shirin Ra'ayoyin Masu Saurare na wannan rana ya tattauna a kai.Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a.
Nasarar lashe zagayen farko na zaɓen ‘yan majalisar Faransa da jam'iyyar RN ta masu ra'ayin riƙau ta samu da kashi 33 cikin 100 a ranar Lahadi, ya tayar da hankalin sauran jam'iyyu masu ra'ayoyin sassauci da na tsaka-tsaki bazama, waɗanda a yanzu haka suke laluben hanyar da za su bi domin hana jagorar masu zafin kishin ƙasar wato Marine Le Pen lashe zaɓen ‘yan majalisar zagaye na biyu da ke tafe a mako mai zuwa. Ko yaya masana ke kallon yanayin da siyasar Faransa ta samu kanta ciki? Da kuma dalilan da suka janyo hakan? Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna Farfesa Kamilu Sani Fagge na Jami'ar Bayero da ke Kano a Najeriya. Kuna iya latsa alamar sauti domin jin tattaunawar...
Gabanin taron da za a gudanar ranar Alhamis a birnin Paris don taimaka wa Afirka dangane da yadda za ta samar wa kanta da alluran rigakafin kariya daga wasu cututuka a wadace, tuni aka samu alƙawurran sama da Euro biliyan ɗaya daga ƙasashe da da kuma ƙungiyoyi daban daban a cewar fadar gwamnatin Faransa. Wadannan kuɗade za a yi amfani da su ne don tabbatar da cewa kamfanonin sarrafa magunguna sun samar da alluran rigakafin cututuka kamar Korona, Cholera da kuma zazzaɓin cizon sauro a cikin nahiyar.Shin me za ku ce a game da wannan tallafi na ƙasashen duniya zuwa ga nahiryar Afirka?Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin
Daga cikin labarun da shirin wannan makon ya ƙunsa akwai harin da wani matashi a Kano ya kaiwa Masallaci ta hanyar cinna masa wuta, wadda zuwa lokacin gabatar da wannan shiri aka tabbatar da salwantar rayukan mutane 15 daga cikin akalla 30 da ke cikin Masalacin. Shirin na kuma ɗauke da tattauna wa da tsohon gwamnan Jihar Jigawa Sule Lamiɗo, kan tuntubar junan da jiga-jigan jam'iyyun dawa suka fara yi a Najeriya, don kafa sabon ƙawancen da zai tunkari jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya. Fira Ministan Senegal ya bayyana rashin gamsuwarsa kan wanzuwar sansanin sojojin Faransa a Ƙasar.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Nura Ado Suleiman.....
Ƙasashen duniya da kuma ƙungiyoyi kaƙƙin aikin jarida da kuma ‘yancin bayyan ra'ayi, sun yi tir a game da matakin rufe wasu kafafen yaɗa labarai da gwamnatin mulkin sojin Burkina Faso ta dauka. Baya ga kafafen yada labaran Faransa ciki har da RFI da kuma France24, matakin rufe kafafen yaɗa labaran ya shafi na Amurka, Birtaniya Faransa da dai sauransu domin kawai wallafa rahoton kungiyar HRW da ke zargin dakarun gwamnati da yi wa fararen hula kisan gilla.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkeen shirin.
A wannan makon Shirin Duniyar Wasanni ya yi duba ne kan yadda ake tufka da warwara game da tsarin tsaro a lokacin gasar wasannin motsa jiki ta Olympics da birnin Paris zai karbi bakunci a watan Yulin wannan shekarar. Shire-shiryen gudanar da gasar wasannin motsa jiki ta Olympics da birnin Paris na Faransa zai karbi bakunci a watan Yuli mai zuwa sunyi nisa, domin dai rahotanni na nuna cewar an kammala tanadin kusan dukkanin inda za a gudanar da wadannan wasanni.Sai dai wani hanzari ba guda ba, duk da matakan da kasar ta Faransa ta dauka na tabbatar da tsaron ‘yan wasa da kuma na ‘yan kallo, bayanai na nuna cewar akwai alamun fuskantar barazanar tsaro a lokacin gasar.Wannan lamari dai ya biyo bayan harin ta'addancin da aka kai birnin Moscow wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 140.A lokacin wata zantawa da aka yi shugaban Faransa Emmanuel Macron a makon da ya gabata, ya ce babu shakka, akwai yuwuwar Rasha za ta kai hari a lokacin gasar da ke tafe.Kai hari a lokacin gasar OlympicsKai hari a yayi gasar gujeguje da tsalle-tsalle ta Olympics a iya cewa ba sabon abu bane, domin a baya an sha samun irin hakan, wanda aka kai a shekarar 1972 a Munich da kuma a shekarar 1996 a Atlanta.Duk da cewa a cikin watan da ya gabata ministar Wasannin Faransa Amelie Oudea-Castera, ta ce a yanzu babu wata barazanar hare-haren ta'addanci da gasar gujeguje da tsalle-tsalle ta Olympics ke fuskanta, sai dai wasu da dama na cewa barazanar abu ne da ke da alaka da rikicin da ake gwabzawa tsakanin Rasha da Ukraine da ya kwashe sama da shekaru biyu anayi, wanda kasashen duniya ciki harda Faransa ke goyonma Ukraine baya domin fafatawa da Rasha.Yadda gasar Olympics ke samar da hadin kaiIta dai wannan gasa ana ganinta a matsayin wata farfajiya ta samar da hadin kai, ganin yadda take hada dukkanin bangarorin duniya waje guda.Domin idan aka koma baya cikin tarihi, bayan kawo karshen yakin duniya na biyu, gasar da aka gudanar ta shekarar 1952, ta kasance taron wasanni mafi girma a duniya da aka gudanar.Ƴan wasa dubu 4 da dari 955 ne suka halarci gasar daga kasashe 69, bayan maido da kasashen Japan da Jamus da wasu kasashe 13 da a karon farko ke nan suka halarci gasar, cikinsu har da Isra'ila wacce ta kasance sabuwar kasar da aka kirkira da ta samu amincewar Majalisar Dinkin Duniya a shekarar 1948, da Vietnam da ke cikin rudanin siyasa.To sai dai ana ganin cewa a wannan karon siyasa ta shiga cikin lamarin wanda ke kokarin kawo rarrabuwar kai.Martanin Rasha game da zargin kai hariTo sai dai a wani martani da Rasha ta maida game da kalaman Macron ta bakin mai magana da yawun fadar shugaban kasar Dmitry Peskov, ta ce zargin na Macron babu tushe a cikinsa kuma wani matakine na yada labaran kanzon kurege da kasashen yammaci ke yiwa Rasha.
Shirin Al'adun Gargajiya na wannan makon ya ziyarci masarautar Sarkin Hausan Turai Alhaji Surajo Jankado Labbo da ke kasar Faransa, inda Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da shi kan wasu batutuwa da suka shafi Hausawa. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa........
Daya daga cikin matsalolin da suka addabi nahiyar Turai a wannan lokaci, shine batun bakin haure, ganin yadda matasa daga nahiyar Afirka ke tafiya mai hadari cikin kwale kwale da zummar zuwa nahiyar, abinda ke kai ga rasa rayuka da dama. Dangane da wannan matsala da kuma matakan da magabata ke dauka wajen fadakar da al'umma illar irin wannan tafiya, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Sarkin Hausawa Turai Alhaji Sirajo Jankado a fadarsa da ke kasar Faransa, kuma ga yadda zantawar su ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tasu......
Shugabannin kasashen kungiyar ECOWAS ko CEDEAO a taron da ya gudana a ranar Asabar a Abuja sun yanke shawarar dage wani kaso mai yawa na takunkumin da aka kakabawa Nijar. Kasashen Nijar, Mali da Burkina Faso, wadanda musamman suka juya wa Faransa baya, kuma suka matsa kusa da Rasha, sun hade a cikin kawancen kasashen Sahel (AES).Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Nasiru Sani.
Rikicin siyasa ya barke a Senegal sakamakon dage zaben kasar da shugaba Macky Sall ya yi a karshen mako. Matakin ya haifar da zanga zanga da kuma arangama da 'yan sanda, yayin da kungiyoyi da manyan kasashen duniya irin su ECOWAS da AU da EU da kuma kasashen Faransa da Amurka suka bukaci daukar matakin gudanar da zaben kamar yadda dokar kasa ta tanada. Dangane da wannan rudanin siyasa da ya mamaye kasar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Moussa Tchangari na kungiyar Alternative a Nijar
Kasar Rasha ta sanar da kulla sabuwar yarjejeniyar soji da Jamhuriyar Nijar, sakamakon ziyarar da tawagar gwamnatin sojin Nijar ta kai Moscow a karkashin jagorancin Firaminista Ali Mahamane Lamine Zein. Dangane da tasirin wannan yarjejeniyar da kuma yadda zai taimakawa Nijar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Dicko Abderrahmane na Jami'ar Zinder, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.....
Daga cikin labarun da Shirin ya kunsa akwai batun yadda yan ta'adda a Najeriya ke gina ramu suna boyewa, saboda barin wutar da suke sha daga sojojin kasar, sai kuma batun kammala ficewar sojojin Faransa a Nijer da dai sauran manyan labaran da suka hada da Burkina Faso, jamhuriyar Benin, yakin Isra'ila da Hamas, tare da dokar yan ci rani da Faransa ta amince da ita.
Majalisar dokokin Faransa ta amince da kudirin dokar da ke neman tsaurara dokokin bakin hauren da ke shiga kasar ciki har da masu neman mafaka, kudirin da bai samu tsallakewa Majalisa ba har sai da aka yi hadaka tsakanin Jam'iyyar shugaba Macron da ta masu tsattsauran ra'ayi karkashin jagorancin Marine Le Pen. Ita dai wannan doka za ta saukaka wa bakin-hauren da suke aiki a fannoni ko ma'aikatun da suke da karancin ‘yan kwadago, samun takardar izinin zama a Faransa, ko da ya ke a hannu guda kudurin zai kuma saukaka damar korar bakin a duk sanda aka so yin hakan, batun da ya sha bamban da ra'ayin jam'iyya mai shugabancin kasar.Tuni dai wasu ministocin gwamnatin ta Macron da daidaikun ‘yan jam'iyyarsa suka fara juya baya ga shugaban, kuma kan hakan ne muka tattauna da Dr Abba Sadiq mazaunin birnin Paris wanda ya yi mana karin haske kan dokar.
A yayin da wakilan kasashen ke kintsawa don zuwa gasar wasannin motsa jiki na Olympic da za a yi a birnin Paris na kasar Faransa a shekara mai zuwa, shirin 'Duniyar Wasanni', ya kawo tarihin gasar, inda ya yada zango a Najeriya, wadda tawagar kwallon kafarta ta 'Dream Team' ta kasance ta farko a nahiyaar Afrika da ta lashe kofin kwallon kafa a gasar Olympiic a shekarar1996.Shirin ya samu damar tattaaunawa da wasu 'yan wasa da jami'ai da aaka dama da su a lokacin. TARIHIN GASAR WASANNI TA OLYMPICGasar motsa jiki ta Olympics an fara gudanar da ita ne a karni na 8 a kasar Girka, sai dai daga bisani aka dakatar da ita.Bayan dakatar da gasar na tsawon lokaci, a shekarar 1940, kwamitin shirya gasar Olympics na Duniya IOC ya zabi babban birnin kasar Finland Helsinki don gudanar da gasar, amma sai dai sanadiyar barkewar Yakin Duniya na 2 aka sake dakatar ita.Bayan kawo karshen yakin, a shekara ta 1946, IOC ya yanke shawarar sake farfado da harkar wasannin Olympics na zamani, inda aka fara gudanar da wasannin gasar a shekarar 1948 a birnin London na kasar Ingila, duk da cewa itama ta kasance kamar sauran kasashen Turai, ta na cikin yanayi na matsi, amma sai da aka sake gina birnin na London don gudanar da gasar wasannin Olympics.Fiye da 'yan wasa dubu 4 ne suka fafata a wasanni 136, sai dai ba a gayyaci kasashen Japan da Jamus ba, yayin da Tarayyar Soviet da aka gayyata ta kaurace wa gasar.Shekaru hudu bayan waccan gasar, birnin Helsinki na kasar Finland ta karbar bakuncin gasar, da aka yi wa lakabi da “gasa ta zamani”.An fara wasanni ne a ranar 19 ga Yuli zuwa 3 ga Agustan 1952, wannan gasa ta Olympics wacce ita ce karo na 15, ta kasance taron wasanni mafi girma a duniya da aka gudanar bayan kammala yakin duniya na biyu.‘Yan wasa dubu 4 da dari 955 ne suka halarci gasar daga kasashe 69, bayan maido da kasashen Japan da Jamus da wasu kasashe 13 da a karon farko ke nan suka halarci gasar, cikinsu har da Isra'ila wacce ta kasance sabuwar kasar da aka kirkira da ta samu amincewar Majalisar Dinkin Duniya a shekarar 1948, da Vietnam da ke cikin rudanin siyasa.Duk da cewar wannan gasar ba a farota da kasashen nahiyar Afrika ba, akwai wakilan nahiyar da suka shigo daga baya kuma suka nuna bajinta, musammanma a bangaren wasan kwallon kafa, inda a shekarar 1996 da kuma 2000 kasashen Najeriya da Kamaru suka taka rawar gani wajen lashe gasar.A shekarar 1996 ce Najeriya ta kafa tarihin samun nasarar lashe lambar zinari a bangaren kwallon kafar gasar, lamarin daya kara karfafawa sauran kasashen nahiyar gwiwa.A biyo mu a kashi na gaba don jin tagomashin da nahiyar Afrika ta samu a wannan gasa ta olympic.
Ministan kasuwancin Faransa, Olivier Brecht ya ziyarci Najeriya a makon jiya, domin tattauna yadda za'a bunkasa harkokin kasuwanci da zuba jari a tsakanin kasashen biyu. Brecht shine ministan Faransa na 3 da ya ziyarci Najeriya a karkashin jagorancin shugaba Bola Ahmed Tinubu. Shugabar Sashen Hausa ta Radio France International, Sophie Bouillon ta tattauna da ministan a kan dalilin zuwansa Najeriya da kuma yanayin dangantaka tsakanin kasashen biyu.Ku danna alamar sauti don sauraron fassarar zantawarsu.....
Yan majalisun dokokin Faransa sun bukaci gwamnatin kasar da ta gaggauta aiwatar da sauye sauye domin inganta dangantakar ta da kasashen Afirka, lura da yadda kasashen Rasha da China ke fadada karfin fada aji a yankin. Dangane da haka Abdoulaye Issa ya tattauna da Abba Seidick masanin siyasa,zamantakewar kasar Faransa.
Shirin "Duniyar Wasanni" na wannan makon yayi duba ne kan kyautar Ballan d'Or da aka bayar a makon da ya gabata, inda tauraron kwallon kafar Argentina da a yanzu ke kungiyar Inter Miami a Amurka, Lionel Messi, ya lashe kyautar gwarzon duniya ta Ballon d'Or karo na takwas. A wannan karon dai Erling Haaland ne ya zo na biyu sannan Kylian Mbappe ya zo na uku a bikin ba da kyautar ta Ballon d'Or. Haka nan shirin ya tabo batun kwallon Zari Ruga da kasar Afrika ta Kudu ta lashe.Wannan ne dai karo na farko da wata kasa ta taba lashe kofin a jere, bayan da zaratan ‘yan wasan na Afrka ta Kudu suka lallasa takwarorinsu na New Zealand da ci 12 da 11 a wasan karshen da aka yi a birin Paris na Faransa.Ku danna alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Shirin Kasuwa Akai Miki Dole na wannan makon ya mayar da hankali ne kan bukin cika shekaru 15 cibiyar bada lamuni da raya kasashe ta kasar Faransa Proparco ta yi ta na gudanar da ayyukanta a Najeriya, inda ta zuba jarin da ya kai dala biliyan daya a kasar cikin shekarun. Shirin zai mayar da hankali ne kan yadda ayyukan cibiyar ke bayar da gudunmawa ga fannonin daban-daban na ci gaban tattalin arzikin Najeriya. Tun bayan kafa cibiyar a shekarar 2008 a Najeriya, Proparco ta mai da hankali wajen hadin gwiwa da cibiyoyin hada-hadar kudi na cikin gida da na wasu kasashen Afirka wajen zuba hannun jari ga kamfanoni masu tasowa da sabbin kafuwa a fannin makamashi mara gurba da muhalli da harkokin noma da kere-kere da kiwon lafiya da dai sauransu…
Bayan jakada da kuma dakarun Faransa, a yanzu kuma sojoji da suka kwaci mulki a Jamhuriyar Nijar, sun umurci shugabar ofishin MDD da ta fice daga kasar a cikin kwanaki uku. Mahukuntan sojin na zargin jami'ar ce da yin kare tsaye a game da muradun jamhuriyar Nijar a matakin kasa da kasa. Abin tambayar shine, ko ya ya wannan takun saka tsakanin sojojin Nijar da kuma kasashen duniya za ta kasancdce? Anya kuwa hakan zai haifar wa kasar ta Nijar da sakamako mai kyau? Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.
Shirin Mu zagaya duniya tare da Nura Ado Suleiman kamar kowanne mako ya yi bita ne kan muhimman labaran da suka faru a makon da muka yi bankwana da shi, inda a cikinsa za ku ji yadda 'yan bindiga suka sace gomman dalibai a Jami'ar tarayya ta birnin Gusau a jihar Zamfara. Haka zalika a cikin shirinza ku ji yadda Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya sha alwashin daukaka kara bayan matakin kotun sauraren kararrakin zabe na kwace nasarar da ya yi a zaben watan Maris.Bugu da kari shirin ya leka sauran sassan Duniya dauke da muhimman labarai na wannan mako, ciki kuwa har da dambarwar bakin haure a Italiya baya ga ziyarar Sarki Charles na 3 a Faransa baya ga ziyarar Fafaroma Francis.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.....
Shirin Lafiya Jari ce a wannan makon tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan wani gangamin gwajin cutar kansar mama da ta bakin mahaifa da mahukuntan Nijar suka gudanar a jihar Maradi a wani yunkuri na lalubo masu cutar tare da yi musu magani. Wannan mataki na gwajin cutukan kansar biyu na da nasaba da sabbin alkaluman da ke nuna karuwar masu dauke da cutar a sassan Faransa.Tuni dai Mata suka yi dafifi wajen yin wannan gwaji wanda aka tattara kwararrun likitoci da ke aikin wayar da kai tare da bayar da shawarwari kan yadda mata za su kula da lafiyarsu kasancewar cutukan kansar guda biyu a matsayin mafiya saurin kisa a tsakanin al'umma musamman a kasashe masu tasowa.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
Ko kun san sabon taken kasa da aka yi a Jamhuriyar Nijar da ma yadda matasan kasar ke kallonsa? Shirin Dandalin Matasa yaa mayar da hankali a kai.
An samu saukin tarzomar da dubban Faransawa ke yi, bayan shafe kwanaki 6, suna zanga-zangar da ta kazance, biyo bayan kashe matashi da wani jami'in dan sanda ya yi. Tun daga ranar Larabar da ta gabata ne dai aka fara samun sassaucin tashin hankalin, inda kididdiga ta nuna cewar mutane 150 jami'an tsaro suka cafke, sabanin masu zanga-zanga sama da 700 da aka a ranar Asabar. Bayanai sun ce motoci sama da dubu 2 masu tarzomar suka kone a Faransa, tare da lalata gine-gine sama da 500. Kan wannan zanga-zanga da wasu lamuranna da suka shafe ta Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Abba Sadiq mazaunin kasar ta Faransa. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar......
Yanzu haka shugabannin kasashen duniya sama da 50 da shugabannin hukumomin kasa da kasa daban-daban, da kungiyoyi masu zaman kansu, sun hallara a birnin Paris na Faransa, domin tattauna yau Alhamis da ake fara taron duniya don shimfida tsarin da zai bai wa kasashen damar samun tallafi da nufin tunkarar matsalar sauyin yanayi. Wannan taro na zuwa ne a daidai lokacin da kasashe da dama ke fama da zaizaiyar kasa, fari, ambaliya yayin da teku ke yi wa wasu birane barazana. Me ku ke fatan taron ya yi don tunkarar wadannan matsaloli? Me za ku ce a game da rawar da rawar da gwamnatocin kasashenku ke takawa domin tunkarar wannan kalubale? Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin tare da Salissou Hamissou.
Shirin Duniyar wasanni tare da Khamis Saleh a wannan mako ya yi duba ne kan yadda aka kammala wasannin lig lig din Turai A farkon wannan watanne aka kammala manyan wasanni musamman a kasashen Ingila da Spain da Jamus da Italiya da kuma Faransa. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.....
Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan karon ya mayar da hankali kan gasar da masoya tashar radiyon Faransa RFI da aka fi sani da ''Club RFI'' suka shirya a birnin Lagos na Najeriya, wadda ke da nufin musayar al'adu da yaruka tsakanin mabanbantan masu sauraron tashar. Gasar wadda ita ce karon farko da aka taba gudanar da makamanciyarta na da nufin fadada fahimtar yaruka tsakanin al'ummomi, tare da bayar da kyautukan kara kwarin gwiwa ga wadanda suka yi nasara.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.......
‘Mu Zagaya Duniya' mai bitar wasu daga cikin muhimman labaran, da suka fi daukar hankali a makon da ya kare, Nura Ado Suleiman daga sashin Hausa na RFI zan jagoranci gabatar da shirin. daga cikin labaren za ku ji cewa Gwamnatin sojin Burkina Faso ta nanata umarnin da ta baiwa sojojin Faransa cewa su fice daga kasar.
Kamfanin Bollore na hamshakin attajirin Faransa, daga jiya laraba, ya kammala cikin kadarorinsa da ke tashoshin jiragen ruwa da kuma ayyukan layin dogo a kasashe da dama na Afirka a kan dalar Amurka bilyan biyar da milyan 700. Bollore Logistics dai yana da cibiyoyi a kasashe 47 na Afirka da suka hada da Cote d'Ivoire, Kamaru, Togo da kuma Najeriya. Shiga alamar sauti domin jin cikakkiyar tattaunawar, Ibrahim Malam Tchillo da Nouhou Abdou Magaji, masani a game da ayyukan kamfanin.
Argentina ta doke Faransa 4-2 a bugun daga kai sai mai tsaron gida, abin da ya ba ta damar lashe Kofin Duniya a wasan da aka buga cikin daren ranar Lahadi a kasar Qatar. Shiga alamar sauti domin sauraron Hauwa Muhammad cikin shirin.
A karshen wannan mako ake kawo karshen gasar cin kofin duniyar dake gudana a Qatar, inda Faransa zata kara da Argentina a ranar lahadi, yayin da Morocco zata fafata da Crotia gobe asabar domin neman gurbi na 3. Dangane da yadda gasar ta gudana da kuma nasarorin da aka samu, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon Sakatare Janar na Hukumar Kwallon kafar Najeriya, Hon Sani Ahmed Toro, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta ce a karshen taron gabatar da manyan manufofin habaka tattalin arziki da kuma kyautata rayuwar al'ummar kasar da aka gudanar daga 5 zuwa 6 ga wannan wata a birnin Paris na Faransa, ta samu alkawurra sama da Euro milyan dubu 45 daga masu saka jari. Shugaban Nijar Mohamed Bazoum ne ya jagoranci tawagar kasar domin fayyace shirinsa na raya kasar da zai aiwatar daga 2022-2026. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin da Hauwa Muhammad ta gabatar.
Gwamnatin Nijar ta kammala taron kwanaki biyu da ta shirya domin gabatar da shirin raya kasar da take da shi ga manyan ‘yan kasuwa da zuba jari daga kasashen duniya. Shugaban kasar Bazoum Muhammad da manyan jami'an gwamnati ne suka halarci taron na kwanaki biyu a birnin Paris na kasar Faransa Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da ministan lafiya na kasar, Dakta Ilyasu Idi Mai-Nasara wanda ya kasance daga cikin tawagar da suka yiwa shugaban rakiya. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron yayin ziyarar da ya kai Amurka,ya jaddada aniyar kasar sa na tafiya kafada da kafada da Amurka duk da sabani ra'ayoyi da aka samu a baya.Shugaban Amurka Joe Biden ana sa bangaren ya fada cewa ya amince da shugaban Faransa Emmanuel Macron kan daidaita hanyoyin da bangarorin biyu ke bi kan batutuwan da suka shafi yanayi da makamashi a daidai lokacin da kasashen Turai ke nuna damuwa kan kariyar Amurka. Bashir Ibrahim Idris a cikin shirin mu zagaya Duniya ya tabo wasu daga cikin muhiman batuttuwa na wannan mako.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya sanar da kawo karshen ayyukan rundunar Barkhane mai yaki da ta'addanci a yankin Sahel daga jiya laraba, to sai dai ya ce Faransa za ta fayyace sabon tsarin ci gaba da kasantuwar dakarunta a Sahel cikin watanni 6 masu zuwa. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Tahirou Gimba, masani tsaro, domin jin yadda yake kallo matakin rusa rundunar da kuma yadda ya kamata alakar tsaro ta kasance tsakanin Faransa da sauran kasashen yankin, ga dai zantawarsu.
Shirin mu zagaya duniya na wannan mako zai yo dubi ne a kan wasu muhiman labaren Duniya tare da Nura Ado Suleiman. A cikin shirin za ku ji halin da ake ciki dangane da tsamin dangantaka tsakanin kasar Mali da Nijar,kazzalika za ku ji a ina aka kwana dangane da wasu kasashen da suka hada da Najeriya,Nijar da yankin Turai.
Shirin Duniyar wasanni tare da Khamis Saleh ya yi duba kan yadda bikin bayar da kyautukan gwarzon dan kwallo ta Ballon d'Or ya gudana a birnin Paris, kyautar da a wannan shekara dan wasan gaba na Faransa da ke taka leda da Real Madrid Karim Benzema ya lashe saboda rawar da ya taka wajen taimakawa kungiyarsa kai labari a mabanbantan gasa cikin kakar da ta gabata. Ayi saurare Lafiya.
Firaministan Mali da sojoji suka nada ya caccaki Faransa da kuma Majalisar Dinkin Duniya a wani jawabin da ya gabatar mai cike da koke kan tabarbarewar tsaro a kasarsa. A makon da ya gabata ne aka nada Kanar Abdoulaye Maiga, a matsayin Firaministan rikon kwaryar Mali, wanda ya zargi Faransa da zamewa kasar sa kayar kifi a wuya. Abdoulaye Issa ya tattauna da Alkassoum Abdourahamane, mai sharhi kan lamuran zamantakewa da siyasar kasashen yammacin Afrika dangane da jawabin Firaministan kasar ta Mali.
Kawancen kungiyoyin fararen hula na M62 a Jamhuriyar Nijar ya gudanar da wani taron gangami domin nuna damuwa game da tsadar rayuwa tare da yin kira ga rundunar Barkhane ta Faransa da ta fice daga kasar kasancewar zamanta bai da wani tasiri a cewar masu zanga-zangar. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin da Hauwa Muhammad ta shirya