POPULARITY
A Najeriya, mutuwar tsohon kakakin rundunar sojin ƙasar Janar Abubakar Rabe mai ritaya a hannun ƴan bindiga, lamari ne da ya yi matuƙar ɗaga hankulan jama'a, tare da ƙara haifar da shakkun game da yiyuwar cewa anya kuwa za a iya magance matsalar tsaro a ƙasar? An dai gaza ceto janar Rabe daga hannun ƴanbindigar, duk da cewa ya share kusan makonni biyu a hannunsu. Shiga alamar sauti don sauraron hirar da Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya yi da Air Commodore Ahmed Tijjani Baba Gama mai ritaya......
Gwamnatin jihar Lagos a Najeriya ta ƙaddamar da wani gagarumin samame kan mabarata da suka cika titunan birnin, inda aka cafke ɗimbin mabarata ciki har da masu fama da naƙasa da kuma waɗanda ke yi musu jagora, kazalika da ma waɗanda ke cikin ƙoshin lafiya. Kwamishin Ma'aikatar matasa da jin ɗadin jama'a na jihar Mobolaji Ogunlende, ya ce daga ƙarshen watan Mayun da ya gabata zuwa yau, sun cafke sama da mutane dubu 1 da 300 tare da hukunta aƙalla 450 daga cikinsu. Lura da cewa mafi yawan waɗanda suka riƙi bara a matsayin sana'a a birnin Lagos ƴan asalin Arewacin Najeriya ne, wannan ya sa Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da ɗaya daga cikin shugabannin al'ummar yankin da ke zaune a jihar, Alhaji Sa'adu Yusuf Ɗandare Gulma, ga kuma ƙarin bayanin da ya yi masa a game da wannan samame. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu.............
A Najeriya, jam'iyyun siyasa sun kammala zaɓen fidda ƴantakarar da za su tsaya musu a matakai daban-daban na zaɓukan da za a yi cikin shekara mai zuwa. To sai dai a ɓangaren adawa, mafi yawan jam'iyyun sun gudanar da zaɓukan ne a cikin yanayi na rabuwar kawuna sakamakon rikicin shugabanci. To akwai yiyuwar wannan rikici na cikin gida ya iya shafar ƙima da kwarjinin adawa a zaɓukan na baɗi? Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar da Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya yi wa Farfesa Usman Mohammed, masani siyasa a Najeriya.
Bisa ga dukkan alamu za a iya samun fahintar juna tsakanin Nijar da kuma maƙociyarta Jamhuriyar Benin, waɗanda ke takun-saka tun bayan kifar da gwamanatin dimokuraɗiyyar ta Mohamed Bazoum yau kusan shekaru uku kenan. Kasancewar Firaminsitan Nijar Mahamane Ali Lemine Zeine a wurin bikin rantsar da sabon shugaban Benin Romuald Wadagni, na ƙara nuni da cewa za a iya samun kusanci a tsakanin ɓangarorin biyu. A game da haka ne Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Adamu Muhammadu Ɗan Madawa, ɗaya daga cikin shugabannin ƴan Nijar mazauna Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraren zantawarsu...
A daidai lokacin da ake kan tattaunawa tsakanin Iran da Amurka don samar da yarjejeniyar kawo ƙarshen yakin da ake yi tsakaninsu, kafafen yaɗa labaran Iran sun ce akwai gagarumin cigaba a tattaunawar. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Malam Mubarak Abdul-Aziz, ɗan Najeriya mazauni Tehran, wanda ya yi masa ƙarin bayani a game da halin da jama'a ke ciki daidai wannan lokaci da ake dakon cimma yarjejeniya don kawo ƙarshen wannan yaƙi. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Kotu a Najeriya ta yi hukunci da ke cin karo da umarnin hukumar INEC da ta nemi dukkanin jam'iyyun siyasa su kammala miƙa mata sunayen ƴan takarar da suka tsaida kafin nan da ranar 31 ga watan da muke na Mayu, duk kuwa da tanadin dokar zaɓen ƙasar da ta sahalewa jam'iyyun kaiwa har nan da watan Satumba gabanin miƙa sunayen. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawar Abdoulkarim Ibrahim Shikal da masanin doka a Najeriya Barista El-zubair Abubakar kan wannan hukunci....
Yanzu haka na ci gaba da bayyana ra'ayoyi dangane da sanarwar da Amurka ta fitar da ke cewa ta kashe Abu Bilal Al-Minuki da ke matsayin jagora a ƙungiyar IS a Najeriya, labarin daga bisani hukumomin tsaron Najeriya suka tabbatar. To domin jin ƙarin bayani a game da wannan ɗan taliki da ake cewa an kashe, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Kabiru Adamu na Cibiyar da ke nazari kan sha'anin tsaro ta Beacon da ke Abuja, ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar...............
A ranar asabar da ta gabata ne, wasu masu fafufutuka da suka haɗa da ƴan siyasa, fararen hula, masana dokoki da dai sauransu da ke zaune a ƙetare, suka ƙaddamar da wani ƙawance da ake kira da suna ADS, (Alliance des Domocrates du Sahel) wanda babbar manufarsa ita ce sake dawo da tsarin dimokuraɗiyya a ƙasashen yankin Sahel da yanzu haka ke ƙarƙashin mulkin soji da suka hada da Burkina Faso, Mali da kuma Nijar. An dai ƙaddamar da wannan ƙawance ne a birnin Brussels na ƙasar Belgium, inda daga bisani Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Sakataren Yaɗa Labarai na ADS Boubacar Ɗan Zourmani, wanda ya yi masa ƙarin bayani a game da manufofinsu. Ga dai ƙarin bayaninsa.
Kamar dai kowace shekara, 3 ga watan Mayu ita ce ranar kare ƴancin aikin yaɗa labarai a duniya, inda rahotannin da ƙungiyoyin da ke fafutuka a wannan fage ke nuni da cewa an samu gagarumin koma-baya ta fannin aikin jarida a cikin shekarar da ta gabata. Dangane da wannan rana, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon shugaban ƙungiyar Ƴan Jarida ta Najeriya (NUJ) Honnorable Alhaji Muhammed Sani Zoro, wanda da farko ya fara yin tsokaci a game da irin sauye-sauyen da aka samu a aikin jarida saboda dalilai masu nasaba da zamani. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
An shiga zaman zullumi a Mali bayan da ƙawancen ƙungiyar Abzinawa ƴan tawaye FLA da kuma kungiyoyin da ke ikirarin jihadi suka ƙaddamar da farmaki kan birane da dama na ƙasar tun a ranar asabar har zuwa jiya lahadi. Tuni dai aka tabbatar da mutuwar ministan tsaro Janar Sadio Camara da kuma wasu mutane da dama a wannan farmaki da ake kallo a matsayin mafi tsaruwa da kuma jajircewa daga waɗannan ƙungiyoyi da suka share tsawon shekaru suna fafatawa da dakarun gwamnati. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Malam Soumaila Amadou, mai sharhi kan lamurran yankin Sahel, ga kuma zantawarsu. Latsa alamar sauti don sauraron hirar Abdoulkarim Ibrahim da Soumala Amadou:
Najeriya da kuma Turkiyya sun ƙulla yarjejeniyar tsaro a tsakaninsu, wadda a ƙarƙashinta matakin farko Najeriya za ta tura zatan sojoji 200 don samun horo na musamman a Turkiyya. Hakan dai na zuwa ne watanni kaɗan bayan da mahukuntan a birnin Abuja suka sanar da ƙulla irin wannan yarjejeniya da ke bai wa Amurka damar turo sojojinta zuwa Najeriya don yaƙi da ta'addanci? Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tsaro lamurran tsaro Dr Yahuza Getso, domin jin tasa fahintar a game da yadda alaƙar tsaron za ta kasance tsakanin Najeriya da kuma Turkiyya. Ga dai zantawarsu.
Ana ci gaba da gudanar da bukukuwan Easter a sassan duniya, wadda Kiristoci suka yi imani da cewa a wannan rana ce aka gicceye Yesu Almasihu inda kwanaki uku bayan hakan ya tashi. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya tuntuɓi Reverand Andrew Doyu, domin jin ƙarin bayani a game da matsayin wannan rana da kuma muhimmancinta ga mabiya addinin Kirista. Shiga alamar sauti don saurarin cikakkiyar hirar...........
Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana fataucin bayi da aka share ɗaruruwan shekaru ana yi daga Afirka zuwa Turai da Amurka a matsayin ‘'cin zarafin bil Adama mafi girma'' da aka taɓa gani a tarihi. Ƙasashen duniya 123 ne suka kaɗa ƙuri'ar goyon bayan wannan ƙuduri, wasu uku wato Amurka, Isra'ila da Argentina suka ƙi amincewa yayin da wasu ƙasashe 52 suka yi ƙememe ta hanyar rowar ƙuri'unsu. To domin tuni a game da lokacin da aka fara ɗibar bayi daga Afirka da kuma yadda hakan ya shafi ci gaban nahiryar, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tarihi Dr Maman Kassou, malami a jami'ar Andre Salifou da ke Damagaram, ga kuma zantarwarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Farashin hajoji da sauran muhimman abubuwa na ci gaba da hauhawa a kasuwannin duniya sakamakon yadda yaƙin da ake yi a yankin Gabas ta Tsakiya ya hana fitar da mafi yawan man fetur da kamfanoni da masana'antu suka yi oda ya maƙale a Mashigin Ruwan Hormuz. To domin fahintar girman wannan matsala da kuma ɓangarorin da suka fi fama da ƙarancin makamashi a duniya saboda wannan rikici, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya tuntuɓi masani tattalin arziki Dr Isa Abdullahi, malami a jami'ar Tarayya da ke Kashere a jihar Gomben Najeriya, ga kuma zantawarsu. A latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawar
Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ba dan tattaunawar da gwamnatinsa ta yi da wani babban jami'in ƙasar Iran ba, to lalle da babu makawa ya ƙaddamar da farmaki domin rusa cibiyoyin samar da wutar lantarki na ƙasar. Trump ya ce ya jinkirta kai farmaki har tsawon kwanaki biyar, tare da yiyuwar hakan ya kasance damar cimma yarjejeniya da Iran a cewarsa. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon jakadan Najeriya a Iran Ambasada Alhaji Abubakar Cika, domin jin tasa fahintar a game da dalilan jinkirta kai wannan hari. Ga kuma abin da yake cewa.
Yanzu haka yaƙin da ake fama da shi a yanzu Gabas ta Tsakiya ya rutsa da ɗimbin ƴan kasashen waje musamman ɗalibai da ke karatu a ƙasar Iran. To sai dai yayin da wasu ƙasashe suka fara kwashe mutane zuwa gida ko kuma wasu ƙasashe, amma har yanzu Najeriya ba su samu irin wannan tallafi daga gwamnatinsu ba. A game da haka ne Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Muhammad Umar Nuruddeen, ɗaya daga cikin ɗaliban ƴan Najeriya wadanda adadinsu ya zarta 500, wanda ya fara da yin bayani a game da yadda rikicin ya tarar da su Ku latsa alamar sauti da ke sama domin jin wannan tattaunawa.................................
A Najeriya, 31 ga wannan watan na Maris ita ce ranar da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya bai wa masu riƙe da naɗaɗɗun muƙaman siyasa su yi marubus muddun suna son tsayawa takara a zaɓuka masu zuwa, kamar dai yadda dokokin zaɓe suka tanada. To domin jin ƙarin bayani a game da wannan doka, da irin mutanen da ya kamata su yi marabus da kuma tasirin dokar wajen samar da ingantaccen zaɓe, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Barrister Modibbo Bakary, ƙwararren lauya da ke birnin Abuja, ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Shugaban Amurka Donalad Trump, ya ce yanzu haka ya samu tabbaci daga wasu ƙasashen duniya cewa za su taimaka don tabbatar da cewa an ci gaba da zirga-zirgar jiragen ruwa a Mashigin Ruwan Hormuz. Domin jin irin sarƙaƙiyar da ke tattare da irin wannan aiki, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tsaro Air Commodore Tijjani Ahmed Baba Gamawa mai ritaya, ga kuma zantawarsu. A lasa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Kungiyar IPOB da ke fafutukar neman ɓallewar Yankin Kudu Maso Gabashin ƙasar daga Najeriya, ta sanar da kawo ƙarshen tilasta wa jama'a zaman gida a kowace ranar litinin yau kusan shekaru biyar kenan. Matakin dakatar da tilasta zama gidan da ƙungiyar ta sanar a jiya lahadi, ya zo ne bayan da gwamnan jihar Anambra ya buƙaci jama'a su bijire sannan su ci gaba fita kowace litinin domin gudanar da harkokinsu na yau da kullum. Alhaji Ibrahim Abdulƙadir Ɗan-Ghali shi ne jagoran ƙawancen ƙungiyoyin ƴankasuwa ƴan asalin Arewacin Najeriya mazauna jihar Imo, ya bayyana wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal matsayinsu game da sanarwar ta IPOB. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
A Najeriya babban abin da mafi yawan mutane ke neman ƙarin haske a kai su ne abubuwan da ke ƙunshe a yarjejeniyar tsaron da aka ƙulla tsakanin ƙasar da Amurka domin kawo ƙarshen ƴanbindigar da Amurkan ta ce suna yi wa Kiristoci kisan gilla. A game da wannan yarjejeniyar ce Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Yahuza Getso, masani tsaro da ke game da ayykan ƴanbingar da suka addabin jama'a, ga kuma yadda zantawarsu ta gudana. A latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar zantawar.
Gwamnatin Iran ta ce tabbas an buɗe hanyoyin tuntubar juna tsakaninta da Amurka, bayan da shugaba Donald Trump ya yi barazanar yin amfani da ƙarfi kan ƙasar matuƙar ta ci gaba da kashe masu zanga-zanga. Mahukuntan Iran dai na ƙoƙarin shawo kan ɗaya daga cikin bore mafi muni da suka taɓa faruwa a ƙasar. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon jakadan Najeriya a Iran Amabasada Abubakar Cika, ga kuma zantawarsu dangane da wannan tarzoma ta Iran. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
A Najeriya, gobe Alhamis 1 ga watan Janairu ne, za a fara aiwatar da sabuwar dokar haraji ta ƙasa, a cikin yanayi da dokar ke shan suka saboda dalilai da dama. Yayin da jama'a ke cewa sabon tsarin karɓar haraji na matsayin ƙarin nauyi ne ga al'umma, hakazalika wasu ƴan majalisa sun yi zargin cewa abin da suka amince da shi ya sha bambam da abin da gwamnati ke shirin aiwatarwa. A game da shirin aiwatar da dokar ne Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dakta Mahdi Shehu da ke fafutuka a Najeriya, ga kuma zantawarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
A jamhuriyar Nijar yanzu haka ana ci gaba da mahawara dangane da matakin da mahukuntan ƙasar suka ɗauka da ke shelanta kafa dokar-ta-ɓaci, wanda a ƙarƙashinta gwamnati za ta iya yin amfani da illahirin al'ummar ƙasar da kuma dukiyoyinsu a duk lokacin da ta ga ya dace don tunkarar barazanar tsaro. Maman Wada na ƙugiyar Transaparency International reshen Nijar Ga dai abin da ya shaida wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal. Shiga alamar sauti domin sauraron karin bayani.....
Kamar dai kowace shekara, 1 ga watan Disamba ita ce ranar da Hukumar Lafiya ta Duniya ta keɓe don yaƙi da cuta mai karya garkuwar jikin ɗan Adam wato HIV ko kuma SIDA. Bikin na bana ya zo ne a cikin wani yanayi da shugaba Donald Trump ya katse tallafin da Amurka ke bai wa ƙasashe masu tasowa ciki har da na ɓangaren yaƙi da wannan cuta. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Nasir Sani Gwarzo ƙwararren likitan yaƙi da annoba a Najeriya, wanda ya fara da bayyana halin da ake ciki game da yaƙi da HIV a ƙasar. Ga zantawarsu.
An buɗe taron baje kolin kafafen yaɗa labarai na Afrika da ake kira AFRICAST karo 14 a birnin Lagos da ke Najeriya, inda masu ruwa da tsaki a harkar yaɗa labarai daga nahiyar da kuma sassan duniya ke halarta.Domin ƙara inganta ayyukan yaɗa labarai, wasu daga cikin mahalarta wannan taro na ganin cewa ya zama wajibi a samar da dokokin da za su sa-ido kan ayyukan kafafen sada zumunta da kuma sauran hanyoyin yaɗa labarai ta yanar gizo. Sanusi Bature Dawakin Tofa, shi ne mai magana da yawun gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Yusuf, kuma wanda ya wakilce shi a taron, a zantawarsa da Abdoulkarim Ibrahim Shikal, ya ce lalle akwai buƙatar samar da gyara a wannan fanni. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar...................
A ƙarshen makon da ya gabata aka fara yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a Kamaru, inda mutane 12 ciki har da shugaba mai-ci Paul Biya za su kara da juna a ranar 12 ga watan gobe na Oktoba idan Allah ya kai mu. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Farfesa Ouba Ali Mahamman, masani siyasar Kamaru da ke zaune a birnin Yaounde, wanda da farko ya bayyana bambancin da ke akwai tsakanin wannan zaɓe da kuma waɗanda aka saba yi shekarun baya a ƙasar. Ga dai abin da yake cewa. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.
Burkina Faso da Mali da kuma Nijar sun sanar da janyewar ƙasashensu daga Kotun Hukunta Laifufuka ta Duniya da ke birnin Hague. A sanarwar haɗin-gwiwa da suka fitar cikin daren Litinin da ta gabata, ƙasashen uku sun ce sun ɗauki matakin ne saboda sun lura cewa kotun ta rikiɗe domin zama ƴar amashin ƴan mulkin mallaka. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani dokokin ƙasa da ƙasa Maitre Lirwanou Abdourahman, domin jin ko wataƙila ya yarda da dalilan da wadannan ƙasashe suka gabatar. Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawarsu.................
Burkina Faso, Mali da kuma Nijar sun sanar da janyewar ƙasashensu daga Kotun Hukunta Laifufuka ta Duniya da ke birnin Hague. A sanarwar haɗin-gwiwa da suka fitar cikin daren litinin da ta gabata, ƙasashen uku sun ce sun ɗauki matakin saboda sun lura cewa kotun ta rikiɗe domin zama ƴar amashin ƴan mulkin mallaka. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani dokokin ƙasa da ƙasa Maitre Lirwanou Abdourahman, domin jin ko wataƙila ya yarda da dalilan da wadannan ƙasashe suka gabatar. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.
A ƙarshen wannan mako ne za a ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa da za a gudanar 12 ga watan gobe na Oktoba idan Allah ya kai mu a Kamaru. To sai dai yayin da jam'iyyar RDPC mai mulki ta bayyana Paul Biya a matsayin wanda zai tsaya mata takara, a nasu ɓangare kuwa, yanzu haka ƴan adawa, na ci gaba da tattaunawa don fitar da mutum ɗaya da zai tsaya musu takara a zaɓen. Kan haka Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Ambasada Malam Mohamed Sani, tsohon jakada a lokacin mulkin Ahmadou Ahidjo, amma a yanzu yake zaune a ƙetare, inda ya bayyana yadda suke kallon wannan zaɓe. Ƙu latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu............
A ƙarshen wannan mako ne za a ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a Kamaru, zaɓen da zai gudana a ranar 12 ga watan gobe na Oktoba. To sai dai yayin da jam'iyyar RDPC mai mulki ta bayyana Paul Biya a matsayin wanda zai tsaya mata takara, a nasu ɓangare kuwa, yanzu haka ƴan adawa, na ci gaba da tattaunawa don fitar da mutum ɗaya da zai tsaya zaɓen amadadinsu. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Ambasada Malam Mohamed Sani, tsohon jakada a lokacin mulkin Ahmadou Ahidjo, amma a yanzu yake zaune a ƙetare, inda ya bayyana yadda suke kallon wannan zaɓe.
A makon da ya gabata ne likitoci da ke neman ƙawarewa a Najeriya suka gudanar da yajin aiki, domin nuna rashin amincewa dangane da yadda gwamnati ke jan ƙafa wajen ƙin biyansu haƙƙoƙinsu.To sai dai bayan da aka fara biyansu wasu daga cikin haƙƙoƙin, sun dakatar da yajin aikin tare da bai wa gwamnati ƙarin makonni biyu domin shafe musu hawayensu. Dr Uzairu Abdullahi, shi ne Editan Mujallar wallafa labarai ta ƙungiyar ya yi ƙarin bayani..... Latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawar da Abdoulkarim Ibrahim Shikal........
Ƙuniyar Agaji ta Red Cross ta ce yanzu haka akwai mutane sama da dubu 23 da suka ɓata a sassan Najeriya. A bayanin da ta fitar a jiya lahadi, ƙungiyar ta ce 68% na waɗanda suka ɓata dukanninsu mata ne, yayin da jihar Yobe ke matsayin jagora ta fannin yawan waɗanda lamarin ya fi shafa. Fatima Baba Fugu, tana aiki ne da sashen da ke haɗa waɗanda suka ɓata da iyalansu a ƙungiyar ta ICRC daga birnin Maiduguri jihar Borno, ta yi wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal ƙarin bayani a game da waɗannan alkaluma da ƙungiyar ta fitar.
Yanzu haka ƙasashe na ci gaba da ɗaukar matakan kwashe al'ummominsu daga Iran da kuma Isra'ila, saboda yadda yaƙi ya tsananta a tsakanin ƙasashen biyu. Bayanai na nuni da cewa ofishin jakadancin Najeriya da ke Iran, ya fara tsara yadda za su kwashe ƴan Najeriya da motoci zuwa Armenia kafin wataƙila a yi amafani da jiragen don dawo su gida. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Muhammad Ibrahim Sa'id, ɗan Najeriya da ke karatu a birnin Qoom mai tazarar kilomita 150 a kudancin Tehran. Ku latsa alamar sauti domin jin zantawarsu........
A wannan litinin an shiga rana ta huɗu da fara yaƙi gadan-gadan tsakanin Isra'il ta Iran, inda kowanne daga cikin ƙsashen biyu ke amfani da manyan makamai don kai wa farmaki a kan manyan biranen ƙasashensu. Domin yin dubi a game da wannan rikici da ake ganin cewa muddun ba a dakatar da shi ba zai shafar ƙasashe da dama, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon jakadan Najeriya a Iran. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hira da Ambasada Alhaji Abubukar Cika.....
Gwamnmatin Jamhuriyar Nijar ta buƙaci ƴan asalin ƙasashen ƙetare da ke aiki a ɓangaren man fetur da su fice daga ƙasar kafin ranar 31 ga wannan wata na Mayu. Mafi yawan waɗanda matakin zai shafa ƴan ƙasar China ne da ke aikin haƙowa, da tacewa, sai kuma waɗanda ke fitar da mai ta bututu zuwa ƙetare. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Alhaji Nouhou Abdou Magaji da Abdoulkarim Ibrahim Shikal.....
An gudanar da ƙwarya-ƙwaryar biki don murnar cika shekaru 18 da buɗe Sashen Hausa na Radio France International, inda aka samu halartar manyan baƙi da suka haɗa da sarakunan gargaji, ƴan siyasa da kuma masu sauraren rediyon da sauran kafafensa na yaɗa shirye-shirye. Ɗaya daga cikin manyan baƙi a taron shi ne Distinguished Senator Aliyu Ikra Bilbis wanda ya bayyana mahangarsa a game da waɗannan shekaru 18 na RFI Hausa. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Abdoulkarim Ibrahim Shikal..............
Yanzu haka ana ci gaba da gudanar da bukukuwan Easter, waɗanda ke matsayin tunawa da ranar da aka gicciye Yesu Almasihu da kuma tashinsa bayan kwanaki uku. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Reverand Andrew Dayyu, wanda ya yi masa ƙarin bayani a game da abin da ake nufi da Easter da kuma muhimmancinta ga mabiyar addinin Kirista. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar zantawarsu.............
Al'ummar musulmi a sassan duniya na gudanar da bukukuwan Mauludi, domin tunawa da ranar da aka haifi annabi Muhammad mai tsira da amincin Allah.To domin sanin muhimmancin wannan rana ga musulmi, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Sheikh Mansur Ibrahim da ke garin Kaduna a Najeriya.
Kwararru game da matsalar sauyin yanayi da kuma wakilan gwamnatoci da na ƙungiyoyi, sun fara gudanar da wani taron kwanaki uku a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar, domin tattauna matsalar sauyin yanayi a Yankin Sahel da kuma Yammacin Afirka. To domin jin muhimmancin wannan taro, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Moussa Hassan Ousseini, jagoran ƙungiyar Jeunes volontaires pour l'environnement du Niger mai rajin kare muhalli a Jamhuriyar Nijar.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.....
Yayin da ake ci gaba da fuskantar tsadar rayuwa a Najeriya, manazarta na ganin cewa ba wata hanya da za ta taimaka domin kawo wa jama'a sauƙi face bayar da damar shigar da kayan abinci da na masarufi daga ƙetare har zuwa cikin ƙasar har zuwa lokacin da lamurra za su daidaita. Alhaji Shehu Yaro Abdulkadir Jimoh, ɗan kasuwa ne kuma shugaban al'umma, na daga cikin masu goyon bayan wannan shawara, ga kuma abin da yake cewa a zantawarsu da Abdoulkarim Ibrahim Shikal.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu
Matsalar tsaro a Jamhuriyar Nijar na ci gaba da ɗaukar sabon salo lura da yadda ake samun ɓullar sabbin ƙungiyoyin tawaye da ke kai hare-hare, inda suke cewa suna yin hakan ne saboda neman a saki hamɓararren shugaban ƙasar Mohamed Bazoum. Bayan da ƙungiyar FPL ta kai hari kan bututun mai da ke sada ƙasar da jamhuriyar Benin, a ranar juma'ar da ta gabata kuwa, wata ƙungiyar mai suna FPJ ta kama da kuma yin garkuwa da kantoman mulkin soji na yankin Bilma da muƙarrabansa a jihar Agadez. Don jin dalilan bayyanar waɗannan ƙungiyoyi da kuma manufofinsu, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Mahaman Sani Roufa'i mai sharhi kan lamurran yau da kullum a Damagarm.Latsa alamar sauti don jin cikakkiyar zantawarsu.......
Mahukunta a Nijar sun ce ba za su bari motocin da ke ɗauke da lambar Jamhuriyar Benin damar tsallaka iyakar ƙasar da Najeriya domin shiga ko kuma fita daga Nijar ba, a maimakon haka, sai dai su zagaya zuwa cikin Burkina Faso da kuma Togo kafin komawa gida. Wannan dai alama ce da ke ƙara tabbatar da cewa alaƙa ta yi tsami a tsakanin ƙasashen biyu tun daga lokacin da aka kifar da gwamnati Mohamed Bazoum. Dan gane da wannan mataki, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Hima Barkire, sakataren tsare-tsare na ƙungiyar masu motocin dakon kaya a Nijar.Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawar ta su......
Duk da matakai da mahukunta a Najeriya ke cewa sun dauka domin tunkarar manyan matsalolin da kasar ke fama da su, da suka hada da na tsaro da kuma tsadar rayuwa, toh amma mafi yawan al'ummar kasar cewa suke yi a zahirance babu wani tasiri da wadannan matakai ke yi wajen shawo kan wadannan matsaloli. Toh sai dai Hon Muktar Ishaq Yakasai, daya daga cikin magoya bayan shugaba Bola Ahmed Tinubu, na ganin cewar ya kamata a yi wa shugaban adalci, lura da irin matsalolin da gwamnatinsa ta gada.Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Abdoulkarim Ibrahim Shikal.....
Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken ya sake komawa a Yankin Gabas ta Tsakiya a ci gaba da kokarin da kasashen duniya ke yi don samar da tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas. Daga farkon wannan rikici wanda ya barke a ranar 7 ga watan Oktoban bara zuwa yanzu, sau da dama Amurka na cewa tana yunkuri domin samar da tsagaita wuta a wannan yaki da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane kusan dubu 35 da kuma raba sama da milyan biyu da gidajensu. Farfesa Tukur Abdulkadir malami a jami'ar jimi'ar jihar Kaduna, na ganin cewa, da dagaske Amurka ke yi, da tuni an kawo karshen wannan yaki.Ku latsa alamar sauti don jin zantawarsa da Abdoulkarim Ibrahim Shikal.......
Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar ta sanar da kawo karshen yarjejeniyar tsaro da ke tsakanin kasar da Amurka, tare da zargin cewa dakarun Amurka wadanda adadinsu ya zarta dubu daya na zaune a kasar ne ba a kan ka'ida ba. Sanarwar ta zo ne kwana guda bayan da wata babbar tawagar Amurka ta kamma ziyarar da ta kai Nijar ta tsawon kwanaki uku. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Farfesa Dicko Abdourahmane, masani tsaro kuma malami a jami'ar Damagaram Zinder, wanda da farko ya fara yin bayani a game da dalilan da suka sa mahukuntan Nijar suka dauki wannan mataki.Ku latsa alamar sauti don jin zantawarsu.......
A Najeriya wata babbar matsala da ake fama da ita a kasar ita ce yawaitar satar kananan yara musamman a yankin arewacin kasar, inda bayanai ke cewa bayan sace su, ana safarar su ne zuwa wasu yankuna da ke kudancin kasar. Malam Ibrahim Yunusa Ibrahim da ke zaune a Gwagwalada kusa da Abuja, daya ne daga cikin gungun iyalai fiye da 50 wadanda aka sace ‘yayansa, kuma yanzu haka suke ci gaba da nema, ya yi wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal karin bayani a game da wannan matsalar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
Kwamitin da mahukuntan Jamhuriyar Nijar suka kafa domin bayar da shawarwari dangane da yadda za a inganta karatun firamire a kasar ya gabatar da rahotonsa ga ministar ilimi. Kafa wannan kwamiti da ya kunshi kwarari, ya biyo bayan lura da yadda aksarin yara ke kammala firamire amma ba tare da sun iya rubutu da karatu ba.A zantawarsu da Abdoulkarim Ibrahim Shikal, Abdou Dan Neito mai fafutuka a cikin kungiyoyin fararen hula ke cewa ya zama wajibi a samar da wannan gyara.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar zantawarsu
Kusan watanni biyu kenan da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin ci gaba da bai wa ‘yan kasuwa da ke shigar da wasu kayayyaki fiye da 40 a cikin kasar damar samun dala cikin sauki daga babban bankin kasar, amma har yanzu bincike na nuni da cewa ba a fara aiwatar da umurnin ba. To sai dai a daya bangare an wayi gari da karin kudaden da ‘yan kasuwa ke biya a matsayin fito ko kuma harajin shigar da kaya a kasar ne saboda an bari kasuwa ta aikinta a fagen canjin Naira zuwa kudaden ketare.Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Zubairu Mele Abba-Ganamma, daya daga cikin shugabannin kungiyar masu aikin fito wato 'Transit Agents', wanda ya yi mana karin bayani a game da hakan.
A Najeriya, sakamakon da Jim Obazee, wanda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada domin binciken yadda tsohon gwamnan Babban Bankin Kasar Godwin Emefiele ya gudanar da ayyukansa ya fitar, na ci gaba da haifar da muhawara a tsakanin jama'a. Tuni dai bankin na CBN ya fitar da wata sanarwa da ke yin kira ga jama'a da su kwantar da hankulansu, domin kuwa ba abin da zai shafi kudadensu da ke ajiye a bankunan da rahoton mai binciken ke cewa tafka kura-kurai wajen sayar da hannayen jarinsu.Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tattalin arziki Shu'aibu Mikati, a game da wannan rahoto da kuma abubuwan da ya kunsa.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar zantawarsu.
Gwamnatin Jamhuriyar Benin ta ce ba za ta bari a kwashe kayayyakin da aka sauke a tashar jiragen ruwan Cotonou zuwa Nijar ba, amma a maimakon haka za ta bai wa ‘yan kasuwar Nijar damar karkata akalar kayayyakin zuwa wasu kasashe, ta hanyoyin mota ko jiragen ruwa. A sanarwar da ta fitar karshen mako, hukumar kula da tashar jijagen ruwan Cotonou ta kuma bai wa ‘yan kasuwar Nijar damar sayar da kayayyakinsu a Benin idan har ba za su karkata akalarsu zuwa wata kasa ba. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Yacouba Dan Maradi, shugaban kungiyar ‘yan kasuwa da ke shigar da kaya a Nijar, domin jin yadda suke kallon wannan mataki. Ga kuma zantawarsu.