POPULARITY
A ƙarshen makon da ya gabata aka fara yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a Kamaru, inda mutane 12 ciki har da shugaba mai-ci Paul Biya za su kara da juna a ranar 12 ga watan gobe na Oktoba idan Allah ya kai mu. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Farfesa Ouba Ali Mahamman, masani siyasar Kamaru da ke zaune a birnin Yaounde, wanda da farko ya bayyana bambancin da ke akwai tsakanin wannan zaɓe da kuma waɗanda aka saba yi shekarun baya a ƙasar. Ga dai abin da yake cewa. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.
Burkina Faso da Mali da kuma Nijar sun sanar da janyewar ƙasashensu daga Kotun Hukunta Laifufuka ta Duniya da ke birnin Hague. A sanarwar haɗin-gwiwa da suka fitar cikin daren Litinin da ta gabata, ƙasashen uku sun ce sun ɗauki matakin ne saboda sun lura cewa kotun ta rikiɗe domin zama ƴar amashin ƴan mulkin mallaka. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani dokokin ƙasa da ƙasa Maitre Lirwanou Abdourahman, domin jin ko wataƙila ya yarda da dalilan da wadannan ƙasashe suka gabatar. Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawarsu.................
Burkina Faso, Mali da kuma Nijar sun sanar da janyewar ƙasashensu daga Kotun Hukunta Laifufuka ta Duniya da ke birnin Hague. A sanarwar haɗin-gwiwa da suka fitar cikin daren litinin da ta gabata, ƙasashen uku sun ce sun ɗauki matakin saboda sun lura cewa kotun ta rikiɗe domin zama ƴar amashin ƴan mulkin mallaka. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani dokokin ƙasa da ƙasa Maitre Lirwanou Abdourahman, domin jin ko wataƙila ya yarda da dalilan da wadannan ƙasashe suka gabatar. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.
A ƙarshen wannan mako ne za a ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa da za a gudanar 12 ga watan gobe na Oktoba idan Allah ya kai mu a Kamaru. To sai dai yayin da jam'iyyar RDPC mai mulki ta bayyana Paul Biya a matsayin wanda zai tsaya mata takara, a nasu ɓangare kuwa, yanzu haka ƴan adawa, na ci gaba da tattaunawa don fitar da mutum ɗaya da zai tsaya musu takara a zaɓen. Kan haka Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Ambasada Malam Mohamed Sani, tsohon jakada a lokacin mulkin Ahmadou Ahidjo, amma a yanzu yake zaune a ƙetare, inda ya bayyana yadda suke kallon wannan zaɓe. Ƙu latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu............
A ƙarshen wannan mako ne za a ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a Kamaru, zaɓen da zai gudana a ranar 12 ga watan gobe na Oktoba. To sai dai yayin da jam'iyyar RDPC mai mulki ta bayyana Paul Biya a matsayin wanda zai tsaya mata takara, a nasu ɓangare kuwa, yanzu haka ƴan adawa, na ci gaba da tattaunawa don fitar da mutum ɗaya da zai tsaya zaɓen amadadinsu. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Ambasada Malam Mohamed Sani, tsohon jakada a lokacin mulkin Ahmadou Ahidjo, amma a yanzu yake zaune a ƙetare, inda ya bayyana yadda suke kallon wannan zaɓe.
A makon da ya gabata ne likitoci da ke neman ƙawarewa a Najeriya suka gudanar da yajin aiki, domin nuna rashin amincewa dangane da yadda gwamnati ke jan ƙafa wajen ƙin biyansu haƙƙoƙinsu.To sai dai bayan da aka fara biyansu wasu daga cikin haƙƙoƙin, sun dakatar da yajin aikin tare da bai wa gwamnati ƙarin makonni biyu domin shafe musu hawayensu. Dr Uzairu Abdullahi, shi ne Editan Mujallar wallafa labarai ta ƙungiyar ya yi ƙarin bayani..... Latsa alamar sauti domin sauraron tattaunawar da Abdoulkarim Ibrahim Shikal........
Ƙuniyar Agaji ta Red Cross ta ce yanzu haka akwai mutane sama da dubu 23 da suka ɓata a sassan Najeriya. A bayanin da ta fitar a jiya lahadi, ƙungiyar ta ce 68% na waɗanda suka ɓata dukanninsu mata ne, yayin da jihar Yobe ke matsayin jagora ta fannin yawan waɗanda lamarin ya fi shafa. Fatima Baba Fugu, tana aiki ne da sashen da ke haɗa waɗanda suka ɓata da iyalansu a ƙungiyar ta ICRC daga birnin Maiduguri jihar Borno, ta yi wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal ƙarin bayani a game da waɗannan alkaluma da ƙungiyar ta fitar.
Yanzu haka ƙasashe na ci gaba da ɗaukar matakan kwashe al'ummominsu daga Iran da kuma Isra'ila, saboda yadda yaƙi ya tsananta a tsakanin ƙasashen biyu. Bayanai na nuni da cewa ofishin jakadancin Najeriya da ke Iran, ya fara tsara yadda za su kwashe ƴan Najeriya da motoci zuwa Armenia kafin wataƙila a yi amafani da jiragen don dawo su gida. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Muhammad Ibrahim Sa'id, ɗan Najeriya da ke karatu a birnin Qoom mai tazarar kilomita 150 a kudancin Tehran. Ku latsa alamar sauti domin jin zantawarsu........
A wannan litinin an shiga rana ta huɗu da fara yaƙi gadan-gadan tsakanin Isra'il ta Iran, inda kowanne daga cikin ƙsashen biyu ke amfani da manyan makamai don kai wa farmaki a kan manyan biranen ƙasashensu. Domin yin dubi a game da wannan rikici da ake ganin cewa muddun ba a dakatar da shi ba zai shafar ƙasashe da dama, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon jakadan Najeriya a Iran. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hira da Ambasada Alhaji Abubukar Cika.....
Gwamnmatin Jamhuriyar Nijar ta buƙaci ƴan asalin ƙasashen ƙetare da ke aiki a ɓangaren man fetur da su fice daga ƙasar kafin ranar 31 ga wannan wata na Mayu. Mafi yawan waɗanda matakin zai shafa ƴan ƙasar China ne da ke aikin haƙowa, da tacewa, sai kuma waɗanda ke fitar da mai ta bututu zuwa ƙetare. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Alhaji Nouhou Abdou Magaji da Abdoulkarim Ibrahim Shikal.....
An gudanar da ƙwarya-ƙwaryar biki don murnar cika shekaru 18 da buɗe Sashen Hausa na Radio France International, inda aka samu halartar manyan baƙi da suka haɗa da sarakunan gargaji, ƴan siyasa da kuma masu sauraren rediyon da sauran kafafensa na yaɗa shirye-shirye. Ɗaya daga cikin manyan baƙi a taron shi ne Distinguished Senator Aliyu Ikra Bilbis wanda ya bayyana mahangarsa a game da waɗannan shekaru 18 na RFI Hausa. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Abdoulkarim Ibrahim Shikal..............
Yanzu haka ana ci gaba da gudanar da bukukuwan Easter, waɗanda ke matsayin tunawa da ranar da aka gicciye Yesu Almasihu da kuma tashinsa bayan kwanaki uku. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Reverand Andrew Dayyu, wanda ya yi masa ƙarin bayani a game da abin da ake nufi da Easter da kuma muhimmancinta ga mabiyar addinin Kirista. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar zantawarsu.............
Al'ummar musulmi a sassan duniya na gudanar da bukukuwan Mauludi, domin tunawa da ranar da aka haifi annabi Muhammad mai tsira da amincin Allah.To domin sanin muhimmancin wannan rana ga musulmi, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Sheikh Mansur Ibrahim da ke garin Kaduna a Najeriya.
Kwararru game da matsalar sauyin yanayi da kuma wakilan gwamnatoci da na ƙungiyoyi, sun fara gudanar da wani taron kwanaki uku a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar, domin tattauna matsalar sauyin yanayi a Yankin Sahel da kuma Yammacin Afirka. To domin jin muhimmancin wannan taro, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Moussa Hassan Ousseini, jagoran ƙungiyar Jeunes volontaires pour l'environnement du Niger mai rajin kare muhalli a Jamhuriyar Nijar.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.....
Yayin da ake ci gaba da fuskantar tsadar rayuwa a Najeriya, manazarta na ganin cewa ba wata hanya da za ta taimaka domin kawo wa jama'a sauƙi face bayar da damar shigar da kayan abinci da na masarufi daga ƙetare har zuwa cikin ƙasar har zuwa lokacin da lamurra za su daidaita. Alhaji Shehu Yaro Abdulkadir Jimoh, ɗan kasuwa ne kuma shugaban al'umma, na daga cikin masu goyon bayan wannan shawara, ga kuma abin da yake cewa a zantawarsu da Abdoulkarim Ibrahim Shikal.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu
Matsalar tsaro a Jamhuriyar Nijar na ci gaba da ɗaukar sabon salo lura da yadda ake samun ɓullar sabbin ƙungiyoyin tawaye da ke kai hare-hare, inda suke cewa suna yin hakan ne saboda neman a saki hamɓararren shugaban ƙasar Mohamed Bazoum. Bayan da ƙungiyar FPL ta kai hari kan bututun mai da ke sada ƙasar da jamhuriyar Benin, a ranar juma'ar da ta gabata kuwa, wata ƙungiyar mai suna FPJ ta kama da kuma yin garkuwa da kantoman mulkin soji na yankin Bilma da muƙarrabansa a jihar Agadez. Don jin dalilan bayyanar waɗannan ƙungiyoyi da kuma manufofinsu, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Mahaman Sani Roufa'i mai sharhi kan lamurran yau da kullum a Damagarm.Latsa alamar sauti don jin cikakkiyar zantawarsu.......
Mahukunta a Nijar sun ce ba za su bari motocin da ke ɗauke da lambar Jamhuriyar Benin damar tsallaka iyakar ƙasar da Najeriya domin shiga ko kuma fita daga Nijar ba, a maimakon haka, sai dai su zagaya zuwa cikin Burkina Faso da kuma Togo kafin komawa gida. Wannan dai alama ce da ke ƙara tabbatar da cewa alaƙa ta yi tsami a tsakanin ƙasashen biyu tun daga lokacin da aka kifar da gwamnati Mohamed Bazoum. Dan gane da wannan mataki, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Hima Barkire, sakataren tsare-tsare na ƙungiyar masu motocin dakon kaya a Nijar.Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawar ta su......
Duk da matakai da mahukunta a Najeriya ke cewa sun dauka domin tunkarar manyan matsalolin da kasar ke fama da su, da suka hada da na tsaro da kuma tsadar rayuwa, toh amma mafi yawan al'ummar kasar cewa suke yi a zahirance babu wani tasiri da wadannan matakai ke yi wajen shawo kan wadannan matsaloli. Toh sai dai Hon Muktar Ishaq Yakasai, daya daga cikin magoya bayan shugaba Bola Ahmed Tinubu, na ganin cewar ya kamata a yi wa shugaban adalci, lura da irin matsalolin da gwamnatinsa ta gada.Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Abdoulkarim Ibrahim Shikal.....
Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken ya sake komawa a Yankin Gabas ta Tsakiya a ci gaba da kokarin da kasashen duniya ke yi don samar da tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas. Daga farkon wannan rikici wanda ya barke a ranar 7 ga watan Oktoban bara zuwa yanzu, sau da dama Amurka na cewa tana yunkuri domin samar da tsagaita wuta a wannan yaki da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane kusan dubu 35 da kuma raba sama da milyan biyu da gidajensu. Farfesa Tukur Abdulkadir malami a jami'ar jimi'ar jihar Kaduna, na ganin cewa, da dagaske Amurka ke yi, da tuni an kawo karshen wannan yaki.Ku latsa alamar sauti don jin zantawarsa da Abdoulkarim Ibrahim Shikal.......
Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar ta sanar da kawo karshen yarjejeniyar tsaro da ke tsakanin kasar da Amurka, tare da zargin cewa dakarun Amurka wadanda adadinsu ya zarta dubu daya na zaune a kasar ne ba a kan ka'ida ba. Sanarwar ta zo ne kwana guda bayan da wata babbar tawagar Amurka ta kamma ziyarar da ta kai Nijar ta tsawon kwanaki uku. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Farfesa Dicko Abdourahmane, masani tsaro kuma malami a jami'ar Damagaram Zinder, wanda da farko ya fara yin bayani a game da dalilan da suka sa mahukuntan Nijar suka dauki wannan mataki.Ku latsa alamar sauti don jin zantawarsu.......
A Najeriya wata babbar matsala da ake fama da ita a kasar ita ce yawaitar satar kananan yara musamman a yankin arewacin kasar, inda bayanai ke cewa bayan sace su, ana safarar su ne zuwa wasu yankuna da ke kudancin kasar. Malam Ibrahim Yunusa Ibrahim da ke zaune a Gwagwalada kusa da Abuja, daya ne daga cikin gungun iyalai fiye da 50 wadanda aka sace ‘yayansa, kuma yanzu haka suke ci gaba da nema, ya yi wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal karin bayani a game da wannan matsalar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
Kwamitin da mahukuntan Jamhuriyar Nijar suka kafa domin bayar da shawarwari dangane da yadda za a inganta karatun firamire a kasar ya gabatar da rahotonsa ga ministar ilimi. Kafa wannan kwamiti da ya kunshi kwarari, ya biyo bayan lura da yadda aksarin yara ke kammala firamire amma ba tare da sun iya rubutu da karatu ba.A zantawarsu da Abdoulkarim Ibrahim Shikal, Abdou Dan Neito mai fafutuka a cikin kungiyoyin fararen hula ke cewa ya zama wajibi a samar da wannan gyara.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar zantawarsu
Kusan watanni biyu kenan da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin ci gaba da bai wa ‘yan kasuwa da ke shigar da wasu kayayyaki fiye da 40 a cikin kasar damar samun dala cikin sauki daga babban bankin kasar, amma har yanzu bincike na nuni da cewa ba a fara aiwatar da umurnin ba. To sai dai a daya bangare an wayi gari da karin kudaden da ‘yan kasuwa ke biya a matsayin fito ko kuma harajin shigar da kaya a kasar ne saboda an bari kasuwa ta aikinta a fagen canjin Naira zuwa kudaden ketare.Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Zubairu Mele Abba-Ganamma, daya daga cikin shugabannin kungiyar masu aikin fito wato 'Transit Agents', wanda ya yi mana karin bayani a game da hakan.
A Najeriya, sakamakon da Jim Obazee, wanda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada domin binciken yadda tsohon gwamnan Babban Bankin Kasar Godwin Emefiele ya gudanar da ayyukansa ya fitar, na ci gaba da haifar da muhawara a tsakanin jama'a. Tuni dai bankin na CBN ya fitar da wata sanarwa da ke yin kira ga jama'a da su kwantar da hankulansu, domin kuwa ba abin da zai shafi kudadensu da ke ajiye a bankunan da rahoton mai binciken ke cewa tafka kura-kurai wajen sayar da hannayen jarinsu.Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da masani tattalin arziki Shu'aibu Mikati, a game da wannan rahoto da kuma abubuwan da ya kunsa.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar zantawarsu.
Gwamnatin Jamhuriyar Benin ta ce ba za ta bari a kwashe kayayyakin da aka sauke a tashar jiragen ruwan Cotonou zuwa Nijar ba, amma a maimakon haka za ta bai wa ‘yan kasuwar Nijar damar karkata akalar kayayyakin zuwa wasu kasashe, ta hanyoyin mota ko jiragen ruwa. A sanarwar da ta fitar karshen mako, hukumar kula da tashar jijagen ruwan Cotonou ta kuma bai wa ‘yan kasuwar Nijar damar sayar da kayayyakinsu a Benin idan har ba za su karkata akalarsu zuwa wata kasa ba. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Yacouba Dan Maradi, shugaban kungiyar ‘yan kasuwa da ke shigar da kaya a Nijar, domin jin yadda suke kallon wannan mataki. Ga kuma zantawarsu.
A Jamhuriyar Nijar, yau 26 ga watan Okotba, watanni 3 kenan da sojoji suka kifar da gwamnatin dimokuradiyyar da ke karkashin jagorancin Mohamed Bazoum, lamarin da ya sa kungiyar ECOWAS da kuma UEMOA suka kakaba wa kasar takunkumai da dama. Yanzu haka dai wannan lamari ya jefa al'ummar kasar a cikin hali na kunci saboda rashin kudi da kuma rashin kayayyakin masarufi. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Ambasada Abubakar Cika, domin jin yadda yake kallon wannan rikici da kuma halin da Nijar ke ciki saboda wannan juyin mulki.
A yanzu haka dai al'ummar musulmi sama da milyan 2 da dubu 500 ne suka tururuwa domin tsayuwar Arafa, da ke matsayin babban ginshinki a aikin hajji, bayan kammala tsayuwar Araf a gobe laraba, musulmi a sassan duniya za su gudaanr da bukukuwan sallar layya, tare da yanka dabbobinsu a matsayin Ibada. Domin jin abin da ake nufi da layya da kuma dabbar da ta cancanci a yi layya da ita, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zantar da Sheikh Dakta Abubakar Hassan Dikko, malamin addinin musulunci a Najeriya.Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar ta su..........
Al'amurran yau da kullum sun fara daidaita a birnin Moscow fadar gwamnatin kasar Rasha, bayan da jagoran kamfanin Wagner Yevgeny Prigozhin ya sanar da dakatar da boren da yake yi wa gwamnatin Vladimir Putin. Shugaban kasar Belarusse Alexander Loukochanko ne ya yi nasarar shawo kan shugaban Wagner domin jingine yunkurinsa na afka wa birnin Moscow, tare da amince wa ya bar Rasha zuwa Belarusse. Domin jin dalilin da suka haddasa tsamin dangantaka tsakanin Putin da Prigozhin, da kuma yadda hakan zai shafi makomar yakin Rasha da Ukraine? Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Janar Idris Bello Dambazau mai ritaya. A latsa alamar sauti don jin tattaunawar ta su.......
Hukumar sa-ido game da yadda ake hada-hadar kudade a Najeriya wato NFIU, ta ce daga ranar 1 ga watan Maris mai zuwa Gwamnatin Tarayya, jihohi da kuma kananan hukumomi, ba su da izinin fitar da tsabar kudi daga asusun ajiyarsu, amma suna da hurumin yin hakan daga bakin zuwa. A cewar shugaban hukumar ta NFIU Modibbo Tukur, ya ce wadanda suka karya wannan ka'ida za su iya fuskantar hukuncin daurin shekaru 3 a gidan yari. Domin jin tasirin wannan tsari, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Kasimu Garba Kurfi, shugaban cibiyar hada-hadar hannayen jari na APT Securities and Fund Ltd da ke Lagos, ga kuma zantawarsu.
Matsanancin sanyin huturu na cigaba da wanzuwa a kasashe da dama na sassan duniya ciki har da na nahiyar Afirka. Wannan dai lokaci ne da masana kiwon lafiya ke gargadi domin daukar matakan kariya musamman ga yara kanana saboda kaucewa kamuwa da wasu cututuka da ke nasaba da sanyin na huturu. Dr Rilwanu Muhammad, shugaban sashen kula da lafiyar al'umma a matakin farko reshen jihar Bauchin Najeriya, ya bayyana wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal wasu daga cikin matsaloli na kiwon lafiya da ake cin karo da su a irin wannan lokaci na sanyin huturu.
Manoma a Najeriya sun bukaci mahukunta da su kara sanya ido, domin yaki da wadanda ke shigar da takin zamani maras inganci a cikin kasar. Alhaji Umar Ya'u Gwajo-Gwajo, daya daga cikin shugabannin kungiyar manoma a Najeriya, kuma shahrarren manomi a jihar Katsina, ya ce tabbas manoma na iya kokarinsu domin wadatar da kasar da abinci, amma duk da haka akwai bukatar gwamnati ta sanya ido domin samar da ingantaccen takin zamani a cikin kasar. Ga dai abin da ya shaida wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal a zantawarsu.
Duk da cewa Najeriya ta sanar da bude mafi yawan iyakoki tsakaninta da kasashe makota bayan da suka kasance a rufe tsawon kusan shekaru biyu, amma har yanzu zirga-zirga da kuma shige-da-ficen kayayyaki musamman tsakanin Najeriya da Jamhuriyar Benin bai kankama ba. Alhaji Zubairu Mele Abba Ganama, daya daga cikin shugabannin kungiyar masu aikin shige-da-ficen kaya a iyakar Seme Border, ya bayyana wa Abdoulkarim Ibrahim Shikal irin matsalolin da suke ci gaba da fuskanta.
Kusan makonni biyu da fara amfani da sabbin kudade a Najeriya, amma yanzu haka tsoffin kudade ne ke ci gaba da yawo a hannayen jama'a hatta a cikin bankuna da kuma wuraren cire kudi da ake kira ATM. Wannan dai na faruwa ne duk da cewa tuni babban bankin kasar wato CBN ya kayyade lokacin da za a daina amfani da tsoffin kudin. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Kasimu Garba Kurfi na kamfanin APT Securities and Funds Limited da ke hada-hadar kudade a birnin Lagos. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
A Najeriya, wasu bayanai na nuni da cewa gwamnatin Tarayyar kasar na shirin kawo karshen sassaucin biyan haraji da ta ke yi wa kamfanonin da ke gudanar da ayyukansu a karkara. Wannan mataki dai na kunshe ne a cikin sabuwar dokar kasafin kudi, wanda yanzu haka majalisar ke yi wa gyara kuma ake kyautata zaton cewa za a amince da ita a cikin wannan mako. Kan hakan Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Muhammad Magaji, Sakataren yada labarai na kungiyar manoman Najeriya.
A Najeriya rashin kyawun hanyoyi da kuma tsadar makamashi musamman diesel, na ci gaba da yin tasiri a kan farashin kayayyakin masarufi a kasuwannin kasar. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Umar Garba Alangawari, daya daga cikin masu motocin dakon kaya daga yankin kudu zuwa Arewacin Najeriya. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Sama da mutane milyan 280 ne ke rayuwa a matsayin ‘yan ci-rani a sassan duniya, wannan kuwa sanadiyyar tashe-tsahen hankula da kuma sauran matsaloli irin na yau da kullum. Wadannan alkaluma ne da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar a ranar Lahadi 18 ga watan Disamba, ranar da ake kebe domin kula da matsalolin da ‘yan ci-rani ke fuskanta a sassan duniya. Abdoulkarim Ibrahim Shikal, ya zanta da Dakta Shehou Azizou, shugaban wata kungiya da ke taimaka wa matafiya a yankin Agadez da ke arewacin jamhuriyar Nijar. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
Duk da cewa Majalisun Tarayyar Najeriya sun nuna fargaba a game da shirin sauya takardar kudin kasar da kuma adadin da za a iya cirewa a kowace rana, amma gwamnan babban bankin kasar Godwin Emiefele ya ce ba gudu ba ja da baya a game da wannan shiri da zai fara aiki a ranar 15 ga wannan wata na disamba. To sai dai a zantawarsu da Abdoulkarim Ibrahim Shikal, Alhaji Ibrahim Ya'u Galadanci, daya daga cikin shugabannin matasa a Najeriya, ya bayyana fargaba a game da wannan shiri, musamman yadda zai iya kara jefa talaka wanda bai mallaki asusun ajiya a banki ba cikin matsala.
Bankunan Kasuwancin a Najeriya sun sanar da janyewa daga tsarin bai wa manoma rancen kudade da babban bankin kasar ke kan aiwatarwa da ake kira da suna Anchor Barrower, bayan da mafi yawan manoman da suka karbi wannan rance su ka gaza dawo da kudaden da aka ba su. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da sakataren yada labaran kungiyar manoman Najeriya Alhaji Mouhammad Magaji, domin jin inda wannnan matsala ta samo asali, da kuma yadda hakan zai shafi makomar shirin, gad ai zantawarsu.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya sanar da kawo karshen ayyukan rundunar Barkhane mai yaki da ta'addanci a yankin Sahel daga jiya laraba, to sai dai ya ce Faransa za ta fayyace sabon tsarin ci gaba da kasantuwar dakarunta a Sahel cikin watanni 6 masu zuwa. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Tahirou Gimba, masani tsaro, domin jin yadda yake kallo matakin rusa rundunar da kuma yadda ya kamata alakar tsaro ta kasance tsakanin Faransa da sauran kasashen yankin, ga dai zantawarsu.
A rana ta biyu da fara taron duniya game da sauyin yanayi da ake kira Cop27 da ke gudana yanzu haka a Sharm el-Sheikh na Masar, Gidauniyar Bill Gates attajirin Amurka ta sanar da ware dala bilyan daya da milyan 400 a matsayin tallafi ga manoman Afirka da Kudancin Asiya. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Kabiru Ibrahim Matazu, na jami'ar Umaru Musa ‘Yar'adua, wanda da farko ya yi karin bayani a game da girman matsalar sauyin yanayi musamman ga bangaren noma a kasashen yammacin Afirka.
Lalacewar hanyoyin mota a Najeriya na ci gaba da haddasa matsaloli da dama da suka hada da tseko ga matafiya, hauhawar farashin dakon kaya da kuma barazanar tsaro ga matafiya. Wannan matsala ta lalacewar hanyoyi ta fi ta'azzara ne a jihar Niger da ke tsakiyar kasar, inda a wasu lokuta masu motocin ke share tsawon makonni kafin ratsa wannan jiha, kan hakan Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Umar Garba Alangawari, daya daga cikin masu motocin dakon kaya daga Lagos zuwa arewacin Najeriya, wanda ya bayyana mana girman wannan matsala.
Shirin 'Tarihin Afrika' na wannan mako tare da Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya kawo muka tarihin Kofi Atta Annan jami'in diflomasiyyar kasar Ghana wanda ya zama babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya na bakwai daga shekarar 1997 zuwa 2006. Amatsayin bakar fata na farko dan kasar Afirka ya dare wannan kujera, ya karbi kyautar zaman lafiya ta Nobel a shekarar 2001. Ya koma ga Allah ranar 18 ga watan Agustan shekarar 2018.
Shirin 'Tarihin Afrika' na wannan mako tare da Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya ci gaba da kawo muku tarihin fiitaccen shugaban kasar Ghana dan gwagwarmaya John Jerry Rawlings da ya mulki kasar na gajartaccen wa'adi a shekarar 1979 gabanin sake shugabantar kasar a wa'adi na 2 daga 1981 zuwa 2001.
Shirin 'Tarihin Afrika' na wannan mako tare da Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya ci gaba da kawo muku tarihin fiitaccen shugaban kasar Ghana dan gwagwarmaya John Jerry Rawlings da ya mulki kasar na gajartaccen wa'adi a shekarar 1979 gabanin sake shugabantar kasar a wa'adi na 2 daga 1981 zuwa 2001. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.
Shirin 'Tarihin Afrika' na wannan mako tare da Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya ci gaba da kawo muku tarihin fiitaccen shugaban kasar Ghana dan gwagwarmaya John Jerry Rawlings da ya mulki kasar na gajartaccen wa'adi a shekarar 1979 gabanin sake shugabantar kasar a wa'adi na 2 daga 1981 zuwa 2001.
Shirin tarihin Afrika tare da Abdoulkarim Ibrahim Shikal a wannan makon ya ci gaba da kawo muku tarihin fitaccen shugaban kasar Ghana dan gwagwarmaya John Jerry Rawlings da ya mulki kasar na gajartaccen wa'adi a 1979 gabanin sake shugabantar kasar a wa'adi 2 na daga 1981 zuwa 2001.
Shirin tarihin Afrika tare da Abdoulkarim Ibrahim Shikal a wannan makon ya ci gaba da kawo muku tarihin fitaccen shugaban kasar Ghana dan gwagwarmaya John Jerry Rawlings da ya mulki kasar na gajartaccen wa'adi a 1979 gabanin sake shugabantar kasar a wa'adi 2 na daga 1981 zuwa 2001.
Shirin tarihin Afrika tare da Abdoulkarim Ibrahim Shikal a wannan makon ya ci gaba da kawo muku tarihin fitaccen shugaban kasar Ghana dan gwagwarmaya John Jerry Rawlings da ya mulki kasar na gajartaccen wa'adi a 1979 gabanin sake shugabantar kasar a wa'adi 2 na daga 1981 zuwa 2001.
Har zuwa cikin daren jiya talata an ci gaba da kokari domin ceto tarin mutanen da da wani gini ya rufta a kansu, lokacin da su ke tsaka da hada-hadar kasuwanci a kasuwar Beirut da ke jihar Kano a Najeriya, duk da ya ke wasu sun yi korafi dangane da yadda aka fara gudanar da ayyukan ceton a makare. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Mai magana da yawun hukumar kwana-kwana a jihar ta Kano wato PFS Saminu Yusuf Abdullahi.
Shirin tarihin Afrika tare da Abdoulkarim Ibrahim Shikal a wannan makon ya ci gaba da kawo muku tarihin fitaccen shugaban kasar Ghana dan gwagwarmaya John Jerry Rawlings da ya mulki kasar na gajartaccen wa'adi a 1979 gabanin sake shugabantar kasar a wa'adi 2 na daga 1981 zuwa 2001.